Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kana Ahankali ya shiga takowa har zuwa inda take.

Batare kuma daya amsa mata duka tarin tambayoyin nata ba, ya kama hannunta kaitsaye suka nufi falonsa dake cikin main parlor din.

Koda suka karasa falon nasa kaitsaye bedroom d’insa suka wuce, still kuma har yanzu yana rik’e da hannunta.

Suna karasawa cikin dakin kuwa, ya maida kofar ya rufe tare da murzawa kofar key.

Numfashi ya d’an fesar, kana Ahankali ya d’ago Kai ya kalli Mamyn, wacce har yanzu takeyi masa Kallon mamaki.

K’asa-k’asa yayi da muryarsa, yadda yasan koda akwai wani adakin To bazai tab’a iya juyo abunda yake fad’a ba, sai ita d’in kawai.

“Kiyi k’asa-k’asa da muryarki Ruk’ayya, kinsan komai babu wani abunda baki sani ba, Dama ce ta samu, hakika naji ajikina cewar komai yana gab da had’uwa waje d’aya, da yardar Allah abubuwa suna ta had’uwa waje d’aya.”


Idanu Mamyn ta zuba masa cike da d’an d’aurewar kai, cikin kuma muryarta da yayi sanyi sosai tace.

“Har yanzu bangane abunda kake nufi ba, meke shirin faruwa ne?”

Ajiyar zuciya Abban ya sauk’e tare da sake rik’o hannunta da kyau.

Again kuma Cikin yin k’asa da murya yace.

“Kintuna Barrister Abdulkarim Saleh Dakata?”

Kai Mamyn ta jinjina, cikin sauri kuma tace.

“Natuna shi mana, har abada kuma bazan manta shiba.”

Kai Abban ya jinjina cike da gamsuwa, yace.

“To wannan bak’on da yazo wajena k’aninsa ne, shima kuma Barrister ne, sunansa Barrister Kabir Saleh Dakata.”

Idanu Mamyn tad’an zaro cike da tsananin mamaki, tace.

“Ikon Allah, Allah mai iko, mai kumayin duk yanda yaso, Lallai Tabbas kuwa na amincewa maganarka, Nesa na matsowa kusa, kuma haske zai bayyana Insha Allah.”

“Insha Allah kuwa.”
Abba ya maimaita cike da k’warin guiwa.

Acan b’angaren Rayyern kuwa...!

*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA




By
*GARKUWAR FULANI*





In Sha Allah kuwa.
Abban ya maimaita cike da k’warin guiwa.

Acan b’angaren Rayyern kuwa, koda ya koma part d’insa, gaba daya kasa zaune yayi, Domin kuwa abubuwa da yawa ne keyi masa yawo acikin tunaninsa.

Direct kuma saman balcony d’insa ya koma, yana nan tsaye ne kuma yaga Barrister Kabir din ya fito.

Hakan yasa cikin sauri ya juya, tare da nufan falon k’asan nasu kaitsaye.

Koda ya fito falon, rashin Ganin Abba acikin falon Yayi masa dadi, wanda kuma hakanne ya bashi daman nufan waje kaitsaye.

Fitowarsa compound din gidan, kuwa yayi dai-dai da mik’awa Baba Maud’o hannu da Barrister Kabir din yayi.

Cikin aminci suka sake gaisawa, inda Baba Maud’o yace.

“Masha Allah har kafito zaka tafi, To mungode sosai a gaida gida.”

Murmushi Barrister Kabir din yayi, tare da cewa.

“Nima Nagode Baba.”

Dai-dai ya juya zai shiga cikin motarsa ne kuma, Rayyern ya k’araso wajen.

Kallon-kallo suka danyi da Barrister Kabir din, Yayinda Barrister Kabir din ke kallonsa cikin sakin fuska.

Shikuwa Rayyern yaken dole yayi, kana anutse yace.

“Har zaka tafi?”

Kai Barrister Kabir din ya jinjina masa alaman.

“Eh.”

Shikuwa Rayyern kaitsaye bud’e murfin motar yayi, b’angaren mai zaman banza ya shiga ya zauna.

Ganin hakanne kuma yasa Barrister Kabir yin murmushi, tare da bud’e murfin motar shima ya shiga ya zauna.
saboda Lallai yasan cewa akwai magana.

Yana zama kuwa Rayyern ya fuskancesa.

Cikin muryar dake bayyana gaskiyar abunda ke cikin zuciyarsa yace.

“Bansan me kake nufi ba, Bansan me kake nema da rayuwata ba, Bansan wani k’ulline kuke nufina dashi, kaida y’an uwanka da kuma abokan kasuwancinka akaina ba, inayiwa fuskarka kyakkyawan gani , da kuma kyakkyawan zato, amma why zakayi min haka? kayi min bayanin yarinyar, kuma na saka baki anbata taimakon daya kama ta a Hospital dina? To yanzu kuma me kuke nema awaje na? Meyasa dole saini zaku zab’a mainayi muku? Ina da yakinin Akwai dubbannin mutanen, da zasu iya taimaka muku akan matsalarku, bawai dole sai lallai niba, To Meyasa kuke son takuramin? Meyasa kuke bibiyata? Meyasa zaka zo da wannan maganan mai kama da tatsuniya? Wanda ko’a labarai ko a fina finai babu irin wannan al’amarin, ni nakan cire kaina acikin duk wani abu danasan babu ruwana, Meyasa kukeson sakani acikin abunda baidace dani ba??”.


Juyowa Barrister Kabir din yayi, ya kalli Rayyern d’in.
Domin kuwa acikin kalaman da yaji sun fito daga bakinsa babu wanda bai fahimta ba ya fahimci Rayyern yanayi musu kuɗin goro shi dasu Alhaji Idi Saleh Dakata dasu Dr Lukman da Abdu Tababa.

Ajiyar zuciya mai karfi ya sauke tare kuma da kamo hannun Rayyern d’in, cikin fuskantar juna yace.

“Rayyern! Rayyern ka yarda dani, Rayyern ka aminta dani, bazan tab’a cutar dakai ba har abada, wallahi babu cutarwa tsakanina da kai, saidai ina tsananin neman taimakon ka, Ina neman taimakonka.
Dan tsiratar da ran Jannart, Jannart marainiya ce, Dr. Rayyern ba zaka gane halin da nake ciki ba, ba ni kuma da isashshen lokacin da zanyi maka bayanin da zaka fahimceni, fatana ayanzu shine Jannart ta kasance ak’ark’ashin inuwarka, ba naso asan ma tana tare dakai, Domin Kuwa auren da zakayi da ita, Aurene na sirri, haka kuma aure ne da zai zamo auren manufa, Dan Allah Rayyern ka amincewa buk’atata, ko badan niba Kodan maraicin Jannart..”

*”Manufa? Auren manufa Wanne irin manufa kenan?”*

Rayyern din ya tambaya, yana me tsare Barrister Kabir da ido.

“Manufa saboda ceto Rayuwarta, da kuma manufar fidda gaskiyar da take b’oye tsawon shekaru ashirin da biyu.”

Idanu Rayyern din ya lumshe, akaron farko cikin kuma halin ko inkula yace.

“To ni meye had’ina da wannan? Meya shafeni da hakan?”

Ajiyar zuciya Barrister Kabir ya sauk’e.

Kana cikin sanyi yace.

“Baka da had’i dashi, amma kuma abad’inance kana da had’i dashi, Domin idan kataimaketa Allah Zaibaka lada, kuma kayi taimakon musulunci.”

Barrister Kabir din ya fada idanunsa na ciko da k’walla.

Lips d’insa ya cije, tare da sake rumtse idanunsa, cikin yanayin dake nuna Kosawa da da maganan yace.

“Har dai yanzu bangane inda komai suka dosa ba.”

Still ajiyar zuciya Barrister Kabir din ya sake saukewa, kana ahankali yace.

“Nidai fatana shine ka amince, Idan ka amince ninasan yanda zan gudanar da komai.”

Kai Rayyern din ya girgiza Cikin kuma rashin gamsuwa, da abunda Barrister Kabir din ke fad’a yace.


“Wannan tatsuniya ne, ko kuma nace mafarkin da bazai kammala ba har gaban abadan, well yanzu me kaje ka fad’awa mahaifina mai kuka tattauna dashi?.”

Murmushi Barrister Kabir din yayi.
Kana yace.

“Idan ka tambayeshi duk zai gaya maka na tabbatar da hakan.”

Kafad’ansa yad’an d’age, batare kuma daya sake yiwa Barrister Kabir din wata, tambaya ba ya bud’e murfin motar ya fice.

Hakanne kuma yasa Barrister Kabir sakin murmushi, tare da dan juyawa yana kallonsa.

Harsaida Rayyern din ya b’a cewa ganinsa, kafun ya yiwa motar key kaitsaye ya fice daga cikin gidan.


Rayyern kuwa kaitsaye part d’insa ya koma, gudun kada wasu banzayen tunanin abunda basu da muhimmanci arayuwarsa su dameshi ne kuma yasa shi, daukan laptop d’insa ya soma shigar da wasu bayanai.

Acan b’angaren Barrister Kabir kuwa, zuciyarsa cike da tsananin farinciki ya Baro gidan su Rayyern din.

Koda ya isa inda zaije kuwa ansoma kiraye kirayen sallan la’asar, bayan yayi sallan ne kuma ya ci gaba da sabgoginsa.


Yayinda acan b’angaren Jannart kuwa, yau din kusan wuni tayi tana bacci, kasancewar acikin magungunan da aka bata a asibitin Mai-nasara’n, akwai way’anda suke sa bacci sosai, babu laifi kuma tana samun kulawa mai kyau, daga wajen Momy da kuma k’aninta Abdull.


10:00 pm

Aunty Dijat ne wacce Tasha wanka cikin night gown, ta turo kofar dakin mijinnata, Ahankali Yayinda bakinta ke dauke da sallama.

Saidai kuma ganin abunda mijin nata keyi ne, yasa taja ta tsaya tare da kura masa ido.

Domin kuwa shigowarta cikin dakin, yayi dai-dai da dirowar Barrister Kabir din k’asa, wanda kuma fitowarsa daga cikin silin kenan.

Idanu Aunty Dijat din ta d’an zaro, cikin kuma yanayin mamaki tace.

“Barrister, yana ganka haka cikin silin fa ka shiga?”

Kansa ya jinjina mata alaman Eh.
Batare kuma daya motsa bakinsa ba, ya koma ya zauna, tare da baje tarin takardun dake hannunsa ak’asa, wanda duk sukayi kura ya soma kad’ewa.

Ganin hakanne kuma yasa Aunty Dijat din cewa.

“Barrister lafiya kuwa, way’annan tarin tsofin takardun duk na meye?”

Juyowa yayi ya kalleta, cikin kuma son samun nutsuwa yace.

“Dijat dan Allah kid’an hakurtamin, Domin ayanzu bani da amsar da zan baki, bincikene akan abunda ya shafi aikina, please kije anjima zanne meki, yanzu Idan kika tsaya zaki iya disturbing dina.”

Ya fad’i hakan yana me Dan tausasa muryarsa.

Aunty Dijat kuwa sanin irin yanayin aikin nasa ne yasa batare da ta musa masa ba, ta juya ta fice daga cikin dakin, saboda tasan watarana Idan tension din aiki Yayi masa yawa, To kwata kwata bayason damuwa.


Shikuwa Barrister Kabir Ganin Dijat din tatafi ne, yasa shi soma bubbud’e takardun dake zube agabansa.

Yayinda kowacce takarda Idan ya bud’e, sunan Barrister Abdulkarim Saleh Dakata ne ke bayyana, da kuma sa hannunsa.

Yayinda acan gefe guda kuwa, kan wani file me kaman document aka yi rubutu da manyan bak’i.

*”Bashir Muhammad Mai-Gaskiya”* shine abunda ke rubuce ajikin file din.

Ajiyar zuciya Barrister Kabir din ya shiga saukewa akai akai, Yayinda kuma yake ci gaba da kimtsa takardun awaje daya.

Saida hakan kuwa ya d’aukesa kaman tsawon 30mn kafun ya kammala.

Kana anutse yasake maida takardun inda ya d’auko su, ma’ana cikin mab’oyansu na musamman.

Acikin zuciyarsa kuwa wani irin k’warain guiwa yakeji, tare da sake yiwa Allah Godiya, saboda ayanzu yasan kowanni shaida yana hannunsa.

Bayan kuma ya kimtsa wajenne, ya shige toilet kaitsaye alwala ya dauro, bayan ya fito ne kuma ya shumfud’a sallaya, tare da tada sallah ya d’anyi nafilfilu, hade da sake godemawa Allah.
Koda ya idar da sallan hannayensa ya d’aga sama.

Kana cikin aminci yace.

“Alhamdulillah Allah Nagode ma, daka bani Aron raida lafiya, har kuma ka kawoni tsawon wannan lokacin, da ake gab da samun nasara akan Jannart, da kuma ida bunne duk wata hujja, kuma ya Allah kataimakeni kabani sa’a, in tono duk wata hujja na bayyanata, gaskiya tayi halin ta..”

Shafa addu’ar tasa yayi, bayan wasu yan mintuna ne kuma ya tashi kaitsaye ya nufi dakin Dijat d’insa.

*Washegari*

Tuesday.

Jannart 8 am dai-dai ta bud’e Idanunta Ahankali, tare kuma da tashi ta mike zaune.

Tabbas taji karfin jikinta sosai yau din, tasan kuma hakan bai rasa nasaba da magungunan da Tasha.

Cikin kuzarin data dan samune kuma ta mik’e tare da fad’awa bathroom tayi wanka.

Koda ta fito, mai kawai ta shafa, batare da ko powder ta kuma mutstsukawa fuskarta ba, ta bud’e drawer dinta, hade da zaro wata Brown din jallabiya na mata, mai kyau da Tsushi ta zura ajikinta.

Sosai kuwa rigar tayi mata d’as ajikinta.
Normal perfume din da ta saba shafawa, ta shafa ajikinta, batare kuma da ta tsaya wani jikiri ba, ta d’auki wayarta kaitsaye ta fice daga cikin dakin.

Direct falon k’asa ta nufa.

Koda ta karasa cikin falon, Momy da Abdull kawai ta samu akan dining table suna breakfast.

Ganinta ne kuma yasa dukansu sakin murmushi.

Inda Cikin tsananin kulawa Momy tace.

“Masha Allah Jannart tayi sauk’i, Alhamdulillah hinyau Lallai kinji karfin jikinki.”

Murmushi Jannart din tayi, adai-dai lokacin da ta karaso dining table dinne kuma tace.

“Good morning Momy, Alhamdulillah naji sauki sosai.”

“Alhamdulillah ai haka akeso, dazu na shiga ai naga kina bacci shiyasa kawai ban tasheki ba, amma tunda kintashi yanzu zoki zauna kici abinci.”

Momyn ta fad’a cikin kulawa.

Abdull kuwa Kallon yayartasa yayi, kana fuskarsa dauke da murmushi yace.

“Sannu Aunty Jannart ya jikin naki, Ina fatan ace yanzu kin gama warkewa har tsere zaki iyayi.”

Dariya duk sukayi Yayinda Jannart din tace.

“Momy Daddy fa?.”

Ajiyar zuciya Momyn ta sauke, kafun daga bisani tace.

“Yau ai Daddynku tun sassafe ya fita, yace yana da ayyuka sosai.”

Kai kawai Jannart din ta jinjina, batare kuma da ta sake cewa komai ba, ta soma cin soyayyen chips and ketchup din da Momy ta saka mata, hadi kuma da fruit salad.

Bayan sun dan tab’a hira ne kuma, Abdull ya mik’e ya tafi makaranta, saboda yau din yana da lecture 10 am.

Itakuwa Jannart falo ta dawo ta zauna, tana falonne kuma Aisha Lawal da kuma Salman suka zo duba ta.

Har cikin falon kuwa ta shigo dasu, sosai kuma zuwan nasu ya debe Mata kewa, Yayinda Momy kuwa tayi musu tarba ta mutumci.

Ita dai Jannart kam yau tana cikin farinciki, saboda har yau Junaid enemy dinta baidawo gidan ba.

Acikin hirar tasu dasu Aisha Lawal dinne kuma, take tambayar Salman, ko wannan mutumin ya kirasa.

Numfashi Salman din yadan fesar, kana Cikin son kwantar mata da hankali yace.

“Har yanzun dai baikirani ba, amma nasan zai kira Insha Allah, karki damu ai daganinsa yasan muhimmancin alkawari, kuma ko yanzu ma da zamu taho saida muka biya wajen wasan polo’n, nayi tunanin zan hadu dashi kamar wancan ranan, amma kuma saidai ko mai kama dashi bangani ba.”

Ajiyar zuciya ta d’an sauk’e, tare da karyar da wuya cikin, sanyi tace.

“To Allah Yasa ya Kira.”

Da “Ameen.” Suka amsa dukansu.

Ganin yanda Jannart din ta damu ne kuma yasa, Aysha Lawal dafa kafad’anta, cike da son bata kwarin guiwa tace.

“Please Jannart karki damu kanki, Insha Allah komai zai tafi dai dai, kuma Koda ma ace baku samu ganinsa yanzu ba, ai ba matsala saboda MD yace ya k’ara miki one week, saboda rashin lafiyarki, kinga before nan ma kin sake warwarewa.”

Jin abunda Aishan ta fad’ane yasa, Jannart sauke Ajiyar zuciya mai karfi.

Cikin Jin dadi tace.

“Alhamdulillah, amma duk da haka nafison naganshi nan kusa, saboda muyi hira dashi asatinnan,kinga hakanne kad’ai zai karamin nutsuwa.”

Kansu suka jinjina dukansu, tare da sake bata kwarin guiwa akan cewar Lallai zata ga DR. Rayyern Bashir Muhammad Mainasara.

Haka dai suka ci gaba da hira, saidai kuma basu wani jima sosai ba, sukayiwa Jannart din sallama suka tafi.

Bayan tafiyar tasu ne kuma Jannart din tabi Momy kitchine Dan Tayata aiki.

Ganin Jannart din acikin kitchine ne kuma yasa Momy cewa.

“A’a Jannart bazaki fara aiki daga yanzu ba, kwata kwata ma yaushe ne kika samu sauki, ki koma ki zauna ni zan karasa komai.”

Jin abunda Momyn ta fad’ane yasa ta k’wab’e, fuska cikin sigar shagwab’a tace.

“Dan Allah Momy kibari nayi aikin ko kad’anne Allah naji sauki sosai.”

D’an Jim Mamyn tayi, saidai kuma ganin yanda Jannart din ta matsa yasa, ta bata bleending na pineapple.

Haka kuwa suka shiga yin aikin suna hira.

Bayan sun kammala ne kuma Jannart ta koma daki koda tayi sallahn Isha kwanciya kawai tayi.

*Littafin TUBALI na kuɗine special Group 1k ne kacal karamin group kuma 500 ne kacal 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, in kuma babu halin turawa ta banki ki sayi katin MTN ki copy number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp number na. Babbancinsu a yawan posting ne, dan girman Allah da Manzonsa kada ki karanta min littafina in baki biya, in kin biya kuma kiyiwa Allah kada ki fitarmin da littafina domin ba kuɗin mallakansa kika biyaba kuɗin samun damar karanta littafin kika bada*


Acan b’angaren Dr. Rayyern kuwa gaba daya sabgogin gabansa yake, musamman ma yau din da duk baisamu zama ba, Domin gaba ɗaya wuninsa acikin Hospital yayi sa, saboda wasu patients da aka kawo masa, masu heart attack yayi musu operation.

Adangane da batun Barrister Kabir kuwa, tuni ya watsar da duk wasu maganganun da sukayi da Barrister din acikin kwandon shara, impact ma shiya manta da wani batun maganan aure da aka fara.

Domin ko yanzu daya dawo gida, bayan yayi sallan isha ko dinner bai tsaya yiba, kaitsaye ya wuce bedroom d’insa.

Bayan ya sake wankane kuma ya dauro alwala, tare da kimtsa kansa cikin wasu tausassun fararen kaya.

Chocolates d’insa masu dadi yaci har kusan Leda uku dake ledan ƙananane, kafun ya daura da ruwa.

Ko takan laptop d’insa bai kuma biba, baccin gajiya ya daukesa.

Ahakama Acan b’angaren Riyyam-nsra, duk wunininsa na yau acikin dakin hotel din Tahir Guest Palace yayi sa.

Yayinda yake manne da wayarsa tsawon awanni kenan yanzu daya ke bad chat da wata sabuwar babe yar k’asar Morocco daya samu.
Kwata kwata yarinyar bata da kunya, da kamun Kai.

Wanda hakanne kuma yasa gaba daya Riyyam nsra ya susuce akanta, tare da b’ata duk wasu lokutansa na yau din akan yarinyar.

Domin kuwa Koda Ramadan ya kirasa akan yazo suyi dinner, cewa yayi sai Gobe da safe zaizo suyi breakfast, saboda yau din bacci yakeji sosai.

Akasin hakan kuwa saida yakai 2 am a online inda suke vedio chat da yarinyar ta Instagram.
Wanda ko kaya babu ajikinta.

Haka take zaune agaban wayarta single, Yayinda shi kuwa Riyyam keta susucewa akanta, Koda suka fara video sex chat, kusan gigicewa yayi, saboda yarinyar ta fisa tsaurin ido da iya iskanci sosai.

Saboda zaucewar da Riyyam din yayi kuwa, harji yayi inama da ace yayi tsuntsuwa ya gansa a Morocco, manne ajikin abokiyar tab’ewar tasa.

Haka dai ya hana idanunsa bacci. Har sai 3am kafun bacci ya daukesa ba kuma ibada yakeyi ba.


*Washegari.*

Kamar kullum kuma kamar Koda yaushe.

8 am dai-dai gaba ki dayansu zaune suke akan babban dining table din.

Abba, Mamy, Rayyern, Ramadan da kuma Riyyam nsra wanda kallo daya zakayi mishi kafahimci cewar bacci bai ishesa ba, saboda yanda idanun nasa sukayi luhu-luhu.

Rayyern kuwa da tun zamansu awajen yake lure da yaron, tass ya fahimci cewar yaron baya bacci da wuri, saboda wani dalili dayayi imani cewa ba dalili mai kyau bane.

Abinci sukeci cike da nutsuwa.

Yayinda Abba kuwa ya dago kansa ahankali ya kalli Riyyam-nsra.

Cikin kuma son sake sanin da wanda suke tare.
Ya ɗan gyara zamanshi tare da cewa.
“Riyyam”.
Da sauri ya amsa tare da kallon Abban.
Shi kuwa Abba cikin tsareshi da ido yace.
"Mahaifinka yana raye? shima Acan ethopian yake da zama ne?.”

Abban ya kare maganar yana me kafe yaron da ido.

Riyyam kuwa daya Kai loman abinci bakinsa, Jin abunda Abban ya tambayeshi ne yasa shi d’ago kansa Ahankali.

spoon din dake hannunsa ya ajiye, lokaci d’aya kuma idanunsa suka cicciko da hawaye.

Labb’an bakinsa ya motsa ahankali, cikin sanyi yace.

“Mahaifina ya rasu.”

Gaba daya dagowa sukayi duk suka kalleshi.

Tare dajin wani irin matsanancin tausayin sa, musamman ma Rayyern da hakanan yaji wani iri acikin jikinsa.


Riyyam-nsra kuwa da gaba daya zuciyarsa tayi rauni, hawaye ne suka gangaro daga cikin idanunsa.

Wanda hakan yasa Ramadan share masa hawayen, cike da tausayawa yace.

“Kayi hakuri kaji Riyyam, Allah yajikansa da Rahama, amma kadaina kuka, addu’a zaka nayi kaji.”

Kai Riyyam-nsra din ya jinjina, kana cikin sanyi yace.

“Insha Allah.”

Ad’an fakaice kuma ya kalli wayarsa da tun dazu take aiki, saboda kiransa da Mammy d’insa tayi, sai kuma ya d’aga ab’oye batare daya fad’awa kowa ba.

Daga can cikin wayar kuwa Mammy duk taji abunda yake faruwa.

Wanda hakan yasa hawayen dake cikin idanunta gangarowa kan fuskarta, haka ma Zaiton dake gefenta, hawayene kwance akan fuskar ta, saboda itama taji abunda akace, Dan Mammyn nasu a hands free ta saka wayar.


Shikuwa Abba har yanzu idanunsa akan Riyyam din yake.

Sake gyara zamansa yayi, tare kuma da duban Riyyam din.
Cikin sanyi da kuma dan bugun zuciyar da yakeji yace.

“Allah ya jiƙanshi da rahma?”


Idanu Riyyam din yadan lumshe, still cikin zubar da hawaye yace.

“Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati ngd matuƙa da addu'arga.”

Ayanzu kam gaba daya tsananin tausayi da kuma raunin yaronne ya rufe musu zuciya.
Hatta Abba kuwa saida yaji zuciyarsa ta raunana.

Nandai sukayiwa Baban Riyyam din addu’a, bayan sun kammala cin abincinne kuma kowannesu ya watse zuciyarsa cike da tausayin Riyyam-nsra.

To ayau din dai kam gaba daya Riyyam din tare da Ramadan suka wuni har dare kuma suna tare.

Inda washegari laraba ne kuma, Jannart taji saukin jikinta yasa ta shirya zuwa aiki, bayan ta gaya wa Daddyn nata cewa zata biya ta gidan Abba Kabeer.

Daddy kuwa Ganin cewa Jannart din bata da wani ishashshen lafiya sosai ne, yasa bai hana ta zuwa gidan Abba Kabeer dinba.

Jannart din kuwa Koda ta fito daga gidan nasu, kaitsaye gidan Abba Kabir ta nufa.


Koda ta isa gidan tarba maikyau ta samu daga wajen Aunty Dijat, bayan sun gaisa ne kuma.

Aunty Dijat din ta sanar mata cewa.

Abba Kabir din na kiranta.

Akaron farko kenan a iya tsawon rayuwarta, da taji wani abu mai kama da faduwar gaba, saboda Abba Kabir din ya kirata.

Sunan Allah ta soma ambato acikin zuciyarta.

Lokacin da ta isa bakin kofar bedroom din nasa ne kuma tayi knocking daga ciki aka bata izinin shigowa.

Ahankali ta tura kofar dakin ta shiga bakinta dauke da sallama.

Bayan Abba Kabir din ya amsa mata sallaman ne kuma yayi mata alama akan tazo ta zauna.

Babu musu kuwa ta karaso ta zauna agabansa, Yayinda shikuwa yake zaune akan gado.

Koda suka gaisa kuwa Almost 5 minutes haka suka zauna shiru.

Ahankali kuma Barrister Kabir din ya gyara zamansa.

Cikin kuma muryar dake bayyana iya gaskiyarsa, da kuma abunda ke cikin zuciyarsa da alamun umarni yace.

*”Jannart Aurenki ya kusa fa zanyi miki Aure!”*

Ya fadi mgnar cikin serious

Wanda hakan yasa Jannart cikin wani irin yanayi mai rauni.
Da harbawar zuciya cikin sauri Jannart din ta D.......




By
*GARKUWAR FULANI*





D'ago kanta ta kalleshi, da Idanunta wanda lokaci daya yanayin cikinsu ya sauya, musamman yadda maganar da taji ya fito daga bakin Abban ya daki zuciyarta matuka gaya.

Abba Kabir kuwa ganin ta d'ago kanta ne yasa shima ya zuba mata ido, fuskarsa sam babu alaman wasa.

Hakannne kuma yasa ta maida kanta k'asa, tare da d'an lumshe Idanunta, a hankali ta soma wasa da y'an yatsun hannunta.

Yayinda takejin zuciyarta na dan bugawa.

Dai-dai lokacinne kuma Aunty Dijat ta bud'e kofar d'akin ta shigo.

Yanayin yanda tagansuda dinne kuma ya sakata sakin murmushi, tare da karasowa ta zauna  akusa da Jannart din.

Kallon Jannart din Aunty
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment