Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kiran ta, taje ta sameshi shida Maman ta a zaune.

"Gani Baba"

Baba yace "Mufeeda yau gidan su Ammar suka kawo kuɗin auren ki, sun kawo kuɗin su har naira dubu hamsin, ɗazu da safe kina makaranta kuma nayi dukkanin binkicen da ya kamata inyi akan sa an tabbatar min da cewar mutumin kirki ne ɗan gidan masu mutunci dan haka na tsaida ranar Auren ku nan da watanni shida"

Da sauri ta kalli Baban nata tace "to ai lokacin ban gama makaranta ba"

Baba yace "Eh wannan shekarar zakiyi Waec i know you can do it, zan sama miki gurin extra lesson, kuna kammala jarrabawa mu sha biki"

Se a lokacin wata kunya ta saukar mata, ta ɗanyi murmushi ta tashi ta fita ta bar ɗakin

Mama kam gaba ɗaya ranta a ɓace yake, gani take ta ko ina an cutar mata da yarinya, ga ƙarancin shekaru da Mufeeda ke da su, ga yarinyar ta babu laifi tana da kyau, sannan izifi talatin ne na Al'qur'ani akan ta amma ace dubu hamsin za'a bata kuɗin aure kamar wata bazawara.

Tunda aka kawo kuɗin Mama take mita, Amma ɓangaren Baba yaji daɗin ganin 'yan uwan Ammar, mutane ne masu karamci da yakana, mahaifin Ammar da kanshi ya sanar da Mahaifin Mufeeda cewar "Ammar yayi karatun sa na zamani, Amma rashin aikin yi ya sashi fara sana'ar babur ɗin a daidaita sahu, ya tabbatarwa mahaifin Mufeeda cewar Ammar baya raina sana'a komai ƙanƙartar ta idan ya samu zeyi yasan Insha Allah ze iya riƙe Mufeeda.

Da Baba ya gaya musu ya saka watanni shida lokacin biki ƙanin mahaifin Ammar yace "yallaɓai wata shida ai bamu gama shiri ba abunka da masu ƙaramin ƙarfi"

Baba yace "karku damu, duk abunda ya sawwaƙa kuka kawo zamu karɓa karku takura kanku, aini duk wanda yake son ɗana ya gama min komai, Ammar ɗana ne komai ya kawo Allah ya amfana zan bashi Auta"

Baban Mufeeda yaji daɗin wannan bayanin dan yana son mutane masu gaskiya.

Ganin da Baba yayi Mitar Mama taƙi ƙarewa ya sashi fara yi mata nasiha

"Sarah wani lokacin bakinmu da kuma ayyukan mu suke lalata auren yaranmu, aure beje ko'ina ba aita samun fitintunu, yanzu wannan kushewar da kike wa auren nan ze iya jefa rayuwar Auren ta cikin hatsari, kina maganar duk yaranki babu wadda ta auri talaka kaman Mufeeda, seki ga kaf yaran babu wanda ya samu kwanciyar hankali a gidan aure kamar ta, Sarah Auren me zuciya yafi auren me dukiya, dan Allah kidena kushe auren nan kisa musu albarka kawai "

Ita dai Mama jinsa kawai take amma sam bata ƙaunar auren nan.

Mufeeda kam murna ta dinga yi, tana faɗin
" Yaya Ammar har yana da ƙarfin daze iya bada dubu hamsin kuɗin aure na? Alhamdilillah amma me yasa be gayamin za'a kawo kuɗin ba? "
Har ta ɗauki waya zata kira shi, ta tuna wulaƙancin da yayi mata yace "mata jaririya kuma ƙwaila" fasa kiran sa tayi ta tura masa saƙo



  "Yaya Ammar Jaririyar ka tayi mamakin kuɗin da'aka kawo mata, dama darajar ta ta kai haka a gurinka?
Jaririya na godiya, Allah yasaka maka da alheri, Allah ya ƙara Arziki da rufin asiri, nagode sosai Yaya Ammar ɗina"



Tana gama tura masa saƙon ta kira Yaya Amina a waya dan sunfi shiri da ita.

***************


Tunda Baba suka tafi kai kuɗin nan Ammar ya rasa meke masa daɗi daya tuna se yaji wata damuwa ta mamaye zuciyar sa, tunda ya fita da safe be kuma komawa gidan ba se dare.
Yana zuwa kuwa ya tarar da Abba a tsakar gida yana jiran sa.

Ba walwala haka ya shiga gidan, Abba yace "Yawwa dama kai nake jira, naga yau tunda ka fita sam baka dawo gidan ba, balle kaji yadda muka yi da gidan su matar ka"

Ammar a ransa yace "Ji Abba da ɗigimi wai Matata"

Ammar yace "to gani na dawo"

Abba cikin fara'ar sa yace "gaskiya Ammar iyayen yarinyar nan suna da dattako, dana ga gidan su na zata mahaifinta ze raina abunda muka kai, Amma yaita murna yana sa Albarka, dukda banga yarinyar ba naji har raina ina ƙaunar ta, Allah ya sanya muku Alkhairi, Baban ta yace ya saka watanni shida insha Allah za'ai bikin "

"wata shida Baba me nake da shi daza'a saka biki nan da wata shida?"

"Yana hannun Allah Ammar, munyi wa mahaifinta magana akan hakan yace duk abunda kake da shi ka bayar Allah ya amfana, kuma muma ba samaka ido za muyi ba zamu tallafa maka da abunda ya samu, fatanmu dai ka riƙe yarinyar nan Amana"

Shiru Ammar yayi bece komai ba, wannan wane irin lamarine yazo masa a gaggauce haka, ba shiri ba komai abubuwa se faruwa suke.

Umman Ammar ta fito daga ɗaki tana faɗin "Ai Baban Ammar a jikina ina jin Allah ya karɓi addu'armu Ammar ya dace da matar ƙwarai samun irin su ita kanta yarinyar da iyaye masu dattaku wahala yake a yanzu, nidai har raina nake son batun Auren nan Allah ya nuna mana lokacin"

Ammar bin mahaifiyarsa yai da kallo a ransa ya maimaita "wai matar ƙwarai dan basu ga yarinyar ba befi a saka zani a goye ta ba"

Shidai Ammar be kuma cewa komai ba ya miƙe ya fice ya bar gidan.

Kai tsaye ɗakin Jabir ya wuce, yana zuwa ya tarar Aminu ma yana can, yana zuwa be kula su ba ya samu guri ya zauna.
Gaba ɗaya suka bishi da kallo Aminu yace
"Mutumin ya akayi ne? Ya muka ganka a haka?"
Shiru ya musu yana jan ƙaramin tsaki, se wani huci yake bayan 'yan mintuna ya kuma jan tsaki sannan yace
"Kuɗin Aure Abba ya kaimin"

Jabir yace "what are you serious Man? Kai wallahi dani mace ne se nayi guɗa, Alhamdilillah"

Aminu yace "to kuma menene abun ɓata ran abun farinciki ya same ka sannan kazo kana cunkushe mana fuska"

Jabir yace "wait wai meyasa baka gaya mana za'a kai kuɗin aurenka ba? Wace me rabon ce ta rabauta da samun a very hardworking man as you?"

Seda Ammar ya kuma tsaki yai musu bayanin komai sannan ya ɗora da cewa "ni faruwar abun har tsoro yake bani ji yadda komai ke faruwa cikin gaggawa"

Aminu yace
"Ammar da yawa suna neman damar daka samu basu samu ba, a wannan marrar ka bawa yarinya budurwa dubu hamsin kuɗin aure iyayen ta su karɓa da murna har suce komai Allah ya hore ma ka kawo zasu baka gaskiya kayi dace"

Ammar yace "wacece budurwar? Ana gaya muku ƙwaila ce kuna wani surutu"

Jabir yace "kai Ammar kai duk wannan ne ya dame ka? Ba'a nan take ba ɗan nuna mana hoton ta mu gani mana muga wai me yasa ka damu da cewar ƙwaila ce"

"Ni bani da hotonta sedai akan dp ɗin ta" ya faɗa yana cunkusa fuska

Yana ɗakko wayar sa yaga message ɗin ta tana godiyar ya kai kuɗin auren ta dubu hamsin.

Shiru yayi yana wani tunani, buɗe what's App ɗinsa yayi ya nuna musu hoton ta na kan DP ɗin ta, ta canza hoto, iya fuskarta ne kawai akai tayi murmushi.

Aminu yace "wow Masha Allah, wallahi Ammar karkayiwa kanka sagededuwa, see fine Baby"

Jabir yace "dan Allah in baka so, ni zan ƙara dubu hamsin abani"

Harar Jabir yayi yasa hannu ya fizge wayar sa sega kira ya shigo, Ammar ya ɗaga kiran kafin yayi magana ta fara

"Yaya Ammar ɗina, bani da lafiya Amma baka kuma cemin ya jiki ba, na turo maka message bakayi responding ba, Anyway nagode sosai ban zaci zaka bada wannan kuɗin a matsayin kuɗin aure na ba, Nagode sosai Baby na"

"What!! Baby kuma?"

Ai take su Jabir suka ƙyalƙyale da dariya dan Ammar ya tsani yaga ana wannan abubuwan.

Mufeeda tace "ba cemin kai ni jariri ya ce ba, gara in maida kai Jariri kaman ni se komai ya tafi daidai, Yaya Ammar dan Allah kazo in ganka please"

"Ke ki rabu dani ki dena wannan rawar kan, Auren nan ba yuwuwa zeyi ba, ni bazan auri ƙaramar yarinyar mara Aji ba kamar ki ba bana son shirirta"

Mufeeda ta kwantar da muryarta cikin kissa da murya me ɗaukar hankali tace

" Ammar ɗina ni kaɗai, kuma Angon ƙwaila to be insha Allah, you know what? Am very lucky daga haɗuwar mu zuwa yanzu komai yana tafiya dai dai, Amma Idan har dan nace ina sonka shine bani da Aji me zakace game da Auran Sayyada khadija da manzon Allah salallahu alaihi wassalam? Idan har kace na maka ƙanƙanta da aure me zaka ce game da Auren Sayyada Aisha da manzon Allah salallahu alaihi wassalam? Haba Yaya Ammar ɗina babu rashin aji a abunda nayi fa"

Shiru Ammar yayi, yayin da Aminu yai ƙasa da murya yace Jabir "Wallahi yarinyar nan ta fi Ammar iya siyasa, kan uba a yanayin hotonta yarinya ƙarama amma tana tsara zance"

"Baby na zan kwanta bacci ka gaidamin dasu Mama, Sannan ka cewa Abokan ka kowa ya tafi gidan su abarmin kai ka huta dan Allah"




Domin gyara sharhi ko ƙorafi
Ayshercool
07063065680

✨✨✨✨
        *WATA KISSAR...... *
                  ✨✨✨✨✨

                      ( *Sai Mata* )

         

                        

*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*_A SHORT LOVE STORY_*

*Story and written by*

'''AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)
The experience writer of ABDUL JALAL'''

Na sadaukar da wannan littafin ga Ɗaukacin masoya na, wanda nasani da wanda ban sani ba

Watpad @ Ayshercool7724

What's app 07063065680

Gmail [email protected]

     

ELEGANT ONLINE WRITER'S

             
                      Page 6



Shewa su Jabir sukayi, Jabir yace

"karki ji komai matar mu zamu tafi yanzu mu barshi ya huta"

Tana jin hayaniyar su ta kashe wayar ta tana murna, gaba ɗaya Ammar ransa ƙara ɓaci yayi yace  "Jabir meye haka wai kuke yi, sekunsa ta fara rainani meye hakan kukayi?"

Aminu yace "kai Ammar saurara tun wuri kasan abunda yake maka ciwo, wannan yarinyar kana ganin ta a haka nan gaba in bakayi wasa ba seta dinga juya ka, dan ta fika baki kai fushin kawai ka iya da zare ido"

"Allah ya kiyaye wannan abar ta juyani"

Jabir yace "ƙyale shi Aminu ze ga wannan abar ganin idon sa, abun da zamuyi yanzu shi ne, ka bamu sunan ta zamu je ayi muku sticker da keyholder za'a haɗa da chewngum wanda zata rabawa ƙawayen ta"

"Amma bada kuɗi na za'ayi wannan shirmen ba ko?"

Aminu yace "kwantar da hankalin ka da kuɗin mu zamu yi ba, da namu zamu yi dan haka akeyi, Amma lokacin da zakayi na kuɗin naka muna gefe"

Jabir yace "Ammar dan Allah kayiwa yarinyar nan hallaci, karka watsa mata ƙasa a ido ji musamman ta kira take maka godiya akan kuɗin nan dan Allah kadena wannan fushin kaman wanda za'ayiwa auren dole"

Ammar yace "to meye wannan in ba auren dolen ba?"

Aminu yace "ka gama muzuran ka a yanzu in ka shiga hannun ƙwaila se yadda tayi da kai"

Ɗaukar wayar sa Ammar yayi ya fice ya bar ɗakin

************
Haka nan badan mama taso ba ta fara shirye2 da siyayyar kayan auren Mufeeda aka sanar da 'yan uwa da abokan arziƙi an saka ranar auren Autar baba, wasu na san barka wasu na ya akayi ita za' a mata aure yanzu bayan 'yan uwan ta seda suka fara karatu (mutane kenan komai se sunyi magana)

Ɓangaren Ammar ma shiri suka fara yi sosai,' yan uwa da abokan sa na ta taya shi ƙoƙarin haɗa kayan aure, dukda baya son auren saboda Yadda iyayen sa suka ɗaukaki auren nan ya sashi dole shima yake nasa ƙoƙarin.

Yau yayyen mufeeda duk sunzo gida da yake sukanyi haka lokaci lokaci mussman lokacin farinciki, sukai ta caccakar Mufeeda akan tana murna Ammar ya bada dubu ɗari kuɗin auren ta ita dai tai musu banza taƙi kula su.

Yaya Fadeela tace "yarinya man kaza ba dai aure ba? Namiji ko gaki gashi nan, yau shiyace yana son ka yaka ƙarke balle kuma kafi damuwa dashi, inaji Mama tana mitar zuwan sa gidan nan befi uku ba amma kin manne masa ko damuwa beyi dake ba, kuɗin aure ya rasa nawa ze kawo se dubu hamsin"

Anty Murja tace  "ni ba wannan bama da ganin wannan koba a faɗa ba yafi ƙarfinki yayi miki girma maimakon ki samo dai dai ke, kin ɗakko wannan murɗaɗen kaman ɗan dambe"

Sarai Mufeeda ta gane inda zancen su ya dosa amma ta basar ta zumɓura baki tace
  "ni wallahi bemin girma ba ai ba a bayana zan dinga goya shi ba, ina ruwana da girman sa"

Fadeela tace  "Ji shashasha bama tasan me'ake nufi ba se ƙoƙarin rashin kunya, zaki cu uban ki kije ki aure shi, zakiyi bayani yadda ya kamata ba dai aure ba? Idan baki goya shi a bayanki ba zaki gane in kin shiga"

Haka suka dinga tsorata ta, Yaya Amina tace  "haba Anty Murja dan Allah, wallahi abunda kuke be dace ba ya zaku dinga razana ta, so kuke tace ta fasa? Dan Allah ku dena"

Mufeeda tace "ƙyale su Yaya Amina bazan fasa ba suyi tayi nidai ina son Yaya Ammar sosai"

Ita Amina Tausayin Mufeeda takeji sosai, rayuwar da suka yi tare su Fadeela ba suyi ta tareda Mufeeda ba.

Mama ta shigo ta same su, suka dinga caccake mufeeda wai tayi rashin kunya ga rashin aji yadda take rawar kai akan Ammar, gashi shiba Wani shahararren mutum ba amma se girman kai da isa a cikin sa.

Ƙarshe mufeeda se bar musu ɗakin tayi, dan taji dana sanin zuwan yayyen ta gidan nan.

Yaya Amina ta fita tsakar gida zata je kitchen ta zubo Abinci, ta jiyo sheshsheƙar Mufeeda a ɗaki. fasa zuwa zuba Abincin tayi ta shiga ɗakin ta samu Mufeeda ta haɗa kai da gwiwa tana kuka cikin tausaya wa Amina tace  "Mufeeda meyasa kike kuka?"

"Yaya Amina daga ke se Baba ne kawai kuke goyon bayana, Wallahi yaya Amina dana san dagaske Mama zata ƙi Ammar dana haƙura, wallahi ban san yadda akayi nake sonshi haka ba, baki ji yadda nake ji a zuciya ta ba ko sunan sa aka ambata, Amma Mama da su Anty Murja se hantara ta suke yi, idan har Mama bata son auren nan nasan idan nayi bazan zauna lafiya ba"
Mufeeda ta riƙo hannun yayarta tace "kin san wani abu Yaya Amina"

Amina ta girgiza kai cike da Tausayin Mufeeda

"Yaya Amine karki gayawa kowa, nasani Nina ke son Ammar bashi yake sona ba, Amma kullum idan na roƙi Allah abunda yafi Alkhairi se inji ina ƙara ƙaunar sa, idan na roƙi Allah ya zaɓa min abunda yake alkhairi ba son zuciya ta ba se inga al'amura na gudana yadda yakamata, ban taɓa tunanin Ammar ze amince ya kawomin kuɗin auren sa ba a haɗuwa uku rak da muka yi ba, ina da damuwowi da yakamata in tattauna da Mama ko Anty Murja amma sunfi karkata ga kushe abunda da nake so, yaya Fadeela harda wai zan auri matsiyaci ɗan napep, naso in mayar mata amma kinga ta girmeni sosai kuma Mama zata min faɗa, Amma ita soyayyar gaskiya ai ba ruwan ta da wannan, dukda Aurena da Ammar be saɓawa addini ba, Yaya Amina dan Allah ki sani a cikin Addu'arki"

Rungume Mufeeda Amina tayi tace  "Autar Baba insha Allah zan ta yaki da addua, Sannan ni har ga Allah ina sonki da Ammar dan ni banga aibunshi ba, musamman yana da nutsuwa ba irin mashiritan matasan nan bane, me ake da namiji mara aji, Ai Ammar ɗin ki yana da class ne shiyasa yawan dariya ai bashi da amfani, karki damu da ana cewa baya fara'a yana da izza wallahi indai zaki masa biyayya kiyi Amfani da wata kissar kin gama da shi, ki dena kuka kinji"

Murmushi Mufeeda tayi tace "shiyasa nake ƙaunar ki Yaya Amina"

Bayan tafiyar su Yaya Fadeela Yaya Amina bata tafi ba saboda mijin ta bezo ɗaukar ta ba, Mufeeda kuma ta tafi Islamiyya.

Amina tace "Mama be kamata ki dinga biye su Yaya murja ba akan auren Mufeeda, Mama wasu suna nan saboda se sunyi boko sun bawa shekara talatin baya babu aure, Kuma abunda auta tayi na faɗar aure take so ba tayi laifi ba, da kuma zuwa tayi ta ɗakko muku magana fa? Mama dukkanin mu 'ya' yankine da aurar da Mufeeda cutar da itane Baba baze yadda ba, ɗazu fa kuka ta tafi ɗaki tana yi, bata jin daɗin yadda kuke kushe Ammar dan Allah mama kidena biye wa su Fadeela "

Ajiyar zuciya Mama tayi tace
"ba ƙin abun nake ba Amina Ni gani nake kaman yaron nan zata sha wuyar zama dashi ya mata girma nesa ba kusa ba, zuwan sa fa uku kacal gidan nan sam bata gaban sa ko waya banga suna yi ba"

"Mama kina tunanin akwai hijabi tsakanin mu da addu'ar kine? Tun muna yara kike mana addu'ar miji nagari, ki sawa ranki wannan shi ne mafi alkhairi a gurin auta, Mama ba kuyi tarbiyar mu akan kwaɗayi ba da son abun duniya, kuma a haka muka tashi, shiyasa kika ga Auta ma abun duniya be dame ta ba, duk abunda ta ɗaga tace tana so, to tana son sa dagaske, dan Allah mama kija Auta a jiki tun yanzu itama ki fara nuna mata zamantakewa kaman yadda muma kikayi mana, in ba haka ba ta fara iƙrarin zata fasa tunda bakya so, kuma idan ta fasa mekike tunanin za tayi gaba? "

Ajiyar zuciya Mama tayi dan jikin ta yayi sanyi tace
" hakane Amina, Allah ya tabbatar mana da Alkhairi, Amma ni auta da wanne ma zan fara mata ne? Ni ƙanƙantar ta nake gani, ta ina zan fara nuna mata dabarun zaman auren?"

Dariya Amina tayi tace " ta inda kika fara mana"

**************

Abokan Ammar suka tambayeshi cikakken sunan Mufeeda saboda sticker daza'ayi musu amma yace be sani ba

Aminu ya sha mamakin abunda Ammar ya faɗa, Jabir yace "Ammar wannan abubuwan fa da kake yawa ne, haba dan Allah ya za'ayi ace baka san cikakken sunan ta ba?"

Ammar yace "to nasani ne? Nafa gaya muku da haɗuwar mu a titi da saka auren nan haɗuwa uku ce zuwa huɗu rak ta yaya zan san sunan ta, nidai naji ana ce mata kome? Muneefa ko Mufeeda i thinks Mufeeda ne"

Aminu ya riƙe haɓa yace "tirƙashi yau nake ganin ikon Allah, Sunan nata ma baka sani ba, Allah kaɗai yasan dalilin daya haɗaku, Allah yasa itace maganin wannan haɗe ran naka"

Jabir yace "Ammar ka kira ta ka tambaye ta dan Allah"

Ammar ya kallesu "Allah ya kiyaye"

"to bamu mu semu kira ta"

Ammar ya miƙa musu wayar sa, Jabir ya ɗakko wayar sa ze ɗau lambar Mufeeda, Ammar yace
"ka kira ta a waya ta"

Haɗa ido Jabir suka yi da Aminu suka ƙyalƙyale da dariya
Ammar ya ƙara haɗe rai dan baya son raini.

Mufeeda kam tana kitchen tana wa Mama girkin dare wayarta ta fara ringing, tana ganin lambar Ammar jikin ta na rawa ta ɗaga wayar

"Hello Yaya Ammar ɗina"

Jabir yace "Ahh yi haƙuri Amaryar mu bashi bane, fatan kina lafiya?"

Yamutsa fuska Mufeeda tayi, tace "ina Yaya Ammar ɗin?"

"yi haƙuri shi yace a kiraki, cikakken sunan ki yace ki gaya mana akwai abunda za'ayi da shi"

Tura baki tayi cikin shagwaba tace "shi meyasa baze tambayeni da kansa ba? Dan Allah yana ina?"

Jabir yace "taɓ lallai abun naku nayi ne, kai ungo wayar ka"

Ammar ya haɗe rai yace "idan bazata faɗa ba shikenan ba zan karɓa ba, bana son shashanci da yarinta"

Mufeeda na iya jiyo abunda Ammar yace, ji tayi hawaye na ƙoƙarin zubo mata jiki a sanyaye tace

"Shikenan nagode sosai, jin muryarsa da nayi ya tabattar min yana lafiya nagode Allah, my regards to him"
ta kashe wayar ta.

Tausayin ta ya kama su, Aminu yace "A gaskiya Ammar ka canza salon ka, masoyi ko mahaukaci ne be cancanci wulaƙanci ba, ji yadda yarinyar nan ke murna tana ɗoki a baka waya, Amma kalli abunda kayi mata haba Ammar"

Jabir yace  "Ammar irinka idan Soyayya ta tashi kama ka ko, se mutum ya tausaya muku, irin wannan halin 'yan matan mu na Hausawa suke tsoro shiyasa basa iya nuna soyayyar su ga maza, Ammar so baya duba girma da shekaru, da yana dubawa da yayi wa Mufeeda Adalci daba ta faɗa soyayya da mutum irin ka  ba"

Sosai suka dinga caccakewa Ammar shi kuwa yayi shiru ya ƙyalesu ko uffan be ce musu ba.

*************

Daƙyar Mufeeda ta ƙarasa girkin nan ji take kaman an ɗora mata dutse a kirjin ta, bata taɓa zaton zata so wani ɗa namiji ya dinga yi mata wulaƙanci haka ba, yayin da wani sashi na zuciyar ta ke ƙara azalzalarta da ƙaunar Ammar.

Mama ce ta kira Mufeeda ɗakin ta suka zauna, Mama tace
"Mufeeda ya Saurayin naki?"
Murmushi tayi ta sunkuyar da kai, Mama tace
"yaushe kuma kika fara jin kunya ta, ɗago kanki magana za muyi, naga tunda aka kawo kuɗin nan bezo ba meyasa? Anya kuwa yana sonki"?

Da sauri Mufeeda ta ɗago tace "yana sona mana"

"to Amma ai ya kamata ai ya dinga zuwa tunda aure zakuyi, da haka zaku fuskanci juna tunda zama zakuje kuyi na dindindin"

"Mama kin san yanayin sana'ar sa baya samun zama"

Mama tace  "dukda haka idan har kana son abu yana da kyau ka dinga zaga shi kana ganin sa, yana da kyau ya dinga zuwa yana ganin ki"

Nan Mama ta dinga yiwa mufeeda nasiha game da rayuwar aure da kuma mahimmancin haƙuri, mufeeda a ranta tace
  "Mama na kenan duk wannan abubuwan na sansu tun abaya da kike gayawa su Yaya Fadeela na haddace su, amma ta yaya zan gaya miki halin da nake ciki nasan tabbas idan na gaya miki abunda ke faruwa zaki iya soke maganar auren nan ni kuma ina ƙaunar Ammar" A zahiri kuwa shiru tayi tana sauraron Mama, seda ta gama sannan ta sallami Mufeeda.


Ammar daya koma gida yana ta tunanin maganganun su Jabir, idan ya tuna yadda tayi magana a sanyaye daga ƙarshe se yaji babu daɗi Tausayin ta ya kama shi, gefe kuma zuciyar sa tace "ai ba kai kace kana son ta ba, koma menene ita taga zata iya"
Ya zauna yana hira da Umman sa a tsakar gida, Umman sa bata da zance se tsare2 da shirin yadda bikin tilon ɗanta namiji ze kasance.

Umma tace  "Ammar yaushe zaka gurin sirikata ne? Ɗazu naje kasuwa naga wata sarƙa me kyau na siyo da sauran kaya a saka mata a lefe"

Ɗan taɓe baki yayi yace
"kaman kin san tana yawan cewa a gaishe ki"

"Allah sarki yarinyar kirki, Amma baka taɓa gayamin ba, nikam Ammar ka nunamin hoton ta mana"

Be ce komai ba ya nunawa Umma hoton mufeeda akan dp ɗin ta, Umma ta karɓa tai shiru tana kallon ta a ranta tace  "tabbas yarinya ce ƙarama, Amma ina fatan ta zama mace tagari sannan sanyin idaniya ga ɗana"
A fili tace  

"tubarkallah Ammar sirikata ba dai kyau ba masha Allah, Ammar dan Allah ka riƙe yarinyar nan da Amana, jikina yana bani ita alkhairi ce a tare da kai, banda hantara da tsangwama dan Allah Ammar na san halin ka"

Halima ce ta fito daga ɗaki tana faɗin "Umma in ganta"
Ammar ya karɓe wayar sa ya shige ɗaki ba tare da Halima ta ganta ba.


Koda Mufeeda ta koma ɗakin ta, kuka ta zauna tana yi, tana goge hawaye gaba ɗaya ranta babu daɗi, wayar ta ta janyo zata kira Yaya Ameena taga miss Calls ɗin Ammar, take wani farinciki ya mamaye ta amma se wata zuciyar tace mata
"ƙila ma abokan sane suke kira bashi ba" tayi tsaki zata ajiye wayar saƙon Ammar ya shigo wayar ta

      

       "Meyasa bakya ɗaga waya?"

Kallon message ɗin take yi ya kuma kiran ta, ɗagawa tayi tasa a kunnen ta tayi shiru, ya saba idan ya kirata da karsashin ta take ɗaga wayar sa, hakan yasa shi yin Sallama dan tabattar da ko ta ɗaga, a hankali ta amsa sallamar tasa

"har yanzu baki da lafiyar ne?"

"lafiya ta ƙalau"

Ammar yace 

Please Login or Register in order to submit comment