Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

take abunda take faɗa.

Hannu yasa ya karɓa, sannan ta karɓi kayan ta, cikin iyayi tace
"yauwa ko kaifa Yayan Mufeeda"

A ransa ya maimaita "Mufeeda"
Tace "ungo wannan invitation ne, bikin yaya ta za'ayi a wannan satin dan Allah kazo kaji Yaya na"

"ban miki Alƙawari ba gaskiya, Amma Allah ya sanya Alkhairi ya basu zaman lafiya"

Wani irin kallo take masa wanda ya kasa gane kallon menene haka?

"Idan ba kazo ba bazanji daɗi ba, kuma zanga kaman kamin wulaƙanci ne, ko kuma maybe... Shikenan dai nagode ka gaida Mama, Allah ya kaika gida lafiya, ya tsareka daga sharrin maƙiya"

Ta juya ta nufi gate ɗin gidan su, yai shiru na ɗan lokaci ya shige baburin sa ya tafi.

Ɗakin Baban su ta nufa, tana zuwa ta tarar da yayyen ta na gidan Aure sun cika falon baban su da mahaifiyarsu suna ta hira ana shirye2.
Tana zuwa taje gaban Maman ta ta ajiye mata kayan ɗinkin tace

"Mama ga kayan nan, me Adaidaita sahu ya kawo min, seki dena haɗemin rai"

Wani daga cikin yayyen ta ya kalle ta

"Ahh kaga professor, kuma Autar Baba da Maman ta"

Mufeeda Ta ɗan tura baki  "Autar Baban dai, Mama tafi son Yaya akaina, kuma na fasa zama professor ana aurar da Yaya nima Aure zanyi"

Dariya suka dinga mata, Babbar yayar su tace  "kiji min yarinya da rashin kunya, kin fasa zama professor kafin kiyi auren?"

"Na fasa dan Yaya na barin gidan nan Mama zata kasheni da sa aiki, dama kaman bata sona nima Aure zanyi"

Mama tai murmushi tace "naji bana sonki ɗin, nafi son Amina ke kam baki da nutsuwa ga wauta, tunda babanki yana sonki ai shikenan, waye ma ze aure ki a haka, baki iya komai ba, se son jiki da rashin kunya, ko Saurayi baki da shi"

"Wallahi na samo Saurayi, me Adaidaita sahun da yakawo min kayana nake so"

Yanayin yadda tayi maganar ne kanta tsaye da confidence ɗin ta yasa ta bawa kowa dariya, suka ɗau maganar tata shirme.


Domin gyara, sharhi, ko shawara
07063065680

Kuma yaseen ba comments se Allah ya kaimu September zan cigaba da typing.
✨✨✨✨
        *WATA KISSAR...... *
                  ✨✨✨✨✨

                      ( *Sai Mata* )

         

                         Page 2

*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*_A SHORT LOVE STORY_*

*Story and written by*

'''AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)
The experience writer of ABDUL JALAL'''

Na sadaukar da wannan littafin ga Ɗaukacin masoya na, wanda nasani da wanda ban sani ba

Watpad @ Ayshercool7724

What's app 07063065680

Gmail [email protected]



"ke bama son shirme, ubanwa ze miki wani aure, tafi kije kici Abincin dare ki kwanta" cewar Yayan Mufeeda

Baba yace "kaga Abubakar ku ƙyalemin professor auta, yadda take so haka za'ayi, tunda gidan su ne, ku yanzu duk ba 'yan gidan nan bane ba' yan karo ne"

Mufeeda tace "Yawwa Baba gaya musu, dan Mama tafi sonsu, yanzu idan muka ga dama duk korarsu zamuyi kowa ya tafi gidan sa"

"sosai makuwa Auta na"

Haka Baban mufeeda ya ci gaba da zigata tana ta zuba taɓarar ta.

*************
Mufeeda se rawar kai take tana iyayi, anata shirye shiryen biki, sati guda ta dauka ta dena zuwa makaranta se yawon rabon Katin gayya ta, komai da ita ake yi, yayin da gefe guda kullum cikin tunani take yi, zuciyar ta na son sake saka Ammar a idon ta.

Mufeeda duk kayan gyaran fatar da Amarya take yi itama se tayi, tare suka je ƙunshi da gyaran kai, komai angone ya biyawa Mufeeda yadda ya ya biyawa Amarya, gidan su mufeeda su takwas ne, huɗu maza huɗu mata, daga Yaya Amina se Mufeeda, shekaru biyar ne tsakanin Amina da Mufeeda.

Angon Yayar Mufeeda yasan Mufeeda sosai, saboda ba ƙaramar gudunmuwa ta bashi ba lokacin da yake neman Auren yayarta, ita ta taya shi campaign gurin Yayar ta, duk saurayin da Amina za tayi indai beyi wa Mufeeda ba in ta dinga kushe shi se Amina taji bata son mutumin nan sun rabu.
daga tace wancan be iya sa hula ba yana da ƙaton kai, ko kunnuwan sa sun fiye tsayi, se tace wancan ƙatuwar ƙafa ce da shi idan ta aure shi zata haifi ɗan se an je kamfani za'a masa takalmi, se tace wancan kwaɗayayye ne kullum yazo aka bashi abu se ya karɓa, harta kai ta kawo idan Amina tayi Saurayi se tace
"Mufeeda zo kiga wannan saurayin yayi kuwa?"
Mama taita faɗa tana "Amina baki da wayo, kina zaune ƙanwar bayan ki, shekara kusan biyar kika bata, Amma ita ke zaɓa miki Saurayi ki biye mata haka zakiyi ta zama a gida ba aure"

Mufeeda bata da jiki sosai, tana da hasken fata, ba doguwa ce can ba, Amma tana da kyau dai dai gwargwado, kana ganin ta kaga yarinya, Amma akwai baki, ga iyayi da rawar kai, dan kusan duk tafi yayyen ta baki, yayyen ta ba ruwan su da hayaniya a nutse suke, basu da yawan magana, Amma mufeeda ta fita zakka, ita akwai baki da neman rigima ga rashin haƙuri, shiyasa sam basa shiri da maman ta.

****************

Ammar yana zaune a tsakar gida dashi da 'yar Yayar sa Halima, Halima itace Babbar jikar gidan su Ammar, daga Yaye Umman sa ta riƙe ta.
Halima ta gyarawa Ammar ɗakin sa ta fito da invitation a hannun ta tace

"Uncle Ammar, waye ya gayyace ka biki ne?"

Seda yaga katin ya tuna, ya ɗanyi tsaki yace
"wallahi wata fitinanniyar yarinya ce ta bani wai bikin yayarta, yadda shi kawai"
"haba Uncle baza ka bikin ba? Ba kyau fa a gayyace ka walima kaƙi zuwa, Amma gayamin ko Anty na ce?"

Haɗe rai Ammar yayi yace "ke bana son shashanci, yarinya ce fa ƙarama kin girme ta"

"Amma ya akayi harta baka invitation? Wallahi uncle seka ga 'yan yaran fa munfi iya soyayya"

"kunfi iya hauka dai, koke baki isa Aure ba, ina zanje ina kula' yar da da aure nayi da yanzu na haife ta"

Dariya Halima tayi
"Allah ya ja da ran uncle ɗina, to ai da haka da haka"
Haɗe rai Ammar yayi kaman bashi ke hira ba yanzu
"Ke rufemin baki, yaushe na fara wasa dake?"
"Allah ya baka haƙuri"

Gyaran murya suka ji a soro, alamar za'a shigo, mahaifin Ammar ne ya shigo ya kalli Ammar yace

"kai dai kam kaji kunya wallahi, Allah Ammar da kai mace ne masallaci zanje in samu duk wanda yayi min in Aura masa kai sadaka, ace mutum ba zuciya duk sa'aninka da ƙannen bayan ka sunyi Aure amma kai kana zaune, se anyi magana ka kama wani kai se 'yar shekara talatin kai bazaka auri yarinya ba, dama wace yarin ya ce zata aureka, duk ka tsofe a titi ka zama tuzuru, tun wuri kayiwa kanka faɗa kafin ayi da kai kai kake yi da kanka, in ba sokake daga ga shiga guri mutane su fara kaffa kaffa da yaran su mata ba, saboda ka tsofe ka zama tuzuru ba Aure, wanda da kayi Aure tuntuni da yanzu kaima nan da 'yan shekaru zaka aurar da' ya"

Ture Abincin da yake ci yayi, dan ji yayi yana tsaye masa a wuya Ire2 wannan faɗan na mahaifinsa ba ƙaramin ɓata masa rai yake ba, ba dama ya shiga cikin gida ya zauna mahaifinsa ya dinga masa mita kenan akan maganar Aure.

Mahaifiyar Ammar ta fito daga ɗaki tana faɗin "dan Allah malam ka dinga haƙuri, Shifa Auren nan lokaci ne, kuma Alhamdilillah tunda rashin auren besa yana ɗakko maka magana a waje ba, ba ruwan sa da 'yar kowa, kuma yin Aure ai se mutum nada ƙwaƙwƙwarar sana' a ko?"

Mahaifin Ammar yace "ai dama ke kike goya masa baya yake ƙara sangarcewa, kalli kowa gidan nan yau faten wake ya sha amma shi kinyi masa girkin sa daban, shi bazeci faten wake ba, yace se ya gama karatu degree biyu yayi, yace seya samu sana'a wannan babur ɗin da yake ja be isheshi ba indai ba ƙarya ya ɗorawa ransa ba, ni anya ma ba Aljana ce ta aure shi ba?"

Ammar kam ya kai ƙarshe a ƙuluwa da irin wannan faɗan na baban sa, dan haka ya miƙe ya bar Abincin, Mama tace "Ammar Abincin fa?"
na ƙoshi ya faɗa a taƙaice yai waje
Mahaifin sa yace
"Eh haka dai, daga nan kuma ze wuce gurin bautar yahudu, gurin ƙwallon ƙafa aikin sa kenan, shi wace mace ce ma zata iya jure wannan baƙar zuciyar tasa, komai abun fushi ne a gurin sa"
Haka mahaifin Ammar ya ci gaba da faɗan sa har ya gaji yai shiru.

Ammar be koma gida ba se gurin ƙarfe tara na dare, ya zauna suna hira da mahaifiyar sa, tana ta ƙara yi masa Nasiha kan ya dinga haƙuri da halin mahaifinsa
Ammar yace "Umma wallahi na rasa me yasa Abba kaman baya son ganina? Sa ya ganni seya fara faɗa"

"Ammar ba sonka ne ba yayi ba, gaskiya yake gaya maka, a duniyar nan kafin ayi da kai kake yi da kanka, kai namiji ne kuma dukkan lafiyayyen namiji a shekarun ka ya kama ta ace ya ajiye iyali"

"Umma baƙin Aure nake ba, yanzu fa zamanin mu da naku ba ɗaya bane ba, da yawa 'yan matan yanzu me kuɗi suke so, ni kuma bani da su, ga kwalin karatu amma babu ƙwaƙwƙwarar sana' a, haƙurin da kuke dashi ku iyayen mu, matan yanzu ba haka bane a gurin su, ba kowace yarinya ce tasan menene zaman aure ba, zama ne na haƙuri wadda zata fuskanci yau in akwai gobe babu, wace yarinyar zata yadda ta aureni ina tuƙa babur ɗin sahu?"

"Ammar duk lalacewar zamani akwai na Allah Ammar akwai matan ƙwarai"

"Hakane amma duk da haka nafi son in samu macen da ta gama hankali ko bazawara ce, danni bazan auri yarinya ƙarama da bata gama hankali inzo ina fama da shashanci ba"

Girgiza kai Maman Ammar tayi tace "yaro dai yaro ne"

****************

Gidan su Mufeeda ya fara ɗaukar harami, baƙi daga sassa daban daban sun hallara ana ta shirin fara Shagalin biki, duk inda Amarya da ƙawayen ta suka saka ƙafa nan Mufeeda take maida tata, ko aike Mufeeda ƙin zuwa take balle asa ran zata taya aiki.

Aka fara Shagalin biki, kowane ranar event Mufeeda ta sha kwalliya kaman itace amarya, taji a ranta inama ace Yaya Ammar zega kwalliyar nan tata data ji daɗi, nan ta fara tunanin yadda zata samu lambar sa tare da addu'ar Allah yasa kafin agama bikin nan ko taro ɗaya ya zo mata.

Ranar ɗarin Aure aka ɗaurawa Yayar Mufeeda Aure, gida ya cika da jama'a anata shiga ana fita.

Maman mufeeda ta bata kaji da snacks akan faranti tace maza taje ta bawa wasu 'yan uwan baban su yanzu zasu juya su tafi.

Mufeeda ta fito da tray a hannun ta, anata tsokanar ta, suna ce mata professor Mufeeda sarkin rigima, da yake ƙofar gate ɗinsu an buɗe ta gaba ɗaya, hakan yasa kana hango masu wucewa, gidan su Mufeeda yana da kyau, ba babba ne can ba amma yana da tsari, yanayin Abincin da'ake shiga ana fita da shi ze nuna Akwai rufin Asiri a gidan.
Idon ta ta sauke akan Ammar, ya saka yadi Ash da baƙar hula, yana ƙoƙarin kunna babur ɗinsa.
"Kenan yazo amma be nemeni ba?"
Ai dire tray ɗin tayi bata san ma wa ta bawa ba, ta fyalla da gudu tai waje tana faɗin
"Yaya Ammar ɗina"
Juyowa yayi yana kallon inda take tahowa, purple ɗin shadda ta saka, ta sha surfani tun daga sama har ƙasa, hannun ta ya sha lalle, ga zobuna da abun hannu, tayi ɗaurin ture kaga tsiya, tayi parking ɗin gashin ta da  keta sheƙi, tayi kyau matuƙa kaman itace Amarya.

Ta ƙaraso inda yake se nishi take, ya kalleta yace
"ke bakya jin kunya kike gudu a gaban mutane?"
Ajiyar zuciya tayi tace "haba Yaya Ammar yanzu da tuni ka tafi bamu haɗu ba, harna fidda ran zakazo" tai maganar a ɗan shagwaɓe
"hmm to ai gashi nazo, ya taro?"
"Alhamdilillah"
"Allah ya basu zaman lafiya"
"Ameen Yaya Ammar, Amma ba har tafiya zakayi ba, kaci Abinci kuwa?
" No bashi nazo ci ba, nazo an ɗaura aure nayi Addu'a" yai maganar tare da shiga babur ɗin sa ze kunna, hannu ta sa ta riƙe makullin tana kallon sa.

Haɗe rai yayi yace "Ya haka? Cika min ina sauri ne"

Dukda wani uban kwarjini da yayi mata musamman daya haɗe rai, bata nuna masa ta tsorata ba ta dake tace "kai kullum cikin sauri kake ne? Ni gaskiya idan baka shigo ba bazanji daɗi ba, ya za'ayi in gayyace ka kuma ka tafi baka ci komai ba?"

Ammar yace "ke wai haka kike? Cikamin key ɗina zan tafi"

Ƙwalla ya gani a idon ta, tana zumɓura baki, tana karya wuya kaman za tayi kuka, ta ƙara riƙe key ɗin gam, ji yayi kaman ya balbaleta da masifa amma yaga ta wani nutsu ta koma kalan tausayi. Ɗan gajeren tsaki yayi yace "muje"
Murmushi tayi tareda cewa "ko kaifa"
Amma still ta cire mukullin ta riƙe a hannun ta dan karma yace ze tafi.

Cikin gida ta shiga dashi har falon baban ta, yana zaune yana gaisawa da baƙin sa tace "Babana ga Yaya Ammar wanda ya kawo min kaya na dana bari a mota na kawo maka shi ku gaisa"
Ammar ya durƙusa suka gaisa da mahaifin Mufeeda, yai masa Allah ya Sanya Alkhairi.
Baba yace
"Masha Allah, Yaya Ammar mungode fa, dan saura ƙiris Auta ta sha duka a hannun Mama, Allah ya saka da alkhairi, mungode sosai"
Ammar yace "bakomai"

Ya miƙe suka fito yace "ke bani key ɗina zan tafi"
Ta marairaice tace "dan Allah kayi haƙuri saura Mama ku gaisa ba dan hali na ba dan Allah"
Haka ta kuma Jan Ammar inda mahaifiyarta take, ya gaishe ta ya musu Allah ya Sanya Alkhairi, Nan ma Mama tayi masa godiya.

Mama tace "Mufeeda kawo masa kayan ɗaurin Auren shima"
Ammar yace "A'a a barshi yana sauri ne"
Mama tace "Ai ba'ayi haka ba, kazo mana taro kace ba zaka karɓi komai ba"
Mufeeda Ta shiga ta haɗo masa kayan ɗaurin Aure fal viva, kaji da lemuka, kayan snacks, Alewa da goro seda ta cika viva da shi, da ta fito da ledar Seda Mama ta bita da kallo ganin haukan da Mufeeda tayi, ba damar tayi magana tunda a cikin taro ne.

Yana tafe tana biye da shi har bakin Napep ɗin sa, yace
"bani key ɗina kuma bazan ƙara zuwa gidan ku ba"
"Saboda me?"
"Saboda kin fiye rawar kai, ni kuma bana son rawar kai"
"to yi haƙuri na dena"

Wani kallo yai mata sannan yace "bani mukulli na in tafi"
Miƙa masa key ɗin sa tayi, Amma ta tsaya a jikin Napep ɗin ta zubawa Ammar ilahirin idanuwan ta tana ƙare masa kallo.
A ran ta tace "Masha Allah gaskiya Ammar yana da kyau"

Ammar ya fara fusata da lamarin Mufeeda, dan dana sanin zuwa gurin ɗaurin auren ma yake, a zuciye yace
"ke Matsa zan tafi, kin sani a gaba kina ta ƙare min kallo"
Memakon taji haushin tsawar da yayi mata, sajen sa ne ya ƙara birgeta, ga ƙamshin turaren sa duk ya gauraye gurin a hankali cikin wani salo me cike da jan hankali ta furta
"Yaya Ammar"
Wani Yarrr yaji a jikin sa, tsigar jikin sa ta tashi sakamakon yadda ta furta sunan nasa, ɗagowa yayi yana kallon ta
"Yaya Ammar se yaushe?"
Kallon ta yayi galala
"kamar ya se yaushe? Me zanzo inyi miki? Kin bar kayan ki na kawo miki, kin gayyace ni biki nazo miki, me kuma ya rage?"
"Alfarma ɗaya nake so kamin Yaya na"
"Ina jinki"
Seda ta ƙara kwantar da murya cikin shagwaba tace
"Zaka min kuwa?"
Gaba ɗaya yadda ƙwailar yarinyar ke magana na nema ya jefa shi cikin wani yanayi dabe zata ba.
A ƙagauce yace "ina jinki"
Miƙa masa wayar ta tayi ta ƙara ƙasa da muryar ta tace
"dan Allah ka samun lambar ka Yaya na"
Hararar ta yayi yace
"ke bana son damu bana son shirme matsa ki ban guri, ko in bige ki da babur ɗin nan"

Noƙe kafaɗa tayi "Allah bazan tafi ba se dai muyi ta tsayuwa, ko ka bigeni da babur ɗin, kuma fa ba damun ka zanyi ba, gaisawa kawai zamu dinga yi fa"

Dafe kai Ammar yayi, wasa2 sun kai mintuna Ashirin a tsaye a gurin nan.

"ke wai bakya ganewa ne ko ba kya ji? Ki matsa nace!"

Seda hantar cikin ta ta kaɗa, Amma memakon yaga tsoro ko karaya a fuskar ta, ɗan rintse ido kawai tayi alamar bata son shouting, ta buɗe idon ta ta kalleshi, ta langaɓar da kai tace
"please Yayana nifa ƙanwarka ce why are you shouting at me? Allah bazan takura maka ba"
Ta miƙo masa tanfatsetsiyar wayar ta, ganin Mufeeda na neman ɓata masa lokaci, kuma ci gaba da tsayuwar su haka zata jefa shi yanayin da ze sha wuya, ya karɓi wayar a gaggauce yasa mata lambar sa ya miƙa mata wayar ta.
Karɓar wayar tayi tare da yin murmushi tace "Nagode Yaya na, Allah ya baka ladan zumunci ka gaida su Mama"

Ta matsa daga jikin Napep ɗin ya kunna yayi gaba yana mamakin hali irin na Mufeeda.

Ta juya zata shiga gida, ɗan Autan su Umman  ta ya kira ta, ƙarasawa inda yake tayi, ya kalleta yace
"Mufeeda waye wancan?"
"Yaya nane"
"kamar ya Yayan ki?" ɗan tura baki tayi tace "dan Allah Uncle karka tsanan ta bincike mene ne?"
Girgiza kai yayi yace "tun ɗazu Yaya ke nemanki, tace ta baki Abinci ki kaiwa ƙannen baban ku, Amma babu ke babu saƙon"
Se yanzu ta tuna dire tray ɗin tayi ta tafi gurin Ammar, taɓdijan ashe zata kaɗe a gurin Mama
"Uncle zomu koma gefe tambayar ka zanyi"
Ba musu ya bita suka samu guri suka zauna tace
"uncle dan Allah me yake sa kaji kana tunanin mutum? Ko ka dinga son ganin sa ko yawan mafarkin sa"
Murmushi yayi yace "Autar Baba kenan, Soyayya ke kawo haka"
Murmushi tayi ta miƙe tace "nagode uncle" tayi gaba abun ta.

Mama a ƙule take da Mufeeda, Amma saboda taro bata bi ta kan ta ba ta ƙyaleta se an gama biki.

Aka gama biki dare yayi za'a kai yayar Mufeeda ɗakin ta, aka kaita gurin Baban su yai mata nasiha sosai, se kuka take kowa ya shigo se yayi wa Amina nasiha akan Aure wannan nayi wancan nayi.
Amina ta rungume Mufeeda tana kukan zata rabu da 'yar uwata dan sun shaƙu sosai.
Mufeeda idon ta ƙyar babu alamar hawaye tace "haba Yaya dan Allah kidena kukan nan, haba se kanki yayi ciwo? Ai ni yakamata inyi kuka bake ba, dan kina tafiya zan shiga uku da aiki a gidan nan, dan Mama ba zata bari in huta ba, dan ta tsani taga ina hutawa, wallahi ina candy zanyi Aure in bar mata gidan "
Wasu nawa Mufeeda dariya wasu na mamakin fitsarar ta.
Wata ƙanwar kakar su ce na ƙauye suka shigo da 'yan uwan su, suka fara yiwa Amina Nasiha akan aure, buɗar bakin mufeeda se cewa tayi

"Dan girman Allah ku kyale ta haka Inna haba tunda kuka zo ake abu ɗaya kuke maimaitawa ai ta haddace, abu ɗaya kuke nana tawa yi nayi bari na bari, wannan ai tun zamanin ku aka dena wannan yi nayi bari na barin,"

"Ubanki Mufeeda kinji ko?" ta jiyo muryar Mama, sam bata san Mama ta shigo ɗakin ba.

Jan bakin ta tayi tai shiru, Mama tace
"inna Ladidi ga motocin can sunzo, kuje a raka ta, Amina na Allah ya bada sa'a"
Ƙara fashewa da kuka Amina tayi, Mufeeda tace
"Mama dan Allah su Inna Ladidi su hau wata motar, ya za'ayi a haɗa ta da tsofaffi su ƙara samin ita kuka, mota ɗaya zamu hau nida ita in rakata"

Mafici Mama ta ɗauka ta jefi Mufeeda amma ta kauce Mama tace
"Babu gidan uban da zaki, kina nan dama a ƙule nake dake, zaki gamu dani ne, fitsararriya"

Seda Mufeeda taga da gaske Amina tafiya za tayi sannan tasa kuka, ita kanta Mama dakewa kawai take yi, Mufeeda kam kuka sosai seda aka kaita gurin Baba shi ya dinga aikin rarrashi, dan in aka ƙyaleta Mama seta zane mata jikin ta.

Kowa ya watse ana ta aikin gyara kayan da'aka ɓata na biki, Amma Mufeeda ta maƙale a gurin Baban ta.

Mufeeda ta shiga ɗakin Mama dan ta canza kaya, Yayyen ta wasu basu tafi ba, se Washegari in an gama gyara gida za su tafi, Mama ta kalli Mufeeda tace

"zan gauraya dake Mufeeda, saboda wulaƙanci na aike ki da kaya ki kaiwa su faruku aka neme ki aka rasa bake babu kayan, kinzo da baƙo daga cewa ki bashi kayan biki kika ciko uwar viva kika bashi se kace ke kika saimin, har aka yi taron nan aka gama magana kike sani, zaki shigo hannu na zakiyi bayani uwar wauta "

Mufeeda ta tura baki tace "Haba Mama, Amma lokacin su Anty Murja in suka zo da saurayin su ai ba haka kike musu ba, ke kike cika musu ledoji fa, Amma ni dama bakya sona shiyasa zaki ce na miki wauta"

Anty Murja ce tace "Wait ƙanwa ta, ki kace me a daidaita sahu ne saurayin ki, wanda kika shigo da shi ɗazu fa? Shi kuma waye?"

Murmushi Mufeeda tayi cikin shagwaba tace "To ai shi ne fa, Shine sirikin Maman, Amma take min mita dan na bashi abu, ranar fa da ta hanani kuɗin mota kyauta ya kawoni gida, na manta kayana ya kawomin, na gayyace shi biki yazo, ai yana da kirki ko Yaya fadila"

Wata irin dariya da shewa Yaya Murja da kuma Fadila suka yi, ita kam Mama baki ta saki tana kallon wauta.

Fadila tace "kan bala'i indai wanda kuka shigo ɗazu ne me ash ɗin yadi, wallahi mufeeda yarinta da ƙuruciya ke ɗawainiya da kanki, kai! kofa ƙirjinsa baki kai ba, inaga da kaɗan kika wuce cikin sa a tsaye, kina ganin namiji a murɗe gashi ko fara'a bayayi"

Cikin tsiwa tace "Wallahi Ammar yafi mijin ki kyau, kuma ina ruwana da girman sa aiba goya shi zan dinga yi ba"

Yaya murja tace "Mufeeda in ma Auren ne ki samo dai dai ke kinji professior Auta, waima ba cewa kikayi se kinyi degree ba, zakiyi Aure?"

"ba wani professor Aure zanyi, kuma Yaya Ammar nake so"


Tofa
More Comments More Typing

Ayshercool
07063065680
✨✨✨✨
        *WATA KISSAR...... *
                  ✨✨✨✨✨

                      ( *Sai Mata* )

         

                         Page 3

*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*_A SHORT LOVE STORY_*

*Story and written by*

'''AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)
The experience writer of ABDUL JALAL'''

Na sadaukar da wannan littafin ga Ɗaukacin masoya na, wanda nasani da wanda ban sani ba

Watpad @ Ayshercool7724

What's app 07063065680

Gmail [email protected]






Ammar ne yayi sallama ya shiga gida ɗauke da leda a hannun sa ya tarar da halima  na tsakar gida tana wa Umman sa kitso, mahaifinsa kuma na gefe akan dadduma yana sauraren radio.

Amsa masa Sallamar suka yi gaba ɗaya, ya samu guri ya zauna a gefen tabarmar da Umman sa ke zaune yace
"Abba sannu da gida"

"Yawwa Ammar ya aikin?"

Ammar yace "Alhamdilillah" sannan ya miƙawa maman sa ledar vivan da ya shigo da ita.

Baban Ammar yace "Ammar ka rage wannan ɗawainiyar da kake mana a cikin gidan nan mungode, ni abunda nafi damuwa da shi ka adana ƙudinka ka tara ƙuɗin aure"

Dafe kai Ammar yayi yace "Abba ba wani abune na siyo ba kayan ɗaurin aure ne da naje aka bani"

"haka dai se aukin yawon zuwa auren wasu amma kai sai jin kan da fushi"

Ammar yayi shiru bece komai ba.

Halima ta ɗakko faranti aka juye kayan akai, Umma ta jinjina kai tace "kai kam Ammar ɗaurin auren waye haka aka baka wannan kayan kaman kaine angon?"

Halima tai farat tace "Wallahi umma wata ce ta gayyace shi, da na zata baze je ba amma.....
Uwar harar da Ammar yai mata ne ya tilasta ta yin shiru.

Abba yace
"me tayi maka kake mata wannan mugun kallon? Ke Halima gayamin ina jinki"

Cikin kame2 Halima tace "Amm.. Dama.. Dama katin ɗaurin Auren

Please Login or Register in order to submit comment