Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kuje gida zaifi”.
Dr Sulaiman yayi mgnar bisa bin umarnin da Dr Rayyern ya kidanya mishi a waya.

Cikin jin daɗin samun lafiyar nata Barrister Kabir yace.
“Toh Alhamdulillah Dr Sulaiman mun gode matuƙa Allah ya bar zumunci”.
Amin Amin yace tare da juyawa ya fita.

Su kuwa biyar dai-dai Barrister Kabir ɗin ya ɗauki Jannart da Mom ya nufi gida dasu.
Suna kan hanya ne Daddy ya kirasu yazo bai samezu ba.
Nan yake ce mishi ai an sallamesu gasu a hanyar gida.

Nan dai suka koma gida Barrister Kabir ya bawa Mom magungunan tare da cewa ta kula da Jannart da shan mgnin.
Ba tare da yayiwa yayan nasa mgnar Junaid ba ya sallamesu ya tafi.


Toh a hankali dai abubuwa ke juyawa suna wakana.
Yau Monday kwana biyu kenan da sallamo Jannart Alhamdulillah kuma jiki yayi sauƙi sosai.
Junaid kuma har yau bai zo gidaba.

Barrister Kabir kuwa duk cikin kwanakin nan bashi da zama yana yawan zirga-zirgan da Aunty Dijat ta gaza gane na menene.



Yau Monday misalin biyar na yamma.
Dr Rayyern Mai-nasara ne dake zaune a yar barandarsa balcony dake sama can jikin Bedroom ɗin sa.
Sanye yake da wasu tattausan riga da wondon iya guiwa rigar kuma irin mara hannun nance.

System ɗinshi ne bisa stoll ɗin dake gabansa sai plate da chocolate sai Bootle water a gefenshi.
Sosai ya dugufa kan aikin da yakeyi.

A hankali ya ɗago kansa cikin tarin gajiya ya juyo ya kalli farfajiyar gidan nasu can bakin gate.
Wani irin juyowa yaye tare da tashi tsaye da masifar fargaba ya zubawa fuskar Barr....!




*TUBALI na kuɗine ki biya kafin ki karanta cikin salama Da Allah.*



*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*



By
*GARKUWAR FULANI*




Da sauri ya miƙe.
Idanunsa ya d’an zazzaro tare da sanya hannu ya dafe forehead d’insa, bakomai ne ya sashi yin hakan ba kuma, face ganin Barrister Kabir da ya shigo cikin gidan.

“Wannan mutumin Again? to me yazoyi? Kardai akan wancan magananne mai kama da tatsuniya ya biyoni har gida? gaskiya Indai hakane bazan iyaba, gwara ma tunda wuri naje na dakatar dashi.”

Ya fad’i maganar cikin sauri, batare kuma daya tsaya wani jinkiri ba kaitsaye ya juya, ya nufi asalin cikin sashinsa, Domin dole saiya sauko kasa, kafun zai iya dakatar da Barrister Kabir din.

Barrister Kabir kuwa Koda ya gama dai-dai-ta parking din motar, budewa yayi ya fito.

Ahankali ya juyo tare da nufo inda Baba Maud’o ke tsaye, idanu Baba Maud’o ya zubawa, fuskar mutumin da yaga yana tunkarosa, babu ko kyaftawa, Yayinda ajikinsa yakejin wani irin yanayi na girgizar kwanya.

“Assalamu Alaikum Barka da aiki.”
Barrister Kabir ya fad’a yana me mik’awa Baba Maud’o hannu, alaman suyi musabaha.

Hakan kuwa shi ya katsewa Baba Maud’o d’an guntun tunanin da yakeyi, hannu ya mik’awa Barrister Kabir din suka gaisa.
Saidai kuma duk yanda Baba Maud’on yaso dauke idanunsa daga Kallon, mutumin dake tsaye agaban nasa ya kasa.

Barrister Kabir kuwa Dan gyara tsayuwarsa yayi, kana cikin sakin fuska yace.

“Ni bak’one kuma nasan baka shaidani ba, amma Dan Allah ko zaka iya yimin sallama da maigidan?”

Still idanu Baba Maud’o ya zuba masa, saidai kuma jin yace Yayi masa sallama da mai gidanne, yasa shi d’an sauk’e ajiyar zuciya.

Kai Baba Maud’on ya jinjina, cikin kuma gamsuwa da yaji acikin zuciyarsa yace.
“To Kajirani anan, ba matsala bari nayi masa magana.”

“To Masha Allah nagode sosai.”

Barrister Kabir ya fad’i hakan, yana murmushi.

Yayinda shi kuwa Baba Maud’o kaitsaye ya nufi cikin gidan.

Aikuwa yana fara tafiyanne hankalin Barrister Kabir gaba d’aya ya tattare ya tafi kanshi, inda ya zubawa bayansa idanu baya ko k’yaftawa.
Musamman tafiyan mutumin, yaso tuna masa da wasu abubuwa.

Saurin girgiza kansa yayi, tare kuma da ture duk wani tunani da yazo cikin k’wak’walwarsa, saboda yasan ma ba hakan bane, maybe yanayi ne kawai yazo d’aya.
Sannan babban abunda yake gabansa ayanzu ma yafi karfin wannan tunanin.

Shikuwa Baba Maud’o Koda ya k’arasa jikin k’ofar babban falon gidan, tsayawa yayi tare da soma dan k’wank’wasa kofar.

Abba kuwa dake zaune acikin falon, Jin ana buga kofarne yasashi, d’an d’ago da kansa, tare kuma da bada izinin shigowa.

Jin anbada izinin shiga ne kuma yasa Baba Maud’o d’an tura k’ofar, ahankali ya saka kansa acikin falon bakinsa d’auke da sallama.

Ganin Baba Maud’o ne kuma yasa Abba dake zaune saurin mik’ewa, lokaci daya kuma ya saki fuskarsa tare da cewa.

“A’a Baba Maud’o yau kaine da kanka, shigo daga ciki.”

Murmushi Baba Maud’o yayi, tare kuma da d’an girgiza kansa, kana murya asake yace.
“A'a ai bama sai na shigo ba, yanzuma daliline ya kawoni, wani mutumi ne yazo yananan awaje, ya kuma ce Kai yakeson gani.”

Kai Abban ya d’an jinjina, tare kuma da danyin shiru na.
Dan wasu sakanni, saboda duk a iya saninsa baiyi da wani akan cewar za’azo nemansa ba.

Watsar da tunanin dake zuciyar tasa yayi, cikin kuma sakin fuska yace.
“To Baba Maud’o ace masa ganinan zuwa.”

Abban ya fad’a yana me gyara zaman babbar rigar dake jikinsa.

Kai Baba Maud’o ya jinjina, batare da yace komai ba kuma, ya juya ya fice daga cikin falon.

Dai-dai lokacinne kuma Rayyern ya gama sauk’owa cikin falon.

Ganin da yayi kuma Abban nasa na shirin fita ne yasashi, dan Sosa k’eyansa, cikin yanayin inda-inda yace.

“Abba fita zakayi ne?”

Juyowa Abba yayi ya d’an kalleshi tare da cewa.
“Eh yanzun nan Baba Maud’o yake cemin wai wani mutumi awaje yana son ganina.”

Kansa yad’an shafa still, kana cikin yin k’asa da murya yace.
“No Abba basai kajeba ai, ba bak’on ka bane bak’onane, kuma nasan ni yake nema.”

Idanu Abban yad’an tsura masa, cikin rashin gamsuwa da hakan yace.

“To kuma Idan ba bakona bane yace kuma yana nema na? Bari dai naje naji ko menene.”

Saurin d’ago da kansa yayi ya kalli Abban nasa, lokaci daya kuma ya marairaice fuskarsa tamkar karamin yaro.
“Abba dan Allah ka zauna, Zanje naji ko menene.”
Ya fad’a yana me kokarin fita wajen.

Kallonsa Abba yayi kana cikin rashin bai yarda da hakan ba yace.

“Anya kuwa Rayyern To waye ne, lafiya dai kam ko?”

“Eh Abba Lafiya kalau, bari naje na sameshi.”
Rayyern din ya fad’a cikin d’an sauri, tare da gudun kada Abban nasa yace Lallai shi da kansa zaije.

“Da kata Rayyern, koma dai wajen waye yazo, ai dai yanzu kam ni ya buk’aci gani ko, To barni naje na sameshi.”

Abban ya fad’a cikin serious, wanda hakanne kuma yasa duk jikin Rayyern din yin lak’was, kansa yad’an langwabar gefe, cikin kuma yanayin sanyi yace.
“Shikenan To Abba Dan Allah muje tare.”
Kai Abban ya jinjina masa alaman to.

Inda Abban yayi gaba shi kuma Rayyern ya biyoshi abaya, Yayinda acikin zuciyarsa yakejin babu dadi, saboda baisan da wacce maganan Barrister Kabir din ya kuma zuwa yau ba.
Saidai koma meye yana fatan ace sab’anin waccan magananne da sukayi last Friday acikin mota.

Koda suka fito compound din gidan, Barrister Kabir dake tsaye ajikin motarsa, yana hangosu ya fadada murmushi da kuma fara’ar dake kwance akan fuskarsa.

Bayan sun k’arasone kuma Abba’n ya mik’a masa hannu sukayi musabaha, kana Rayyern ma ya bashi hannu suka gaisa.

D’an Kallon Barrister Kabir din Abba yayi, cikin yanayin sakin fuska yace.

“Sannu bawan Allah saidai kuma gaskiya ban shaida fuskar taka ba.”

Murmushi Barrister Kabir din yayi, tare da gyara tsayuwarsa, still kuma fara’a fad’ad’e akan fuskarsa yace.

“Eh gaskiya bazaka shaidani ba, Domin wannan zuwan nawa, shine zuwana na farko cikin gidanka, sunana *Barrister Kabir Saleh Dakata!!”*

Dammmmm dammmmm haka zuciyar Baba Maud’o tayi wani irin bugawa, a lokacin da yaji sunan mutumin dake tsaye agaban nasa.
A hankali ya lumshe idanunsa sabida jin zuciyarsa na wani irin harbawa da karfi, tamkar zata faso kirjinsa ta fito.

Abba kuma kai ya jinjina nawa Barrister Kabir alamun gamsuwa.

Rayyern dake tsaye agefensu kuwa, Dan lumshe idanunsa yayi, cikin kuma yanayin kosawa yace.

“To Barrister mungode k’warai da ziyara.”
Ya k’arasa maganar tasa atak’aice Domin Sam bayason daga haka mutumin ya sake fad’an wani abu kuma.

Barrister Kabir kuwa fahimtar hakanne yasa shi, sakin murmushi, batare kuma daya lura da shock din da suke ciki ba yace.

“Alhaji wajenka nazo Idan babu damuwa kozan iya samun lokacinka muyi magana.”

Saurin girgiza Kai Rayyern yayi, lokaci daya kuma gaba daya mood d’insa ya sanja.
Kallon Barrister Kabir din yayi, kana cikin dagiya yace.

“Mun gama magana dakai tun a wancan ranan.
To yanzu kuma ai inaganin babu buk’atar kace lallai saika yi magana da Abbana, Dan Allah kaje kawai.”

Dr. Rayyern din ya k’arasa maganan, cikin son kin bawa Barrister Kabir din dama.

Shikuwa Barrister Kabir murmushi yayi, batare kuma daya ce komai ba, ya sake gyara tsayuwarsa.

Abba kuwa wani irin boyayyar ajiyar zuciya ya sauk’e, tare da d’an juyawa ya kalli Rayyern dake bayansa, wanda yayi kicin kicin da fuska.
Tabbas zuciyar Abban ta raya masa wani abu.
Hakanne kuma yasa shi dawo da kallonsa ga Barrister Kabir d’in.

“Shikenan badamuwa Barrister Kabir Saleh Dakata mushiga daga ciki.”
Abban ya fad’a yana me juyawa, kaitsaye, Barrister Kabir kuma ya rufa masa baya.

Rayyern kuwa idanunsa ya rumtse, cikin haushi da takaici ya d’an ciji Labb’an bakinsa, sam kwata kwata ba haka yaso ba, yaso ace Barristern bai samu attention din Abban nasu ba.

Juyawa yayi shima asukwane yabi bayansu.

Yayinda Baba Maud’o dake zaune akan d’an bencinsa kuwa duk yabisu da idanu.

Acan cikin falon kuwa, suna shiga Abba ya nunawa Barrister Kabir din wajen zama.
Bayan duk sun zaunane kuma, Abban ya kalli Rayyern, da yake shigowa yanzu.
Kuma shidinma waje ya samu acikin falon ya zauna, saboda ya fiso duk wani abu da Barrister din zai fada ya jita acikin kunnensa.

Abba da Barrister Kabir din kuwa sake gaisawa sukayi, kafun duk sukayi shiru na d’an wasu sakanni.
Still Abban ne kuma da har yanzu zuciyarsa bata daina bugawa da karfi ba, ya kalli Barrister Kabir din, tare da cewa.
“Barrister inajinka meke tafe dakai?”

K’akk’afar ajiyar zuciya Barrister Kabir ya sauk’e, lokaci daya kuma duk wani mood d’insa ya sanja, tsananin rauni da kuma karyewar zuciya ne suka bayyana akan fuskarsa, Yayinda zallan damuwa ta fito tayiwa fuskarsa kawanya.
Gyara zamansa yayi ahankali, cikin kuma sanyin murya dake bayyana tarin fargaba hadi da damuwarsa yace.

“Tabbas ni mabuk’aci ne awajenku, sannan kuma banzo dan komai ba, saidan saka rai da kuma fatan cewa watakila zaku dubeni..”

Dan Jim yayi kana cikin k’ank’an dakai yace.
“Taimakon had’i da Alfarma nazo nema awajenku, Dan isar Allah da Manzonsa idan zaku iya.”

Shiru gaba d’aya falon ya d’auka, Yayinda kuma har yanzu zuciyar Abba keci gaba da bugawa, saidai kuma jin abunda Barrister Kabir din ya fad’ane yasa shi, sauk’e ajiyar zuciya, tare da kallon Barrister Kabir din cikin, kuma rashin gane inda kalamansa suka dosa yace.

“Inajinka Barrister wacce irin taimako kake nema awajenmu, Allah Dai yasa zamu iya sabida yadda ka haɗamu dashi da fiyayyan halitta in ban iya maka shiba zanji ciwo a raina.”

Idanunsa da suka d’an ciko da hawaye lokaci daya ya lumshe, cikin sanyin da jikinsa yayi ne kuma ya d’an zamo jikinsa daga kan kujeran, batare kuma dasu Abban sun farga ba, sai ganinsa sukayi ya durk’usa guiwowinsa biyu agaban Abban.

Cikin wata irin muryar dake bayyana karyewar zuciya da kuma tsananin damuwarsa yace.
“Dan Allah Dan Annabi Sallallahu alaihi Wasallam. kuyimin taimako, da kuma alfarma kamar yanda na buk’ata a farko, saboda tseratar da rai da kuma lafiyar y’ar Adam.”

Again gaba d’aya falon shiru ya dauka, babu abunda ke tashi acikinsa kuwa face bugawan zuciyoyi, Yayinda kwakwalwar kowanne daga cikinsu ke kawo masa tunani na daban.

Bama kamar Abba da gaba d’aya kalaman Barrister Kabir din suka d'aure masa Kai, tare da juya masa tunaninsa izuwa wani waje na daban.
Yayinda shikuwa Rayyern gaba daya ya dauke kansa gefe, tare da hade fuskarsa.

Kallon Barrister Kabir din Abba yayi, cikin kuma rashin fahimta da kasa sanin makaman kalaman nasa, hadi da rudun daya samu kansa aciki yace.

“Barrister har yanzu dai ban fahimci inda kalaman naka suka dosa ba, bamusan me kake nufi ba? Rayuwar waye zamu tseratar, sannan me hakikanin zancen naka yake nufi?”

Idanu Barrister Kabir ya d’an lumshe, sannan kuma murya araunace yace.

“Tana tsananin buk’atar taimako, Tabbas Jannart tana buk’atar Garkuwa, had’i da ingantaccen mafaka, tana buk’atar haske acikin rayuwarta, wanda yake dauke da sarkakiya maitarin yawa, gaba daya duhu da bakinciki sunyi tasiri acikin rayuwarta, hakika tana buk’atar taimako, da kuma samun ceto daga irin azabar da d’an uwanta yake gana mata, Dan Allah ku taimaka ku bata mafaka, ku taimaka ku tayani inganta rayuwar marainiyar da Allah kejin kanta akoda yaushe.”

D’an tsagaitawa da maganan nasa yayi, tare da d’ago kansa akaro na barkatai ya kalli Abba daya zuba masa ido.

Saidai kuma awannan karon irin Kallon da yakeyiwa Abban ya banbanta dana sauran lokutan.

Bakinsa ya bud’e Ahankali cikin kuma fata da addu’an cikar burinsa yace.

*”Dan Allah Ina meneman alfarma agareku, Ina nemawa y’ata auren d’anka Dr. Rayyern Mai-nasara!!” zan bashi ɗiyata bisa yarda da gamsuwa da tarbiyarshi da gskyarsa da amanarsa*

Wani irin bugawa maitsananin karfi zuciyar Abba tayi, wanda kuma harsaida rud’u da kuma mamakin daya shiga ya kasa b’uya akan fuskarsa.
Idanunsa ya d’an zazzaro waje, da tsananin mamaki al’ajabi hadi da tu’ajjudi, yake Kallon Barrister Kabir din, saboda zai iya yin rantsuwa cewar maganan da Barrister Kabir din ya fad’a, ta daki zuciyarsa sosai, Yayinda kuma ta rarraba masa tunaninsa zuwa wani waje na daban.

Rayyern dake zaune kuwa idanunsa ya rumtse da k’arfi, adai-dai lokacin da maganan Barrister Kabir din ta daki dodon kunnensa.

“Aure! Aure!! Aure kuma!!!” Abba ya fad’a cikin bayyana tsananin mamakinsa, saboda shidai zaice tunda yake bai tab’ajin anyi irin hakan ba, sai awasu k’asashen kamar India, koda ma kuwa anan din anayi to ya sani ba acikin zuriyar Hausa Fulani ba gidan mata suje nemawa yarsu auren gidan maza.

Barrister Kabir kuwa Kai ya jinjina, fahimtar da yayi kuma cewar sun yiwa maganan nasa wata kalar fahimta ne yasa asanyaye yace.

“Kuyi hakuri banzo da maganar dan yin kaina, ko kuma wani abu na daban ba, saidai halin matsalar da nake ciki da kuma wanda nake shirin fuskanta yasa nazo muku da wannan buk’atar, nasan bakusanni ba baku kuma San komai akaina ba, amma Idan har buk’ata ta bazata samu ba, Dan Allah kuyi mini alfarma na kawo Jannart gidanku, ku b’oyemin ita, ku bata kariya kuma ku zame mata Garkuwa, ta yanda baza’a tab’a sanin cewa tana nan ba, kamar yanda na fad’a muku a farko, Jannart Marainiyace, marainiya kuma wacce take tsananin buk’atar taimako, amatsayinku na y’an uwa musulmai Dan Allah kuyi min wannan taimakon, ku zama kariya ga Jannart!!”

Barrister Kabir ya kare maganar yana me had’e hannayensa duka biyu waje d’aya, alaman rok’o.

Wani irin doguwar ajiyar zuciya Abba ya sauk’e, tare dasa hannunsa ya dafe zuciyarsa, da ayanzu ta rage yawan harbawan da takeyi tun lokacin da yaji sunan Barrister Kabir, maida bayansa yayi ya jingina da jikin kujerar da yake Kai.
Idanunsa ya lumshe, Yayinda yake amsar duk wani tunani da ke yawo acikin k’wak’walwarsa, wanda kuma har yakeji tamkar zasu hautsuna masa k’wak’walwa.

Tabbas ayanzu duk wani nazarinsa ya tsaya cak.

Yayinda Rayyern kuwa dake can gefe, idanu ya tsurawa Abban nasa zuciyarsa na bugawa, saboda sam bayason Abban nasa ya aminta da maganar Barrister Kabir din.
Domin shi agaba daya rayuwarsa babu maganan wata Mace acikin tsarinsa, ba kuma yajin zai iya auren wata, balle kuma ya karb’i wani ajiya ji rainin hankali wai ajiya!? Kamar a garin gaɓa-gaɓa.

Abba kuwa kusan mintuna 5 kenan yanzu da ya nutsa acikin duniyar tunanin da yake.

“Lallai Wannan shine k’arin dama, abubuwa nata kusantowa, nesa na matsowa kusa, Yayinda haske ke shirin bayyana ya mamaye duhun duhuwan daya danne kekkyawan Tubalin da yake gine tun da dadewa.”
Abban ya fad’i hakan acikin zuciyarsa, adai-dai lokacinne kuma ya dawo daga duniyar tunanin daya tafi.

Ajiyar zuciya mai karfi ya sauk’e, tare kuma da dawo da kallonsa ga Barrister Kabir dake zaune agabansa.
Kwarai ya aminta da shawarar da zuciyarsa ke basa, ya kuma yi Na’am da hakan domin akwai wani ƙulli a tsakani.

Numfashi me zafi ya fesar, cikin kuma yarda da kai hadi da gamsuwa yace.

*Littafin TUBALI na kuɗine dan girman Allah da Manzonsa da darajar iyayenku kada ku karanta min littafina in baku biyaba, 1k ko 500 da kika biya ko zaki biya kuma bawai kuɗin mallakan littafin bane, kuɗin samun damar karanta Littafin ne, kiya girman zatin ubangijin daya bamu rai da lfy, kada ku fitarmin da littafin, dan darajar Allah kada kuyi ta posting na littafina. Special Group 1k ƙaramin group kuma 500 yawan posting ne babbancinsu, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, in ba halin turowa ta account ki sayi katin MTN ki copy number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp number na*


*”Ni Alhaji Bashir Abban Rayyern na amince da buk’atar da kazomin dashi Barrister Kabir, saboda haka na amincewa d’ana Auren Jannart!!” bisa tsarin Musulunci mu zamu nemi aurenta*

Tamkar rugugin tsawa asararin samaniya haka Rayyern yaji fitan kalaman Abban nasa, hakanne kuma yasa shi mik’ewa tsaye agigice, hankalinsa amatukar tashe yake Kallon Abban nasa baya ko k’yafta idanunsa, wanda lokaci daya sukayi jajur.

Barrister Kabir kuwa idanunsa ya lumshe, zuciyarsa cike da matsanancin farinciki, hadi da jin dadi marar misaltuwa, saboda tsabar farincikin da yaji acikin zuciyarsa ne kuma, yasa wasu irin hawaye suka gangaro kan fuskarsa.

Hannayensa ya had’e waje guda, tare dayin shiru Dan yama kasa sanin da wacce irin kalmace zai godewa Abban.

Rayyern kuwa da gaba d’aya jikinsa ya d’auki rawa, kansa ya soma girgizawa cikin, wata irin murya dake bayyana gaskiyar abunda ke cikin zuciyarsa yace.

“A’a Abba Dan Allah kada.....”

Saurin dakatar dashi Abban yayi, ta hanyar d’aga masa hannu, mai dauke da alamun dakatarwa, wanda kuma hakan shiya tilastawa Rayyern din yin shiru tare da haɗiye ragowar mgnarsa.

Idanunsa ya rumtse da karfi, tare da taune jajayen labb’ansa, haka yakejin kansa na wani irin juyawa, arayuwarsa kwata kwata bayason jin wata magana da ta shafi mata, Babu mata atsarin rayuwarsa, saboda ya aminta cewa, zai iya rayuwa ko babu Mace a kusa da shi, Domin ko a addinance Aure bai zama dolen dole ba, matuk’ar zaka iya kare kanka daga aikata Zina da fasikanci toh shi bai kawo mace a rayuwarsa ma bare wani abu ya kwashesa.

“Kabamu wuri!!”
Abban ya fad’a atak’aice fuskarsa babu alaman wasa ko wargi.

Idanunsa da sukayi ja sosai ya bud’e ya kalli Abban nasa, saidai kuma yanayin da ya gani akan fuskar Abban nasa, yasa shi juyawa cikin sauri ya nufi stairs din dazai sadashi da part d’insa, ransa amatukar jagule.

Barrister Kabir kuwa ganin Rayyern din ya tafi ne, ya sashi juyowa ga Abba.
Kansa ya d’an sunkuyar fuskarsa dauke da tsananin farinciki yace.

“Tabbas Alhaji Bashir kayimin halacci, kayi min abunda bakowane zaiyi minshi ba, nagode matuka na gode sosai da sosai, nagode Alhaji Allah Ubangiji ya biyaka ya sanya farinciki mai dorewa acikin ahalinka.”

Kai Abban ya d’an girgiza Barrister Kabir din, tare da cewa.

“Bakomai Barrister Kabir ai duk yiwa kaine, Fatana da kuma burina shine Allah yasa hakan shine sanadiyar kawo haske acikin rayuwar da gaba da bayanta ke dauke da duhu da kuma rashin sani.”


Kai Barrister Kabir din ya jinjina, batare kuma daya zurfafa tunaninsa akan maganan da Abban ya fad’a ba ya ci gaba da yi masa godiya.

Haka dai suka dauki kusan 30mn suna maganganu irin tasu ta manya.

Kafun daga bisani Barrister Kabir ya mik’e da niyar tafiya.

Har bakin kofar falon kuwa Abba ya rakosa, ba tare kuma daya tsaya yaga tafiyarsa ba, ya maida kansa cikin falon.

Juyowarsa cikin falon kuwa yayi dai-dai da fitowar Mamy dake cikin kitchine, wanda kuma tun d’azu take tsaye tana sauraran maganganun da suke fad’a.

Kallon Mamyn Abban yayi, Yayinda ita kuwa Mamy keyi mishi Kallon mamaki.

Fuskarta d’auke da damuwa sosai tace.

“Duk naji abunda kuka tattauna Alhaji, amma kwata-kwata banajin hakan dai-dai ne, tayaya zaka amincewa mutanen da baka sansu ba? Tayaya zaka dauk’o wasu daban ka sakosu acikin rayuwar mu? Wayesu mene hadinmu dasu, da har ka amince akan Rayyern ya auri y’arsu?”

Ajiyar zuciya mai k’arfi Abban ya sauk’e,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment