Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ido
Daga nan sukayi sallama.
Kana ya juyo ya kalli Usman kana a taƙaice yace.
"Mu je".
Da sauri Usman yace.
"Sir ina muka nufa?".
Cike da mamaki Usman ya ɗago kanshi da sauri ya zuba mishi ido cikin al'ajabin jin yana cewa.
"Nigeria".
Ya buɗe baki zaiyi magana ya ɗaga mishi hannu tare da nuna mishi ƙofar fita.

Haka yasa ya gimtse maganar kana ya ɗauki kayyakin nasu
Suka fita.


Boke International Airport Addis Ababa Ethiopian.Suka nufa kai tsaye

Still Kai tsaye Airport parking suka nufa.
Bayan Driver'n'shi yayi parking.
Da sauri Usman ya fito ya buɗe mishi, marfin motar.
Cikin nitsuwa ya zuro ƙafarsa ta dama waje , tare da sauƙeta ƙasa ahankali, Saidai kuma da sauri ya rumtse idanunshi tare da dafe ƙahon zuciyarshi saboda wani irin m...!





📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

ASSALAMU ALAIKUM, Masoyana ma karantan littattafaina, ina mai farin cikin sanar daku, yau d’in nan MON, 18 OCT 2021 za'a fara biyan kud’in samun damar karanta littafin TUBALI akan farashi mai sauk’i Biya 500 k’aramin farashin na k’aramin group, kana sai *Special people Group* akan farashi mai sauk’i 1k kacal babban group a yawan posting babancinsu yake, zaku biya ta asusuna.

ACCOUNT NO 0661110170.

BANK NAME: AISHA ALIYU GARKUWA

BANK GTBank

sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan numben tawa da nakeyin whatsApp da ita 09097853276.

*PLS TAKE NOTE BAND VTU*
kada kiyi min VTU ko transfer'n katin ta wannan numben etisalat d’in idan kuwa kikayi wlh babu ruwana dan na fad’i miki. Please and please in dai da hali kada ki turo min katin, kiyi min transfer'n ruwan kud’i ta bank account na, in kuma babu dama to sayi katin MTN sai ki copy number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp.

Gareku mutanen jamhuriyar Niger ku tuntub’i Mommy akan layinta +22790899076, ta wurinta zaku biya, hoton katin zaku d’auka ku tura mata ta wannan numben a whatsApp, Special people group 1k ne (1000) k’aramin group kuma (500) kacal,
Please dan Allah babbar macece mai yara da tarin jikoki da y’ay’an jikoki mu kyautata lafazi da mu'amala gareta dan Allah don in ka girmama iyayen wasu wasu zasu girmama naki🙏🏻...

Littafin TUBALI littafine na musamman mai salo na musamman mai cike da abubuwa masu tarin yawa.
*Tausayi, Sark’ak’iya, jan hankali, Fadakarwa, Nishad’antarwa, ilimantarwa, al'ajabi, Sa'ar rayuwa, riƙon amana, cin amana, ribar kyautatawa, kana da sassayar soya mai salon narke jiki da zuciya*

Ga number wayata da nakeyin whatsApp da ita, 09097853276 idan kina son biyan kudin samun damar karanta littafin TUBALI sai ki biya ta wannan ac no din dai 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, dan Allah ki biya kafin kiyi min mgn kina turo shaidar biyanki ina gani zan saki a group, in Kuma baki da ac no ko yanayin zaman wani k’asa ko wani luggun ki sayi katin MTN na 1k in special group kikeso ki turo min. In Kuma k’aramin Group kike so ki sayi katin *MTN ki copy number's din ki turo min ta whatsApp number'n na 09097853276 kada kiyi min VTU ko transfer'n katin 9mobile dan layin nada matsala*

Za'ayi tsawon mako ɗaya ana biya ina kafin in fara update domin samun sassaucin aiyukan sauraron mutane, za'a fara biya yau *MON 18 OCT 2021. Kana zan fara posting ranar MON 25 OCT 2021 rana ita yau kenan in mai kowa mai komi ya kaimu bisa rai da lfy*

🙏🏻Na rokeki da girman zatin ubangiji in dai kin san zaki sayane dan ki fidda min littafina dan Allah ki bar kud’inki kiji tausayin marainiya, kada ku cutar da marainiyar Allah,😭🙏🏻🙏🏻🙏🏻.


Nasan daga yau har zuwa na gama littafin Chart zaimin yawa zai hausawa aiyuka zasu yawaita gareni, amman babu kamar makonni ukun forko zuwa biyar, Please ina neman al'farmar uzuri in kinga kinyi min mgn ban amsa mikiba, na tuba kiyi haƙuri ba raini bane ko wulak’anci face yawan mutane wata k'il ban isa kan Chart naki bane, Amman muddin na isa na kuma bud’e na gani tabbas zan baki amsa in katine zansashi yana shiga zan saki a group in bai shiga kuma in gaya miki, in Kuma ta account kika turamin ina ganin shaidar biyanki zan saki a group, 🙏🏻Dan Allah in kinsan ba littafi ko maganin gyara namu na mata kikeso ba to kiyi haƙuri da min mgn sai na d’an samu salama🤝🏻😘🙏🏻😂.


*Sayan na gari maida kuɗi gida sai kinzo*








By
*GARKUWAR FULANI*









📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*

PAGE 4

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*



ASSALAMU ALAIKUM, Masoyana ma karantan littattafaina, ina mai farin cikin sanar daku, yau d’in nan MON, 18 OCT 2021 za'a fara biyan kud’in samun damar karanta littafin TUBALI akan farashi mai sauk’i Biya 500 k’aramin farashin na k’aramin group, kana sai *Special people Group* akan farashi mai sauk’i 1k kacal babban group a yawan posting babancinsu yake, zaku biya ta asusuna.

ACCOUNT NO 0661110170.

BANK NAME: AISHA ALIYU GARKUWA

BANK GTBank

sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan numben tawa da nakeyin whatsApp da ita 09097853276.

*PLS TAKE NOTE BAND VTU*
kada kiyi min VTU ko transfer'n katin ta wannan numben etisalat d’in idan kuwa kikayi wlh babu ruwana dan na fad’i miki. Please and please in dai da hali kada ki turo min katin, kiyi min transfer'n ruwan kud’i ta bank account na, in kuma babu dama to sayi katin MTN sai ki copy number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp.

Gareku mutanen jamhuriyar Niger ku tuntub’i Mommy akan layinta +22790899076, ta wurinta zaku biya, hoton katin zaku d’auka ku tura mata ta wannan numben a whatsApp, Special people group 1k ne (1000) k’aramin group kuma (500) kacal,
Please dan Allah babbar macece mai yara da tarin jikoki da y’ay’an jikoki mu kyautata lafazi da mu'amala gareta dan Allah don in ka girmama iyayen wasu wasu zasu girmama naki🙏🏻...

Littafin TUBALI littafine na musamman mai salo na musamman mai cike da abubuwa masu tarin yawa.
*Tausayi, Sark’ak’iya, jan hankali, Fadakarwa, Nishad’antarwa, ilimantarwa, al'ajabi, Sa'ar rayuwa, riƙon amana, cin amana, ribar kyautatawa, kana da sassayar soya mai salon narke jiki da zuciya*

Ga number wayata da nakeyin whatsApp da ita, 09097853276 idan kina son biyan kudin samun damar karanta littafin TUBALI sai ki biya ta wannan ac no din dai 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, dan Allah ki biya kafin kiyi min mgn kina turo shaidar biyanki ina gani zan saki a group, in Kuma baki da ac no ko yanayin zaman wani k’asa ko wani luggun ki sayi katin MTN na 1k in special group kikeso ki turo min. In Kuma k’aramin Group kike so ki sayi katin *MTN ki copy number's din ki turo min ta whatsApp number'n na 09097853276 kada kiyi min VTU ko transfer'n katin 9mobile dan layin nada matsala*

Za'ayi tsawon mako ɗaya ana biya ina kafin in fara update domin samun sassaucin aiyukan sauraron mutane, za'a fara biya yau *MON 18 OCT 2021. Kana zan fara posting ranar MON 25 OCT 2021 rana ita yau kenan in mai kowa mai komi ya kaimu bisa rai da lfy*

🙏🏻Na rokeki da girman zatin ubangiji in dai kin san zaki sayane dan ki fidda min littafina dan Allah ki bar kud’inki kiji tausayin marainiya, kada ku cutar da marainiyar Allah,😭🙏🏻🙏🏻🙏🏻.


Nasan daga yau har zuwa na gama littafin Chart zaimin yawa zai hausawa aiyuka zasu yawaita gareni, amman babu kamar makonni ukun forko zuwa biyar, Please ina neman al'farmar uzuri in kinga kinyi min mgn ban amsa mikiba, na tuba kiyi haƙuri ba raini bane ko wulak’anci face yawan mutane wata k'il ban isa kan Chart naki bane, Amman muddin na isa na kuma bud’e na gani tabbas zan baki amsa in katine zansashi yana shiga zan saki a group in bai shiga kuma in gaya miki, in Kuma ta account kika turamin ina ganin shaidar biyanki zan saki a group, 🙏🏻Dan Allah in kinsan ba littafi ko maganin gyara namu na mata kikeso ba to kiyi haƙuri da min mgn sai na d’an samu salama🤝🏻😘🙏🏻😂.


*Sayan na gari maida kuɗi gida sai kinzo*


Masifeffen harbawa da babbar jijiyar bayanshi tayi, tare da bugawan ƙirji a jere-a jere, har sau uku.
Rumtse idanunshi yayi da ƙarfi dan bai taɓa jin hakan ba,
Wani irin tsuma fatan saman idanunshi suka farayi, kamar shi yake juya su.

Kanshi ya jingina da marfin motar can ƙasan maƙoshin sa, ya fara mai-mai-ta.
"Hasbunallahu wani'imanwakil, innalillahi wa innailaihi rajiun. Subahanallahi Alhamdulillah".
Shiru PA yayi tare da ratsa gefe, yana mai kallonshi.

Tsawon daƙiƙu 3 suka ɗauka a haka, kana ya yunƙura ya miƙe tsaye tare da ambaton sunan Allah.
Bayan ya fita ne kuma PA ya maida marfin motar ya rufe.
Kana Driver'n'shi da gwamnatin kasar ta bashi, da ƴan tsaron shi suka fito suka mara mishi baya.
Yayinda PA dinsa ke gefenshi.
Saida Suka shiga har cikin iya inda matafiya ne zasu shiga.
Kana sukayi musabaha duk suka juya suka tafi.

Shi kuwa da Usman PA Suka nufi cikin farfajiyar jirgin kasan cewar an fara cikiyan matafiya.

A can ɗaya sashin kuwa. Riyyam-nsra ne, tsaye gaban Mammynsu.
Yayinda Zayton ke manne da kanta bisa kafaɗarshi, tana rau-rau da idanu alamun zubda hawaye.
Cikin yanayi na rauni da taraddadi Mammy ta kalli Riyyam-nsra cike da jaddawa ta kamo hannunsa ta riƙe da ƙarfi ido cike da hawaye tace.

“Kasan manufar tafiyarka, itace burinmu da farin cikin rayuwata.
Ka kuma sani ina tsoron duk abinda zai rabani da kai.
Riyyam ka sani, kaine GARKUWAta nida ƴar uwarka.
Lallai tabbas munada ciwo a zuciyarmu.
Ina tsoron kada garin gyaran gira in rasa ido.
Kada ban samu baɗiniba in rasa zahiri."
Cikin ƙarfin hali da jarunta yace.
"Mammy babu abinda zaki rasa, in sha Allah ƙari zaki samu. Da izinin ubangiji.
Babu wani abu na duniya da zai miki hijabi da mallakinki".
Cikin zubda hawaye Zayton tace.
"Mammy kin ganshi ko, shi baya tsoro, kada yaje yayi abinda zamu rasashi".

Hannunshi yasa ya share mata hawaye tare da cewa.
"Koda zaku rasani sai kun samu madadina".
Da sauri Mammy tace.
"Kamin al'khairi cewa, zaka kiyaye shiga hurumin da ba naka ba, kayi iya abinda ya kaika ka dawo".
Hannunshi ya ɗaura kan nata tare da cewa.
"Nayi al'ƙawari Mammy na".
Rungumeshi tayi shida Zayton ɗin jin anata neman matafiya".
Kanshi ta shafa tare da sa mishi al'barka.
Kana shi yayi ciki, su kuma sukayi baya.


Yana rataye da jakarsa bisa kafaɗa,
yayi matuƙar kyau cikin shigarsa ta matasan zamani.
Kamanninsa da Rayyern sun ƙara bayyana matuƙa, kasan cewar irin shigar Rayyern ɗin yayi.
Wayarshi ya zaro, ya fara ɗabi'ar tasu ta Tiktokers viewing ya farayi, yana jujjuyawa ƙasan jirgin.
Tare da fara, mgn da Hausa.

“Assalamu alaikum Al'ummar Nigeria".
Sai kuma ya haura ya ajiye wayar bisa steps din marfin jirgin, kana ya dawo baya, ya fara takowa a hankali yanayi yana ɗan rawa, da tsalle.
Mafi akasarin mutanen dake bayansa matasane, shiyasa suka tsaya suna murmushin calikancinsa.

Yana isa gab da wayan second ɗin daya saita na video na cika.
Dan haka yasa hannunshi ya ɗauki wayar kana ya kutsa kai cikin jirgin...


Zaune yake bisa kujera no 23 acan sama VIP, kusa da jikin windown jirgin.
Yayinda Usman ke bayanshi.
Wasu files ya zaro cikin briefcase ɗinsa, tare da biro, a hankali ya sunkuya ya fara buɗe takardun, yana sa hannu a cikinsu ɗaya bayan ɗaya.

Shi kuwa Riyyam-nsra tafiya yakeyi yana ɗan dudduba no ɗin kujerun.
Yana isa kusa da Rayyern ya tsaya tare da cewa.
"Yesss! Kunga ga maƙocina, sarkin aiki har a jirgima aiki yakeyi".

Bai ɗagoba kuma baici gaba da rubutun da yakeyi ba sai ƙirjinsa dake bugawa.

Jakarsa ya zare a kafaɗarsa ya sakata a mazaunin ta.
Wanda haka yasa saida ya matso kusa da Rayyern.
Yatsun sawun yaron ya zubawa ido cike da mamakin ganin yatsun iri ɗaya sak da nashi yatsun Har nails dinsu.
Da sauri ya ɗan ware idanunshi.
Ganin wani ɗan ɗigon tawadan Allah kan tsakiyar farcen babbar yatsar Riyyam-nsra.
A hankali ya ɗan motsa kafafunshi dan sai yaga kamar ƙafarsa ce.

Shi kuwa Riyyam-nsra zama yayi bisa kujerar dake manne data Rayyern, tare da sauƙe numfashi kana ya lumshe idanunshi saboda wani irin masifeffen bugu da zuciyarsa keyi.

Yayinda gaba ɗaya cikin jirgin kuma kowa ya zauna mazauninsa.

Tsit kowa ya nitsu.

A hankali Riyyam-nsra ya buɗe kwayar idanunshi sabida,
Jin alamun an rufe marfin jirgin kana jirgin ya fara ƙugin tashi.

Shi kuwa Rayyern har yanzu idonshi na kan kyawawan sawun Riyyam-nsra.
A hankali Riyyam-nsra ɗin ya juyo ya kalli gefen da Rayyern ɗin yake.
Da sauri ya ɗan sunkuyo da kanshi ganin inda Rayyern ya fuskanta.
Janye sawunshi yayi tare da cewa.
"Salamu alaikum".
Da sauri Rayyern ya juyo sabida muryar yaron sak muryar ƙaninsa Ramadan.

Yana juyowa shima Riyyam-nsra yana juyowa ya fuskanceshi.
Wani irin zabura Riyyam-nsra yayi tare da zazzaro idanunshi waje, kana ya yunƙuro zai tashi.
Da sauri ma'aikaciyar jirgin dake bayanshi ta nufoshi da sauri tana cewa.
"Hey Are you okay? please sit down!!”
Ta ƙare mgnar da ɗan sauti sabida lokacin jirgin, yake raba tayoyin shi na gaba da ƙasa, anfi buƙatar kowa a zaune.

Shi kuwa Riyyam-nsra wani irin masifeffen kaɗuwa al'ajabi mmki da tu'jjudine suka rufeshi, gaba ɗaya jikinshi rawayake.
Cikin buɗe baki ya nuna Rayyern da yatsarshi manuniya kana ya nuna kanshi.
Da sauri ma'aikaciyar ta sake cewa.
"Please I say sit down!."
Jin hakanne da kuma ganin yanda yake baya baya.
Yasa ya koma bisa kujerar ya zauna.

Cikin kaɗuwa da wani irin fuska mai cike da mmki yace.
"Tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai, daya haliccemu da kamanni iri ɗaya."
Shiru Rayyern yayi yana mai kallonshi da gefen ido.
Bai iya shiga sabgar da ba ta saba, a rayuwarsa baya taɓa sa kansa a lamarin da bai shafeshi ba.
Da sauri ya juyo jin Riyyam-nsra na cewa.
"Ina ma Mammy na ta ganka.
Allah mai iko.
Inama ace jirgin nan bai tashi ba, da na roƙeka da girman Allah da Manzonsa muje Mammy na taga mai tsananin kama dani."
Sai kuma ya kalli sajen Rayyern cikin tsananin farin ciki, so, ƙauna, bege, yace.
"In sha Allah nima daga yau zan fara tara saje irin naka".
Sai kuma ya matso kusa da Rayyern tare da dago wayarshi.
A hankali Rayyern ya ɗan juyo kwayar idanunshi kan fuskarshi ganin alamun zai manna kanshi bisa kafaɗarsa.
Fuskarshi ya tsuke tare da tsareshi da ido.

Da sauri ya kwaɓe fuska tare da karkata kai cikin turo baki yace.
"Na tuba".
Sai ya ganshi lammanim ƙaninsa Ramadan sak da yayi haka, dan haka Ramadan kanyi mishi duk sanda ya tsareshi da ido.
Ido ya ɗan zubawa lips ɗin shi yana cewa.
"Please kayi haƙuri hoto zamuyi zan nunawa Mammyna ne, zata so ganinka".
Ya juyo da nufin zaice a a.
Kawai sai yaji Riyyam-nsra ya ronƙofo kanshi da kyau.
Ya manna kansa bisa kafadarsa.
Yana murmushi yayi musu selfie.
Sai ya zama suna kallon juna.
Kafaɗarshi ya ɗan manna da nashi dan jin bugun zuciyarsu ya dai-dai-ta yana harbawa a tare a tare, dib-dib.

Sai kuma ya zuba mishi ido ganin ya taso ya zauna ya juyo ya fuskanceshi da kyau.
Hannunshi ya miƙa mishi tare da sallama.
Dole ya bashi hannu ya kuma amsa sallama tunda horaswar Musulunci ne.

“Sunana Zakariyya amman Riyyam-nsra nakeso a kirani, ni ɗan ƙasar Ethiopia nanne, ban taɓa zuwa Nigeria'n ba sai yau.
Dalilin abokina Nasiru Ahmad zanje.
Kai kuma fa?".

Fuska ya kuma kwaɓewa ganin ya janye hannunsa bai kuma ce mishi komai ba.
Cikin yanayin shagwaɓa yace.
"Please dan Allah gaya min".
A nitse ya juyo ya kalli yaron da yakeji.
Sonshi da ƙaunarshi na ratsa mishi jinin jiki da zuciya, haka nan yaji wani aminci na musamman a kan yaron.
Cikin tattausan muryar da irinta yakewa Ramadan mgn yace.

“Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara".
Ruggumeshi Riyyam-nsra yayi tare da cewa.
"Nice name. Please Zan iya ce maka Yaya?”
Kai ya jujjuya mishi alamun a a.
Da sauri yayi rau-rau da idanunshi tare da cewa.
"Dan Allah fa, to me zan ce maka".
A taƙaice yace.
"Hamma Rayyern".
Wani irin murmushin jin daɗi yayi tare da cewa.
"Hamma Rayyern".
Sai kuma ya gyara riƙon da yayiwa wayarsa da tun tuni yake musu video.
Kusan a tare suka sauƙe ajiyan zuciya lokaci da jirgin ya gama ɗagawa, yayi sama ya rabu da ƙasar Ethiopia.
A hankali ya ɗan juyar da kanshi kana yaci gaba da aikin da yakeyi.

Da sauri ya kuma kalli Riyyam-nsra da ma'aikaciyar jirgin nan tazo tana ce mishi lfy kuwa, ɗazu yake ta rawan jiki ta ƙare mgnar cikin yanayin saninsa da son suyi hoto tare.
Murmushi yayi tare da nuna mata Rayyern kana yayi ƙasa da murya yace.
"Yayana ne zai zaneni wai na cika surutu".
Murmushi tayi tare da kallon fuskar Rayyern kana tace.
"Ka cika rawar kai, ba kamar yayanka ba."
Sai kuma ta ɗan kalli Rayyern tare da cewa.
"Sir a rinƙa yi mishi faɗa yaron nan baya jin mgn a TIKTOK".
Kai ya gyaɗa mata ba tare da ya kalleta ba.

Hoto sukayi da Riyyam-nsra kana tayi gaba.

Usman PA kuwa yana can baya.

A hankali jirginsu yayi ta keta gajumare, yana ratsa sararin samaniya.
Tafiya ta nisa kowa sabgogin gabansa yakeyi.
Amman banda Riyyam-nsra gaba ɗaya ya shigewa Rayyern shigewa mai tarin yawa.
Ya kuma kasa yakice yaron.
Duk yadda yayi sai yake jin zuciyarsa mai raunice a kan yaron.
Wani irin son yaron yakeji har cikin ƙahon zuciyarshi.
Ga mamakinsa ko yanayin cimar da suka fiso iri ɗaya ne.
Domin tunda Riyyam-nsra ya shigo bakinsa bai zauna banza ba, sweet da chocolate ya cisu iri daban-daban.
Ya lura yaron bakinsa bai zama shiru.

Hoto kuwa yayi musu sunfi hamsin video kuwa sun kai goma.

Haka sukaci gaba da keta hazo...

A nan gida Nigeria kuwa gidan Alhaji Idi Saleh Dakata.

A hankali Jannart ta fara motsi, alamun farkawa daga baccin da allurar ya sa tayi na tsawon.
Awanni biyu da rabi.
A hankali ta fara motsa fatar idanunta da sukayi mata nauyi.
Dai-dai lokacin kuma Barrister ya turo ƙofar ɗakin tare da sallama.
A hankali Mom dake zaune gefenta ta amsa mishi.
"Wa alaikassalam, Barrister ka dawo".
Cikin kula ya gyaɗa mata kai tare da ƙarasowa bakin gado.

Ido suka zuba mata cikin tausayawa, ganin hawayen dake bin gefen idanunta suna sauƙa har cikin kunnenta.

A hankali Mom tasa tafin hannunta ta fara share mata hawayen.
Ba tare kuma da ta buɗe kwayar idanun nata ba, ta fara sakin Shessheƙan kuka.

Zama Barrister yayi a bakin gadon, tare da kamo hannunta ya riƙe, cike da tausasawa da kulawa yace.
"Sorry Jannart kiyi haƙuri ki dena, kuka dukkan abinda yayi tsananin zaiyi sauƙi".
Jin muryar ƙanin mahaifin nata, mafi kulawa a gareta ne.
Yasa ta buɗe Idanunta, tare da yunƙurawa, zata tashi zaune.
Da sauri Mom ta tallabota, ta zauna tare da jingina bayanta jikin allon gadon.
Gyara zama Barrister yayi tare da kallon Mom yace.
"Mom Abdul a kawo mata wani abu ta ɗan ci".
Da sauri Mom ta miƙe tare da cewa. "Toh". Ta nufi hanyar fita cike da kekyawar niya da zuciya.

Shi kuwa Barrister ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙe tare da juyowa ya kalli Jannart data gaza tsaida hawayenta.
Murya can ƙasan maƙoshi ta fara mgn.

“Abba ƙirjina yana ciwo! Kaina yana bugawa, tunani ya hanani samun sauƙi, na gaza gano Yah Junaid wanne irin ɗan uwane a duniyar nan.
Anya kuwa Abba Yah Junaid yana da cikekken hankali da sanin haramcin babban fasadin da yake son ai katawa gareni."
Sai kuma hawaye shar-shar, suka soma zubo mata ta kasa ƙara sa mgnar.

Shi kuwa Barrister cikin tsananin tashin hankali da kaɗuwa da firgici mai birkita tunanin iyaye na gari yace.

“Me kike nufi Jannart wanne irin fasadi kuma?".
Murya na rawa ta kalleshi cikin rauni tace.
"Abba Yah Junaid fa fyaɗe yake son yamin, a lokuta ma banbanta, yana ƙudirin yi min Fyaɗe, idan na ƙi amince mishi ne, yake yunƙurin kasheni.
Abba cewa yakeyi fa zai kasheni in ban amince da shiba.
Ya kuma ce muddin na gayawa wani zai kasheni.
Wlh Abba zai kasheni.
Abba ya zanyi? Ina zan shiga a rayuwata in samu sauƙi, Ɗan Allah Abba ka rabani da gidan nan in ba haka ba Yah Junaid zai kasheni kuma Daddy ba zai hanashi ba".

Ta ƙare mgnar cikin tashin hankali.
Da ya ta azzara nitsuwar Barrister Kabir saleh Dakata.
Wata iriyar fitinenneyar zufa ce mai zafi ta soma tsastsafo mishi.

Cikin tuno abubuwa da dama na rayuwar duniya, ya kamo hannunta tare da fuskantar ta da kyau kana yace.
"Jannart! Jannart!! Jannart!!!".
Ya kirata sau uku duk da amsa mishi da takeyi.
Cikin yin ƙasa da murya yace.

“In sha Allah, Junaid bazai kashe kiba, da izinin ubangiji sai kin rayu, rayuwa mai Al'barka domin ke ayace, kuma izinace sannan taƙin shaida mai ƙarfi".
Hannunta ya kuma riƙewa cikin irin sona uba da ɗiyarsa yace.

“Jannart zaki rayu cikin aminci.
Domin Ubangijin daya raya Annabi Musa acikin gidan Fir'auna cikin lfy da aminci.
Shiya rayaki a gidan nan cikin lafiya da aminci.
Ya rigada lokacin ya ƙurewa Magautan, bazasuyi nasaraba, dan sunyi nasararsu tun shekarun baya sun gama nasara, yanzu nasarar tamu ce.
Gsky zatayi halinta, in sha Allah zanci gaba da zame miki jigo. Kuma zan nema miki GARKUWA, cikin gaggawa kafin su juyo garemu".

Shiru tayi tana jin kalaman ƙanin mahaifin nata, sai dai ta kasa sama musu mizanin da zata aunasu ta ajiyesu ta fahimci manufarsu.
Gogewar hausarta batayi surfin ta Ƙanin mahaifin nataba.
Cikin ruɗanin da kalamanshi suka saka mata tace.
"Abba ni na gaji da zaman gidan nan, dan Allah ka sake roƙon Daddy ya bakani ko zai yarda, in koma gidanka."

Cikin sauƙe nannauyan numfashi yace.
"Jannart sake roƙar tashi tamkar wasa da rayuwarki ne, kamar dai kusanto da a ...".
Da sauri ya haɗiye ragowar mgnar sanin ƙwaƙwalwarta bazata fahimci zancen nasa ba.
Ita kuwa cikin sanyi ta zuba mishi ido.

Dai-dai lokacin kuma Mom ta shigo da tray a hannunta, cup ɗin tea ne mai kauri, sai soyayyan irish da ƙwai.
Cikin nitsuwa tace.
"Abba to..".
Hannu ya ɗan ɗaga mata tare da cewa.
"Ya isa da yamma zan dawo muyi mgn Jannart kada ki kuma yin kuka".

Ya ƙare mgnar yana miƙewa tsaye.
Kai kawai ta gyaɗa mishi kana ta bishi da ido har ya fita.

Bayan ya fita Bathroom ta shiga, ruwa ta ɗan watsa, bayan tayi brosh kana ta fito.
Ba laifi ta ji sauƙin sosai numfashin ta ya dai-dai-ta.

Tea ɗin kawai ta iya sha.
Kana ta koma ta kwanta dan Alllurar bata ida saketa ba.


Can cikin bacci taji wayarta na suwa.
"Mahmoud".
Tace tare da amsa kiran.
Nan yake shaida mata cewa.
Dr Rayyern Mai-nasara yana hanyar dawowa Nigeria tun safe jirginsu ya taso.
Zuwa azahar zasu sauƙa Abuja.
Kuma yau ɗin zasu shigo Kano cikin alamun bacci tace.

“Toh ya akayi kuma lbrin ya sauya Mahmoud ba sai jibi ba kace?”

Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"Uhumm kin kuwa san waye Dr Rayyern, mutun yana nan tamkar Wahainiya gane shirinsa ko manufarsa fa wuyane dashi.
Ke dai in kin samu dama kiyi ƙoƙarin zuwa Airport da yamma wata ƙil a dace, zan turo miki hotuna Yah Usman PA Yayan Abokina Deen wanda yayisu a bayan motocin Dr Rayyern ɗin so sai ki ɗauki number's ɗin motocin ta wannan hanyar zaki iya samun damar bibiyarsa".
Cikin sanyi tace.
"Toh Ngd matuƙa".

Daga nan sukayi sallama.
Salman ta kira yana ɗagawa yace.
"Ya jikin namu?".
Cikin sanyi tace.
"Da sauƙi waya gaya maka?".

“A'isha Lawal ce ta gaya min tace ɗazu data kira Mom ce ta ɗaga wai jikinki ya tashi."

Ayyah tace a taƙaice kana ta mishi bayanin da Mahmoud ya mata ta ƙara da cewa.
"Ka shirya da yamma muje Airport ɗin bari in turoma hotunan".
Toh yace kana sukayi sallama.


Ƙarfe biyu dai-dai jirginsu ya sauƙa cikin international Airport Abuja.

Bayan wasu ƴan daƙiƙu, aka fara fitowa.
Mutun kusan 21 suka fito.
Kana Rayyern ya sako ƙafarsa ta dama kan matakalan forko.
Wani irin sassanyan numfashi ya shaƙa a hankali tare da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment