Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kai Fa'iza tayi, a ranta tace "dole inje in ziga Yaya Maryam itama, zata taimaka min"
Suka ci gaba da hirar su daga nan suka yi sallama.


A hanya Fa'iza tana tafe tana zancen zuci akan ya zata ɓullowa lamarin Ammar, taji ana mata horn tsayawa tayi ta juya, me motar yazo dai2 inda take sannan ya sauke baƙin gashin motar yace
"Manya maganin ƙanana, ke kuwa talaka na ganin ki"
Murmushi tayi tace "Ba gashi ka ganni ba, yaushe rabon da in ganka?"

"Shigo motar se muyi magana" ba musu ta zagaya ta buɗe gaban motar ta shige.
Ya kalleta yace "Ni ko a bikin Ammar ban ganki ba ina kika shiga haka?"
Tsaki ta ɗanyi tace

"me zanje inyi masa a gurin bikin, dan abun kunya kuna gani kuka barshi ya auri wannan 'yar mitsitsiyar Yarinyar, bayan a duniya ya tsani Auren ƙaramar Yarinya"

"kinfi kowa sanin Halin sa ɗan uwan ku ne, ke zaki gayawa wani halinsa, shekaranjiya na haɗu da shi da matar tasa ya kaita Asibiti se zuba shagwaba take yi, Wallahi Yarinyar nan za tayi saurin tafiya da Imani namiji, duk jin kan Ammar lallaɓa ta yake ranar, ina ga ko ciki ne da ita "

Wani dogon tsaki ta ja tace
"dan Allah ka dena ɓata min rai, dan abun kunya 'yar wannan Yarinyar Ammar zewa ciki, mtseww"

Dariya sosai Faruk yayi yace "Kai
Fa' iza, to shi kna ruwan sa, Wallahi tun ranar ɗaurin Aure da naga yarinyar nan na kasa samun nutsuwa, wallahi dana ga Yarinyar nan kafin bikin su da bazan taɓa bari Ammar ya aure ta ba, Idan naga Yadda take wa Ammar shagwaba wani irin kishi ne yake kamani, Wallahi ina jin ƙaunar yarinyar nan har a cikin zuciya ta"

Wani irin Murmushi Fa'iza tayi tace "dagaske kana son ta"
"Wallahi Fa'iza ina mata so bana wasa ba, ni ko ban Aure ta ba kawai dai in same ta, kin gane ai balle ma ina son in Aure ta, wallahi tunda naganta mata ta dena birgeni"

Jinjina kai tayi tace
"Me ze hana mu haɗa kai mu taimaki juna?"

Ya gyara zama yace "kamar Yaya kenan?"
Murmushi tayi tace "zamuyi waya"


********************

Kasa nutsuwa Yaya Jidda tayi, dan haka ta tambayi mijin ta zata fita unguwa, shiryawa tayi ta tafi gidan su Ammar.

Koda Mufeeda ta buɗewa Jidda ƙofa taga kammanin ta da Ammar, sannu da zuwa tayi mata tai mata iso ciki, wani irin kallon banza take bin Mufeeda dashi.

Tun kafin Jidda ta shiga falon idon ta ya sauka akan jibgin kayan Abincin dake ɗakin tsakar gida, tayi ƙwafa suka shiga falon.

Ta kalli Mufeeda tace
"Ina Ammar ɗin?"
"be daɗe da fita ba kuma, yana gida tun ɗazu, amma se in kira shi a waya"

"Ammar ɗin da yake fita tun farar Safiya shine yake zaune a gida har bayan azahar sannan ya fita"

Shiru Mufeeda tayi tace "bari in kawo miki ruwa"

"Ke dawo bana son gulma, ni bazan sha ruwan ki ba, sannan ki buɗe kunne da kyau ki jini, Wallahi daga yau idan wani daga dangin mu yazo kika kuma masa wulaƙanci sekin bar gidan nan dan baze yuwu ba, 'yar mitsitsiya dake kin san wulaƙanci, su Fa' iza sa'anin kine da zasu zo ki musu rashin mutunci, ko gidan uban kine? "

Mufeeda ta girgiza mata kai alamar A'a, Mufeeda a ranta tace" wannan ce Jidda kenan? "

" to ko yanzu yai niyya ze iya sakinki ya auri wata, 'yan uwa kuwa ba' a canza su, ance miyar ki hadda kaji alhalin be kaiwa namu iyayen ba, shafaffiya da mai, ni ina tunanin kin haɗawa Ammar da ƙulumboto dan Ammar ba sakaran namijj bane, daga zuwan ki ki kainainaye shi, kalli uban kayan Abincin daya tile miki a ɗaki, Amma iyayen mu ko oho, se anyi magana yace bashi da kuɗi ina ya samu kuɗin daya siya miki wannan kayan haka? Algunguma baki isa ki rabamu dashi ba"

Jidda taiwa Mufeeda cin mutunci tsaf, Sam Mufeeda bata tanka mata ba, se dai zuciyar Mufeeda kaman ta fashe, ga Jidda ta girme ta sosai balle tace zata rama.

Seda ta gama sannan ta tashi ta tafi, bayan tafiyar ta se da Mufeeda tayi kuka dan ba ƙaramin jin zafin abunda Jidda tayi mata tai ba.


Ammar ne ya dawo ya tarar da ita a falo, ba haka ya saba ganin ta haka ba in ya dawo, amma ya basar ya miƙo mata leda yace

"gwada wannan takalmin in gani ɗazu na ganshi yayi kyau na siyo miki"

Ƙoƙarin maida hawayen idon ta take, Ammar ya ga idon ta da ƙwalla, ya ɗan haɗe rai yace
"kukan me kike yi?"

"bakomai bafa kuka nake ba"

"bana son ƙarya, meke damunki?"

"bana jin daɗi ne"

A fusace yace "ƙarya kike lafiyar ki ƙalau, meya same ki? Bana son ƙarya"






Domin sharhi, gyara ko shawara
Ayshercool
07063065680
✨✨✨✨
        *WATA KISSAR...... *
                  ✨✨✨✨✨

                      ( *Sai Mata* )

         

                        

*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*_A SHORT LOVE STORY_*

*Story and written by*

'''AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)
The experience writer of ABDUL JALAL'''

Na sadaukar da wannan littafin ga Ɗaukacin masoya na, wanda nasani da wanda ban sani ba

Watpad @ Ayshercool7724

What's app 07063065680

Gmail [email protected]

     

ELEGANT ONLINE WRITER'S

             

           

                  

                        Page 16

Ƙura mata ido yayi, a hankali tace "bafa wani abun damuwa bane, radio nake ji aka faɗi wani labari daya bani tausayi, shikenan fa bari in gwada takalmin nan dan tun kan isa na hango ƙafa ta tayi cif a ciki"

Ammar yabi Mufeeda da kallo ba dan ya yadda da abunda tace ba, amma ƙiri ƙiri ta basar da zancen ta karɓi takalmin ta saka, na zaman tsakar gida ne amma kalar pink ne me tudu yayi kyau sosai, ta miƙe ta ɗanyi juyi tace
"yaka gani yayi min kyau kuwa?"
Gyaɗa mata kai yayi,
tace "Nagode mijina Allah ya baka gidan Aljanna"
"Ameen ya Allah"

*****************

"Maman Sadiq maƙociyarki me kallon gidan ki ta shigo miki kuwa? "

Maman sadik tace "Hmm ta shigo min maman Amir ke kin ganta wata 'yar yarinya da ita, amma mijin ta baki ganshi ba ƙato da shi, ni ba dan na ganta kalar wayayyu ba da cewa zanyi a ƙauye ya auro ta"

Ɗayar tace "dan Allah ta shigo muku? Ranar da ta shigo muku ina ga bana nan, kaddai' yar Yarinyar da naga ya sata a a daidaita sahun sa ce matar?"

Maman Amir tace "Wallahi itace maman Nur"

"Taɓɗijan niko zanso in ƙara ganin ta"

Maman Sadiq tace "ke kina ganin ta 'yar Yarinya se shegen ji da kai, watan ta guda a unguwar nan fa sannan ta shigo mana, tana wani jin kai a gurguje ta tafi, nace kin gamin yarinya da kinibibi,' yar da da auren wuri aka min na haifeta"

Maman Nur tace "Kedai bari da mijin nata wata tsiyar ne da shi da ta ɗaga mana kai, amma duk layin nan shi ne matsiyaci ɗan adaidaita sahu ne fa"

Maman Ameer tace "kema dai kya faɗa"

Maman Sadiq tace "Maman Nur ya kamata akaiwa maƙociyar tamu ƙyallen Ankon sunan ki na haihuwa"

Maman Amir tace "wallahi kuwa mu kai mata muga meza tace"

Maman Nur tace "haka za'ayi ɗakko ƙyallen muje"

Suka ɗakko ƙyallen Atamfa suka nufi gidan Mufeeda.

Tana tsakar gida tana aikace aikacenta aka buga ƙofa cikin ƙaramar Muryar ta tace
"waye?"
Suka amsa da "mune".

Ta buɗe musu ƙofa suka shigo, tun daga tsakar gidan suka fara ƙarewa gidan nata kallo basu yi zaton cikin gidan ta yana da kyau haka ba.

Tai musu iso cikin falon ta suka gaisa, ta kawo musu ruwa da ɗan abun motsa baki na garar ta, nan suka dinga ci suna zuba surutu, ita dai Mufeeda sam bata da saurin sake wa da mutane dan haka sedai ta kallesu tayi murmushi kawai.

Can maman Amir tace "yawwa Mufeeda dama ƙyallen ankon sunan Maman Nur ne muka kawo miki ko mai gidan ze sai miki"

Mufeeda ta karɓi ƙyallen ta gani tai murmushi ta miƙa musu tace

"Aikuwa Atamfar tayi kyau sosai, se dai ni da ban daɗe da Aure ba kayan lefe na na nan ko taɓawa banyi ba, sedai ince Allah ya rabaki da cikin lafiya, idan kika haihu zan sako abunda Allah ya horemin in shigo inyi miki barka"

Ɗan buɗe baki maman Nur tayi tace "kodai me gidan ne baze miki ba, amma Atamfar fa babu tsada dubu biyar ce fa"

Mufeeda tace "Anty kenan aike yanzu kinfi buƙatar Addu'a fiye da wannan Atamfar, kuma insha Allah zan saki a Addu'a Allah ya raba ki da cikin nan lafiya"

Maman Sadiq tace "ai insha Allah zata rabu da cikin nan lafiya, duk 'yan layin nan za suyi fa anko zamuyi, mene dan ya miki lefe kwanan nan, ke yarinya bari kiji mazan yanzu ba' a tausayin su, ki zage duk abunda kike so ki sashi gaba seya miki"

Murmushi sosai Mufeeda tayi tace
"to nikam se an jimanku zan shiga kitchen, nagode sosai da shigowar da kuka yi"

Ta tashi ta barsu a falon, suka fito suna mamaki gami da zage zage.

Maman Sadiq tace "yau naga kinibabbiyar yarinya, wani wai kinfi buƙatar addu'a akan anko ji munafuka"

Maman Nur tace "ke niba wannan ba ina mijin ta ɗan a daidaita sahu ne, kawai base naga saman fridge ɗin ta da kayan shayi ba hadda su butter ga biscuits da kayan daɗi, naga dai bata haihu ba amma data buɗe fridge zata ɗakko mana ruwa hadda chocolates a cikin fridge ɗin, wallahi raina ya biya, bari gobe in Allah ya kaimu aikawa zanyi ta sanmin milo"

Maman Amir tace "hmm kedai bari muda mazajen namu suke da sana'oi da suke samun kuɗi rabona da baban Amir ya saimin kayan shayi tun haihuwar Amir yanzu yara na uku, danma ba kiga ɗakin nan na tsakar gida ba ke kinga kayan Abinci kamar a kanti?"

Maman Nur tace "wallahi shiga gidan zan dinga yi nida yara, a dinga shan madarar nan damu"

Maman Sadiq tace "in kinga fuska muma semu biyo ki"

Suka cigaba da gulmar su dai

**********************

Mussaman Jidda ta shirya ta tafi gida, domin ta ziga Umma akan Auren Mufeeda da Ammar.

"Umma wallahi Idan ba'a tsaya akan Ammar ba, wallahi ze zama mijin tace, su Fa'iza basu gaya miki abunda yarinyar nan tayi musu ba"

Umma tace "A'a nidai sunzo nan Halima ta rakasu gidan Sa amma ba su dawo ta nan ba"

"to sun biya gida na, sun gayamin yadda ta dinga musu wulaƙanci"

Halima tai farat tace "Wallahi ƙarya sukeyi, tare fa muka je ba wani wulaƙanci da tayi musu"

Jidda tace "dan ubanki dake nake magana? Ko kuma ƙanwar uwaki ce da zaki goyi bayan ta?"

Tura baki Halima tayi tace "ai ni gaskiya na faɗa"

Umma tace "to ni Jidda na kasa gane inda maganganun ki suka dosa sam, wani irin wulaƙanci ne haka?"

"wallahi Umma rashin mutunci ta dinga yi musu, kuma da naje gidan ta baki ga kayan Abinci ba kamar abun banza, kashe mata kuɗi yake kaman kaman me amma ku nan baya kawo muku, se anyi magana yace ba shi da kuɗi"

Umma tai Murmushi tace "To meye a ciki dan ya kashe mata kuɗi matar sa cefa, kuma Ammar ko be mana a yanzu ba a baya yayi mana balle har yanzu Ammar yana iya ƙoƙarin sa akan kyautata mana, Jidda lokacin da mahaifinku yake da shi na wata ya ya kashe min kuɗi kaman babu gobe, shi ba mace ce ta haife shi ba? Ko kuma lokacin da yake kashe mana kuɗin meyasa ba kiyi complain cewar be kyauta ba? Ina yanzu keda 'yan uwanki kuma' ya'yan wasu kuke aure kuma suke muku hidima, dan me za kuce ɗan uwan ku baze wahaltawa wata ba? Ai abun Alfaharinku ne ace ɗan uwan ku ya auro 'yar mutane kuma yana iya riƙe ta, nikam Alhamdilillah Ammar har yanzu yana ƙoƙarin kyautata mana, kuma ni ina ƙaunar ta, Dukda murɗaɗen hali irin na Ammar duk da yadda bashi da tarin dukiya tace tana sonsa a haka ni ta gama yi min komai ina ƙaunar ta"

(ƙalubale gareku iyaye, haka ya kamata ku zamo masu adalci ga matayen 'ya' yan ku, dukda wasu sirikan basu da kirki, amma da yawan lokuta ƙannen miji da yayye suke jawowa matar ɗan uwansu a gurin iyayen su, su faɗi abunda akayi da wanda ba'ayi ba suce anyi, ku kuma iyaye babu binki ce babu komai ku hau kai ku zauna, Allah ya kyauta)

Jidda tace "Shikenan Umma tunda baki yadda ba, zaki gani da kanki wataran ai"

********************

Ammar ya dawo ya shiga ɗakin sa, ƙaton flower Mufeeda ta zana da sunan sa da Nata, gefe tayi rubutun kalaman Soyayya ta ajiye masa akan gado ɗan girgiza kai Yayi a ransa yace

"sam Yarinyar nan bata rabo da shiriri ta"

Ya fito falo ya tarar da Abincin sa sedai be ganta ba, yayi tunanin ko tana wani abun ne, dan haka ya zauna ya fara cin Abincin sa, sam Abincin baya masa daɗi saboda babu Mufeeda a kusa dashi balle taita masa wannan shirirtar tata, yana gama ci har ya tafi ɗakin sa ya dawo ya duba yaga ko tana lafiya, yana buɗe ɗakin ta ya tarar tayi ɗaiɗai akan gado tana bacci, ta tafi ƙarshen gado wanda idan tayi ƙwaƙwƙwaran juyi zata iya faɗowa, kome ya sata bacci da wuri haka oho?

A hankali yaje gaban gadon nata da niyyar ya gyara mata kwanciyar, yana ɗagota ta firgice ta saka ihu.

Rirriƙeshi tayi tana zare ido, yace
"Ke menene haka? Nine fa"

Ajiyar zuciya tayi ta lumshe ido tace "wallahi ka bani tsoro, wani ɗan jaririn ƙadangare ne ya shigo gidan nan shiyasa na taho ɗaki fa"
tai maganar tana kwanciya a jikin sa.

"Yanzu Jaririn ƙadangaren ne yasa kika dawo ɗaki kika kwanta hadda rufe ƙofa?"

"eh mana idan kuma ya shige min ɗaki fa?"

"Shikenan cikani zanje in kwanta"

Ta ɗan kalle shi tace
"kaci Abinci kuwa?"

"Naci kwanciya zanyi yanzu"

Ta langaɓar da kai tace "nifa yau ban ganka sosai ba"

"Nifa bana son rigima, cikani ki koma baccin ki"

Wani irin kallo take masa, lumshe ido take alamar akwai bacci akan ta sosai amma Ammar gani yake kaman da gayya take masa wannan kallon.

"I love you sweetheart" shine abunda ta furta masa a hankali.

"Naji, karki manta gobe in Allah ya kaimu ki shirya da wuri zamu fita"

Jinjina masa kai tayi tana lumshe ido, ya zame ta daga jikin sa, ya kwantar da ita sosai akan filo ya fita ya koma ɗakin sa.

Daya koma ɗakin ma tuni ta dafa masa ruwan wankan sa kafin ta kwanta, da zafi sosai ya haɗa ruwan yayi wankan, sannan ya samu guri ya kwanta, tunani yake da ƙoƙarin sama wa kansa mafita akan zaman sa da Mufeeda, baze yuwu su ci gaba da zama a haka ba dan ba ƙaramin cutuwa yake ba, yana mata kallon Yarinya ƙarama amma a lokuta da dama kasancewar su tare yana ƙara jefa shi cikin wani hali, lallai salon da take amfani da shi yana matuƙar tasiri ga zuciyar 'yan mazan.

Haka yaita tunani har yayi bacci.

Da safe Mufeeda tana ta ɗoki zata fita, watan ta biyu a gidan nan amma sau ɗaya taje Asibiti sekuma maƙota data shiga, Suna gama breakfast ta saka Ammar a gaba suka ware kayan Abincin gara da su rarraba da wanda zasu tafiwa da su Umma, har na su Yaya Maryam seda da su Jidda seda ta ware masa, ta rarraba kayan zaƙin nan na alkaki ta warewa kowa nasa hadda wanda ze bawa abokan sa su Jabir su bawa matan su.

Ammar ya kalle ta yace "Ai wannan kayan da kika rarraba sunyi Yawa, saboda ke aka kawo be kamata ki kwashe ki rabar ba, wanda zaki bawa su Umman ma ya isa nagode"

"Abunda kaci kashi ne wanda ka bayar shine rabon ka, ka sani ko dalilin bayarwar da mukayi Allah ya ninka mana, ai abun duniya ko ka bayar ko baka bayar na seya ƙare"

"Amma babu wanda zaki bawa a family ɗin ku? Be kamata ace kin rabar da kayan nan haka ba"

"Ai kowa seda aka bashi kafin a kawomin, kaga wannan ai ya ishemu kaima kwana biyu seka huta, Allah dai ya ƙara maka buɗi babban mutum, ciyarwa ba aikin rago bane, kana ƙoƙari sosai seka huta kafin su ƙare"

"maganar hutu ai babu shi tunda na riga na ajiye ki, dole in fita in nemi abunda zan riƙe ki, kaman yadda yake a shari'a"

Miƙewa tayi tsaye tace  "kana ƙoƙari mijina, Allah ne kawai ze biyaka ladan ɗawainiyar da kake, Allah ya ƙara Arziki, bari inje in shirya karmuyi rana"

Ya jinjina mata kai, ta koma ɗakin ta ta shirya cikin doguwar rigar atamfa, tayi to match da mayafin ta da Jakarta, Mufeeda akwai Gayu, da ta fito falo Ammar be fito ba ta bi shi ɗakin sa, tana zuwa ta tarar ya shirya yana ƙoƙarin saka links ɗin hannun rigar sa.
  Da sauri ta ƙarasa inda yake, ta fara ƙoƙarin saka masa tace

"Babban mutum kayi kyau sosai kaman in sace ka in gudu"

Kallon ta kawai yake ba tare da yace mata uffan ba, amma itama tayi kyau sosai, amma sam ba tayi kama da matar Aure ba.
Ta ɗakko turare ta feshe masa jikin sa, tace
"Allah ya barni da abun sona har ƙarshen Rayuwa ta" ita dai duk wani motsi da zata yi se tayi masa Addu'a kokuma tayi masa kirari, kota nuna masa irin soyayyar da take masa, lokuta da dama har mamaki take bashi.

Haka ya shiga gaba tana binsa a baya, suka kulle gidan suka fita, Ammar idan ya fita tare da Mufeeda baya ɗaukar passenger.

Seda tasa Ammar ya tsaya suka saiwa su Abba Fruit sannan suka tafi, Basu tsaya ko ina ba se gidan su Ammar, Mahaifin Ammar yana tsakar gida yana jin radio suka shiga da Sallama.

Abban Ammar yana ɗaga ido, Mufeeda ya fara kallo ganin su tare da Ammar yasa ya gane itace Sirikar sa, Murmushi yayi yace
"barka da zuwa Yarinyar kirki sannu da zuwa sirika ta"

Har ƙasa Mufeeda ta durƙusa tana murmushi ta gaida Mahaifin Ammar, shima cikin dattaku ya amsa mata, yace
"Zauna mana sirika ta" gefen tabarmar Abba ta zauna

Ammar ya ɗanyi gyaran Murya yace "tunda ni baka maraba da zuwa na, bari in koma"

Abba yai Murmushi yace "ni ai ka daɗe muna tare, ni nayi 'ya dama ba a Auta da namiji babarka tayi Auta da kai, ni yanzu ga auta ta nan"

Ammar yace
"Aikuwa zaka ga halin Auta kam"

Murmushi Mufeeda tayi tace
"dama shima ɗan auta ne?"

Abba yace
"ƙannensa uku ne suka rasu, kinga kuwa shi ne ɗan Auta"

Dariya Mufeeda tayi, Umma ce ta fito daga ɗaki hannun ta ɗauke da carbi, alamar sallar walha ta yi, tace

"Yau Allah yayi an kawo min Mufeeda kenan? Tun ina magiyar har na gaji"

Nan ma cikin girmamawa Mufeeda ta gaida Umma, ana haka Halima ta shigo daga aiken da aka yi mata, tana ganin Mufeeda ta fara murna tace

"Anty Mufeeda ashe zaku zo ɗin tun ɗazu nake kallon hanya"

"Yaya Halima ni na makarar damu ai, Amma ai gashi munzo"

Duk rashin saurin Sabon Mufeeda yadda iyayen mijin ta suka karɓeta ba ƙaramin yi mata daɗi yayi ba, sun nuna mata karamci da dattako, jinsu take kaman iyayen ta, sosai ta sake suna hira, anan Har hira ta kawo Abba yake gaya mata yana kiwon dabbobi a kangon jikin gidan sa, nan suka shiga hira sosai har Mufeeda take nuna sha'awar ta akan kiwo.

Yadda take hira da iyayen sa cikin mutuntawa kaman iyayen ta ba ƙaramin burge Ammar yayi ba, Ammar ya miƙe yaje Napep ɗinsa ya kwaso kayan Abincin da suka zo dasu da Yadda aka kasafta kayan.

Abban Ammar yace
"A ina ka samo wannan kayan haka Ammar?"

"Dama kayan garar Mufeeda ne"

Abba yace "gara kuma Ammar? Ina fatan ba zuwa kayi kace se an maka gara ba, dan nasan halin ku matasan yanzu akan gararar nan se kuyi wa mace gori dan abin kunya" Abba ya ɗanyi maganar a hasale.

Wato Abba halinsu ɗaya da Ammar, sam basa son aga gazawar su, musamman akan abunda yake haƙƙin su ne suyi shi.

Mufeeda tace "A'a Abba, da cewa yayi ma baze karɓa ba, Baba ne ya kawo haka yake yi duk wadda ya aurar ya bata gara, Amma dan Allah kayi haƙuri ba shi yace a kawo ba"

Abba ya kalleta ganin kaman ba taji daɗin yadda yayi wa Ammar ɗin ba, yace "Hmm zaki kare mijinki ko? To ni a yanzu yamin laifi zan iya zane shi ma"
Sunkuyar da kai Mufeeda tayi tana murmushi, daga nan yayi musu Nasiha da Addu'oi.

Seda Mufeeda tabi Abban Ammar ya nuna mata yadda dabbobin sa da yake kiwo suke, a cikin maganar sa zaka gane tsohon ɗan boko ne, Ga Mufeeda da shegiyar tambaya, duk abunda ta tambaye shi se yayi mata bayani dalla-dalla. .


Bayan tafiyar Mufeeda Abba yace "Ammar kana surutan cewa Kai tayi maka Yarin ta, to a manyan da kake hange da wuya ka samu Yarinya me hankalin ta, dukda nagani tana nuna ƙuruciyar wasu lokutan amma ka bita a hankali Yarinya ce me biyayya, ina jin nauyin ta ne amma ba dan haka ba seka koma da kayan Abincin nan, ka kula da matar ka, ka sauke dukkanin haƙƙoƙin ta da yake kanka"

Ammar yace Insha Allah suka yi Sallama da Abba ya bar Mufeeda a gidan su.

Bayan tafiyar Ammar ya kira Halima a waya, tana ɗagawa yace
"kiyi wa Mufeeda kitso kafin in dawo ɗaukar ta"
Ta amsa masa da "to"

Mufeeda da Halima ne suka zage suka tsiri alkubus, Yadda Mufeeda take aiki ba ƙyuya babu ganda ba ƙaramin bawa Mahifiyar Ammar mamaki tayi ba.

Da azahar suka kammala girki, suka gyara ko ina, aikuwa sunyi santin girkin nan sosai, Halima tayi wa Mufeeda kitso ƙanana masu kyau ba tare da ta gaya mata Ammar ne yace ayi mata ba, Bayan sun gama kitson Kuma tai mata jan lalle, kaman wata amarya tayi kyau sosai.

Ta samu food flask ta ɗibarwa Ammar Abincin, ta ajiye masa se bayan sallar isha'i sannan Ammar yazo ɗaukan ta, taji daɗin wuni a gidan su Ammar dan sun mata kara suka nuna tamkar su suka haifeta, sosai suka karrama Mufeeda.


Da zasu tafi Abba ya kira Ammar ya nuna masa Akuya Aure ɗaya da kaji masu ƙwai yace ya bawa sirikarsa, za'a cigaba da kula mata dasu anan.
Ammar yace "ba shakka an gode, to ni wanne ka bani?"
Abba yace "kai sau nawa ina baka dabba, idan kaza ce ka yanka ka cinye abarka, ai bazan kuma baka ba"

Mufeeda tai murmushi har ƙasa ta durƙusa tana yiwa mahaifin Ammar godiya.
Abba yace "bakomai 'yar Auta, Allah ya baku zaman lafiya ya ƙara muku ƙaunar juna, muma mungode sosai"

Umma ma seda ta haɗawa Mufeeda su tsintsiya da manyan jakar omo, sannan suka yi sallama.

Seda Ammar ya biya da ita gidan Yaya Maryam ta gaishe ta, taita mita akan meyasa be kawo ta da wuri ba se a daren nan, suka bata nata kayan da suka kawo mata sannan suka tafi gida.

Suna komawa Mufeeda ta gabatar masa da Abincin da tazo dashi, seda Ammar ya kwashi girki ya ƙoshi sannan yace
"waye yayi girkin nan?"
"Nice" ta bashi amsa

Ya basar yace "shiyasa beyi daɗi ba"

Ta kalle shi tace "Abba dai yace yayi daɗi"

"Ai dan karki ji babu daɗi ne yasa shi cewa yayi daɗi, amma babu daɗi"

Seda yaga ya ƙoshi ya wani fara beyi daɗi ba, tattare Kwanukan ta fara yi tana tura baki, se yanzu ya lura da hannun ta da yayi Jawurrr da lalle, ƙurawa hannayen ta ido yayi, ta kwashe Kwanukan ta, ta kai kitchen ta wanke tai tafiyar ta ɗaki.

Ƙin zama tayi a falo, shi kam Ammar dariya ma ta bashi, ita a dole fushi take.

Har ƙarfe goma Ammar yana falo yana kallon wani Film a Bollywood, ba zato babu tsammani yaga Mufeeda ta ɗare cinyar sa, shi a zaton sa tuni tayi bacci, se ƙamshin turare take, rigar ta ta bacci iya gwiwar ta,

Please Login or Register in order to submit comment