Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ita ma ta d’ago kanta ta kalli Dr. Rayyern MAI-NASARA dinba tace.

“Toh Doctor mu dan koma baya.
Kaba da shawara akan cewar aduk’ar da asibitotin kudi, a tada na Gwamnati, ta hanyar zuba ingantattun likitoti da kuma kayan aiki, To irinku fa masu asibitotin kudi yaya zakuyi kaida ire-iren ka masu privet Hospital's, kodai kuma zaku dawo aiki a asibitotin Gwamnati ne! Ku watsar da naku asibitocin!!?.”
Cikin gamsuwa da yarda da kai yace.
“Kwarai kuwa, saboda ai hakan bawai gazawa bace, Indai muka had’e hannu da Gwamnati dan musamar da ingantaccen kulawa ga al’umma, To mu hakan kamar alkhairi ne agaremu, ba kuma najin hakan zai tauyemu ko ya ragemu da wani abu.”

Ya fad’a atak’aice saboda ya fara gajiya da amsa tambayoyin yarinyar mai shegen baki cai-cai surutu tuni yawun bakinsa sun kafe.
Hannunshi yasa ya ɗan shafa sajenshi har zuwa kan lips ɗinshi sabida ji yayi kamar bakinshin yayi tsawo ne da surutu.

Jannart kuwa, again cikin sanin makamar aikinta tace.

“Amma kamar baka goyon bayan duk wani privet hospital, in na fahimceka.
Kuma naga kaima kana da naka hospital din, wanda kuma bana gwamnati bane, ya akayi to hakan ta kasance? meyasa baka had’a hannu da Gwamnatinba!? kun ingata Koda asibiti daya ne!!!?”.

Wannan Tambayar ta saka duk magautan
Dr. Rayyern Mai-nasara dake Kallon tv suka saki Murmushin mugunta, saboda atunaninsu yarinyar ta kawosa makura inda bazai iya amsa tambayoyin nata ba Alhaji Idi Saleh Dakata kuwa.
Saida yaji tamkar ya shiga TV ya goya ɗiyar tasa Jannart, sai yakeji kamar dan su tayi mishi wanna tambayar dan ta kure musushi.
Dr Lukman kuwa hannunshi ya dunƙule tare da jinjinawa Jannart harda yimata alamar kiss dan masifar daɗi.

Ita kuwa Jannart batama san sunayi ba, kuma bada wata manufa tayi tambayarba sai dan dacewar hakan tunda tasan yanada asibitin.

Shikuwa Rayyern ko ajikinsa baiji wani abu ajikinsa dangane da tambayar da Jannart din tayi masa ba, hasalima Dan gyara zamansa yayi, cikin kuma kwarin guiwan da ako yaushe yake tare dashi yace.
“Banyi karatun likita Dan yin aiki akarkashin wani ba, asali Tubalin karatuna shine Idan na kammala na raya asibitin, dake gine tun kan zuwata duniya.
saboda amfanar al’umma, bawai iya mai kudi ba kawai harda talakawa, saboda babu wani wanda, asibitin Mai-nasara Hospital yafi karfin zuwansa, koda kuwa bashi da karfi, Mai-nasara Hospital muna da foundation na taimakawa marassa karfi dashi mukeyin dukkan taimakon daya dace, sannan kuma Mai-nasara Hospital bawai irin asibitotin nan ne da kowa ya sani ba, Ina da confidence akan Hospital dina, ako ina kuma zan fada batare dajin na fadi ba daidai ba!!!.”

Kai Jannart ta jinjina, saboda ayanzu kam amatsayinta na y’ar jarida ta gamsu da duk kalaman mutumin, musamman da ta fahimci with full confidence yake magana, ba irin na wasu mutanen ba, da mafi yawancin maganansu Kame kame da kuma k’aryane.
Domin sometimes ma suna fad’an karyane Dan su kare kawunansu daga titsen yan jarida.

Daga can gefe kuwa, Asiya ce dake tsaye take ta aikin bankawa Jannart d’in Harara.
Yayinda takejin wani irin kuna da radadi acikin zuciyarta, Lallai Tabbas taso ace itace ta samu wannan damar, taso ace yau itace akan stage din tare da mutumin da kyau, nutsuwa da kuma haibarsa suka matuk’ar tafiya da hankalin ta, kana kuma mutumin da take ganin cewa, samun daman magana dashi ma wani matakin nasara ne.

Kamar kuwa yanda Asiya ke jin tukukin bakinciki acikin zuciyarta, haka ma Dr Lukman, yakejin kamar ya shiga cikin tv’n ya shak’o wuyar Dr Rayyern.
Abunda yasan bazai taba samun daman aikatashi ba a gaske kenan.

Kallonsa ya mayar gasu Alhaji Idi Sale Dakata, cikin takaici yace.

“Lallai wannan Dr Rayyern din shege ne, ko ta Ina so yake ya tauyeni, bakinsa baya tab’a mutuwa, kowacce tambaya akwai amsarta acikin kansa.”

Murmushin daya fi kuka ciwo Alhaji Idi Sale Dakata’n yayi, cikin takaicin daya lullub’e zuciyarsa yace.

“Nan kusa wannan bakin nasa bazai sake motsawa ba, wannan alk’awari ne na daukawa kaina.”

Murmushin Jin dadi Dr Lukman da kuma Alhaji Abdu Tababa sukayi, saboda sanin hali irin na Alhaji Idi Sale Dakata da sukayi, Domin sunsan duk abunda yace zai aikata saiya aikata Tabbas.

Ab’angaren Gidansu Rayyern kuwa, Abba Mamy, Ramadan da kuma Riyyam-nsra ne zaune afalo suna kallon shirin, gaba daya sun bada hankalinsu akan shirin, musamman ma Abba, da tunaninsa ya rabu izuwa wani waje na daban.
Kallon Rayyern da kuma yarinyar da takeyiwa Rayyern din tambayoyi yake baya ko k’yaftawa, Yayinda acikin zuciyarsa yakejin wani irin abu na daban.

Su Ramadan kuwa Hamman nasu suka tsurawa ido,suna mai jinjina kawunansu saboda irin amsoshin da Hamman nasu ke bayarwa, yana matukar ratsa zuciyarsu, acikin zuciyarsu kuwa babu wanda bai yaba da irin kyawun yarinyar da takeyiwa Rayyern din tambayoyi ba.

Jannart kuwa, akaro na barkatai ta d’ago ta kalli camera’s din dake haska su, mike din dake gefenta ta gyara, tare da cewa.

“Kamar dai yanda kuka sani, ayanzu zamu bud’e layukan wayoyinmu saboda, masu kira.
Dan fadar ra’ayoyinsu da tambaya, ga numbar layin namu kamar haka...
Tana gama fad’an numbers dinne kuma ta kunna wata waya mai kaman telephone dake aje agabansu, kan wani had’add’en table.

Aikuwa kaman jira ake sukunna layin saiga kiraye-kiraye suna shigowa.
Wanda manyan mutane-ne suke kiran.

Numfashi ta ɗan fesar tare da gyara zamanta.
Kana ta ɗan kalli wayar da wani kiran ya kuma shigowa tun kan ta ajiyeta.
Picking call din Jannart tayi, tare kuma da latsawa tasa wayar a hands free.


Cikin zazzakar muryarta tace.

“Assalamu Alaekum.”

Daga can b’angaren aka amsa mata, da murya irin ta manyan mutane.

Jin hakanne kuma yasa ta cewa.

“Barka da shigowa filin bakon mako.”

“Yauwa Barka dai”.
Aka faɗa daga daya sashin cikin girma.
Ita kuwa Jannart lumshe idonta tayi tare da cewa.
“Ko zamu iya sanin waye akan layi?.”

“Sunana Alhaji Abubakar Ginsau S.A protocol na gwamna, nakira ne kuma Domin na jinjinawa babban Bak’o DR. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, agame da maganganu masu amfani daya fad’a, Insha Allahu kuma maganan zata isa ga kunnen way’anda ya kamata suji, sannan muna godiya k’warai matuk’a, da irin shawarwarin daya bayar.”

Kai Jannart ta jinjina, tare da dan satan Kallon Dr Rayyern din, wanda ya kauda kansa gefe, kamar baiji ana yabonsa ba.

“Girman kai rawanin tsiya.”
Tafad’a acikin zuciyarta, Yayinda afili kuwa cewa tayi.

“To S.A protocol muma godiya muke sosai, sannan bakon mu Dakta shima yana godiya.”

Daga haka kuwa kiran S.A din ya katse, wani kiran kuma ya sake shigowa.

Cikin tashin hankali Dr Lukman ya mik’e tsaye, tare dasa hannunsa ya dafe kansa, zuciyarsa cike da takaici yace.

“Lallai wannan yaron ya shallake duk wani tunani na, ba a banza ba ake kiransa da Mai-nasara ba, tunda gashi yayi sara akan gab’a, daga maganansa har S.A da kansa ya kira, ya kuma shaida cewa maganar zata tafi har wajen governor, wannan wanne irin Dan iskan yaro ne? Mai sa'a”.
Cikin tsananin takaici tsana Alhaji Idi Saleh Dakata ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ai yamafi Dan iska wannan yaron da kake gani Dr Lukman, shegen yaro ne kwance-kwance yake mana, da sannu Idan bamu tashi ba, duk sai yabi ya sare mana duk wani reshen mu, b’arna babba yake aikata mana, batare da ko damuwa da hakan yayi ba, Tabbas kuma ya kafu iya kafuwa, da wayannan kalaman nasa masu ratsa zuciya yake yaudarar mutane, waishi ala dole mai tausayin talakawa, yana abu tamkar Dan siyasan da yake barar neman kujerar takara, hmmmm Lallai zanyi maganin wannan yaron, zan kawar dashi kamar yanda na kawar da way’anda suka fishi tsauri a baya.”

Alhaji Idi Sale Dakata ya ƙare mgnar yana me sakin zazzafan numfashin takaici.

Yayinda Alhaji Abdu Tababa kuwa yace.

“Lallai kawar dashi daga doron k’asa shine hanya mafi a’ala, Idan ba haka ba kuwa duk sai ya fito damu waje cikin rana daga gidajenmu.”

“Hakan bazaiyi wuba kuwa.”
Alhaji Idi Sale’n ya fad’a yana me mikewa tsaye.

Yayinda acan gidan su Rayyern kuwa, har yanzu su Abba basu matsa daga gun tv’n ba.

Sunanan zaune kowannensu dauke da farincikin, irin nasaran da Rayyern din ke samu.

Haka ma agidan Barrister Kabir har yanzu shima yana zaune agaban tv’nsa.

Dai-dai lokacin da ake cigaba da haska shirinne kuma, Aunty Dijat ta fito daga daki.

Zama tayi akusa da mijinnata tare da soma kokarin had’a masa coffee.

Kallon ta Barrister Kabir din yayi, kana cikin tausasa murya yace.

“Dijat kalli tv kiga, Jannart da matashin saurayin nan dake zaune agefenta”.

Da sauri ta miƙa mishi cup ɗin tare da zubawa tv ido tare da cewa.
“Masha Allah”.

Kurban coffee'n yayi tare da cewa.
“Sundace ko?.”

Ware ido Aunty Dijat din tayi ta kalli tv’n, dai-dai lokacin kuwa aka sake matso da fuskokin Jannart dana Rayyern din kusa.

“Masha Allah, ai kuwa Abban Hafeez matukar dacewa ma sukayi, kyau da kyau kenan.”

Murmushi Barrister Kabir din yayi, tare da gyara zamansa a takaice yace.

“Shine mijin dana zab’a mata, kuma shine wanda zata aura amma batare da ta sani ba.”

Ya fad’a yana me karb’an coffee din da aka had’asa masa.

Idanu Aunty Dijat ta d’an zaro waje, cike da tsananin mamaki hadi da zallar farinciki tace.

“Allahu Akhbar, Lallai girman Allah iko da buwayarsa tana da yawa, Masha Allah Lallai Jannart ta dace da hazik’in Namiji kuma jarumi, mai dauke da nagarta, Tabbas ka cika Uba nagari, ai kuwa zamusha biki yaushe ne Auren?”

Murmushi Abban yayi, tare da girgiza mata Kai, Ahankali kuma yace.

“A’a bayanzu zan gaya miki ba, abun namu sirrine.”



*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA

By
*GARKUWAR FULANI*




Murmushin Jin dadi Aunty Dijat din tayi, kana cikin sakin fuska tace.

“Alhamdulillah nidai ko yaushene ma ina jira.”

Barrister Kabir dinma murmushi yayi, batare kuma daya sake cewa komai ba, ya cigaba da shan coffee d’insa.

Acan cikin tashar kuwa, zuwa yanzu kira na 15 kenan Jannart din ta amsa, wanda kuma daga kan kira na 15 dinne ta katse layin gaba d’aya, tare da d’agowa ta kalli cameras din dake jere agabansu.

“To masu kallonmu laifin dadi dai ance karewa, Domin naga lokaci yana daga mana hannu, saboda haka duka duka anan muka kawo k’arshen shirin namu Na Bak’on Mako, sai kuma wani sati Idan mai kowa mai komai ya kaimu, Insha Allah zamu sake zuwar muku da wani bak’on na musamman.”

Dan Juyowa tayi ta kalli Rayyern dake zaune, Cikin kuma sakin fuska kamar yanda ta sabayiwa kowa tace.


“Doctor ayiwa masu kallo da sauraronmu sallama.”

“Assalamu Alaikum.”
Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din ya fad’a atausashe, saboda yasan izuwa yanzu duk su Abbansa suna kallonsa.

Jannart kuwa juyowa tayi ta fuskanci Camera hadi da cewa.

“To masu kallonmu duka duka anan muka kawo k’arshen shirin namu, tare da babban bak’onmu”.
Ta ƙare mgnar da juyowa tana kallon Dr Rayyern.
Numfashi ya ɗan fesar tare da cewa.
“Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara”.

Gyara zamanta tayi tare da cewa.
“Sai kuma ni dana shirya na kuma gabatar JANNART IDI SALE DAKATA. Nake, mana fatan mu hade awani sati Idan Allah ya kaimu a huta gajiya.”

Cuttt haka masu d’aukan shirin suka katse tare da kashe cameras dinsu.

Dai-dai lokacin ne Kuma anan gidansu Rayyern din Zuciyar Abba tayi wani irin bugawa, saboda sunan Yarinyar da yaji acikin kunnuwansa.

“Jannart Idi Sale Dakata!!”.
Abba ya maimaita sunan acikin zuciyarsa, cikin sauri kuma ya d’ago da kansa ya kalli Mamy, wacce ita dinma shi take kallo, fuskarta dauke da tsananin mamaki.

Atare kuma suka sake maida kallonsu ga tv,n.

“Idan har sunan da yarinyar ta fad’a shine sunanta na gaskiya, To Lallai kuwa, wannan itace yarinyar da Barrister Kabir yazo musu da maganarta.”

Abban ya fad’i haka azuciyarsa, fuskarsa cike da tsananin mamaki, hadi da tu’ajjudin faruwar hakan.

Tuno wani abu da yayi ne kuma yasa Lokaci daya ya saki wani irin murmushi, mai dauke da tsananin jin dadi, hadi da cin nasara.

Tabbas ayanzu ya sake gaskatawa, cewar Nesa tazo ta kusa.

Acan TV station din kuwa Zumbur haka Dr Rayyern din ya mik’e tsaye, wanda hakan yasa cikin sauri MD da kuma sauran assistance managing director hadi da manyan masu muk’amai na tashan suka nufo wajen Rayyern din kaitsaye, hannayensu suka dinga mik’a masa daya bayan daya suna gaisawa cikin mutuntaka.

Inda MD da farinciki yasa bakinsa kasa rufuwa yace.

“Mungode Kwarai Dr. Rayyern, Allah Ubangiji yasa kafi haka, nida sauran ma’aikatan wannan tasha, muna godiya agareka, daka samu daman zuwa wannan tasha.
Tabbas zuwanka ya sake daga darajar tasharmu.”

Yar sauk’ak’ekk’iyar Murmushi kawai yayiwa MD’n, Yayinda MD kuwa yasa a daukowa Dr. Rayyern din kyauta ta musamman, wanda sukayi dan nuna godiyarsu agaresa.

Salman, Aysha Lawal da kuma Aunty Fauziy D Sulaiman dake gefe kuwa, hannayensu suka d’agawa Jannart alaman jinjina, kowannensu fuskarsa cike da farincikin, irin nasaran da Jannart din ta samu, Domin kuwa ta kafa tarihin da akab gidan television’s din dake Nigeria babu wanda ya tab’a kafawa.
Ta kawo musu babban hazikin Dan kasuwa kuma Doctor, mutumin da kowa yake fatan ganinsa, yau gashi Jannart din ta kawosa ta kuma bayyanawa duniya fuskarsa, daya jima yana b’oyeta.

Murmushi Jannart din tayi musu, tare kuma da k’arasowa ta kalli Salman, wanda azahirance yana cikin tsananin farinciki, akasin hakan kuwa, shine Sam bayajin dadin zuciyarsa, saboda tun zaman Jannart da kuma Dr. Rayyern din daya gani awaje daya, yaji zuciyarsa ta karye, badan komai ba kuwa saidan tsananin matching din da yaga sunyi, sosai suka haska tamkar wasu taurari, sai kuma ayanzun ya sake tabbatarwa da kansa, cewar kwata-kwata ma Jannart Dakata ba sa’ar sa bace, Jannart matar manyan mutane ce.
Kana kuma Jannart zara ce acikin taurari, furta wani abu daya shafi so agareta, kuwa tamkar karambani ne, saboda ya sani bashi da wannan matsayin.

Haka dai jikinsa adan sanyaye ya juya suka rufawa su MD din baya, wanda tuni sun nufi hanyar waje, Dan raka Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara mota.

Cikin masu rakiyan kuwa harda Asiya, wacce takejin kamar ta fashe da kuka, ko tasa ihu.
Badan komai ba kuwa, saidan ta samu ko kallo daya ne Dr. Rayyern din yayi mata.

Jannart kuwa kaitsaye Office dinsu ta wuce, batare da tabi yan rakiyar ba, Sam ita rakasa ma baya gabanta, hasalima mamaki take akan yanda taga, y’an Office din nasu suna karramasa, Tabbas Koda ga wahalan da tasha wajen nemansa, tasan cewar shidin babban mutum ne.

D’an tab’e bakinta tayi alokaci da ta samu waje ta zauna.

Hakanan takejin zuciyarta wasai, tamkar an zare mata wani mashi dake sukanta.

“Alhamdulillah Allah, Kai katsaramin komai, yanzu bazan rasa aikina ba, bana kuma da wata fargaba, Thanks for everything Allah.”

Ta fad’i hakan abayyane Cikin kuma tsananin farinciki, dajin dadi.
Saboda duk wata fargabanta yanzu ya yaye.

Acan compound din tv station din kuwa, har wajen mota su MD suka rako Dr. Rayyern, bayan sun bashi kyautar karramawa.

Kasancewar kuma tun kafun su isa, Hadi'nsa ya bud’e masa murfin motar tasa ne, hakan yasa yana zuwa batare da wani b’ata lokaci ba ya shiga ya zauna.

Still harya rufe murfin motar kuma godiya su MD sukeyi masa, tare dayi masa fatan sauk’a lafiya.

Anutse kuwa Hadi yaja motar suka fice daga cikin gidan tv’n.

Fuska Asiya ta had’e tamkar zata had’iyi zuciyarta haka takeji.

Lallai tayi takaicin wannan ranan, saboda ko kallo daya bata samu daga wajen Dr. Rayyern din ba, hasali mai irin halittarta ma baisan tana wajen ba.

Dan Kallon kanta tayi, can cikin zuciyarta kuma taja tsaki, tare da cewa.

“Tayaya ma zai kalleni, tunda akwai irin waccar mayyar aduniya, natsaneki wallahi Jannart natsani ma Koda ganinki, saboda ke ne zaman office dinnan ya fara yimin kunci, kinzo kin hanani sakat, wai kawai saboda kina da kyau, mcheewww.”

Tak’are maganar nata da jan tsaki tare da juyawa ta koma Cikin office din, dan zuwa yanzu ita kad’ai aka bari awajen.

Acan cikin Office din kuwa, MD dakansa ya shigo cikin Office din su Jannart din, tare da bud’e hannayensa ya soma tafa mata.

Aikuwa Ganin haka yasa duk sauran ma’aikatan suma bud’e hannayensu suka soma tafa mata.

Cike da jinjina hadi da yaba k’wazonta MD yace.

“Congratulation Jannart, Lallai kin cika hazikar yar jarida, na kuma jinjinawa kwazonki, Tabbas samun irinki acikin aikin jarida abune mai kyau, ayau ta sanadiyarki tasharmu ta sake daukaka, kin shammace mu Kwarai, dole ne mu baki lambar yabo, zaku ma muyi miki karramawa ta musamman.”

“Kwarai kuwa Jannart hakika kinyi Namijin kokari, Tabbas kin cika hazikar Mace mai kishi da kuma son aikinta congratulations.”

Cewar Aunty Fauziya D Sulaiman.

Jannart din kuwa murmushin daya bayyana kyawawan hakwaranta tayi, cikin tsananin jin dadi tace.

“Congratulations to you all my colleagues, Domin duk wannan nasaran nasa meta ne da k’arfafawar guiwanku, musamman Salman, Thank you so much Salman.”

Murmushin Jin dadi duk sukayi, Yayinda Salman kuwa ya sunkuyar da kansa kasa yana murmushi.

Asiya dake gefe kuwa ji take kaman tayi hauka, tsabar k’unci takaici da kuma bak’in Cikin daya cika zuciyarta.

Haka dai suka ci gaba da tattaunawa atsakaninsu, Yayinda fuskar kowannensu ke dauke da tsananin farin ciki.
Amma banda na Asiya da har hawayen takaici saida suka tara.

MD kuwa yau din da kansa yasa akayi musu order’n delicious food, tare da kayan drinks.

Anan cikin babban falon da suke ajiye baki, suka gudanar da d’an kwarya kwaryan party.

Inda kuma sukayiwa Jannart din tanadin Karin matsa yi na musamman.

Bayan sun gama yar kwarya kwaryan Partyn nasu ne kuma ta dau Jakarta Kai tsaye ta wuce, gida zuciyarta cike da tsananin farinciki.

Yayinda daga can b’angaren Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara kuwa, daga tv station din kaitsaye gidansu ya nufa.

Suna isa bakin gate din kuwa Baba Hadi ya danna horn, cikin sauri da kuma azama Baba Maud’o ya karaso ya bude musu gate din, direct Baba Hadi ya tura motar cikin gida, tare da dai-dai-ta parking dinta a parking space.

Ahankali Rayyern din ya bud’e motar ya fito,
Kana ya juya ya nufi wurin da Baba Maud’o yake tare da ɗan longoɓar da kai alaman gaisuwa.
Murmushi Baba Mauɗo yayi tare da mishi sannu. kafun kaitsaye ya nufi babban falon gidan.

Inda Mamy da Abba dasu Ramadan ke zaune.

Shigowarsa cikin falonne kuma yasa duk suka d’ago Kai suka kalleshi, Riyyam-nsra ne ya taso da d’an hanzari ya rungumeshi, tare da cewa.

“Gaskiya ko Hamma Rayyern kaina musamman ne, ka iya amsa duk wata tambaya da akayi Ma.”

Kansa kawai ya Dan jinjina saboda duk ji yakeyi kansa a gajiye, karasa shigowa cikin falon yayi, tare da yiwa Abba da Mamy sannu da gida.

“Yauwa Rayyern sannu da dawowa.”
Mamy ta amsa masa, Yayinda Abba kuwa Da Kai ya amsa masa.

“Hamma Rayyern congratulation.” Ramadan ya fad’a k’asa k’asa yayinda yake Dan danne dariyarsa, badon komai ba kuma saidan sanin halin Yayan nasa da yayi, kwata-kwata baya son yawan magana amma kuma yau gashi wata tasashi yayi ta magantuwa.

Da kai kawai Rayyern din ya amsa masa, batare daya zauna acikinsu ba kuma kaitsaye ya wuce part d’insa.

Wanka yayi tare da dauro alwalan sallan magriba, bayan ya kimtsa kansa acikin wasu kaya marar nauyi ne kuma, ya fito inda dukansu suka had’a hanya wajen zuwa masallaci.

Koda sukaje masallacin kuwa kamar Koda yaushe basu dawo ba saida aka Sallame sallan Isha.

Suna dawowa gidan kuwa suka samu Mamy ta had’e musu lafiyayyen dinner, hakan yasa duk suka k’arasa kan dining table din suka zazzauna.

Yau din kuma Riyyam-nsra ne da kansa ya amshi Mamy wajen yin saving dinsu, shida kansa ya zubawa kowa abincin banda Abba da Mamy ta zuba mishi nashi, sannan da kansa ya had’awa Hamma Rayyern din tea.

Bayan ya kammala had’a musu ne kuma, kowa ya soma cin abincinsa, anutse Abba ya d’ago da kansa ya kalli Rayyern cikin jinjina da kuma ya bawa yace.

“Tabbas hirar da akayi da kai yau, tayi armashi da kuma ma’ana, sannan shawarwarin daka bayar shawara ne masu kyau, gaskiya na jinjina maka,”.
Sai kuma ya ɗan tsagaita kana ya ɗan kalleshi tare daci gaba da cewa. “Amma da kashawarce ni kafun hakan, To fa da bazakaje ba.”

Zazzafan tea din dake bakinsa ya had’iya, kana cikin yin kasa dakai yace.

“Kayi hakuri Abba nima banaje Dan son raina bane, naje ne kawai saboda nayi musu alk’awari, sannan banason wanda aka bawa kwangilar nema na din ya rasa aikinsa, kamar yanda manyansa suka bashi zab’i.”

Kai Abban ya jinjina, batare kuma daya ja zancen yayi tsawo ba yace.

“Shikenan To Rayyern Allah ya taimaka ya tsare min kai.”

Da Ameen duk suka amsa.

Bayan sun kammala cin abincinne kuma, kaitsaye Rayyern din ya wuce daki’n sa.

Yayinda Ramadan da Riyyam kuwa suka dawo Cikin falon suka ci gaba da hirararsu, daga karshe ma game suka had’a, suka soma yi.

Ganin hakanne kuma yasa Abba da Mamy wucewa sashinsu.

Rayyern kuwa yana shiga dakinnasa kwanciya yayi, Cikin mintuna kad’an bacci yayi nasaran daukarsa.

Acan falon kasa kuwa Ramadan da Riyyam, duk kowannensu saman kujera ya d’ale ya kwanta, su kansu ba zasu iya sanin tayaya nema bacci ya kwashesu ba, kowannensu da abun buga game din ahannunsa, haka sukayi bacci kasancewar dare ya nisa.

A sashin Jannart kuwa yau tun 9 tayi baccinta mai cike da nutsuwa, Yayinda takejin zuciyarta wasai babu sauran wani fargaba.


Washegari.

Friday.

Tun tashinsa karfe 7 ya gama shirya kansa, saidai shigarsa ta yaudin ta banbanta dana kullum.

saboda wani riga da wando mai Taushin gaske ya saka ajikinsa, sabanin suit daya saba sakawa akowacce rana.

Sosai kayan Yayi masa kyau, musamman daya daura boyfriend jacket mai kyau akan kayan.
Wasu bakaken shoe masu tsada da watch ya daura a tsintsiyar hannunsa .

Bayan ya gama kimtsa kannasa ne kuma, ya dauki wayarsa tare da duba sakonnin da suke ta shigo masa ta Twitter, saboda yanda duniyat Twitter din ta Dinke da hotunansa, gaba daya shi kawai ake watsawa, da kuma bayani akan hirar da akayi dashi.

Kashe data dinnasa yayi, tare da juyawa ya nufi k’asa kaitsaye.

Anan cikin falon ya samu su Abba, harma da Riyyam nsra wanda yake ta hamma da alama bacci bai ishesa ba.

Dan Koda asuba ma Abba ne daya fito
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment