Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Domin shi sai yanzu ne ma yakejin haushin yarinyar da aketa kira da Jannart din.

Mamy kuwa kaitsaye kitchine ta nufa, bayan ta d’auki abincinne kuma ta wuce sashin Jannart.

Jannart kuwa dai-dai lokacin ta fito daga wanka, bayan tayi wankanne kuma ta sake maida doguwar rigar da ta cire.

Tana tsaka da maida hijab dinta ne kuma, Mamy ta shigo hannunta dauke da cup da kuma plate din indomei.

Akan wani Dan stull Mamy ta ajiye cup da plate din, tare da duban Jannart din Cikin kulawa tace.

“Yauwa Jannart kinfito ko, ga abinci nan kici, sai kisha magani saboda naji jikinki akwai zafin zazzab’i.”

Kai Jannart din ta Dan sunkuyar kasa, kana aladabce tace.

“Mamy nakoshi.”

“A’a kam Jannart, saboda kefa na shiga kitchine na dafa abincin nan, saboda haka ki zauna kici, kada kiyimin gardama kinji, koso kikeyi na barki haka, Allah ya kama mu kefa amanace awajen mu, zo maza ki zauna kici.”

Mamyn ta fad’i haka cikin matukar kulawa.

Wanda hakanne kuma yasa Jannart din karasowa, ta zauna akan lallausan sofan dake malale agaban gadon.

Abincin Mamy ta ajiye mata, Ahankali kuma ta soma tsakuran abincin tana kaiwa bakinta.

Kasancewar kuma da gaske bata wani jin yunwa sosai ne, yasa bata wani ci abincin sosai ba, saidai tea din da Tasha har fiye da rabin kofin.

Dan matsar da plate din abincin tayi gefe, tare da yiwa Mamy alama akan ta koshi.

Hakanne ko yasa Mamy b’are maganin ta bata tasha.

“Ki kwanta to ki huta, Dan Allah karki sakeyin kuka kinji Jannart, kinga shine ya haddasa miki wannan zazzab’in.”
Mamy ta fadi haka tana me daukan plate da cup din abincin.

“To Mamy.” Jannart din ta fad’a, tana me mikewa tsaye ta haura saman gadon ta kwanta.

Murmushi Mamy tayi saboda a iya yaudin kawai ta yada da hankali,da kuma biyayyar da yarinyar take dashi.
Cikin kula tace.
“A'a Jannart tashi kiyi addu’a kinji, kada bacci ya daukeki batare da kinyi addu’a ba.”

Aikuwa da d’an hanzari Jannart din ta tashi zaune, hannayenta ta hade waje guda, falaq,suratul nass, da kuma suratul Iqlas, k’afa uku uku, kursiyu da amarasulu sai kuma Hasbiyallahu la’ilaha illahuwa, alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim, k’afa 7, sai kuma suratul Khafirun kafa uku shima.

Bayan ta shafa ne kuma ta koma ta kwanta.

Mamy kuwa cike da farincikin samun ya kuma surkuwa ta gari, ta ragewa Jannart gaba daya hasken wutan dake dakin.
Bayan sunyiwa juna saida safe ne kuma Mamyn ta juya ta fita.

Bayan ta maida plate and cup din kitchine ne kuma, kaitsaye Mamyn dakin Abba ta nufa.

Koda taje Zaune ta sameshi akan gado.

Zama ita dinma tayi agefensa, kana cikin tausasa murya tace.

“Tabbas Rayyern ya samu mata, yayi dace da yarinyar arziki mai ladabi da biyayya”.
Cikin jin daɗi Abba ya juyi ya fuskanceta yana mai jinjina kai alamun gamsuwa.
Ita kuwa Mamy cikin girmamawa tace.
“Toh amma Alhaji meyasa ka umarceni dana kaita wancan dakin, bayan ganan sashin Rayyern.”

Murmushi Abba yayi, tare da maida kallonsa gareta yace.

“Nace ki kaita wancan part dinne Saboda, sai anyi gyara a b’angaren Rayyern kafun ta koma can.
Kadafa ki manta fa amaryace, Koda cewar auren ba dan shiri bane, amma yana da kyau a inganta mata komai nata”.
Da sauri tace.
“Eh gsky hakane kam”.
Ɗan gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“Sannan kuma baki ga dan naki bahagon yaro bane, kwata-kwata na kasa gane inda ya dosa, Sam bai fahimci abunda muke nuna masa ba, atakaicema gani yake kamar takurasa mukeson yi.
Bayan haka kuma ganan Ramadan shima yana saman.
To dole yanzu zai dawo k’asa, kafun adai-dai-ta komai ta koma side din nasu.”
Kai Mamy ta jinjina cike da gamsuwa.
Kasancewar ta gaji ne kuma yasa ta zame ta kwanta gefensa.

Acan b’angaren Rayyern kuwa, akwance kawai yake amma duk zuciyarsa babu dadi.
Ak’alla saida ya kwashe sama da 50mn kafun bacci b’arawo ya iya satan shi.

Jannart kuwa tun fitan Mamy ta lumshe idanunta.
Yayinda tunani kala-kala ke yawo aciki kwakwalwarta, akaro na farko kenan tun tashinta izuwa yanzu, da zata kwana awani gida sab’anin nasu dan ko gidan Barrister Kabir Daddy bai taɓa barin ta ta kwana ba sai kuma asibiti.

Tunani ne fal zuciyarta, saidai kuma kamar yanda tayiwa Mamy al'ƙawari, batayi kuka ba, da taimakon maganin zazzabin da tasha ne kuma bacci ya dauketa.

Yayinda acan gidan Alhaji Idi Sale Dakata kuwa, kowa ya kwana sharbar bacci batare da tunanin Jannart bata cikin gidan ba, Domin wasu daga cikin mutanen gidan har da gwartin su, saidai banda Junaid Wanda ya taso sad’ab sad’ab ya nufi d’akin Jannart din, saboda gaba daya ya kasa bacci.
Daya rufe idanunsa Surar Jannart dinne keyi masa gizo, shiyasa yazo domin rage zafin abunda ke damunsa.

Koda ya karasa kofar dakin nata, kaitsaye ya tura kansa ciki.

Saidai kuma rashin ganinta da baiyi acikin dakinba, yasa shi cije labbansa, lokaci daya kuma ya raya cewar ko tana toilet Murmushin mugunta yayi, tare da nufan toilet din kaitsaye.

Tura kofar yayi batare daya jira komai ba kuma ya soma zare belt din wandonsa, saboda ya gama targetting yana ganinta zai Afka mata, amma kuma saidai meye?

Wayam haka yaga toilet din, ba alaman ma anshigesa tsawon sama da 1hour.

Tsuka yaja tare da fitowa, yana kwafa haka ya fice daga cikin dakin, cike da takaicin rasa damar da yayi.

Badan ransa yaso ba haka ya koma sashinsa ya kwanta a tunaninsa ko tana dakin Mom.

*Washegari*

8:00 am dai-dai Mom ta gama kammala musu breakfast, wanda kuma har zuwa tsawon wannan lokacin ba taga Jannart ta fito ba.

Hakanne kuwa yasa bayan ta gama setting dining table, kaitsaye tatafi izuwa dakin Jannart din.

Koda ta isa bakin kofar knocking ta fara yi, har na tsawon mintuna 2 kuwa bataji ko motsin za’a bud’e kofar ba, hakan yasa Ahankali ta tura kofar d’akin, tare da kutsa kanta ciki.

“Jannart! Jannart!!” Momyn ta kira sunan Jannart din, saboda rashin ganinta da tayi adakin.

Jin shiru ne kuma yasa Momyn juyawa ta fita, saboda atunaninta ko Jannart din tana cikin toilet ne.

Kaitsaye dining table ta dawo, tana zuwa kuwa, Daddy da Abdull suma suka fito suka zauna.

Momyn ce tayi saving dinsu, tana cikin saving dinnasu ne kuma, Junaid ya shigo cikin falon, yana fito, daga shi kuma sai t shirt da gajeren Wando.

K’arasowa dining table din yayi, batare daya gaisar da kowanne daga cikinsu ba, cikin iskancinsa irin na wasu masifaffun sojoji yace.

“Ina Jannart?”

D’agowa duk sukayi suka kalleshi.

Sanin halin rashin mutumcinsa ne kuma yasa Mom tace.

“Yanzu na dawo daga dakinta banganta ba, tun safe kuma bata sauko ba, amma Ina tunanin ko tana toilet ne.”

“Bawani bata gidan nanne ma gaba d’aya, y’ar iskar yarinya, jiya ma da dare ai naje dakinta amma bansa meta ba, wallahi Idan na kamata sainaci Uwarta.”

Baki Momy ta tab’e, tare da kallonsa cikin yanayin mamaki tace.

“To kai meya kaika dakinta da dare?.”

“Oho bansani ba, munafurci kawai.”

Junaid din ya fad’a kaitsaye, babu wani shakka ko shayi.

Duk da Abba yana jinsa kuwa, haka yayi shiru bai tanka masa ba, saima Kallon Momyn da yayi, yace.

“Kije ki duba toilet din, ko me ta keyi kice mata ta bari, injini tazo mu yi breakfast.”

“To.” Momyn tace, tare da juyawa tasake nufan dakin Jannart din.

Tana zuwa ta tura kofar, but still Jannart bata ciki, da d’an mamaki Momy ta karasa jikin kofar toilet din, tare da kasa kumnenta.
Waiko zataji karar ruwa, saidai bataji komai ba, hakan yasa Momyn ta tura kofar tana me kiran sunan Jannart.

Saidai meye, idanunta ba abunda suka gane mata, domin kuwa Jannart bata cikin toilet din.

Mamaki ne ya kama Momyn, saboda Sam bata taba tunanin Jannart bata cikin toilet din ba.

Juyawa tayi cikin sauri ya dawo falo.


“Alhaji Jannart fa batanan, na duba bata dakinta kuma bata bayan gida.”

Cak Alhaji Idi Sale Dakata yatsaida duk wani abu da yakeyi, cikin yanayin mamaki had’i da razana yace.

“Bangane mekike cewa ba, wannan wani irin maganar banza ce, tayaya zakice bata dakinta kuma bata bayan gida, wannan gashi anan dinma batanan, To ko tana dakinki ne?”

Kai Momy ta girgiza da sauri, tare da cewa.

“A'a wallahi bata dakina, tun Safe ma banga sauk’owarta ba, zaiyi wahala ace ma tana dakina.”

“Kije ki duba ta yanzu.”

Dadyn ya fada cikin bacin rai.

Hakan yasa da sauri Momyn ta juya zuwa dakinta, kamar yanda ta zata kuwa hakanne, domin Jannart bata cikin dakinta.

Dawowa falon ta sakeyi, tare da Kallon Daddyn tace.

“Alhaji Jannart fa bata dakina.”

Idanu Daddyn ya zazzaro waje, Abdull kuwa da mamamki yace.

“Ha’a To Ina Aunty Jannart ta shiga ita da yawo ma bayinsa takeyi ba, amma bari na duba compound ko Garden ko tafita shan iska.”

Yana gama fadin hakan ya mik’e ya fita.

Kaitsaye garden dinsu ya nufa amma baiganta ba, hakan yasa ya dawo, fuskarsa dauke da damuwa yace.

“Daddy banganta ba.”

Kwafa Junaid yayi, tare dasa hannayensa a aljihun wandonsa, cikin bakar muguntan dake cinsa yace.

“Nifa Tunjiya na fada muku banganta ba, maybe yawon iskancinta ma ta tafi, dama ai ta saba tafiya kwanan gida.
Rijiyace kowanni dan iska yana iya zuwa ya zira gugansa yaja ruwa son ransa.”

Idanu Momy ta rumtse saboda har acikin zuciyarta bataji dadin bakar maganar da Junaid din ya fada akan Jannart d’in ba.

Daddy kuwa Wayarsa ya zaro daga cikin aljihun rigarsa, tare da lalub’o numbern Jannart din ya danna mata kira.

The first time akace masa wayan nata, is switch off, da Mamaki Daddy ya sake dialing airtel number dinta, still switch off, wani irin bugawa yaji kirjinsa yayi, cikin sauri yace.

“Junaid je maza ka duba side dina, watakila ko taje gaisheni ne.”

Juyawa Junaid din yayi, Inda kaitsaye ya nufi side din Daddyn, Koda ya karasa baiganta ba, har cikin bedroom na Dad din ya shiga amma babu ko alamarta.

Dawowa yayi yana ta kwafa, yace baiganta ba.

Mik’ewa tsaye Daddy yayi, cikin tsananin tashin hankali ya nufi kofar fita daga falon, batare kuma daya lura ba har tuntub’e yake.

Kaitsaye compound din gidan ya fito, tun daga nesa kuma ya soma k’walla kira.

“Ado! Ado!!”

Baba Ado dake bakin gate wurin Ashiru ne, Jin irin kiran da Alhajin keyi masa ne kuma yasashi tahowa da sauri.

Kallonsa Alhaji Idi Sale Dakata’n yayi, kana cikin dan daga murya yace.

“Jannart ta fita ne?”

Kai Baba Ado ya girgiza kana cikin girmamawa yace.

“A’a Alhaji Jannart bata fita ba, kwata kwata tunsafe Ina zaune anan banga wani ma daya fita acikin gidan nan ba.”

Shiru Daddyn yayi, na yan wasu mintuna, kamar kuma Wanda aka tsikara yasoma k’wala k’iran Guards.

Su kuwa k’attin banzan ma sai yanzu suka tashi daga nannauyan baccin daya daukesu.

Jin kiran da Ogan nasu keyi musu ne kuma, yasa cikin sauri duk suka k’araso.

Kallonsu Daddyn yayi tsab cikin hade fuska yace.

“Ina Jannart, dawa ta fita acikin ku?.”

Kai suka girgiza dukansu, kana suka had’a baki wajen cewa.

“A’a bamuga Jannart ba, mu yanzu ma tashinmu wata kila tana cikin gida.”

“Wani irin cikin gida kuma, bayan babu Inda ban duba batanan, maza ku zagaye duka gidan nan ko zaku ganta.”
Dadyn ya fada cikin bacin rai.

Nan take kuwa guard din suka bazu ako ina dake cikin gidan, amma ko alamar Jannart basu gani ba.

Hankalin Daddy yayi masifar tashi, musamman daya sake kiran wayanta yaji akashe.

Haka ya dawo falon afujajan, Yayinda Momy kuwa ta kasa zaune ta kasa tsaye, saboda abune kaman wasa amma yana neman Zamowa gaskiya.

Kallon Daddyn tayi, tare da Daukar wayarta tace.

“Bari na kira Barrister Kabir.”

Dialing number’n Barrister Kabir din tayi, bugu hudu kuwa Barrister Kabir ya dauka.

Bayan sun gaisa da Momynne kuma, cikin tashin hankali tace.

“Barrister bamuga Jannart bafa, munnemeta sama da kasa acikin gidan nan amma bamu sameta ba, munkira wayarta kuma akashe, Kodai tazo wajenka ne?”

Daga can b’angaren Barrister Kabir ya mik’e tsaye tare da daga muryarsa cikin nuna tashin hankali yace.

“What!! Wannan Wace irin magana ce, Ba’a ga Jannart ba, annemeta anrasa? Ita kudi ce da za’ace annemeta anratsa? Ko kuma ita din wayar hannu ce da za’ace an nemeta anrasa.”

Ya k’are maganar cikin yanayin tsawan, dake nuni da bazai iya tolerating nonsense akan Jannart ba.

Momy kuwa cikin tashin hankali tace.

“Wallahi Barrister bamuganta ba, body guards dinta da masu gadi duk sunce basu ganta ba.”

“Gani nan zuwa.” Barrister Kabir din ya fada agigice.

Tare da kashe wayar.

Bayan ya kashe wayartasa ne kuma ya saki wani irin murmushi tare da juyowa ya kalli Aunty Dijat dake zaune.

“Sakarkaru sai yanzu suka lura da cewar Jannart bata gidan, hmmm da sannu munafukan boye zasu fito fili, kowa kuma zai girbi abunda ya Shuka.”

Dariya Aunty Dijat tayi.
Yayinda shikuwa ya dauki key din motarsa ya fice.

Kaitsaye gidansu Jannart din ya nufa.

Yana isa gidan kuwa ko gama dai-dai-ta parking baiyi ba, ya fito.

Inda Daddy kuwa ke tsaye, gaba daya hankalinsa atashe yake sai safa da marwa yake, Yayinda kuma yake ta balbale guard din da fad’a, tankar zai hausu da duka, sai cewa yake, su je su nemo Jannart duk inda ta shiga ta fita.

Barrister Kabir kuwa agigice ya karaso, hankalinsa amatuk’ar tashe yace.

“Yaya ina Jannart? Waya dauke mana Jannart? Ina kuka kaita?.”

Kai Alhaji Idi Sale Dakata ya girgiza, cikin tsananin damuwar da yake ciki yace.

“Bansani ba Kabir, bansan Ina Jannart tayi ba, munduba ko ina amma babu ita babu alamanta.”

Hannu Barrister Kabir ya daura akai, lokaci daya kuma ya jujjuya idanunsa sukayi jajur, ahaukace ya soma neman Jannart din, tare kuma da soma zagaye cikin gidan yana leka har cikin followers, sunan Jannart din kawai yake kira da iyaka karfinsa.

Daddy kuwa bala’i da tashin hankali ne ke cinsa, cikin zafin nama kuma ya kalli Ashiru.

Afusace yace.

“Ashiru Ina Jannart waya bude mata kofa ta fita, ka fadamin nace ko kuma yanzu nasa bindiga na harbe kanka.”

Yakare maganar atsawace tare dasa hannu kuma ya dauke Ashirun da lafiyayyen Mari.

Kai Ashiru ya girgiza, cikin shanye zafin marin yace.

“Alhaji banganta ba, tun jiya gidannan akulle yake, gaba daya jiyama kowa ya sani bataje aiki ba, tunjiya bata fito ba, ga guards dinta nan suma shaidane.”

Sake hasala Daddyn yayi, Wanda hakan yasa ya sake gallawa Ashiru mari, tare da juyowa ya soma balbale Body guards din.

Cikin fushi yake cewa.

“Aikin banza k’attin banza kawai, angaya muku ahaka kawai na daukeku aiki ne, sokaye kun kwanta bacci sai kace matattu, yan iska kusan duk inda zaku ku nemomin y’ata.”

Barrister Kabir kuwa, zuwa yanzu har muryarsa ta Dishe, saboda yanda yake ta k’wala kiran Jannart.

Gaba daya lokaci daya jikinsa har karkarwa yakeyi, hankalinsa ya matukar tashi, inda yake reaction tankar da gasken gaske shima baisan inda Jannart din take ba.

Cikin kuma tashin hankalin daya nuna yana ciki ne kaitsaye ya nufi dakin Jannart din.

Yana shiga kuwa ya soma wargaza komai dake cikin d’akin, ananne fa kuma idanunsa suka sauka akan wayarta.

Da sauri ya dauki wayar dake kashe ya kunna, batare ma daya jira wayar ta karasa kawowaba ya dawo cikin falon, inda dukansu ke tsaye, cikin kuwa harda Junaid dake zukan shisha.

Wayar nata na kawowa Barrister Kabir ya shiga cikin dialing call dinta.

Aikuwa last sunan wanda tayi waya dashi Ne ya bayyana.

“Yah Junaid”

Idanu Barrister Kabir din ya zazzaro cikin matukar hasala, kuwa ya karasa cikin falon, batare da wata wata ba, ya Ware yatsunsa biyar ya zabgawa Junaid zazzafan Mari.

Tare kuma da juyawa afuce ya nunawa Dady screen din wayar Jannart din.

Cikin tsananin fushi yace

“Ba gashi ba, shine last mutum din da tayi magana dashi awaya, koma meye shi yasan inda take, Ina ya kaita? Yaya ka tambayeshi Ina ya kaita nace!!!!!!”.

Barrister Kabir din ya fada amatuk’ar tsawa ce, tsawan kuma daya saka hantar cikinsu kadawa.

Shi kuwa Barrister Kabir kuwa cikin fushi Ya...!





*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*

By
*GARKUWAR FULANI*






Ya shak’o wuyan Junaid din, ransa amatukar b’ace, cikin kuma son d’and’anawa Junaid din thesame azabar da yake ganawa Jannart yace.

“Ina kakai Jannart! Kafadamin Ina kakaita, kasan inda take tabbas, ba kuma abunda bak’ar zuciyarka bazata iya sawa ka aikata ba, kafadamin Ina ka kai mana Jannart!!!?”

Barrister Kabir din ya k’are maganan cikin tsawa sosai.
Tare da sake makure wuyan Junaid.

Junaid kuwa idanunsa ya Dan zaro cike da mamaki yace.

“Wai Abba mekakeson fad’ane? Ni ban San inda Jannart take ba, ba kuma nina d’auketa ba, na d’auketa ma nakaita Ina, watakila tanacan ta tafi yawon banz......”

Wani irin wawan mari Barrister Kabir din ya zabgawa Junaid din akan fuskar sa, cikin tsananin b’acin rai da hasala, ya kuma sake zabga masa wani marin, wanda har saida hakan yasa fuskarJunaid din tayi jajur mgnar da yake son fitarwa kan Jannart ta makale, idanunsa ya zazzaro lokaci daya tare da somayin huci.

Barrister Kabir kuwa ji yake Kamar ya rufe Junaid din da duka, ransa yakai kololuwa wajen b’aci da irin mugayen furucin da Junaid din ka jefar Jannart dasu.
Cikin fad’a sosai ya juyo ga Daddy dake tsaye yace.

“Yaya ka fad’awa Junaid na bashi nanda anjima yaje duk inda ya kaita ya daukota, ni nasani shine ya sace ta, domin kuwa shine last mutumin daya kirata awaya.
Uban meya gaya mata a wayan?
sannan meye dalilinsa na kiranta awaya?
Shi ya sace ta, saboda ya cika banzan burinsa na dabbanci akanta, komai zaiyi kuma bakayi masa magana, gashi nan kaga illar da hakan ya jawo ko Yaya?, gashi nan ya saceta ya rabamu da ita, ya kaita inda zai cutar da ita.
Yaya kana mance Jannart marainiyace amma ya maida cutar da ita tamkar abinci da ruwan shansa, Allah ya wadaran hali irin naka Junaid.”

Barrister Kabir din ya kare maganar cikin muryar kukan daya zo masa”.

Momy da Abdull dake tsaye agefe kuwa, gaba dayansu kuka suka saka, saboda.
Sunsan cewa tabbas Junaid din zai iya aikata hakan, ballema jiyan Momy da kunnuwanta taji yana cewa saiya cika burinsa akan Jannart din.

Daddy kuwa ransa Idan yakai dubu to yayi masifar b’aci, akaron farko kuma cikin fushi, ya dawo da kallonsa ga Junaid, tare kuma da ta sowa ya nufi kan Junaid din.

“Ina kakaita Junaid, Ina kakai min Jannart?
Ka fad’amin Ina kakaita? Junaid me zakayi da ita.” Daddyn ya tambayesa atsawace.

Abunda Bai tab’ayiwa Junaid din ba kenan, musamman akan Jannart.

Ganin hakanne kuma yasa Junaid din soma girgiza kansa, cikin mamakin tuhuman da sukeyi Mishi yace.

“Wallahi Allah Daddy bani na dauketa ba, bansan inda take ba, bani na sace ta ba.”

Cikin nuna ɓacin rai a fili Barrister Kabir dake tsaye.
Cikin rufe idaunsa da kuma mance alak’ae dake tsakaninsu yace.
“Nabaka nan da awa 2 Junaid, Lallai-Lallai kanemomin Jannart, duk inda ka kaita, kaje ka daukota Idan kaki kuma nida kai bibbiyu, wallahi-wallahi saikayi dana sanin sace marainiyar Allah da kayi.”

Sake dawo da kallonsa ga Daddy yayi, kana cikin tafasar zuciyar dake bayyana zai iya aikata komai akan b’atan Jannart din yace.

“Yaya kasa baki kasake tuna masa, awa 2 na basa ya fito da ita daga inda ya b’oyeta, sannan yanzu zan.
Kaiwa y’an sanda report, bayan haka kuma zan zagaya cikin duk wani asibiti da nasan yana cikin garin nan, dole ayau asamo inda Jannart take.”

Yana gama fad’an haka ya juya kaitsaye ya nufi hanyar fita daga gidan.

Koda yazo bakin gate harara ya watsawa Ashiru, kana cikin takaici yace.

“Shashasha kana nan tsaye abakin gate Koda yaushe, amma ka kasa sanin fita da shigan mutane sakaran banza kawai.”

Ya Kai karshen maganan nasa yana me bankad’e Ashiru’n, Cikin pretending yasakai ya fice daga Cikin gidan.

Daddy kuwa zuwa yanzu saboda tsananin bakinciki, da takaici da kuma Tarin bacin rai, jikinsa har rawa ya somayi yayinda yake jin, tamkar yasaka hannayensa aka ya kurma ihu, saboda b’atan Jannart din.

Sanin bashi da wata makamane kuma yasa shi, soma balbale guards din, Jannart din.

Cikin fushi hadi da bala’in dake cinsa yace.

“Bantab’a nadaman ajiyeku
Acikin gidana ba sai yau, k’attin banza k’attin wofi kafuran arnan da basa sallah, tayaya ma za’ace yarinyar da nake biyanku mak’udan kud’i duk wata akanta, za’a nemeta a rasa, ashema k’attin wofi dana banza na tara, lusarai way’anda basu da aiki sai ci da kwanciya, ku fita ku barmin gidana yanzu basai anjima ba, dukka na sallameku, kada na sake.
Ganin Koda mummunar fuskar daya daga cikinku ne, ku fitamin agida.”

Daddyn ya kare maganan cikin bacin rai.
Dan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment