Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ce ta kuma ringing ganin Sulaiman ne yasashi miƙewa tare da buɗe Fridge Chocolate masu yawa ya ɗiba daskararru kana ya zaro goran ruwa da sauri haka yasa bai san wanda ya daskare ya ɗaukoba.

Cike da mamaki Mamy ta bishi da ido jin yana cewa.
"Mamy sai na dawo ana nemana a asibiti, Mamy abu mai ruwa-ruwa nake so in na dawo”.
Kai Riyyam-nsra ya jujjuya kana a hankali yace.
"Allah sarki Hamma Rayyern sam baya samun hutu, lokacin cin abinci ma rasawa yakeyi bawan Allah.
Dan Allah Hamma Ramadan muje ka tayashi”.
Kwaffa Ramadan yayi tare da dungure mishi ƙeya kana yace.
“Dan Allah Barshi shi baida wani uzuri sai aiki ni kuwa ina fama da uzurin soyayya.
taso mu tafi kaga Auntynka yaro”.
Ai kuwa da sauri ya miƙe.

Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara yana fitowa Hadi da PA suka miƙe.
Da sauri yace.
“Noh Hadi bari. PA mu tafi”.
Da sauri PA yace “Toh”. kana yabi bayansa.
Yana shiga motar yaja.
Hadi kuma ya buɗe musu gate, suka fita.

Saida suka fita sun hau titin da zai kaisu Mai-nasara Hospital ne ya ɗan miƙawa PA goran ruwan alamun ya buɗe mishi.
Amsa PA yayi tare da cewa.
“A daskare yake fa”.
Hannu yasa ya amshi gorar ya ɗan jijjiga tare da jan tsaki sam rabinsa duk a daskare yake.
Aje goron yayi kana ya ɓalle ledan Chocolate ɗinsa ya fara taunawa da yawa-yawa sabida azabebbiyar yunwar da yakeji.

A nitse ya zurawa motoci uku dake bayansu idanu.
Binshi sukeyi gadan-gadan kamar masu niyar takashi.
Da sauri yayi kwana ya shiga hannun damansa.
Ga mmkinsa sai gashi sun biyoshi a guje har na gaban na gab da buga mishi motarsa.

Cikin ransa yace.
“Okay!!!” sai kuma ya juya hagu da gudu.
Cikin nitsuwa yace.
"PA ko zaka sauƙa!”
Da sauri PA yace.
“A'a muje in ba matsala, naga motocin nan binmu sukeyi fa, ba halin tsayuwa”.
Kai ya gyaɗa mishi kana ya juya akalar motarsa dan canza hanya.
Sabida sanin ana buƙatarsa a asibiti in ba don hakaba zai tsaya yaji dasu.
So amman ganin duk inda yayi suna biye dashi kamar inuwa ne yasashi juya akalar motarsa kai tsaye titin da zai kaishi Jan bulo ya nufa.
Ganin haka ne kuma yasa motocin nan uku suka tsagaita da binshi.

Gaba ɗaya ransa ya hatsala ya tafasa sabida yadda suka sashi dole ya fasa zuwa inda akeda buƙatarsa da neman taimakonsa ya nufi inda baya son zuwa.
Wani irin masifeffen tsaki yaja tare da taka motarsa ƙirar B.M.W. fara kal mai masifar kyau da sheƙi.
Takata yakeyi a fusace.

Kai tsaye layin gidan Alhaji Idi Saleh Dakata ya shiga.
A hasale yake danna horn babu k’ak’k’autawa wanda hakan yasa mai gadin buɗe masa gate ɗin jiki na rawa.

Yana buɗewa kuwa ya kutsa kai.

A can gidan Barrister Kabir kuwa.
Cikin tsoro Jannart ta kalli wayarta inda ta samu miss call 17.
13 daga ciki na Yah Junaid ne biyu na Daddy ɗaya kuma Salman ɗaya Hajia Rabi'ah.
Murya na rawa tace.
"My Aunty zan tafi kawai kinga har yanzu Abba bai dawoba ga Daddy ma nan yanata kirana ga kiran Yah Junaid goma sha".
Ganin yadda jikinta ke rawane yasa cikin sanyi tace.
“Toh gsky kam harda kiran Daddy kam kije, in ya dawo zaije yaji ko lfy".
Ledan da take miƙa mata ta amsa tare da cewa.
"Nah shiga uku kinga yanzuma ga Yah Junaid yana kira”.
Ta ƙare mgnar tana nufar woje, Dijat na biye da ita a baya.
Tana fita sakarkarun suka muƙe da sauri ta shiga mota jiki na rawa Baba Ado yaja jin yadda take ce mishi.
“Baba Ado mu tafi mu tafi, awa uku Daddy ya bani gashi har biyar nayi.”
Ajiyar zuciya Dijat ta sauƙe lokacin da suka fita.
Jiki a mace ta koma cikin gida.

Su kuwa a 360 suka nufi gidan.

Cike da Mamaki Usman yake kallon Dr Rayyern Mai-nasara daya fita cikin motar fuska a murtuƙe yacewa mai gadin.
"Ina Ubangidan naku?”.
Cike da mamaki mai gadin ya kalleshi kana ya juyo ya kalli ƙofar babban falon Alhaji idi Saleh Dakata wanda daga nan bakin gate ana iya hangoshi.
Baya buƙatan ƙarin bayani sabida yadda mai gadi yayi ya tabbatar masa ogan nasu na ciki.
Kana kuma ga tarin takalma alamun da mutane a cikin.

Cikin wani irin taku mai cike da haiba ya nufi falon.
Yana zuwa yasa yatsunshi biyu ya ɗan bugi ƙofar.
Da sauri duk suka juyo suka kalli ƙofar Junaidu dake baƙin kofarne yasa hannunshi ya buɗe dai-dai lokacin kuma shima ya turo ƙofar.
Ganin Dr Rayyern Mai-nasara na kutso kai cikin falon ne yasa Junaid matsowa tare da cewa.
"Kai lfy ina zaka je waye kai!?”.
Ya ƙare mgnar yana tsare gaban Dr Rayyern Mai-nasara din.

Wani irin kallon daya hautsina hanjin cikin Junaidu.
Rayyern ɗin ya watsa mishi, tare dasa hannunsa ya dafe gefen kafaɗun Junaid da yatsu biyu kana ya tureshi da ƙarfi, har saida ya bugi gini kana yace.
"Matsa yaro ba wurinka nazoba wurin tsohonka nazo”.
Ya ƙare mgnar yana nufan cikin falon gadan-gadan.
Wani irin kallon mamaki shakka mai haɗe da tsoro Alhaji idi Saleh Dakata, da Alhaji Abdu Tababa, da Dr Lukman suke mishi kamar idanunsa zasu faɗo ƙasa.
Da karfi ya jawo kujerar dake gefenshi kana yasa ƙafarshi ya tureta guuuu ta tafi har gaban Daddyn Jannart cikin rashin tsoro ya zauna bisa kujerar tare da jawota ya motso shi da kyau suna fuskantar juna cikin kakkausar murya yace.
"Meh hakan! Me kake nemana kana tura waɗan can karnu kan naka nemana, gani gabanka, ka gaya min me kake buƙatar inyi maka da kake sawa ana bibiyata.
Nace me kake son inyi maka!!!”.
Ya ƙare mgnar da masifar ƙarfi tare da buga santer table ɗin dake gabansa har saida cups ɗin saman suka kwanta suka gangara ƙasa.
Kana hakan yasa duk suka kame jikinsu da zazzaro idanunsu.
Da sauri Alhaji Idi Saleh Dakata ya ɗagawa Junaidu hannu dan ganin ya yunkuro zai kama Rayyern.

Shiru sukayi baki ɗayansu, shi kuwa Rayyern cikin tafasan zuciya yace.
“Da ka barshi ya isoni ai.”
Yayi mgnar yana tsare Daddy da idanu.
“Mitssssss”. Yaja wani dogon tsaki tare da cewa.
“Ina da aiki mai mahimmanci ka sani na baroshi nazo nan dan inji uzurinka sannan kayi shiru kana zaro min jajayen idanu kamar na (DUJI) to wlh hawainiyarka ta kiyayi Ramata.
Kada kasa in juyo kanka na wuni ɗaya wlh zaman kasar Kano zaifi karfinka.
Ya za'ayi ina girmama furfurarka kana kaucewa, to muddin baka kiyayeni ba tabbas zaka rasa gemun naka gaba ɗaya.”
Da sauri ya juyo ya watsawa Dr Lukman wani kallon da yasa shi jin zufa tun daka cikin naman jikinsa dan masifar tsoron da idanun Dr Rayyern Mai-nasara din ya bashi.
Cikin sauri yayi ƙasa da kanshi tare da cewa.
"Yaro man kaza lallai ka bimu a hankali dan wlh in kace zaka ja damu to wlh.
Ko na'urar jin bugun zuciya ka dena riƙewa.”
Wani irin gigitaccen tsawa ya dakawa Dr Lukman har saida ya miƙe tsaye dan firgita.
Da yatsa ya nuna shi kana ya jujjuyata sannan yace.
"Mu zuba Ni da kai magwaji ya gwada ya gani”.
Sai kuma ya kalli Alhaji Idi da Alhaji Abdu Tababa da suka zuro mayun idanunsu suka kafesa da ido suna masu nazarin wanne irin kisa ya kamata su yiwa yaron nan ne mai shegen taurin kai ko wani irin illa mafi muni za suyi masa rayuwarsa.
Cikin gargadi ya nunasu da yatsa kana yace.
"Wlh idan kuna cin ƙasa, to ku kiyayi ta curi.
ina mai tabbatar muku in baku kiyayeni ba zaku shiga uku.
Tun wuri ka gayawa waɗan can karnukan naka su dena bina, in kuwa ba hakaba zaka rubta rami.
Kada ku mance na gaya muku.
Idan nace zan taka mutun bashi da GARKUWA a kaina zan takashi domin tsakanina daku faɗane tsakanin gsky da ƙarya.”

Gaba ɗaya jikinsu tsuma yakeyi.

Yayinda Junaidu kuma zufar tsoro ta keto mishi.
Dai-dai lokacin kuma motocinsu Jannart suka shigo gidan.
Da sauri ya juya ya fita sabida hango sun da yayi kasan cewar ƙofar a buɗe take.


Yana isa wurin Jannart na fitowa kasan cewar ta bayanta yazo bata san ya isoba.
Wani ƙauuuuu taji lokacin daya yarfa mata wani irin masifeffen mari ta bayanta kuma kan kunneta.
Wani irin dummmm taji ya biyo bayan kauuu ɗin cikin gigita ta juyo...


Dai-dai lokacin kuma Barrister Kabir ke tsaye gaban Dijat dake mishi bayanin abinda yasa Jannart ta tafi.
Ta kara da cewa.
"Ɗan Allah Abban Hafiz ka bita, kaga meke faruwa kada Junaidu ya mata wani abu”.
Cikin sauri Barrister Kabir yace.
"Zai matama maza ku koma ciki bari inje”.
Ya faɗi mgnar yana komawa cikin motarsa.
Ita kuma taja hannun Hafiza tayi gaba Hafiz na biye dasu a baya.

Shi kuwa Barrister Kabir cikin gudu yake tuƙib ya nufi gidan yayan nasa.


A gidansu Jannart kuwa.
A falon Daddy cikin wani irin masifeffen hatsala Dr Rayyern Mai-nasara ya juya zai fita.
Har yaje bakin ƙofar sai kuma ya tsaya tare da juyowa ya kallesu kana yace.
"Wallahi Ni nan Muhammad Rayyern wargine dai-dai da ƙugun ko wanne mugun tsohon ɗan riba”.
Yana faɗin haka ya sako kai ya fito.

Dai-dai lokacin kuma Junaid yayiwa Jannart wani irin shaƙa mai ƙarfi kana ya wurgata ƙasa.
Hakan yasa ta saki wani irin raunataccen kuka mai masifar wahala tare da yunƙurawa ta kuma tasowa.
Tana mai yarfa hannun tare da ja baya gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi.

Wani irin gigitaccen mari ya kuma zuba mata kan kunneta wanda yasa ta buga wani irin tsalle tare da ihun wahala a tare.
Dai-dai lokacin kuma Rayyern ya iso parking lot ɗin.
Da sauri ya juyo ya kalli gefen da yaji ihun sabida karadin ihun ya cika masa kunne da ƙarfi har saida yaji kansa ya sara.

Siraran idanunshi ya zubawa fuskar yarinyar tabbas ya ganeta.
Kai ya rausayar ya juya tare da taɓe bakinsa alamun.
Oho yama kasheki in yaso kunfi kusa ai.


Barrister Kabir kuwa gudu yakeyi sosai sabida kiran Jannart da yayi har sau uku bata amsaba ya tabbatar masa ba lfy ba.

Shi kuwa Junaidu cikin tsananin mugunta da son huce haushinsa ya kuma shaƙo wuyanta.

Wanda yasata yin wani irin kakari tare da zazzaro idanunta woje.

*Dan girman Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki fitar min da littafina dan kin biya kudin karantawa bawai yana nufin kin mallakeshi bane, na roƙeki da isar zatin ubangiji daya bamu rai da lfy, don soyayyar manzon tsira dan mutuncin iyayenki kasa ki karantamin littafina in baki biyaba, tun forko kunsa littafina na kuɗine, kada ku tauye hakkina kuji tausayin maraicina*


Wanda kuma su Baba Ado da Ashiru mai gadi kab suka rumtse idanunsu da ƙarfi sabida ganin yana son kashe baiwar Allah.
Wani irin kallo Rayyern yayiwa Usman P.A dake cewa.
“Innalillahi zai kashe tafa".
“Toh me ruwanka ba gidansu ɗaya ba”.
Dr Rayyern ɗin ya fad’a,

Waɗannan ƙattin samudawan kuwa suma cirko-cirko sukayi to ya zasuyi.
Ɗan uwanta ne wa zai hanashi in ba mahaifinsu ba.

Su kuwa su Alhaji Abdu suna jin ihunta amman basu fitoba hakama Daddy.

Mom kuwa dake wonka sauri-sauri takeyi dan ta samu ta fito.
Abdul kuwa gefe ya tsaya yana zubda hawaye.

Wani irin gigitaccen duka fa Junaid ya fara yi mata tamkar zai ɗauke ranta.

P.A kam tuni shima hawayen tausayin yarinyar ya cika masa idanu.

Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara cikin yanayin halinsa na babu ruwansa da shiga harkar da bata shafeshi ba,
yayiwa motar key kana ya tada ya juya akalarta zuwa bakin gate.
Hon ya danna amman ina Ashiru mai gadi baima san yanayi ba.
Cikin jan tsaki ya kuma danna horn still Ashiru baima san yanayi ba.

Shi kuwa Junaid cikin huce haushinsa ya daddage ya yarfa mata wani irin marin.
Da yasa ta saki ihu da ƙarfi.
"Wayyo wayyo Allah na Wayyo Mom Wayyo Abba Yah Junaid zai kasheni Daddy”.
Bata ida rufe bakinta ba ya kuma zabga mata wani marin azabebben mari.
Wanda yasa jinin haɓo ɓallo mata ta hancinta.

Da k’arfi Dr Rayyern ya rumtse ƙwayar idanunsa, kana ya bud’esu a hankali.

Dai-dai lokacin kuma Abba ya iso bakin gate ɗin, ganin yanata dannan hon ba'a buɗe mishi bane yasashi.
Buɗe mota ya fito.yana fitowa yana jin ihunta.
Haka yasa ya kutsa kanshi da gudu cikin gidan ta ƙaramar kofar.

Dr Rayyern kuwa kashe motar yayi ganin ba'a buɗe mishi gate ba.
A hankali ya meda bayanshi ya jingina da jikin kujerar kana yasa hannunshi ya dafe saman marfin motar sabida yayi ƙasa da glasss ɗin.
Tallabe kanshi yayi da tafin hannunsa kana a hankali yace.
"Bari muga ƙarshen Game ɗinnan ko P.A”.
Cikin tausayi P.A yace.
"Sir zai kasheta fa”.
Ganin kallon da ya mishi da idanunsa da suka time zuwa launi jane ne kuma yasa yayi shiru.

Kana ya zuba musu ido ta cikin mirror motarsan sabida zuwa yanzu sun dawo bayanshi kusa da motarshi ƙanƙance idanunsa yayi tare da zubasu kan madubin yana kallon duk yadda Junaid ke mata.

Isowarsu bakin motar tasa ne kuma, yasa Junaid damk’o tarin sumar kanta, wanda gaba ki daya ya watse akan gadon bayanta, saboda tsananin wahalan daya bata, irin damk’an da yayiwa fashion nata ne kuma yasa ta sakin wani irin azababben ihu, batare da ko gama rufe bakinta tayi ba, ya bugata da jikin motar.
Wanda hakan yasa Ta fad’a kan motar, atake kuwa jinin dake zuba daga hanci da bakinta ya tsananta ya fara zurarowa har kan motarsa.
Da ƙarfi ya rumtse idanunshi tare da kame jikinsa.
Da yaji zuciyarshi tana wani irin masifeffen harbawa da wani irin masifeffen tsalle kamar zata fito woje.
Dai-dai lokacinne kuma Abba Kabir ya shigo cikin gidan hankalinsa amatukar ta she.

Ashe kuwa baimaga komai ba a tashin hankali ba, saida yaga yanda Junaid din ya buga Jannart ajikin mota.

Wanda hakan yasa ko ihu mai karfi ta kasa fitarwa, ga kuma jinin dake ci gaba da fita ta hancinta ba ƙaƙƙautawa.

Cikin wani irin tashin hankali kiɗima maitsanani Abba Kabir ya nufosu a guje.

Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara wani irin masifeffen tsuma yaji naman jikinshi nayi gaba ɗaya babbar yatsarshi da Jannart ta fasa mishi had’uwarsu ta forko sai wani irin karkarwa takeyi.

Abba kuwa yana gudun nufosu yana.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun. Junaid! Junaid!! Junaid!!! Baka da hankali ne kasheta zakayi ne. Kai wanne irin azzalumi ne!?”.
Ya ida mgnar yana isa inda suke.
Batare da wani jinkiri ba kuwa ya d’auke Junaid da wani irin gigitaccen Marin da yasa Junaid yayi tagal-tagal ya koma baya,
Cikin tsananin fusata da makatar ido da zuciya yasa hannunshi duka biyu, ya hankaɗeshi, saida ya faɗi ƙasa.
Abu da ɗan giya dama ba ƙarfi ba.

Jikinsa na rawa kana kuma Ransa amatukar bace yace.

“Baka da hankali ne Junaid wannan wani irin dabbanci ne, ko kasheta kakeson yi?”

Abba din ya fada amatuk’ar tsawace.

Tare kuma da sunkuyowa kan Jannart dake kwance akan motar Dr Rayyern jini na ci gaba da fita ta hanci da bakinta.

“Jannart! Jannart!! Jannart!!!”.
Ya kirata da azaban ƙarfi cikin tarin ruɗani.
Wanda sautin kiranta da yayine yasa Dr Rayyern Mai-nasara buɗe kwayar idanunshi da suka sauya launi daga fari zuwa jazir.
Idon ya zuba musu ta cikin madubin yana ganin yadda Barrister Kabir yake jijjigata a gigice yana mai cewa.

“Jannart Bud’e idanunki nine Abbanki ne yazo bud’e idanunki Jannart!!!”

Barrister Kabir din ya fada da muryarsa wacce tayi rauni sosai, kana kuma yana me dan jijjigata tuni ya gama gigicewa gaba ɗaya jikinshi rawa yakeyi rauni mai tarin yawa ya rufeshi.
Duk wanda ya ganshi yasan yana cikin tashin hankali.

A dai-dai lokacin ne kuma Rayyern ya bud’e murfin motar tasa ya fito, wanda ya fito ne kuma saboda yiwa Junaid warning, akan jinin daya shafa masa ajikin sabuwar motar sa.
Kana kuma ya sashi ya wonke mishi jinin daya zuba mishi jikin motarsa, in ba wani salon sharri bane yake neman sa dashi.

Barrister Kabir kuwa dake dukufe akan Jannart jin motsin mutum da yayi abayansa ne yasashi saurin juyawa, inda idanunsa suka sauka akan Dr Rayyern Bashi Muhammad Mai Nasara din koda yana cikin gigita ya gane waye ne shi.

Aikuwa azabure ya mike tsaye, batare kuma da wani dogon tunani ba ya kamo hannun Rayyern d’in, cikin muyarsa dake rawa yace.

“Dan Allah Dr. Rayyern ka taimakamin, kalli Jannart jini take ta zubarwa, Dan Allah Kataimaka kada ta rasa rayuwarta.
Dan Allah ka ceceta ka ceci tsohuwar gsky itace hujja ɗaya gareni...”

Yanayin yanda yaji maganar mutumin dake rik’e da hannunsa ne, yasa akaron farko yakai dubansa, ga Jannart d’in dake kwance, kan motarsa jini na zuba mata ta hanci da baki.

Idanunsa ya d’an k’ank’ance saboda, yanda yaga numfashinta na sama da k’asa.
Lallai Tabbas yasan cewa Idan bai taimaka mata ba, To zata iya fad’awa cikin wata matsalar daban kana ya lura wannan mutumin mutum ne mai daraja da Kekkyawar zuciya, a hankali ya kuma kalli yadda hancinta keta zubda jinin haɓo.

Da sauri ya Juya.
tare da kutsa kansa acikin motarsa, cikin sauri ya d’auki wannan bottle water din nasa mai matukar sanyi.
Sabida muryar Barrister Kabir da yaji yana kuka da kiranta.
Da sauri ya juyo ya
K’arasowa kan Jannart din wacce.
Yanzu Barrister Kabir ya ɗagota daga kan motar ya tallabeta a jikinsa yana kiran Daddy.
“Yaya! Yayah Idi !!!”.

Da sauri ya ƙara so gabansa tare da murɗa marfin gorar faron mai masifar sanyin nan.

Kanta da Abba ke tallabe dashi ya saita tare da d’an sunkuyowa ya soma zirara mata ruwa mai bala’in sanyi a tsakiyar akanta.
Yayi hakanne kuma saboda bata taimakon gaggawa sabida yasan idan ya zuba mata ruwan sanyi akanta, Lallai jinin dake fita a hancin nata zai tsaya.

A dai-dai lokacin da yake tsaka da zuba mata ruwanne kuma, Alhaji Idi Sale Dakata, da kuma aminansa da suke cikin babban falonsa suka fito zuwa tsakar gidan, ganin abunda ke faruwane kuma yasa suka nufo kansu gadan-gadan.

Jannart dake kwance akasa kanta bisa cinyar ƙanin mahaifin nata kuwa sanyin ruwan da Rayyern din ke zuba mata ne yasa ta, jan wani irin dogon numfashi, lokacin ɗaya kuma jinin dake zuban ya tsaya.


*Kiyiwa Allah da Manzonsa kada ki fitar min da littafina, in kin San kin sayane dan ki fitarmin da littafina ki gaya min in meda miki kuɗin dan girman Ubangiji ɗayae haliccemu, kada ki karantamin littafina in baki biyaba ganan account na 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU, sai ki turo shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 ko kuma ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp*

Ganin jinin ya tsaya ne kuma yasa.
Dr Rayyern Mai-nasara juyawa sauran ruwan ya zuba a jikin motarsa inda junin yake ya gangara yayi ƙasa.
Kana ya juya ya shiga motarsa tare dayi mata key da danna horn.
Cikin sa'a kuwa Mai gadin ya fara kiciniyar buɗe mishi gate yanayi yana sharce hawayen tausayin Jannart.


Ita kuwa Jannart Lokaci ɗaya kuma gaba daya jikinta ya d’auki karkarwa, take ta soma fitar da wani irin numfashi mai kaman sheshshek’a alamun kuma athsman ɗinta yana tasowa.

Idanu duk suka zuba mata, Yayinda Abba kuwa ya tsaida idanunshi kan ƙirjinta.

Inda yake Kallon yanda bugun zuciyarta ke tayin k’asa.

Adai-dai lokacin da bugun zuciyar nata ya tsaya cak ne, kuma Idanunta suka soma kakkafewa, lokaci d’aya ta saki wani irin nishi’n daya saka Abba firgici.
Dai-dai lokacin kuma k’irjin Dr Rayyern Mai-nasara yayi wani irin masifeffen harbawa.

Take kuwa numfashinta ya d’auke D’ibbbbbb.....



_Dan Allah ba danniba dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenku nace kada ku fitarmin da littafina in kin sayane don ki fitar kiyiwa girman Allah ki gaya min in meda miki kuɗinki, dan Allah kada ki karantamin. In baki biya kuyiwa Allah kada ku watsa min littafina baku san wahalar da nake sha kan rubutun nanba._






BY

*GARKUWAN FULANI*





📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*

PAGE 16
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*


*FREE PAGE NE*

*FREE PAGE sunzo karshe, daga gobe zamu gama FREE PAGE, ki biya ki karanta. 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number 09097853276, ko kuma ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp na. Special people group 1k ne karamin group kuma 500 ne, wanda bonus ne wa fan's na, asalin kudin littafin 1k ne saukine ga masoyana in an gama kuwa document 1k ne*


Cikin tsananin tashin hankali, da kuma tsananin rud’ewa, Barrister Kabir ya sanya hannayensa duka biyu ya tallafo Jannart d’in.

“Jannart! Jannart!! dan Allah bud’e idanunki Jannart!!! innalillahi wa inna Ilaihirraju’un! Yaya Idi Jannart ta suma, bata numfashi!!!”

Barrister Kabir din ya fad’a yana me.
Kallon Yayan nasa, wato Alhaji Idi Saleh dakata, cikin matsanancin tashin hankali.

Shima kuwa Alhaji Idi Saleh Dakata'n tashin hankali ne, kwance akan fuskarsa, cikin yanayin rud’ewan da yayi, ya kalli Dr Lukman dake tsaye, tare da cewa.

“Dr. Lukman ka duba mana ita dan Allah.”

Jin hakanne kuwa yasa Dr Lukman dake tsaye, d’an matsowa kusa dasu,
dan duba Jannart din, wacce ita yanzu bata masan duk wata Waina da ake toyawa acikin gidanba.

Idanu Barrister Kabir ya d’ago tare da watsawa, Dr Lukman din muguwar harara, cikin kuma yanayin fushi da tsananin b’acin rai yace.
“Kada kayi kuskuren tab’a min y’a.
Domin kuwa na jima da sanin muguwar cutar da kakeyi mata ta karkashin k’asa.”

Cak Dr.Lukman din ya tsaya, tare da matsawa gefe batare kuma daya karaso wajen ba, saboda jin abunda Barrister Kabir din ya fad’a.

Barrister kuwa sungumar Jannart din yayi, kaitsaye kuma cikin sauri ya nufi hanyar fita daga cikin gidan.

Da hanzari kuwa maigadi ya bud’e masa dan madaidicin kofar dake jikin gate din gidan ya fice.
Koda ya fito kuwa murfin motarsa na gidan baya ya bude, tare da tura Jannart din ciki ya kwantar da ita.

Batare kuma daya jira komai ba, ya zagaya ya shiga b’angaren driver, ahanzarce ya tada motar, tare kuma da cillata kan titi, kaitsaye yabi bayan motar Dr Rayyern Mai-nasara dake ta sharara gudu, akan shumfud’add’en titin kofar gidan daya mike santa yana mai jin jijiyoyin kansa na tsananta harbawa sabida ihu da hayaniyar da akayi tayi a kanshi .

Shi kuwa Barrister biye dashi yake a hamzarce.
Wanda kuma yayi hakanne saboda sanin matsayin Rayyern da yayi, na likita zai iya taimaka musu.

Yayinda ab’angaren Rayyern kuwa tuk’in motar yake, yana maijin wani irin b’acin rai acikin ransa, badan komai ba kuwa saidan b’ata masa rai da lokaci da akayi agidan Alhaji Idi Salte Dakata, Tabbas yasan cewar.
Koda ace yaje asibitin nasa yanzu, babu wani abu da zai iya aikatawa, Domin yafi kowa sanin kansa Idan ransa na b’ace baya tab’a iyayin komai, koda ma kuma ace yayi din bisa dole, to abun bazai zama hundred percent yanda yake so ba ga kuma alamun ciwon kansa da yake ji.

Y’ar k’aramar tsuka yaja, tare kuma da d’an buga kan steering motar tasa, kaitsaye ya sanja akalar tafiyar tasa, inda ya saki hanyar asibitin nasu daya kama, direct ya shari kwana tare da hawa kan titin da zai sa dashi da gidansu.

Ganin hakanne kuma yasa P.A d’agowa ya kalleshi, kamar zaice wani abu kuma saiya fasa, saboda yasan halin maigidan nasa, da yawan lokuta bayason adameshi da yawan magana.

Barrister Kabir dake bayan su Rayyern din kuwa, shima gudu yake shararawa, still kuma har yanzu yana mebin ba yansu, sai-dai duk bayan mintuna kad’an yana juyawa ya kalli Jannart dake kwance flat agidan baya, babu alaman numfashi ko d’igo ajikinta.
Wanda hakan kuwa shi yake k’ara sanya Barrister Kabir din acikin tashin hankali.

Tafiyar da bata wuce ta 30mn ba sukayi, isowarsu wajen wani jection ne kuma yasa, Usman P.A d’an d’ago kai ya kalli Rayyern din.
Sake Kallon bayansu Usman P.A din yayi, still kuma ganin motar da tun d’azu yake ankare da ita, na binsu abayane , yasa shi d’an muskutawa cikin kuma yanayin mamaki yace.

“Sir kaman fa binmu wannan motar dake bayanmu takeyi.”

Idanu Rayyern din ya d’aga, tare da maida kallonsa ga madubin motar wanda yake haska musu duk abunda ke bayansu.

Tabbas shima ya lura da motar, saidai kuma bai d’auki hakan amatsayin wani serious abuba, batare kuma daya tankawa Usman P.A ba, kaitsaye ya hau kan titin daya shigar dasu layin gidansu.

Suna isa bakin gate din tamfatsetsen gidan nasu ne kuma, barrister Kabir ya taka wani irin birki.

Wanda kuma hakan yayi dai-dai da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment