Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fashe da kuka.

"Mufeeda idan kinsan akwai matsala ki gayamin, idan wani abun yake miki ki faɗa tun wuri ayiwa tufkar hanci, nasan halin Ammar sarai ɗan uwana ne amma zama dashi se me haƙurin gaske ki gayamin idan akwai matsala"

Shiru Mufeeda tayi sannan ta ɗago ta kalli Anty Maryam tace
"Anty Maryam gaskiyar kenan na gaya miki ki yarda dani" tai maganar tana ƙoƙarin maida ƙwallar dake ƙoƙarin zubo mata, ganin Mufeeda bata da niyyar gaya mata abunda ke damun ta yasa ta ƙyaleta, aka jima tai mata sallama ta tafi.

Kusan gaba sosai Ammar yake da Mufeeda ba tare da tasan laifin da tayi masa ba, ko haɗa hanya suka yi, idan yayi mata tsawa se tayi dana sanin haɗuwar da suka yi.
Gaba ɗaya ya zame mata tamkar wani dodo, duk da jin kansa amma yanayin yadda suke kasancewa tare, suci Abinci tare yanayi ne da yake matuƙar sata nishaɗi, Amma ƙirƙiri yanzu fargabar ganin sa ma take yi balle su haɗa hanya, gashi ita bata san laifin da tayi masa ba.
Duk wani abu da ya kama na ciyar wa be fasa ba, Amma ba zata dafa yaci ba ko gaisuwa bata haɗa su.
Sosai zaman da suke yi yake damun ta ya kamata ace idan laifi tayi masa ya gaya mata, dan haka ta yanke shawarar zuwa ta same shi taji laifin da tayi take fuskantar wannan hukuncin me matuƙar tsauri.

Ɗakin sa taje ta same shi yana shiri ze fita, ɗagowa yayi ya kalleta ya ɗauke kansa, jiki a sanyaye tace

"Yaya Ammar ka dubi zatin Allah ka gayamin laifin da nayi maka kake min wannan hukunci"

Banza yayi mata ya ɗau wayarsa ya saka a Aljihu yana ƙoƙarin kewaye ta ya wuce, tare shi ta kuma yi cikin kuka tace
"Yaya Ammar zuciya ta ba zata iya ɗaukar wannan hukuncin ba, dan Allah ka gayamin me nayi maka haka?"

A fusace yace "get out from my sight bana son wannan salon yaudarar taki, 'yar ƙanƙanuwar yarinya dake amma kin iya yaudara"

Zubewa tayi akan gwiwoyin ta tace "Naji na yadda amma dan Allah kayi haƙuri dukda ban san laifin da nayi maka ba, Amma kayi haƙuri"

Ture ta yayi daga gaban sa yasa kai ya fice, da gudu ta kuma binsa falon tana riƙe rigar sa tana kuka.

Fizge rigar sa yayi yace
"Karki ƙara riƙe min riga munafuka mayaudariya, seda na yadda dake zaki tozartani ki bani kunya"

"Yaya Ammar me yayi zafi kake kirana da wannan miyagun maganganun? Wani laifi ne haka na aikata? A zaman mu da kai bana tunanin na aikata wani kuskure dana cancanci wannan kalmomin daga bakin ka"

"Tambaya ta ma kike yi? Da Aurena a kanki kike Soyayya da wani a waje, kin san zaki yi soyayya da wani dan me kika dage sekin Aureni kike yaudara ta da cewar kina sona, kinsan me kuɗi kike burin Aure meyasa kika Aureni kikemin daɗin bakin cewar ni kike so ba abun hannu na ba? An kiraki a waya na ɗaga wani ɗan iska yana faɗin yayi missing ɗinki, na fita sallar Asuba an tareni ance an ganki ƙiri ƙiri da wani me mota kina zance, akan me zakimin haka? Har yanzu zuciya ta ta kasa Amincewa zaki min hakan, sakamakon kalaman yaudara da kike Amfani dasu akaina, nasan da mace na Aura me hankali da inaga duk hakan bata faru ba, nayi nadamar Auren ki da nayi "

Shiru tayi seda yayi ya gama ta ɗago idanun ta da suka koma Jawur ta kalli Ammar tace
"Ba dan sharrin Soyayya ba Ammar babu abunda zesa in soka in zauna da kai da wannan halin naka, Yaya Ammar ko a kotu Alƙali yana bawa mai laifi damar kare kansa koda kuwa a gaban Alƙalin me laifi ya aikata laifin, ba kai ya kamata ka yi dana sani ba, ni ya kamata inyi dana sanin yin Aure, A iya zamana da kai na gane abubuwan da mahaifiya ta da 'yan uwana suke jiye min, Yaya Ammar ko dan Darajar Soyayyar da nake maka ya kamata kayi min Adalci ban cancanci jin wannan kalaman daga bakin ka ba, a zaman mu da kai a Alkhairaina guda nawa ka yaba? Amma yau akan kuskuren da baka da tabbas na Aikata ka hukunta ni da kalamai masu muni, kalaman da bazan manta ba har in koma ga Allah, Shikenan Nagode sosai, sannan bazan gajiya ba Allah ya baka haƙuri, idan ka sakko daga Fushin nayi maka bayanin abunda ya faru, Adawo lafiya Allah ya kiyaye hanya "

Tana gama maganar ta tafi ɗakin ta tana shehssheƙar kuka me tsuma zuciya, seda Mufeeda tai wannan maganganun sannan Ammar ya dawo hayyacin sa ya fara tunanin Anya kalaman da yayi Amfani da su sun dace? Take kuma yaji kamar be kyauta ba gaba ɗaya jikin sa yayi sanyi, tabbas ya kamata ya bincika kafin yayi mata hukunci, haka nan ya ɗau key ɗin babur ɗin sa ya fice.

Bayan fitar sa Mufeeda gaba ɗaya ji tayi ta tsani zaman gidan, gaba ɗaya ta rasa abunda yake mata daɗi ga zuciyar ta da take ta faman bugawa da ƙarfi, miƙewa tayi tasa hijjabin ta ta ɗau wayar ta ta fice, tafiya kawai take dan wani matsanancin ciwon kai ne ke damun ta ga Jiri da take ji dan haka kawai jefa ƙafar ta take, tana fita bakin titi ta tare me Napep ta gaya masa unguwar daze kaita ta faɗa ciki tana goge Hawaye.

Akan idon Sa'idu me kayan miya hakan ta faru, dan haka ya jinjina kai yace "Yau akwai zazzafar Jarida"

Me Napep ɗin daya ɗauki Mufeeda kuwa tsoro ya fara ji karta mace masa a Babur, dan wata irin shaƙuwa take tana sauke numfashi da ƙyar, seda ya kaita har ƙofar gidan Yaya Amina, Mufeeda ta fito daga A daidaita sahu abu ya faskara dan harta fara fita daga hayyacin ta da ƙyar take numfashi.

Ƙwanƙwasa gate ɗin Yaya Amina me Napep ɗin yayi, akayi sa'a Yaya Amina ce ta buɗe, suka gaisa dame Napep sannan yace mata

"dama waccan baiwar Allah na ɗakko tace nan zan kawo ta, kuma gashi munzo ta kasa fitowa kamar bata da lafiya"

Aikuwa Yaya Amina na leƙawa ta hango Mufeeda a cikin Napep ɗin ta riƙe ƙirji, da Sauri Yaya Amina ta koma cikin gida ta ɗakko mayafi suka fito tare da mijin ta, Mufeeda na ganin Yaya Amina ta sake fashewa da kuka, suka ɗakko ta daga A daidaita sahu zuwa cikin gidan, mijin Yaya Amina ya sallami me Napep.



A tayani Share ba dan halina ba 😍😍😜


NAGA NAFARA ƁATAWA 'YAN TEAM ƊIN MUFEEDA RAI, ANA CEWA HAƘURIN MUFEEDA YAYI YAWA, GA WATA TAMBAYA, DA MUFEEDA BATA KASANCE ME HAƘURI BA WANI IRIN ZAMA KUKE TUNANIN ZATA YI DA WANNAN MIJI NATA ME BAUƊAƊƊEN HALI? IDAN BA TAYI HAƘURI BA TAZAMA ME YAWAN ƘORAFI YANA HAƊA SHI FAƊA SA 'YAN UWAN SA A SANNU WATARAN SE IYAYEN MIJIN TA SUN FARA JIN HAUSHIN TA.
AYIMIN HAƘURI LABARIN NE YAZO A HAKA DAN HAKA KU BIYONI SANNU A HANKALI DAN JIN YADDA ZATA KAYA
KISSA BATA NUFIN KWALLIYA DA KWARKWASA BANE, AKWAI HAƘURI DA JURIYA.

Taku har Kullum Aisha Humaira, Daddy's girl ko ince Ayshercool, ina godiya sosai da ƙauna da kuma bibiyar littafin da kuke

Domin sharhi gyara ko shawara
07063065680
✨✨✨✨
*WATA KISSAR...... *
✨✨✨✨✨

( *Sai Mata* )

*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*_A SHORT LOVE STORY_*

*Story and written by*

'''AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)
The experience writer of ABDUL JALAL'''

Na sadaukar da wannan littafin ga Ɗaukacin masoya na, wanda nasani da wanda ban sani ba

Watpad @ Ayshercool7724

What's app 07063065680

Gmail [email protected]

Please follow me on Wattpad, vote and Comment

https://www.wattpad.com/1096499534?utm_source=android&utm_medium=com.fmwhatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Ayshercool7724&wp_originator=NWkhlySuZ8Eug%2BopXFfcycv2JGS3axjaccC5%2FbUYT6YzeXAYV4ybw7FnTr8fHQDwo5ncF8TNfQfelSdeR5t0OZi0%2FKAiAcvwuLa561y0j%2BMpxBPI15z3EyzU4ZruY9KP


__Happy marriage life to my lovely friend_, __MARYAM MUSA ƁAIDU_I WISH YOU A VERY HAPPY MARRIAGE LIFE DEAR_

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                 
             
                          Page 22


Har Ammar ze share wayar ya tafi ɗakin sa se kuma ya ɗau wayar ya nufi ɗakin Mufeeda.

Yana zuwa ya tarar har tayi bacci ta dunƙule a guri ɗaya ko kayan jikin ta bata canza ba da alama dai baccin ba shiri ya ɗauke ta, fuskarta duk hawaye se ajiyar zuciya take.
Ɗan girgiza kai Ammar yayi ya zauna gefen gadon ya ɗagota ya cire mata hijjabin jikin ta, a wasu lokutan Mufeeda na da  nauyin bacci sosai dan haka ya rage mata kayan jikin ta data kwanta da su, ya ƙura mata ido ta ɗan rame sosai, Amma tubarkallah tana da kyau dai dai gwargwado, musamman idan tana bacci se yaga ƙuruciyar ta ta ƙara fitowa,  iya goshin ta ya ɗau zafi sosai yayin da sauran jikin ta yayi sanyi saboda kuka.

Ammar ya daɗe yana kallon ta yana jin wani abu na masa yawo a jikin sa ba tare da ya tabattar dame hakan ke nufi ba, a hankali ya janyo pillow ya kwantar da ita a kai yana cigaba da kallon fuskarta, sosai yake jin tausayinta be kamata ya cigaba da yi mata faɗa any how ba, hakan yana sata a cikin damuwa sosai, gefe guda wayar Mufeeda na ci gaba da vibrating, har ya miƙe ze bar ɗakin yaga vibration ɗin wayar ze iya tashin ta dan haka ya dawo ya sunkuya ya ɗau wayar, baƙuwar lamba ce babu suna ya danna alamar amsawa ya kai kunnen sa zeyi magana, shiru yayi yana sauraren abunda me wayar yake faɗa, kunnuwan Ammar ba zasu iya jure jin abunda wannan la'anannen dabe san darajar Aure yake faɗa ba, Idan kunnuwan sa ba ƙarya suka jiye masa ba to tabbas kalaman soyayya ne wanda ya kiratan yake faɗa

"tun ɗazu nake kiran ki saboda inji daddaɗar muryar ki ko da zagina kiyi in samu inyi bacci cikin kwanciyar hankali, Amma kinƙi ɗaga waya ta, kice wani abu mana mufeeda, Shikenan tunda ba zaki magana ba ɗaga wayar da kika yi ma ya tabbatar min kina lafiya, Ina son ki fiye da yadda wannan mijin naki me girman kai da baki da tabbacin yana sonki"

A hankali Ammar ya ajiye wayar, zuciyar sa tana wani irin bugu da ƙarfin gaske tamkar zata tsaga ƙirjin sa ta fito, gashin jikin sa duk ya mimmiƙe saboda ɓacin rai, ya kalli inda Mufeeda take kwance tana bacci, se faman sauke ajiyar zuciya take she's looking so innocent.

Da ƙyar Ammar yaja ƙafar sa ya bar ɗakin yana ci gaba da jin Yadda zuciyar sa take bugawa.

Ɗakin sa ya koma ya samu gefen gado ya zauna ya dafe kansa da yake jin tamkar ba nasa ba, yanzu duk iƙrarin Soyayyar da Mufeeda take masa ƙarya take, zata iya cin Amanar sa tayi soyayya da wani a waje da Auren sa a kanta, lallai mata ba abun yarda bane.

Yana wannan tunanin message ya shigo wayar sa
"KA SA IDO AKAN MATARKA TANA AIKATA RASHIN GASKIYA A BAYAN IDON KA"

Wannan shi ne ire iren saƙon da'ake yawan turo masa

"to Amma waye wannan yake turo masa saƙon? Ya akayi me turo saƙon ya samu lambar sa har yasan Matarysa tana aikata rashin gaskiya a bayan idon sa?"
Yadda Ammar ya ga dare haka ya ga rana, bacci ya ƙauracewa idanunsa.

*********************

Ƙarfe biyu da rabi na dare Saima ce kwance tana bacci yayin da gefen ta Jabir ke kwance  yana chatting, A hankali ta buɗe ido tana kallon sa ba tare da yasan tana kallon sa ba, voice message ɗin da aka turo masa ya buɗe yana saurarar, amon muryar mace ne ya fara tashi

"My Jabir i can't wait to see you as my husband, na ƙagu lokaci yayi ni kaɗai nasan me make ji akan ka, Amma ni matsala ta ɗaya gaskiya bana son zama da kishiya, bazan iya sharing ɗin ka da wata 'yar talakawa ba, Daddy ze baka gida ya canza maka mota wataƙila ma har muƙami yayi maka a cikin kamfanonin sa, Amma gaskiya ni batun zama da wata ne akwai damuwa"

Jabir yayi ƙasa da muryar sa yace
"My love karki ji komai ni kaina na ƙagu in mallake ki, dan babu wani farinciki da nake tsinta a Auren nan, Mata ta babu abunda ta iya, Ni ban san wani irin tsautsayi ya kaini na Aure ta ba, bayan ga irin ki, yanzu dai so nake ta haihu tukuna kar ace na sake ta da ciki, Amma da zarar ta haihu zan san abun yi"

Ba shiri Saima taji abunda yake cikin ta yayi wata irin juyawa saboda maganganun da Jabir yake yi, A hankali ta miƙe zaune saboda nauyin cikin dake jikin ta, Jabir yana kallon ta haka ta dinga bin bango da ƙyar ta shiga banɗaki, tana shiga ta durƙushe ta dinga zubar da Hawaye tana tuna yadda ta ƙaunaci Jabir, lokacin da take hasashen tayi dacen miji, take tunanin duk cikin mane manta Jabir ne ze riƙe ta ya kula da maraicinta, se gashi Jabir ɗin nata ya sauya komai ya dagule mata, babu wanda zata kaiwa kukan ta se Allah, ba uwa ba Uba, a hannun ƙanin mahaifinta ta girma, cike da tsangwama da bautarwa basu da burim da ya wuce suga ta wulaƙanta dan haka batun ta kai kokenta gidan su be taso ba, ta daɗe a banɗaki tana kuka sannan ta fito, yanzu ma a durƙushe ta dawo ta sa hannu ta ɗau fulo ta kwanta a ƙasa Jabir yana kallon ta amma be ce mata uffan ba ya ci gaba da Chatting ɗin sa.

Bacci ya ƙauracewa idanun Saima, har ƙarfe uku na dare Sannan Jabir ya kwanta, a hankali ta kuma jan jikin ta zuwa banɗaki tayi alwala ta koma ɗaya ɗakin ta shimfiɗa sallaya, nafila tayi ta idar ta ɗaga hannun ta zata yi Addu'a amma ta kasa se kuka me taɓa zuciya da ta dinga yi.

*******************

Babban abunda ya bawa Mufeeda mamaki be wuce yadda tun Asuba da Ammar ya fita salla be ƙara dawowa ba kuma be fita da babur ɗinsa ba, har ƙarfe sha ɗaya na safe babu shi babu alamar sa, Wayarta ta ɗauka ta kira shi amma sam yaƙi ɗagawa daga ƙarshe ma ya kashe wayar sa ta dena shiga.

Addu'a Mufeeda ta dinga yi na Fatan Allah yasa na lafiya dan be taɓa yin hakan ba, Mufeeda ko karyawa ta kasa yi, dan damuwar da take fama da ita kwanan nan, da yawan kukan da take yi yasa take fama da ciwon kai dan sam ko Abinci ba ta iya ci.

Wasa wasa har Azahar babu Ammar babu ɗuriyar sa, da ƙyar ta dafa tea ta sha kaɗan ta ajiye gaba ɗaya hankalin ta a tashe yake.

***************

Maman Nur ta saka mijin ta a gaba "wai ni da kaje ka samu wannan me Napep ɗin game da abunda matar sa tazo tayi min me yace maka, baka yi min bayanin komai ba fa"

Baban Nur yace  "to me zance miki labarin bame daɗi bane, dan naga alamar baya son laifin ta, cemin yayi wai ba yadda zata tayar da faɗa idan ba wani abun akayi mata ba, shi matar sa ba fitinanniya bace"

"kan bala'i haka ma yace, to kai me kace masa?"

"Me kuwa zance masa? Nace masa dai ya ja mata kunne"

"Amma wallahi ka fiye abun haushi, wato kaine baka kishi na ko? maimakon kayi masa rashin mutunci ka nuna masa ɓacin ranka akan abunda tayi, kawai se kace yaja mata kunne, be yadda tayi laifi ba ta ina ze ja mata kunne? Tunda kai ba zaka iya ba ni zanyi, wallahi se fitowa da rana ya gagari yarinyar nan dani take zancen zan sauke mata wannan girman kan nata"

"Akan me zaki hana ta fitowa da rana? Ke kika ajiye ta?"

"kaga ba ruwan ka dan Allah kasa ido kawai, zata gane bata da wayo zan koya mata hankali yadda gaba in ance  idan ta ganni tayi min rashin mutunci seta gudu da ƙafar ta"

******************
Mufeeda ta tsorata sosai da rashin dawowar Ammar gida, gashi har magariba tayi amma babu shi babu alamar sa, waya ta ɗauka tana ƙoƙarin kiran Umman Ammar ta sanar mata abunda yake faruwa amma wayar taƙi shiga, shiru tayi ta fara tunanin ko wani abunne ya same shi, Alamar buɗe gate taji, dama idan ya dawo yana da key, yake sawa ya buɗe kawai.
Da sauri ta tashi ta fito tsakar gida, Ammar ne ya shigo fuskar nan tasa tamkar kumurci babu alamar Afuwa, tana ganin yanayin sa gaban ta ya faɗi, Amma ta dake tace "lafiya kuwa Yaya Ammar daga tafiya sallar Asuba na neme ka na rasa? Hankalina fa ya tashi sosai"
Wani mugun kallo yayi mata dase da 'ya' yan cikin ta suka juya, ya wuce ta ya shige falo, da ya shiga ɗinma be tsaya a falon ba ɗakin sa ya wuce kai tsaye.
Bata karaya ba tabi bayan sa dukda irin mugun kallon da yayi mata.
"Mijina dan Allah ka gayamin ina ka tafi haka?"
"get out from here" yai mata wata irin tsawa da ta razana ta matuƙa.
"Yaya Ammar daga tambaya sekamin tsawa haka?"
"Ki fita tun ban tattaka ki a gurin nan ba, ki fitar min daga ɗaki nace"
Gaba ɗaya jikin ta rawa yake, ga Yunwa ta wuni ba taci Abinci ba ga ɓacin rai ga wannan masifar da Ammar yake da bata san dalilin ta ba, wani irin jiri ne yake nema ya kada ita ƙasa dan haka ta dafe kanta ta fita.

Gaba ɗaya hawayen ma yaƙi zubowa se zafi da ƙirjinta yake yi, bata taɓa tsammanin halin Ammar ya kai haka ba, bata taɓa tunanin zafin zuciyar sa ya kai haka ba? Shikenan laifi wanda tasan tayi da wanda ba tayi ba se ya ɗora mata yaita faɗa, ko'a ɓata masa rai a waje yazo ita ya sauke mata, abun ya fara damun ta.

********************
Sosai Saima take dana sanin sanin Jabir a rayuwar ta, gaba ɗaya taji Aure ya fita daga ranta, ta ɗauki shawarar Mufeeda idan Jabir yana mata rashin mutunci ƙyale shi take bata tanka masa, tsanar da tayi wa Jabir a yanzu harta kai ga taji bata ƙaunar cikin dake jikin ta, dan haka ta ƙudurce a zuciyar ta ranar data haihu zata karɓi takardar sakin ta daga hannun Jabir tun kafin yaci zarafin ta ya kore ta akan 'yar masu kuɗin da yake hari, yake ganin zasu yabke masa talauci idan ya auri ' yarsu, sannan ta ajiye masa abunda ta haifa idan yasa kowa ze Auro tazo ta kula masa da ɗansa amma ba zata shayar da abunda ta haifa ba, Abunda Jabir yake mata yasa gaba ɗaya haushin maza take ji ta ƙudurce a ranta ba zata ƙara yin wani Auren a rayuwar ta ba, idan har Jabir da suka shafe shekaru suna soyayya ze mata haka bayan Aure to bazata sake Aure ba dan babu sauran wani namiji me imani da yayi saura duk haka halin su yake.

*******************
Mufeeda tana ta fama da damuwa ta kasa gayawa kowa dan gani take hakan tamkar tona Asirin Auren tane, kuma koda ta gayawa iyayen ta aka sasanta komai ze iya wucewa a gurin ta, Amma ba lallai ya wuce a gurin iyayen ta ba.
Tana kwance akan kujera bata jin daɗin komai aka ƙwanƙwasa ƙofa, jiki ba ƙwari ta tashi taje buɗe, tana buɗewa taga Anty Maryam ce, Yayar Ammar, murmushin dole Mufeeda ta ƙaƙalo tayi wa Anty Maryam tare da yi mata maraba.

Suka gaisa Maryam tace "kin ganni unguwa naje na dawo naga na biyo ta layin unguwar ku nace bari inzo mu gaisa"

"Aikuwa naji daɗi Anty Maryam, dama baya nan duk kaɗaici ya dameni, bari in dafa miki Abinci"

"A'a Mufeeda ba sekin wahalar da kanki ba, kin ganni seda na cika cikina na fito"

Nan suka shiga hira da Mufeeda, Amma Anty Maryam ta karanto damuwa ɓoye a bayan murmushin da Mufeeda take yi, ta ɗan dube ta tace
"Mufeeda baki da lafiya ne?"
"A'a Anty Maryam lafiya ta ƙalau"

"Amma naga kinyi wannan ramar haka? Kodai wani abun yana damunki ne?"

Wani murmushin dolen Mufeeda ta kuma yi tace "Ba abunda yake da muna fa ke kika ga na rame, amma komai lafiya" tana magana ne yayin da ƙasan zuciyar ta ji take kaman ta fashe da kuka.

"Mufeeda idan kinsan akwai matsala ki gayamin, idan wani abun yake miki ki faɗa tun wuri ayiwa tufkar hanci, nasan halin Ammar sarai ɗan uwana ne amma zama dashi se me haƙurin gaske ki gayamin idan akwai matsala"

Shiru Mufeeda tayi sannan ta ɗago ta kalli Anty Maryam tace
"Anty Maryam gaskiyar kenan na gaya miki ki yarda dani" tai maganar tana ƙoƙarin maida ƙwallar dake ƙoƙarin zubo mata, ganin Mufeeda bata da niyyar gaya mata abunda ke damun ta yasa ta ƙyaleta, aka jima tai mata sallama ta tafi.

Kusan gaba sosai Ammar yake da Mufeeda ba tare da tasan laifin da tayi masa ba, ko haɗa hanya suka yi, idan yayi mata tsawa se tayi dana sanin haɗuwar da suka yi.
Gaba ɗaya ya zame mata tamkar wani dodo, duk da jin kansa amma yanayin yadda suke kasancewa tare, suci Abinci tare yanayi ne da yake matuƙar sata nishaɗi, Amma ƙirƙiri yanzu fargabar ganin sa ma take yi balle su haɗa hanya, gashi ita bata san laifin da tayi masa ba.
Duk wani abu da ya kama na ciyar wa be fasa ba, Amma ba zata dafa yaci ba ko gaisuwa bata haɗa su.
Sosai zaman da suke yi yake damun ta ya kamata ace idan laifi tayi masa ya gaya mata, dan haka ta yanke shawarar zuwa ta same shi taji laifin da tayi take fuskantar wannan hukuncin me matuƙar tsauri.

Ɗakin sa taje ta same shi yana shiri ze fita, ɗagowa yayi ya kalleta ya ɗauke kansa, jiki a sanyaye tace

"Yaya Ammar ka dubi zatin Allah ka gayamin laifin da nayi maka kake min wannan hukunci"

Banza yayi mata ya ɗau wayarsa ya saka a Aljihu yana ƙoƙarin kewaye ta ya wuce, tare shi ta kuma yi cikin kuka tace
"Yaya Ammar zuciya ta ba zata iya ɗaukar wannan hukuncin ba, dan Allah ka gayamin me nayi maka haka?"

A fusace yace "get out from my sight bana son wannan salon yaudarar taki, 'yar ƙanƙanuwar yarinya dake amma kin iya yaudara"

Zubewa tayi akan gwiwoyin ta tace "Naji na yadda amma dan Allah kayi haƙuri dukda ban san laifin da nayi maka ba, Amma kayi haƙuri"

Ture ta yayi daga gaban sa yasa kai ya fice, da gudu ta kuma binsa falon tana riƙe rigar sa tana kuka.

Fizge rigar sa yayi yace
"Karki ƙara riƙe min riga munafuka mayaudariya, seda na yadda dake zaki tozartani ki bani kunya"

"Yaya Ammar me yayi zafi kake kirana da wannan miyagun maganganun? Wani laifi ne haka na aikata? A zaman mu da kai bana tunanin na aikata wani kuskure dana cancanci wannan kalmomin daga bakin ka"

"Tambaya ta ma kike yi? Da Aurena a kanki kike Soyayya da wani a waje, kin san zaki yi soyayya da wani dan me kika dage sekin Aureni kike yaudara ta da cewar kina sona, kinsan me kuɗi kike burin Aure meyasa kika Aureni kikemin daɗin bakin cewar ni kike so ba abun hannu na ba? An kiraki a waya na ɗaga wani ɗan iska yana faɗin yayi missing ɗinki, na fita sallar Asuba an tareni ance an ganki ƙiri ƙiri da wani me mota kina zance, akan me zakimin haka? Har yanzu zuciya ta ta kasa Amincewa zaki min hakan, sakamakon kalaman yaudara da kike Amfani dasu akaina, nasan da mace na Aura me hankali da inaga duk hakan bata faru ba, nayi nadamar Auren ki da nayi "

Shiru tayi seda yayi ya gama ta ɗago idanun ta da suka koma Jawur ta kalli Ammar tace
"Ba dan sharrin Soyayya ba Ammar babu abunda zesa in soka in zauna da kai da wannan halin naka, Yaya Ammar ko a kotu Alƙali yana bawa mai laifi damar kare kansa koda kuwa a gaban Alƙalin me laifi ya aikata laifin, ba kai ya kamata ka yi dana sani ba, ni ya kamata inyi dana sanin yin Aure, A

Please Login or Register in order to submit comment