Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tsayawar motar Rayyern din shima, cikin kuma zafin nama da zafin ciwon kan sa yakeji ya bud’e murfin motar ya fito, saboda duk atunaninsa Alhaji Idi Sale Dakata ne, bai daddara da gargadin daya yi masa ba, ya sake turo masa wasu mutanen dan su bibiyeshi.

Fitowarsa daga cikin tasa motar ne, kuma yasa Barrister Kabir fitowa shima cikin hanzari, kuma ya nufo Dr. Rayyern d’in.

Muryarsa na rawa yace.

“Dan Allah Dr. Rayyern ka taimakamin, kada Jannart ta rasa ranta, Dan Allah ka taimakawa rayuwarta, wlh itace kaɗai babbar *HUJJATA,* ita kad’ai ce Hujjar da zan nuna anan gaba, please ka taimaka min!!”
Barrister Kabir din ya fad’i haka cikin tsananin tashin hankali, da kuma muryarsa wacce take fitar da sautin kuka.

Dr. Rayyern din kuwa Jin amo da kuma sautin, muryar Barrister Kabir din dake fita cikin kuka ne, da kuma amo mai shiga kunne, yasa shi rumtse I danunsa, tare dasa hannunsa na dama ya dafe kansa, dake wani irin sarawa, dan lokaci daya yaji kaman ana buga masa gudu ma a tsakiyar kannasa, abu na farko da bayaso arayuwarsa shine, yi masa magana cikin sigar kuka da kuma d’aga murya, sannan kuma aduk sanda wani ya buk’aci taimako afujajan awajensa, ya kanji zuciyarsa ta karye.
Balle kuma Barrister Kabir din da yake ta had’ashi da sunan Allah.

*Inama ace makaranta zasu kasance kamar Dr Rayyern in an had’asu da Allah zasuyi abu ko zasu bari, dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenku idan Free PAGE ya kare kada ku fitarmin da littafina, in kinsan kin sayane dan ki fitar dan Allah ki gaya min in meda miki kuɗinki Dan girman Allah da tsarki littafinmu akwai karami. Group 500 ne kacal 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 ko ki sayi katin MTN ki copy edin ki turo min ta WhatsApp*

“Usman!”
Rayyern din ya kira sunan Usman P.A da wata irin murya.
Jin amo da kuma sautin muryar Rayyern din cikin wani irin yanayi na dabanne kuma yasa, cikin sauri Usman ya fito, tare da k’arasowa yana Kallon Ogan nasa.

“Ka kaishi hospital Usman kacewa Sulaiman ya duba patient din, please kuje Usman kutafi daga nan please.....”

Rayyern din ya fad’i hakan, cikin wani irin yanayi marar dadi dayakejin kansa aciki, tare kuma dasa hannayensa duka biyu ya kama kansa.

Usman kuwa fahimtar halin da Ogan nasa ke cike ne yasa shi, saurin kallon Barrister Kabir.

Ahanzarce yace.
“Muje na rakaku hospital dinsa akwai Doctor's zasu dubata in sha Allah zata samu lfy.”

Ko jiran abunda Barrister Kabir din zaice kuwa baiyi ba, ya bud’e murfin motar barrister din, nan b’angaren mai zaman banza ya zauna.

Ganin hakanne kuma yasa Abba Kabir din shima komawa cikin motar, a 360 ya murzawa motar key tare da cillata kan titi, kaitsaye suka nufi asibitin Mai-nasara Hospital, saboda dama Barrister Kabir din yasan asibitin.

Ganin sun miki hanyar asibitinne kuma yasa Usman P.A ciro wayarsa ya dannawa Dr Sulaiman Kira.

Bugu biyu kuwa Sulaiman ya dauki wayar, bayan sun gaisa ne kuma Usman P.A ke fad’awa Sulaiman din cewa.
“Gamunan a hanyan Mai-nasara Hospital zamu kawo emergency patient, bisa umarnin Dr Rayyern.”

Da “to.”
Kawai Dr. Sulaiman ya amsa, Yayinda shi kuwa Usman P.A ya katse kiran.

Rayyern kuwa da har yanzu ke tsaye abakin, motar tasa hannayensa duka biyu yasa ya cigaba da rike kansa dake sarawa.
Jin da yayi cewar bazai iya jurewa tsayuwar bane, yasa shi nufar gate din gidannasu, koda ya isa jikin gate din, hannunsa ya daura akan y’ar karamar kofar dake jikin gate din, tare da tura ta ciki.

Baba Maud’o dake zaune abakin kofar dan Part ɗin sa, yana me sauraran radio ne ya d’ago kansa, saboda ji da yayi an tab’a kofar shigowa gate din.

Aikuwa yana d’aga kansa ya sauke idanunsa akan Rayyern, da har yanzu yake dafe da kansa da hannuwansa duka biyu.

“Rayyern!!!”
Baba Maud’o ya kira sunansa, cikin yanayi na mamaki da kuma zallar damuwa.

Batare kuma daya bari Rayyern din ya amsa masa ba, ya d’aura da cewa.

“Subahanallah Rayyern maiya sameka? Lafiya kuwa? Meke damunka? Bugewa kayi akan naka ne? Ko kuwa wani abune ya same ka?”

Baba Maud’o yayi masa duka tambayoyin cikin bayyana tsananin damuwarsa.

Shikuwa Rayyern da ayanzu, yakejin idanunsa sun fara yi masa nauyi, kai kawai ya iya girgizawa Baba Maud’on, batare kuma daya iya cewa komai ba, kaitsaye ya wuce cikin gidannasu.

Hakan da yayi dinne kuwa yasa Baba Maud’o, Jin wani iri acikin zuciyarsa, take kuma damuwa maitsananin yawa ta bayyana akan fuskarsa, saboda ya sani ba karamin abubane zai sa Rayyern din dawowa acikin irin wannan yanayin, Lallai akwai abunda yake damunshi.

“To kodai awajen aikin nasa ne aka bata masa rai? Kodai kuma ciwon kansa ne?”

Baba Maud’o yayiwa kansa tambayar da bashi da mai amsa masa ita, sai Rayyern din.

Ganin da yayi zancen zuciya bazai kaishi bane kuma, yasa shi dan bud’e kofar gidan ya lek’a waje, ganin motar Rayyern din da yayi fake akofar gate dinne kuma yasashi saurin fitowa, tare da leka cikin motar, ganin akwai key ajikin motar ne kuma yasa, da kansa ya wangale makeken gate din, tare da dawowa ya shiga cikin motar, da kansa ya shigo da motar ciki, saboda a lokacin shi kad’aine ya rage agidan, Hadi driver da kuma sauran masu bawa flowers ruwa duk basanan.

*Dan Allah da Manzonsa idan free PAGE sun kare kada ku fitar min da littafi, ina rokon nanne da yakinin duk Musulmin kirki mai cikar imani da sanin darajar Allah da Manzonsa da darajar iyayensa nasan bazai fitarmin da shi ba, ko ya karanta na watan*


Rayyern kuwa Ahankali yake tafiya, yana me d’an jujjuya kai tare kuma da rumtse idanunsa, da yakejin sunyi masa matukar nauyi.
Isowarshi jikin kofar da zata sadashi da babban falon gidanne kuma, yasa shi d’aura hannunsa akan handle din kofar.

Dai-dai lokacin kuwa Abba da Mamy ne ke zaune acikin falon da alamun tattauna abu mai mahimmanci sukeyi.
Inda Abba ya d’ago kansa ya kalli Mamy, cikin yanayin yin ƙasa da murya da alamun tsawatarwa yace.

“Kinsan abunda yake bunne, wanda kuma har yanzu bamu shirya tono shi ba. Meyasa kikeson ki bada kofa da abubuwa da yawa zasu iya wakana ba tare da mun shirya musuba.
Wannan sirrin mai karfi ne da cikar rauni, Tono shi kuma dai-dai yake da tsayawar bugun zuciyar wasu mutanen, musamman Rayye......”

Sauran maganan dake bakin Abban ne kuwa, suka mak’ale, asakamakon jin motsin bud’e kofar falon da akayi,
Wanda hakan yasa cikin sauri duk suka maida kallonsu ga bakin k’ofar.

Ganin Rayyern din da sukayi dafe da kai ne kuma, yasa duk suka mimmik’e,

“Rayyern lafiya kuwa?”
Abba ya tambaya hankalinsa atashe.

Kai Rayyern din ya d’an girgiza musu, batare daya ce komai ba, kuma ya k’arasa shigowa cikin falon, tare da nufan kan 3 seater, din leather cushion dake Cikin falon ya kwanta.
Still kuma hannayensa ya sake maidawa duka biyu ya rik’e kansa.

Al’amarin daya sanya hankalin su Abba da Mamy matukar tashi kenan.
Da sauri Abba ya k’arasa inda Rayyern din ke kwance, hannunsa ya d’aura akan Rayyern din, cikin muryar dake bayyana zallan damuwarsa da farga yace.
“Rayyern me yake damunka, kodai ciwon kanka ne ya tashi!?”

Kai Rayyern din ya jinjina alaman “Eh.” Saboda ayanzu yakai wani stage da bayajin zai iyayin wata magana.

Zazzafan numfashi Abba da Mamyn suka sauƙe, cike kuma da alhinin tashin ciwon kannasa, Abba ya zaro waya dan kiran Ramadan.
Yayinda Mamy kuwa ta matso kusa da Rayyern d’in, anutse ta zauna tare da soma shafa masa tarin sumar dake kansa.

A dai-dai wannan lokacin kuwa, Ramadan ne ke zaune acikin wani had’add’en lambu, dake cikin wani katafaren gida, yayinda ya k’urawa wata fara kyakkyawar matashiyar budurwar dake zaune agefensa idanu.
duk da cewar kuma ak’alla budurwar dake zaune agefen nashi, ba zata wuce 20 years ba, amma tana da cikar halitta mai kyau, da ganinta kuma kasan cewa yar manyan mutane ne, Rayhanna kenan kyakkyawar matashiyar budurwar mai alkunya.

Yayinda ad’an gefe da Rayhannan kuwa Riyyam-nsra ne zaune, yanata yiwa Hamman nasa tsiya.
Cikin kuma ya bawa da zab’in Ramadan d’in yace.

“Gaskiya Hamma Ramadan ka iya zab’en kyakkyawar budurwa, tamkar daga saudiya aka sassak’ota.”

Murmushin Jin dadi Ramadan yayi, tare da sanya hannunsa na dama ya dafa kafad’an Riyyam din, again kuma cikin kasa dauke idanunsa daga kan Rayhanna’n nasan yace.

“Angaya maka cewar ni na wasa ne, ai kwata kwata bana sanya, ko da ka d’auka cewar ni irin suma Hamma Rayyern ne waliyai.”

Dariya Riyyam nsra ya saka, Yayinda ita kuma Rayhanna ta sanya mayafinta ta rufe fuskarta, wanda tayi hakanne kuma saboda Sam bazata iya jurewa, irin Kallon da Ramadan din keyi mata ba, Domin kallone da yake bayyana tsananin kauna da soyayyarsa agareta.

Baki Ramadan din ya bud’e da niyar cewa wani abu, amma kuma sai k’aran wayansa dake tashi, acikin aljihun rigarsa, ya hanashi furta komai.

Zaro wayartasa yayi, ganin sunan Abba na yawo akan screen din wayar ne, kuma yasa shi d’agawa da sauri.

Daga can b’angaren kuwa Abba dake tsaye agefen Rayyern ne yace.

“Ramadan, Rayyern! Rayyern ciwon kansa ya tashi!”

Idanu Ramadan din ya dan zazzaro tare kuma da, mik’ewa tsaye cikin tashin hankalin daya samu kansa aciki yace.

“Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un, Abba maiya samu Hamma Rayyern din, yaushe kuma ciwon kan nasa ya tashi?”
Ya tambayi Abban cikin tashin hankali, gami da tsananin damuwa.

“Bansani ba Ramadan, Domin yanzu dawowanshi gida, yanzu haka gashinan a kwance sai faman rike kan na yakeyi.
Maza Ramadan kabar duk abunda kakeyi ka dawo gida, sannan ka biya ta pharmacy ka had’o masa magunguna.”

Abban ya fad’i hakan, cikin muryar dake bayyana cewa, kwarai yana cikin damuwa.

Ramadan kuwa idanunsa da suka ciko da k’walla, saboda tausayin dan uwannasa yad’an lumshe, kana cikin muryarsa da tayi rauni sosai yace.

“Shikenan Abba ganinan zuwa.”

Yana gama fadan hakanne kuma Abba ya katse kiran.

Riyyam-nsra da tun d’azun shima ya mik’e tsaye hankalinsa atashe matuka, yace.

“Hamma Ramadan mai yasamu Hamma Rayyern? Dan Allah karkacemin wani abu na cutarwa ne ya sameshi.”

Idanu Ramadan din ya bud’e, cikin yanayin sanyi yace.

“Ba abunda ya sameshi Riyyam, kawai dai ciwon kansa ne ya tashi, wanda dama kuma yana dashi, saidai bai cika tashi ba, harsai da dalili, Idan ciwon kannan ya tashi Riyyam, Hamma Rayyern yana shan wahala, saidai duk da haka gwara ciwon kan, akan matsanancin ciwon cikin da yake tashi mishi, awasu mabanbanta lokuta.”

D’an rank’wafowa yayi ya kalli Rayhanna, da itama gaba daya damuwa ta bayyana akan fuskarta, saboda tasan matsayin Dr Rayyern din awajen Ramadan, tasan yanda Ramadan ya dauki Rayyern, da kuma yanda yake girmama duk wani abu daya shafesa, haka kuma tasan yanda Ramadan din ke daukan duk wata matsala ko damuwar yayansa, Domin sauda yawan lokaci Ramadan din, kan fad’a mata cewar Hamma Rayyern dinshi, shine duk wani Garkuwa’rsa, shine kuma wanda ya tsaya masa akan jindadi da farincikinsa.

“Hanna zantafi, Hamma Rayyern bashi da lafiya, zamuyi waya later.”

Ramadan din ya fada murya asanyaye.

Mik’ewa tsaye Rayhanan tayi, tare da cewa.
“Shikenan badamuwa, Allah Ubangiji ya bashi lafiya, yasa zakkan jikine.”

Da “Ameen.” Ya amsa, har wajen da motarsa kirar Benz ke fake kuma Rayhanan ta rakosu, inda tayiwa Riyyam-nsra sallama.

Saida taga ficewarsu daga cikin compound d’in gidan nasu, kuwa kafun ta koma ciki.
Duk zuciyarta babu dadi, saboda duk wata damuwa da tagani akan fuskar Ramadan to ta shafeta.

Ramadan kuwa suna ficewa daga cikin gidansu Rayhannan, wani irin gudu ya soma shararawa akan titi, wanda hakan yasa cikin mintuna kadan suka iso, babban pharmacy dinsu.

Ko gama dai-dai-ta parking din motar baiyi ba, haka ya fito ya shiga cikin pharmacy din, duk wasu magunguna da yasan Rayyern din zai buk’ata ya had’a, tare da fitowa agurguje yaja motar suka nufo gida kaitsaye.

Isowarsu bakin gate din gidanne kuma yasa, Ramadan soma danna horn.

Wannan yasa cikin sauri Baba Maud’o dake zaune abakin gate din, yayi jigum, yazo ya bud’e musu, gaba d’aya bayajin dadi acikin zuciyarsa, saboda sai ayanzunne ma yake tunawa da cewar, halan ciwon kai din Rayyern dinne ya tashi, saboda aduk cikin gidan babu wanda baisan da cewar, Rayyern na fama da ciwon kai dana ciki ba.

Ramadan kuwa yana shigowa cikin gidan yayi parking motar, cikin sauri kuma shida Riyyam suka fito, kowannensu fuskarsa dauke da matsanancin damuwa suka shige cikin gidan.
Tunkafun su karasa shiga cikin babban falon gidan kuma, Ramadan ya soma b’abb’alle magungunan da zai bawa Rayyern din.

Wanda hakan yasa suna shiga cikin falon, direct Riyyam-nsra ya k’arasa gaban deep freezer, tare da dauko bottle water marar sanyi kasan cewar ba'a jima da sasuba.

Koda ya dawo goran ruwan ya mik’awa, Ramadan wanda zuwa lokacin harya gama b’are magungunan, inda da kansa ya tallafo Hamman nasa, tare da zuba masa magungunan, kana ya had’a masa da ruwan faro.

Atake kuwa Rayyern ya had’iye magungunan, saidai kuma cikin radadin ciwon kan nasa da yakeji, ya sake komawa ya kwanta, Yayinda sannu Ahankali yake ci gaba da d’an jujjuyawa kan nasa.

Idanu duk suka zuba masa, kana cike da tsananin tausayawa sukeyi mishi sannu, Riyyam-nsra kuwa zama yayi dab’as ak’asa, idanunsa da suka cicciko da hawaye ya zubawa Hamma Rayyern d’in, acikin ransa kuwa yana me addu’a, da fatan Allah Ya bawa hamma Rayyern dinnasu lafiya.

Rayyern kuwa dake kwance kannasa ya sake rikewa, tare da lumshe idanunsa, wanda sukayi jazur, saboda tsabar wahalan da yakeji kuwa, hatta jijiyoyin dake kwance akan goshinsa saida suka fito rud’u rud’u.

*Dan girman Allah masu sayan littattafai dan su fitar su watsashi kuyi hakuri kada ku saya littafina dan Allah nace in kin saya kuma ki gaya min in meda miki kuɗinki*

Bayan kaman mintuna 15 dashan maganin nasa ne kuma, ya soma sauke wani irin wahalalliyar ajiyar zuciya.
Yayinda sannu ahankali yakejin relief nad’an saukar masa.

In a 20mn kuwa batare da zato ko tsammani ba, bacci mai nauyi ya daukesa.

Jin yanda numfashinsa ke fita da d’an fusga ne kuma, yasa su Abba gane cewar yayi bacci, ajiyar zuciya suka sauk’e dukansu, Yayinda Abba kuwa ya d’an rankwafa tare da gyarawa Rayyern din kwanciya.

Bayan ya koma ya zauna akan kujera ne kuma yasa hannunshi duka biyu yayi tagumi cikin alamun tarin fargaba, tashin hankali, so, da tarin tausayin d’an nasa .
Ido Ramadan ya ɗan zuba mishi kana a hankali yace.
“Abba ba komai fa in sha Allah zai samu lfy”.
Numfashi ya ɗan sauƙe a hankali kana murya asanyaye yace.

“Hakika yanzu aduniya babu wani abu da yake, damuna da kuma matuk’ar d’agamin hankali sama da ciwon Rayyern.
Ciwon Rayyern yana damuna, musamman ciwon cikinsa da Idan ya tashi masa, yakeyin kamar zai rabamu dashi, Tabbas Ina matuk’ar tsoron ranan da ciwon nasa zai tashi, Ina fargaban hakan akoda yaushe, Ina mai kuma addu’a da fatan, Allah ya yayemishi wannan ciwon kai da ciwon cikin, Domin kuwa aduk sanda d’aya daga cikinsu ya tashi, shi kad’ai yasan wani irin zafi da yakeji tunda har yake fidda shi hayyacinsa.”

Abban ya kai k’arshen maganan nasa, cikin raunatacciyar murya, Yayinda idanunsa kuma suka cicciko da hawaye.

Ganin hawaye a idanun Abban ne kuma, yasa Mamy, Ramadan, Riyyam duk sukaji jikinsu yayi sanyi, take kuma idanun Mamayn ma duk suka cicciko da hawaye, kasancewar ta Mace ne kuma, yasa ta kasa controlling hawayen nata, harsaida suka sauk’o kan fuskarta, batare kuma da ta bari kowa yaga hawayen nata ba, ta share da sauri.

Dai-dai lokacin kuwa Baba Maud’o dake tsaye abakin k’ofar shigowa falon, ya d’an d’aga muryarsa wajen yin sallama.

Jin muryar Baba Maud’o dinne kuma yasa, Ramadan mikewa ya k’arasa tare da bud’e kofar, Cikin kulawa yace.

“Baba Maud’o bismillah ka shigo mana.”

Kai Baba Maud’on ya girgiza, tare da cewa.
“A’a basai na shigo ba Ramadan, dama nazo ne na tambaya naji ya jikin Rayyanu.”

Ajiyar zuciya Ramadan ya sauk’e, cikin kuma son kwantarwa da Baba Maud’on hankali yace.

“Jikinsa da sauki sosai Baba Maud’o, yasha magani kuma yanzu haka ma bacci yake, Insha Allah kuma Idan ya tashi daga baccin, zai ji saukin ciwon kan.”

Kai Baba Maud’on ya jinjina, cike kuma da gamsuwa yace.

“Masha Allah! Allah Ubangiji ya k’ara masa lafiya da Nisan kwana mai amfani.”

Da “Ameen.” Ramadan ya amsa, ganin Baba Maud’on ya juya ya tafi ne kuma, yasa shima komawa cikin falon.

Baba Maud’o kuwa Koda ya nufi dakinsa dake cikin gidan, hannayensa yasanya ahankali ya share hawayen da suka gangaro daga Cikin idanunsa, wanda kuma yayi imani cewa, da ace bai bar wajen Ramadan din da wuri ba, To da akan idanun Ramadan hawayen nasa zasu zubo.

_Littafin TUBALI na kuɗine ki biya ki karanta cikin salama special Group 1k ƙaramin group 500 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 ko ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp_

Acan b’angaren su Barrister Kabir kuwa, da wani irin speed suka shiga cikin asibitin.

Wanda kuma suna shiga ko gama parking ba suyiba, aka turo wasu nurses da gado irin maitayannan, su dakansu nurses din suka d’aura Jannart akan gadon, tare da kutsawa da ita cikin asibitin, kaitsaye zuwa emergency.

Suna shigar da ita emergency din kuwa, Dr. Sulaiman, da kuma Dr. Imran, kana da Dr. Fatymah, suka shiga emergency din, tare da duk’ufa akanta, cikin sauri suka soma bata taimakon gaggawa.

Yayinda acan waje kuwa, hankali atashe Barrister Kabir ya karasa receiption na, Hospital din dan bud’ewa Jannart din folder.

Koda yaje kuwa baiwani dau lokaci ba layi ya iso kanshi.

Mai bud’e folder dinne ya dago kansa ya kalli Barrister Kabir tare da cewa.
“Sir me sunan patient din?.”

D’anjim Barrister Kabir yayi, natsawon wasu mintuna, kafun ya dago kai, cikin aminta da abunda zuciyarsa ta yanke yace.

“Sunanta *Jannart Abdulkarim Saleh Dakata.”*

Kai mai bud’e folder’n ya jinjina, tare da maida kansa k’asa ya rubuta abunda yaji mutumin ya fad’a masa.
Yan cike cike yayi cikin abunda bai wuce 5mn ba kuwa, ya bud’ewa Jannart folder acikin Hospital din.

Barrister Kabir kuwa ganin komai ya kammala ne, yasa shi komawa bakin emergency room din ya zauna, tare da sanya hannayensa akan fuskarsa ya zuba tagumi, Tabbas a yanzun abubuwa da yawa ne ke damunsa, amma babban burinsa shine farfadowar Jannart da kuma dawowa cikin hayyacinta.

Acan cikin Emergency room din kuwa, sosai su Dr. Sulaiman suka duk’ufa akan Jannart don ceto rayuwarta, saidai kuma duk yanda suka dauki abun ya wuce nan.

Dr. Sulaiman daya shaida fuskar yarinyar ne ya sharce gumin dake goshinsa, tare da d’auko wani abu mai kaman dutsin guga guda biyu ya manna akan kirjin Jannart din, ganin da yayi batayi motsi bane kuma, yasa shi jin wani irin fad’uwar gaba, saboda sanin da yayiwa abun, sau uku kawai ake dannashi ak’irjin mutum, Idan aka dannawa mutum sau daya, ya farfado ya koma, aka kuma na biyu still bayan ya farfado ya sake komawa, To Idan akayi na uku mutum baiko motsa ba, Lallai alamace dake nuna cewar bashi da rai.

Sake danna mata abun Dr. Sulaiman yayi akan kirjinta, cikin sa’a kuwa yaji taja wani irin numfashi, saidai kuma kafun su ankara numfashin harya koma.

Kallon-kallo sukayiwa junansu, kafun Dr. Sulaiman ya sakeyin shahadan danna mata abun da karfi akan kirjinta.
Wani irin dogon numfashi maikama da shak’uwa taja, tare da mimmik’e jikinta, lokaci daya kuma bugun zuciyarta ya...!


*littafin TUBALI na kuɗine, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU*


*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta,
akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki ta karkashi D.H.L. in dai kin cika jakarki baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*



By
*GARKUWAR FULANI*







📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*

PAGE 17
NA

DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment