Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

akayi a gidan Jabir suka haɗu, Jabir yayi farincikin zuwan su, Yace
"Kai Ammar Mufeeda ta ɓoye ka, ko a hanya sam bama haɗuwa, ga yadda kayi kumatu"
Yaita zolayar Ammar sannan yai musu iso zuwa cikin gidan, falon sa ya kaisu suka zauna suka dinga hira, Can Ammar yace

"Jabir abar hirar nan muyi abunda ya kawo mu? Ina matar gidan ne?"
Jabir yace
"tana gidan ɗakin ta"

"a gaskiya naji wani labari dabe min daɗi ba game da auren ka, Jabir ya'akayi haka ta faru?"

Jabir yace "bari Ammar ai nayi zaɓen tumun dare dana san haka Auren yake da banyi ba, wallahi mata basu da mutunci nayi dana sanin Auren Saima"

Ammar yace "Dana sanin mene?"

"Yarinyar nan sam bata da Mutunci bata ganin girma na, bata da tarbiyya Sam, ban isa in gaya mata taji ba, wallahi badan ina tsoron abunda iyayena zasu ce ba da tuni na sake ta"

Aminu zeyi Magana sega Saima ta fito, tana ganin su ta faɗaɗa murmushin ta tace
"Manyan Baƙi aini har nayi fushi, sau ɗaya kuka zo mana tun bayan bikin mu, Ammar ina Amaryar?"

"tana gida, idan ma baku zoba zan kawo ta Insha Allah"
Saima tace
"Insha Allah ai zanzo har gida mu gaisa, Jabir baka gayamin sunzo ba ai be kamata abar baƙi babu ko ruwan sha ba, bari in baku ruwa"

Ta wuce ta nufi kitchen, Jabir yaja wani uban tsaki yace
"Munafukar Banza"
Aminu yace "Subhanallah, haba Jabir a gaban mu kake kiran ta Munafuka"

"mece idan ba Munafukar ba, danta ganku take nuna ita ta Allah ce, Amma tafi sheɗan iya rashin mutunci"

Saima ta dawo da lemuka da ruwa faranti da kofuna, ta ajiye Musu a gaban su.
Saima ta kalli Su Ammar idon ta fal Hawaye tace
"Aminu wallahi Abokin ku Azzalumi ne, dan Allah ku gaya masa idan mutum ya auri mace baya na nufin ya auro baiwa bane, Jabir Jahili ne besan darajar ɗan Adam ba"
Miƙewa Jabir yayi yana zare ido, ya fara narko mata Ashar, Saima tace

"Wallahi ba iyaye na ba sedai naka"

Da sauri Aminu ya miƙe ya riƙe jabir yace "Jabir meye haka? Matarka ta Aure kake wa wannan mummuna ashar agaban abokan ka?"

Saima tace "baka ga komai ba a gurin sa, dana san haka yake wallahi bazan Aure shi ba, mutanen kirki suka fito suna sona na liƙe nabi soyayya nace seshi, amma bayan Auren mu, shine kullum cikin chatting da 'yan mata, ba dare ba rana lokacin da nake buƙatar lokacin sa lokacin ne yake chatting, idan nayi magana seya ce wai na taɓa ganin anyi campaign bayan zaɓe? Da ina haƙuri ina ƙyale shi, Amma Ba damar inyi masa laifi se ya fara zagarmin iyaye, wallahi baka isa ba iyaye basu fi iyaye ba kakuma zagarmin iyaye sena zagi naka iyayen "

Ammar yace
"Saima yi haƙuri ki koma ɗaki, zamuyi magana da Jabir "

Haka ta wuce ɗaki tana kuka, Aminu yace
"gaskiya Jabir kaine mafarin samar da matsala a cikin gidan ka, ta yaya zaka dinga ce mata ba'a campaign bayan zaɓe, hakan fa na nuna bata da wani mahimmanci a gurin ka, haba dan Allah Jabir kaman ba wayayye ba kaima fa kana da ƙanne mata baza kaso ayi musu haka ba, kuma wallahi in gaya maka kaida ta ƙara ganin mutuncin ka har gaban abada sedai tayi pretending, amma a matsayin ka na namiji daga lokacin da ka buɗe baki ka zage ta ka zagi iyayen ta mutuncin ka ya zube a idon ta musamman idan ta buɗe baki ta rama, Jabir meye Amfanin hulɗa da 'yan matan daba Auren su zakai ba bayan ga matarka ta halal a gefen ka? Kawai ka zauna fadi banza faɗi wofi a haka har sheɗan ya kawo muku wani tunani na daban"

Ammar shiru Yayi yana tunani, ya tuna Yadda Jabir yake Soyayya da Saima kaman babu wata mace da tai Saura a duniya sama da ita.
Ammar yace
"tabbas Jabir kana da laifi, ba kowane ze iya jure ka zagi iyayen sa yai maka shiru ba duk mutuncin ka da yake gani, karka manta da haƙoran ta bayan iyayen ta sun gama ɗawainiya da ita ka ganta ka aura, babu yadda zata iya jure cin zarafin su gaskiya, kaman yadda bamu da juriya da jarumta irin na iyayen mu haka suma matan basu da haƙuri da biyayya kaman na iyayen mu duk sedai muyi haƙuri da juna, amma batun chatting da 'yan mata lokacin da matarka ke buƙatar lokacin ka, to tabbas idan me raunin Imani ce hakan zesa itama ta fara tunanin fara chatting da wasu mazan"

Suka dinga yiwa Jabir Nasiha, zasu tafi ne Saima ta fito idon ta jawur saboda kuka ta miƙawa Ammar turaren wuta, da humra tace
"Ammar gashi ka kaiwa Amarya a bata haƙuri, Insha Allah ina nan tafe mu gaisa, Kaikuma Aminu se Fiddausi ta haihu ma haɗu"

Ammar yace "to mungode zan gaya mata Insha Allah, sannan Adinga haƙuri ana kai zuciya nesa saima, a unguwar mu babu wanda be san Soyayyar ku da Jabir ba, be kamata ace daga yin Auren ku hakan tana faruwa ba"

Murmushi me ciwo Saima tayi tace "Ammar kenan, Soyayyar nan duk a baki ce ya nunamin, kudai ina muku fatan Alkhairi ku gaida gida" ta juya ɗakin ta tana sharce hawaye.

Ammar yake tunanin ita kuwa wani irin pain take ji a zuciyar ta har take wannan kukan haka. Su kayi wa Jabir sallama suka tafi, seda Ammar da Aminu suka ƙara tattaunawa akan batun, Ammar yace

"gaskiya Aminu lamarin rayuwar nan akwai ban tsoro, shiyasa naita gudun yin Aure a baya"

"Ammar kenan, ai abun dace ne, kaga ni babu wata babbar matsala da nake fuskanta tsakanina da fiddausi se tarkacen ƙawaye da yawon maƙota, sune babbar matsalar ta, nayi nayi ta dena taƙi, Amma ta wani ɓangaren idan na duba alkhairan ta se in share ta kawai inyi haƙuri tunda nima haƙuri take dani"

Suka gama taɗinsu sannan Ammar ya nufi gida, ya ɗan tsaya a hanya yaiwa Mufeeda siyayya, sannan ya tafi gida, tunani yake tayi ya gano me Mufeeda take yi wanda baya so, amma ya kasa ganowa se yai tunanin ko dan Yarinya ce, ko kuma tana jin tsoro nane yasa bata min wasu abubuwan? Ko dan bamu daɗe tare ba? A'a wannan Yarinyar da tana jin tsorona da bata tunkareni ta kalli tsabar idona tace tana sona ba wata zuciyar ta bashi amsa.

Da wannan tunane tunanen yaje gida, se daya duba agogonsa yaga sha ɗaya na dare.
Aikuwa yana shiga tana falo a zaune tana rarraba ido, tana ganin sa ta miƙe
"Yaya Ammar ina ka tsaya haka? Har na fara tsorata ko wani abun ne ya same ka"
"Sarkin tsoro, ba abunda ya sameni gani na dawo"
"gaskiya ka daɗe sosai"
"Ai gani na dawo dai, ya jikin naki?"
"Naji sauƙi Alhamdilillah"
"Haka ake so, ungo gashi nan ki samu Kisha, tunda yau baki ci Abun kirki ba"
Ƙatuwar Jarkar yoghurt ce a ciki,
Murmushi tayi tace "Masha Allah, Nagode sosai mijina Allah ya baka Aljanna maɗaukakiya, Yasa ka gama da duniya lafiya"
"Ameen"
Ta ɗakko kofi ta zubawa Ammar ta bashi yace shi baya sha, ita dai ta sha ya sata a gaba ta sha sosai sannan ta ajiye sauran.
Ta kalle shi tace "Mijina meke damunka ne? Naga kaman akwai damuwa tare da kai"
Kallon ta yayi da mamaki ya akai ta gane yana da damuwa.

Ya maze yace "gajiya ce ni babu wata damuwa dake raina"

"idan gajiya ce kawai take damun ka ina ganewa, yau yanayi ya nunamin bayan gajiya akwai damuwa"

Miƙewa yayi yace "jeki kwanta seda Safe"

Bayan sa tabi da kallo daga bisani ta miƙe ta tafi ɗakin ta, yau ta sha baccin rana, saboda rashin lafiyar ta, dan haka ta kasa bacci, tana ta tunanin meke damun Ammar? "dole inyi wani abu kar ya kwana da damuwa.

Ta ɗakko wayar ta tura masa saƙo
"My love, hau online kaga wani abu"

Ya tura mata "me kike baki Bacci ba?"

"Nakasa baccin ne, ka hau ka gani"

Ya buɗe data ɗinsa ya shiga what's App, hoton ta ta tura masa, tayi wa gashin kanta ado, ga wata body hook ce a jikin ta pink, leɓen ta raɗau da jambaki se shining yake, ta ɗan turo baki ta lanƙwasa wuya, a haka ta ɗau hoton ta ɗora waƙa me daɗi akan hoton.

Ammar na buɗe hoton besan lokacin da ga tura mata
"Wow Masha Allah"
Wani murmushi tayi tana daga kwance ta tashi zaune, ta tura masa
"Nayi kyau?"

"Ba laifi kin kusa yin kyau, dama kin girma ne da se yafi kyau"

Sosai Mufeeda tayi dariya, baze ce tayi kyau ba sedai ya kushe ta.

Ta tura masa
"Mijin baby wani jambaki yafi min kyau?"

"kowanne" ya bata Amsa.

"shikenan gobe idan na saka zaka ce nayi kyau?"

"ba tabbas dan ba wani kyau kike ba idan kin saka, seki koma kaman 'yar ƙauye" ya rubuta yana murmushi.

Emoji ɗin haɗe rai ta tura masa tare da "nice mummuna ko? Sena gayawa Umma kana cemin mummuna"

"Ke ki kwanta dare yayi fa"

"to My love, you do your task very well today ka kula da Jaririyar ka, nagode sosai Allah ya ƙara Arziki, da naso inyi fushi saboda kasa anmin Allura, amma bazan iya ba nagode sosai da kulawar ka miji nagari, Allah ya barmin kai har ƙarshen rayuwa ta"

"Me a daidaita sahun kike so har ƙarshen rayuwar ki?"

"Ko sana'ar da kake bata kai ta a daidaita sahu ba, ai halal kake nema, kuma ni ba sana'arka ce a gabana ba, kai nake so Ammar ɗina"

Tayi mai voice message kaman me raɗa take cewa "I love you my Ammar have a nice dreams"

Shiru Ammar yayi yana jujjuya wayar a hannun sa yana kuma duba chatting ɗin sa da Mufeeda.
Murmushi yayi ya kwanta wani daddaɗan bacci yayi awon gaba da shi.

(to su Yaya Ammar ko an faller ne🙄🙄🙄)





Ina godiya da ƙauna da kulawar ku.
Ƙofata a buɗe take, domin gyara sharhi, ko kuma shawara nagode sosai 😍 😍 😍
Ayshercool
07063065680
.✨✨✨✨
        *WATA KISSAR...... *
                  ✨✨✨✨✨

                      ( *Sai Mata* )

         

                        

*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*_A SHORT LOVE STORY_*

*Story and written by*

'''AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)
The experience writer of ABDUL JALAL'''

Na sadaukar da wannan littafin ga Ɗaukacin masoya na, wanda nasani da wanda ban sani ba

Watpad @ Ayshercool7724

What's app 07063065680

Gmail [email protected]

     

ELEGANT ONLINE WRITER'S

             

           

                  

                        Page 15

Da Safe Ammar ya fito, se dai Mufeeda bata saka jambakin ba kaman yadda yayi tsammani, haushin kansa ne ya kama shi, komeya na son ganin ta da Jambakin ma oho, haka sama sama ya tambaye ta ya jiki, Sarai ta gane abunda yasa shi haɗe rai
Tace

"Jiki da sauƙi Alhamdilillah tunda Mijina yana tare dani"

Ƙin kula ta yayi ya karya abunsa yana wani basarwa.
Da ya gama ya kalle ta yace

"ya kamata ki shiga ku gaisa da maƙwabta, ɗazu mun haɗu da maigidan dake kallon namu, yace min baki shiga kun gaisa da matan su ba, kuma haka ake yi"

"to idan naje me zance musu?"

"nima ban sani ba" ya bata amsa.
"ce musu zanyi nice matar gidan nan, kokuma Jaririyar Yaya Ammar?" shiru ya mata tare da yi mata wata uwar harara.
Mufeeda tace "shikenan zan shiga Insha Allah"
"Sannan kuma ba cewa nayi kuma kidinga shige2 ba da tarkacen Maƙota ba, cewa nayi kawai ku gaisa bana son shige2"
"Shikenan insha Allah zan kiyaye, dama niba me shige shigen bace, saboda bana son takura da sa ido"

Ya gama karyawar sa ya shirya ya fita, yana ƙoƙarin tada babur ɗin sa ya fita da shi ne Mufeeda ta ƙaraso da sauri ta riƙe ƙarfen Babur ɗin, cikin shagwaɓar ta ta tace

"Wai fita zakayi?"

"A'a zama zanyi, in kinji yunwa ki dafani ki cinye"

"idan na dafa ka na cinye na zauna da wa? Wani abu nake son baka ne"
Juyowa yayi yana kallon ta, ba zato ba tsammani ta sumbace shi a kumatun sa na hagu tace

"take a good care of your self My love, Allah ya kiyaye hanya, ya wadata mu da halal" tsayawa yayi yana kallon ta, yayin da ita kuma ta koma gida.


Seda ta kammala aikace2 da zata yi a gidan sannan ta shiga maƙota suka gaisa kaman yadda Ammar ya urmace ta, wasu sun bayyana mamakin su kan cewar itace matar gidan, yayin da wasu kuma suka ɓoye hakan, ita kuwa ko a jikin ta, tai musu sallama ta koma gida.

Ta koma gidan ta babu daɗewa Yaya Usman ya kira ta a waya yace "ke buɗe mana ƙofa muna waje.

Aida gudu ta miƙe ta tafi gate ta buɗe, gurin Baba ta tafi da gudu ta rungume shi, Baba ya shafa kanta yace
"I really miss you Auta na"
Mama tace
"Baban ki kaɗai kika gani ko? Ni baki ganni ba"

Ta ɗan tura baki tace "Aini duk fushi nake, tunda aka kawo ni masoyyiya Amina ce kawai tazo gidan nan"

Yaya Usman yace "mu koma kenan?"
Tai murmushi tace "ni bance ba"
Mota biyu suka yi, duk Yayyen ta da yaran su, haka suka zo.

Mufeeda ta rasa inda zata saka ranta dan murna, nan suka shiga shigo da kayan Abinci na garar Mufeeda.

Yaya Fadeela tace "Auta naga kin ƙara haske ko dai an gamu ne?"

"Eh na gamu dake mana"

Anty Murja tace "Lallai Autar Baba, wallahi kin ƙara nutsuwa"
Suka dinga tsokanar ta.

Taji daɗin ganin 'yan gidan su, nan suka dinga hira, tana raha.

Sedai ba' azo da Yaya Amina ba cikin ta ya tsufa.

Mufeeda tace "Mama bari in kira shi, yazo ku gaisa"
Mama tace "A' a, ƙyale shi kar a takura masa"

Iyayen Mufeeda sunji daɗin yadda suka ga Mufeeda ƙalau da ita, alamu sun nuna gidan Ammar ba yunwa yana iya ƙoƙarin sa.

Se la'asar sannan suka yi mata Sallama, da zasu tafi Baba ya bawa Mufeeda Naira dubu goma taita godiya, suka ce ta gaida Ammar, sannan suka tafi.

Mufeeda taga uban kayan garar da Baba yayi mata, ta dinga murna tace "Allah ya biya ka da Aljanna Baba na, kwana biyu Yaya Ammar ya huta"

Bayan la'asar Ammar ya dawo, seda ta bari yaci Abinci ya huta take gaya masa su Mama sunzo.

"meyasa baki kirani kin gayamin ba?"

"Baba ne yace in ƙyale ka, maybe kana aiki kar a takura maka"

"Gaskiya banji daɗi ba, naso a ce nazo na tarar dashi"

"Dukan su suka zo harda su Anty Murja gaba ɗayan su"

"Naso mun haɗu dasu, but insha Allah very soon zamuje"

"duk suna gaishe ka"
"Ina amsawa"

Yana zaune yana kallo, yaga Mufeeda tana cin wani abu, ya kalleta yace
"me kike ci? Se an jima ki lanƙwashe kice ciki na ciwo ko?"

"gullisuwa ce fa"

Ammar yace "Madarar  kike gullisuwa da ita, za'a raba madara kowa ya ɗau tasa, in kika ƙarar da taki seki koma shan tea baƙi ko kuma cin cornflakes ba madara"

Ɗan tura baki tayi tace  "idan na shanye semu koma shan taka"

"Seki sha ɗin in gani"

"Ai da kanka zaka bani, saboda bazaka iya shan shayi da madara ni kuma ka bani ba madara ba"
Hararta yayi ya ɗauke kansa

Wani cup ta ɗakko me kyau da murfin sa a jiki ta miƙa masa kofin tace  "ungo naka"

Ya kalleta yace
"meye wannan?"
"taka gullisuwar ce"

"Ni bana shan wannan kayan shiriritar da yarinta, kedai kije kiyi tayi"

"da daɗi fa ka ɗanɗana kaji"

Girgiza mata kai yayi yace
"Ke nace bana so"

Ta ƙyale shi bata kuma takura masa ba, se bayan ya dawo daga sallar magariba Mufeeda tace

"Yaya Ammar zo kaga"

Tana ɗakin tsakar gida, dan haka ya leƙa ɗakin, kayan Abincin daya gani a ɗakin ne ya sashi yin turus, yace "Wannan fa?"
"Kayan gara ne dasu su Baba suka kawo mana"
Shiru yayi yana kallon kayan yace

"Amma wannan kayan ai sunyi yawa ya zamuyi dasu, ni badan ina tsoron kar Baba yaji babu daɗi ba gaskiya da bazan karɓi kayan nan ba"

"Haba Yaya Ammar meye sa? Ai bamu kaɗai zamuyi Amfani da kayan ba, za'a ɗibarwa su Abba, Su Yaya Maryam ma duk a basu, Baba zeji ba daɗi idan kai magana akai"

Ɗan girgiza kai Ammar yayi yace "Kayan nan sunyi Yawa fa"

"Yaya Ammar babu wani yawa da suka yi, da Baba baze iya ba baze takura kansa yace se yayi ba, dan Allah kawai ka bar zancen nan, muci Abincin mu kawai ko?"

Tai maganar tana leƙa fuskarsa, wani ɗan murmushi yayi wanda iya kacinsa leɓensa, ya koma falo, ya kalleta yace

" Ni zan kwanta seda safe"

"Amma ina fatan ba ranka ne ya ɓaci ba akan kayan nan?"

Girgiza mata kai yayi yace
"A'a inajin Bacci ne kawai"

"shikenan Allah ya tashemu lafiya"
Yace "Ameen" ya wuce ɗakin sa itama ta wuce nata.

Harta kwanta taji kawai bata ji daɗin yanayin yadda ya tafi kwanta ba, dan haka ta miƙe ta fito ta tafi ɗakin sa.

Har ya kashe fitila ya kwanta, ta shiga da sallama sannan ta kira sunan sa
Amsa mata yayi sannan yace
"Ya a kayi?"

Gadon ta hau ba tsammani yaji Mufeeda a jikin sa, a hankali yace "lafiya kuwa?"

"Yaya Ammar zuciya ta ta kasa samun nutsuwa, gaba ɗaya yanayin ka tun jiya zuwa yau baya mun daɗi, dan Allah idan laifi nayi maka kayi haƙuri"

Ajiyar zuciya ya sauke yace
"Ni nace kin min laifi ne?"

"Yanayin ka ke nuna kaman na maka laifi, bana jin daɗin ganin ka a haka, idan kuma akan kayan nan ne se in kira Yaya Usman yazo a mayar da su"

Tai maganar jikin ta a sanyaye, gyara kwanciyar sa yayi yace
"ni babu abunda kika yi min, kawai dai ɗan Adam dole wataran ya tashi babu daɗi shikenan kawai"

Kwanciya tayi sosai a jikin sa tace "Duk da haka yana da kyau in san damuwar mijina, dukda Mijin nawa yana ganin Yarin ta ta, Amma bazan so in ganshi cikin damuwa ba"

Nannuyar Ajiyar zuciya Ammar ya sauke, yace
"Naji zan dena damuwa, tashi kije ki kwanta seda safe"

"Zan tafi Amma buɗe bakin ka"

"Me yasa zan buɗe bakina"

Yana maganar ne ta saka masa Gullisuwa a bakin sa, shiru yayi yana tunawa, tayi masa daɗi Sosai dukda shi irin wannan abubuwan basa gaban sa yana ganin kaman shirita ne.

Wata ta kuma saka masa a bakin sa, ƙamshin turaren jikin ta, da yadda ta kwanta a jikin sa ya sashi cikin wani farinciki dabe san dalilin sa ba.
A hankali cikin raɗa tace masa
"da Daɗi kuwa?"
"Babu daɗi kaman inyi amai"
Murmushi tayi tace
"koma babu daɗi tunda ka riga ka sha shikenan za'a raba madara dai dai, kuma tawa seta fi Yawa"

"Naji tashi ki bani guri, mara kunya ji yadda kika biyoni har ɗaki kika wani kwanta min a jiki"

"Ba jikin mijina bane, kuma dai naga ni Yarinya ce"

Kasa cewa komai yayu, Ƙasan zuciyar Ammar kuwa bugawa yake da ƙarfi yana saƙawa yana kwance abubuwa daban daban game da matar tasa da yake mata kallon tayi ƙanƙanta da Aure.

Miƙewa Tayi daga jikin sa, ta sumbaci goshin sa tace
"Honey seda safe, I love you Baby"

Riƙe hannayen ta yayi, kaman ya hana ta tafiya, se wata zuciyar tace masa "She's still young, Yarinya ce raini ze shiga tsakani na da ita, tayi ƙanƙanta"

Sakin hannayen ta yayi kaman an masa dole yace "Seda Safe" ya juya mata baya.

Dukda a cikin duhu ne bin bayan sa Mufeeda tayi da kallo tareda ɗan girgiza kai, Ammar akwai taurin kai da izza.

Ta koma ɗakin ta, Ammar kam baccin sa rabi da rabi ne, juyi kawai yake akan gadon har Asuba.

Da safe yana fitowa yai tozali da ita akan kujera ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, tana ta kaɗa ƙafa ta sha kwalliya ta kashe ɗauri, bakin ta se shining yake da jambaki, ga ƙamshin girki dana turare ya gauraye falon, gani yake kaman tana sane take wannan abubuwan.

A hankali ya tako falon kamar wanda ƙwai ya fashewa a ciki, ya samu guri ya zauna, ta ɗago ta kalle shi tare da yi masa murmushi, ta taso daga inda take tazo gaban sa ta durƙusa ƙasa tace "Barka da Safiya Yallaɓai" kallon ta yayi tayi kyau sosai, yana jin daɗin yadda lokuta da yawa take bashi girma, wani lokacin kuma ta maida shi kaman ƙaramin yaro, yace

"lafiya ƙalau prof. Kin tashi lafiya?"
Miƙewa tayi ta zauna a kusa dashi ta ɗan tura baki tace
"Bayan jiya dan naje ɗakin ka ka koreni"
Murmushi ya ɗanyi bece komai ba, ji yake kaman yace mata tayi kyau, amma ya fasa.
Ta jingina a jikin sa tace
"A kawo breakfast ne?"
"Bari se anjima kaɗan"
"yau bazaka fita da wuri bane?"
"Eh se lokacin salla yayi zan fita"
Mufeeda a ranta tace

"Yaya Ammar manya maganin ƙanana, na gane Lagon ka sarai, Jambakin nan da gashin nan ba ƙaramin tafiya suke da kai ba"

Ta kamo hannun sa tace
"Yau Friday ya kamata a yanke maka farce" bece komai ba ita kuma ta ci gaba da wasa da yatsun hannun sa, can ta ɗaga kai ta kalli fuskar sa takai hannun ta fuskar sa tace
"in taɓa?"
"in kika taɓa sekin biya"
"dan Allah sau ɗaya fa"
"kika isheni sena aske gemun nan"
"aikuwa idan ka aske na dena kulaka, dan ina son gemun nan sosai"
Ammar yace
"tashi ki kawomin Abinci"
Ta tashi ta kawo masa Abinci, ta haɗa musu Tea, zata sa masa Madara yace "bar madarar nan ki shanye abarki, naga ta kusa ƙarewa"
"Se insha tea da Madara kai kuma ka sha ba Madara?"
"Eh kece 'yar gayu ai, ni ban damu da shan me Madara ba, kiyi Addu'a Allah ya hore kafin ta ƙare in siyo wata"

Shiru tayi tana kallon sa, duk faɗan Ammar yana da sauƙin kai Sosai, kuma yana matukar ƙoƙarin ganin ya wadata da Abinci, baya bata Abinci mara daɗi, ko alawar da tayi jiya da madarar be mata faɗa ba.

"Allah ya ƙara maka Arziki na halal My love"
"Ameen" ya amsa mata.

Suka kammala karyawa, ta ɗakko nail cuter ta yanke masa farce tsaf.

Ammar yace "in Allah ya kaimu ranar Saturday zamu ɗan fita, Umma nata mita har yanzu ban kaiki ba"

"Wayyo Allah daɗi, Allah ya kaimu lafiya nima na ƙagu ka kaini in gansu"

Wasa2 Ammar seda ya kusa makara zuwa masallaci saboda yadda Mufeeda ta narke masa a jiki take ta zuba taɓarar ta iri2.

Se azahar sannan yai wankan juma'a ya fita salla.


******************

Fa'iza taga abubuwa sunƙi tafiya yadda take so, ta kuma wanke ƙafa ta tafi gidan Yaya Jidda, suna ta hira Fa'iza fa sako maganar gidan Ammar
"Nikam Yaya Jidda kinje gidan Yaya Ammar kuwa?"

"hmm ina fa naje, idan naje gurin wa zani gurin wannan ƙwailar Yarinyar kokuwa? Bani da lokacin su daga shi har ita"

"Amma ai gidan ɗan uwan ki ne Yaya Jidda ya kamata ku dinga zuwa kiga a wani hali hake ciki? Idan kuma ya tattara ya koma gurin ta gaba ɗaya fa, ku kuma ko oho kenan?"

"Aini bana son zuwa inga abunda ze ɓata min rai, ranar da nayi masa magana akan wulaƙancin da tayi muku, seda mukayi faɗa dashi ya kare ta"

Fa'iza tace "kinji abunda nake gaya miki ko Yaya Jidda wallahi ki dinga zuwa, idan ba haka ba ana ganin ƙanƙantar ta da haka zata raba shi da kowa, tunda tun yanzu ya fara goyon bayan ta"
Jidda tace "kuma fa hakane, zanyi ƙoƙari inje gidan nasa, zan kuma yiwa umma maganar ta ja masa kunne, akan ya kula da 'yan uwan sa, dan nasan ita zata gaya masa yaji ko kuma Maryam, in be ga dama ba idan Maryam ta faɗi magana ze rusa maganar uban kowa ya ɗau tata, duk wannan masifar tasa ita baya yi mata"

Fa' iza tace "haba dai Yaya Maryam ɗin?"
"ita fa, ai baya shiri da kowa a cikin mu kamar ita, indai Maryam na san abu ze hana kansa ya hana uban kowa ya bata"
Jinjina

Please Login or Register in order to submit comment