Join Our WhatsApp Group

ARNAN DAJI 1 and 2 Complete Hausa Novel Document by ARNAN DAJI 1 and 2


ARNAN DAJI 1 and 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 85304



ARNAN DAJI 1 and 2

Reading Time: 7 Hours

Added On: 21, Jul 2023

Author: Fareeda Abdullahi ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : KAINUWA WRITERS?? ASSOCIATION

Author Phone : +234 810 679 5647

Book License : Free

Category: Adventure novels

File Size: 474.19 kb

File Type: txt

Views: 2319+

Download: 893+

Last download: 3 days ago

Description/Story: [9/11, 22:29] +234 810 679 5647: ?*ARNAN DAJI*?


FAREEDA ABDULLAHI

An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
__





*BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM DASUNAN ALLAH ME RAHMA ME JINKAI INAFATAN ALLAH YA TEMAKENI YABANI IKON RUBUTA WANNAN LABARI DANA DAKKO BA AKAN WANI KO WATABA KAGAGGEN LABARINE WANNAN SHINE LABARINA NA FARKO INAFATAN ALLAH UBANGIJI YABANI IKON YINSA CIKIN AMINCI KUBIYONI DAN KUGA IRIN SALON DAYAZO DASHI*



NASADAUKAR DA WANNAN LITTAFIN GA MAHAIFIYATA WADDA TA RAINENI TA KULA DANI TSAWON SHEKARU MASU YAWA JINJINA GAREKI MAHAIFIYATA




1-5

Garin kuguru dajine wanda wasu mutane ke rayuwa a cikinsa basu dawani addini dayawuce bautar wani katon gunki Wanda duk shekara sai anyanka masa mutane guda biyar yasha jini sukuma mutan garin suci naman suna bikinsu na al'ada duk shekara suna fita iyakar garinsu suna kama mutane duk Wanda Allah yasa tsautsayi yashigo dashi dajin suna kamasu su dauresu sai karshen shekara suyankasu subawa gunkinsu jinin sugasa naman aci asha burkutu basu da wata sittira sai dai susa fata ko ganyaye su rufe gabansu da ita matan Kuma su dan kara a mamansu idansun zama yammata suna daura auren duk wata budurwa a karshen shekara a abikinsu na shekara shiyasa ba karamin gagarimin taro akeba sarkin garin azzalimine bashida imani ko kadan idan kuma kikai haihuwar fari za a dafa dan acinyeshi Wanda sai anfara kaiwa sarki naman wannan kenan.





Tenkwai tenkwai way kina inane kije kidebo mana ruwa a rafi kinsan gidan nan bamu da ruwa ko kadanko ko sai dare yayi kinsan garin nan almuru na kawo Kai ba a zuwa rafi saboda mugayen abubuwan dake hanyar,Kai lamunde ganinan bara nabiyawasu rama, da aduke,sai mutafi yauwa kuyi sauri dai karku jima,tenkwai tasa kai da tulunta a hannu tana tafe tana wasa tabiyawa rama da aduke suna tafe suna hirar wasan daza ay na wannan shekarar aduke tace tenkwai wayko meyasa haryau kinki kisaurari ja'ene yakamata izuwa yanzu kibashi hadin kai tunda kinga har yanzu baki Sami Wanda ya kwanta mikiba tenkwai ta kalleta tace nifa banasan wannan rayuwar ta mutanen garinmu kawai Dan bansan yadda zanyiba amma gaskiya wannan yanka mutanen banasansa duk fa jinsunmu daya irinmu guda kuna kallo idan aka rasa mazanmu ake yankawa kanaji kanagani za a yanka abunda kahaifa Dan rashin imani ba afita agarin nan bame shigo mana duk wanda ya shigo sunansa matacce inafatan sanji yazo mana a wannan gari nisam bansan ja'e saboda dan sarkin garinnan ne shima bashi da imani tamkar mahaifinsa kinsan Kuma insarki ya fadi shine sarki amma zankara tunani akai zanyi shawara da lamunde.






Anan suka nemi waje suka zauna sunata hiarsu da hirar yanda wasansu na wannan shekarar zekaya yarda ake wasa da wuta awajen da macizai aduke tasa tulunta tana debo ruwa tanata basu labarin saurayinta tace tana dagowa saitaga kamar wani abu na yawo asaman ruwa tazabura ta firgice ta kwalawa tenkwai wani razanannen Kira dubamun kamar abu nake gani asaman ruwannan menene wannan tenkwai jaruma batada tsoro zuciyarta adake take amma akwaita da tausayi ta matsa kusa rama da aduke sai ja da baya suke tasa kafarta tashiga ruwan tana jawowa saitaga wani abu tasaki wata razananniyar kara wadda ta furgitasu gaba dayansu suka zura da gudu sukabarta a wajan tana maida wani irin numfashi saboda bata taba ganin irinsaba tunda take a rayuwarta.



Shin me tenkwai taganine daya furgitata kubiyoni a page nagaba.



*Feedyn bash*
[9/11, 22:29] +234 810 679 5647: ?ARNAN DAJI?*




*?KAINUWA WRITERS?? ASSOCIATION??*
{United we stand and succed;our ambition is to entertain &motivate the mind of readers}





FAREEDA ABDULLAHI

10-15







NASADAUKAR DA WANNAN PAGE DIN GA MASOYA WANNA BOOK NAWA INAJIN DADIN YADDA BOOK DINA YA KARBU GAREKU JINJINA AGAREKU MASOYA ????????????


A guje lamunde ta karasa kanta kafin ta isa micijin ya gudu tarasa yadda zatay ga tenkwai a kasa a kwance ga wani mutum daya firgitata ta rasa yadda zatay tadinga zagaye chan ta tuna tajanye mutumin zuwa wani surkukin chan cikin dajin tausayinsa ya ratsata ta dawo kan tenkwai taruke ta idonta yasanja kala yay kore shar aguje ta direta tabazama dawa akwai wani masanin micizai cikin dajin shiyasan kan dajin tana zuwa ta zube ta rushemasa da kuka durka katemakamun diyata na tsakiyar daji maciji ya sareta katemakamun a firgice ya Mike ya dakko jakar maganinsa ta fata ya biyo bayansa suna zuwa yana kallonta yace wannan kububuwace waddata addabi mutannen Bata taba saran wani be mutuba itama wannnan diya taki ba saranta tayiba hucintane amma yanzu zan mata magani ya dukufa nan da nan cikin sa a tadawo hayyacinta lamunde tadinga zabga masa godiya ya tashi ya koma dawa jiki b kwari yana ina lamunde yana ina kitemakamun munemoshi mutemakeshi banaso suganshi sukamashi lamunde ta toshe mata baki nina noyeshi Dan kar me magani yaganshi tashi muje mu dakko shi takamata suka mike da kyar take tsaiwa amma haka ta karfafi jikinta suka nitsa dawa lamunde ta dagashi dakyar tenkwai ta temaka mata suka fara tafiya saboda gari harya fara haske







Ana idar da sallah ta kwalawa me aikinta Kira ke maryama zonan aguje tafito saboda masifar tsoronta datake zan fita asra da ansar basu tashi ba idansun tashi ki kula dasu ki hada musu abinci ki shiryasu su tafi makaranta ni natafi tasa Kai tabar gidan oh ko ina zata da duku duku haka Allah ya kyauta ita mijinta ya Bata amma ko ajikinta wani farin cikima takeyi tasa Kai ta koma dakinta a guje take tukin kamar zata tashi Sama tana zuwa kofar gidansu afra tadinga danna mata horn takirata kefa nake jira gani nan jarababbiya uwar rashin hakuri fitowa zanyi tana fitowa ta shiga gaban motar kawata baki da hakuri da rayuwa duk wannan abun da kikai be ishekiba sai kin hada da boka yazama dole kodan muci kudi hankalinmu kwance amma da suhail ya tara kudi iya kudi yahanamu mu wala bayasan yabarni naje wasu kasashen shi kawai sai wata saudia nagaji da zuwa sai Egypt itama sai dai banda lafiya suko yara kina kallo sai dai akaisu jidda inaso inzama big madam yaki yanzu ay kinga yaywa kansa yana barzahu mukuma muci kudi mi wadaka muje kasar damukeso mu wataya hhhhhhh suka kyalkyale da dariya kina wutaaa wallahi inabinki da gas chewar afra sai wajen goma suka shiga garin zariya saboda sun hadu da cinkoso a hanya nan suka dauke hanyar makarfi suka nutsa cikin wani daji suka tsaya inda mota take tsayawa nan suka fara tafiyar kafa suna hawa dutsuna suna sauka saida sukai tafiyar awa guda sannan sukazo bakin wata katuwar tsamiya nan sukaji wani amo mara dadin saurara nan aka kyalkyale dawata mahaukaciyar dariya muguwa Yar gidan muguwa kinyo gado gado ba karambaniba naga komeke tafe dake abu guda dayane tsofaffinnan bazasu manta da dansuba bazasu dena masa addu a ba abu daya za'ay zamu cire musu tunaninki aransu bazasu kara zuwa wajenkiba bazasu karayi miki maganarsuba Amma sai kin maida musu da yayansa shi kuma kaninki angama dashi ga wannan kije tsakar rana karfe daya kidinga turare kina ambatar sunansu tsawon kwana uku to boka ga wannan a asiyawa aljanu shanu su sha jini ta ajiye bandir din yan dubu dubu guda goma hhhhhhh kufita da rarrafe aka daka musu tsawa da rarrafe suka taho suna tahowa sunzo dai dai wani dutse suka hada ido da ita suka zubaa mata ido cikin tsananin mamaki a matukar razane ta kallesu.








(Anan zan dakata fans sainaji ra ayoyinku yawan comment dinku shike kara mun karfin gwiywa cigaba da rubuta wannan littafin nice taku a Koda yaushe )





*Feedyn bash*
[9/11, 22:29] +234 810 679 5647: ?ARNAN DAJI?*




*?KAINUWA WRITERS?? ASSOCIATION??*
(United we stand and succed;our ambition is to entertain &motivate the mind of readers)





FAREEDA ABDULLAHI

5-10


Cikin firgici ta kara kallonsa taganshi kwance lankwam cikin ruwa Bata taba ganin mutum me kyau irinsaba tabbas wannan badan yankinsu bane ruwane ya kodashi nan gabar to amma kamar fa be mutuba tasa iya karfinta tajawoshi saitaga kansa a fashe yanata zubar da jini tasa kunnenta akan kirjinsa taji yana numfashi ta jawoshi gefe taboyeshi abayan bishiya yadda ba wanda zeganshi ta shiga daji tadebo ganyayyaki na tsaida jini tasa a wajen dayay rami ta dinga danna cikinsa ruwa yanata fitowa ta hanci ta baki amma be farfadoba yanata dai attishawa,



Da gudu aduke tashiga gidan tana Kiran lamunde yau mushiga tara badu ya temakemu tenkwai tana bakin ruwa tayi gamo lamunde ta dora hannu ta dinga runtuma ihu Kira take badu katemakeni ka kubutarmun da yata ita kadaice dani banda kowa banda komi sai ita kadai badu ka kawon temako rama kuwa tuni tagarzaya gidan sarki tana zuwa abakin shiga tagamu da ja e tazube tana haki fadi take jinjina gareka magajin kaho badu ya temakeka tenkwai na bakin ruwa tayi gamo inaga zuwa yanzu ba tenkwai kaimun aikin gafara sarkin gobe yana jin wannan magana ya mike a zabure ya saki wani ashar nan da nan ya kira fadawa suka dunguma sai daji suna bakin ruwa suna tafe sunata zage zage.





Tana zaune ta dora kansa akan cinyarta tajiyo kamar hayaniya daga chan nesa da sauri ta tashi tajashi chan chiki wajen wata bishiya tayi nesa da bakin ruwan tay maza tadawo bakin ruwa tana fitowa suka karaso ja'e ya kalleta ta kalleshi yace inayake meyasameki a gigice yake tambayarta tace ba komai naga jini a jikinki meyasamekine me kike boyemun bakomai nagayama wani dabbace tafito daga ruwa Amma na kasheta ba abunda yasameni kintabbata tace hakane yadakawa fadawan wata mahaukaciyar tsawa yace Kai kuduba lungu da sako kuga bawani abu nacutarwa anan nanda Nan suka bazu cikin dajin da gefen koshin suna lalube hankalinta yay masifar tashi dataga daya ya durfafi wajen data boye shi tadinga addu ar badu yatemaketa har ya kusa zuwa wajen ja'e yakwalo masa Kira yace kai kuzo mutay ku dakko wayan nan tulunan dukansu yasata agaba sai wayensa take suna tafe ja'e yanata mata hira Amma Sam hankalinta baya kansa yace ki amince dani bikin shekarar bana tunda yakusa a daura mana aure mutum daya ake nema daga nan zuwa wata biyu masu zuwa za agabatar da bikin ki amince dani ina Sam Bata San meyake cewaba hankalinta yana kan wannan mutum data tsinta abakin ruwa tana fatan karya farka ya shigo gari akamashi tunda dama mutum daya ake nema hankalinta yatashi gashi ba a shiga wannan dajin da daddare yanzu yazatay meye mafita sai da ya tabota sannan rayi firgigit Koda wata matsalane a a ko tunanin aurenmu kike tay yake yace karki daga hankalinki duk wata wahala ni zan dauke miki ita baku da matsala tace kabari zanyi magana da lamunde yadda mukayi zangayama ya bata rai ita zata zauna dani toko kinasona ko bakyaso kishirya aure a wannan shekarar nagaji da binki danake kina mun wasa kinsanni kinsan halina nine magajin garin nan Dan haka dole na samu abunda nakeso ban taba nema abu na rasaba bazan Fara akankiba nagaya miki dankinga inasanki a fusace ta juyo ta kalleshi tsakar ido saboda bata da tsoro tace bance bazan aurekaba amma baka isa kaimun dole ba sai nayi shawara Dan ba a karkashin kanakeba balle kaimun zalincinka daka saba ransa a matukar bace yace ni kike gayawa haka ya daga hannu ze mareta tarike hannun tace karka Fara Danni ba sakarya bace tawuce tabarshi rai bace.





Laminde na zaune kawai taga tankwai ta shigo kamar anjehota tana huci da gudu lamunde taringumeta tana kuka tace akacemun wani abu ya kamaki a bakin ruwa ki kwantar da hankalinki ba abunda yasameni ina cikin kwanciyar hankalina duk inda nake badu yana tare dani kawai tsorone irin nasu aduke tace nifa nagafa abun asaman ruwa amma kice ba komai dagaske nake gaya miki banga komai ba kawai wata dabbace a ruwa kuma na kasheta ku kwantar da hankalinku ga shi chan ankai muku tulunanku gida maza kuje kar anemeku nagode maku.





Way lafiyarki tunda kika dawo kin kasa magana ki zubawa waje guda idanu ko dai kinyi gamone tenkwai dakefa nake magana...


Read / Download ARNAN DAJI 1 and 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album