Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

taje ta samu Baba ta gaya masa ga Autar sa can tana kuka Mama tace zata zane ta, Baba yasa aka kira masa Mufeeda, Ya dinga rarrashin ta yana mata nasiha ƙarshe a ɗakin Baba ta kwana.

Kasancewar bata samu bacci ba sosai daren jiya yasa bayan sallar Asuba tai kwanciyar ta tana bacci, Baba kuma ya hana a tashe ta har ƙarfe tara na safe aka kafa rumufunan ɗaurin Aure tana bacci.



Da ƙyar Baba ya bari aka tashe ta ta karya, sama sama aka mata kwalliya shima tana yi tana kuka.

Ammar  ya sha shaddrsa fara ƙal yayi kyau kaman a sace shi a gudu se zuba ƙamshi yake, Amma se wani cin magani yake kaman wanda za'ayiwa auren dole, Aminu yace

"gaskiya Ammar ka saki ranka ba ze yuwu muje gurin ɗaurin auren nan kana wannan hade ran ba, se mutanen nan suce azabtar musu da 'ya zakayi, yau ranar farinciki ce a gareka"

Ɗan tsaki Ammar yayi yace

"nikam bana farincikin saboda dani da wanda da wanda ba aure zeba duk ɗaya, ni garama in zauna ba auren, na ɗauki wannan Auren a matsayin ƙaddara ta ne kawai"

Jabir yace "Ammar be kamata ka ɓata Auren ka da bakin ka ba, dukda ƙaramar yarinya ce idan kasa gidan Auren ka ze zame maka dausayi na farinciki, yarinyar nan kai take so zata iya zama da kai a kowane yanayi na rayuwa, dan Allah ka saki ranka ka dena wannan ɓata ran"

Haka suka ci gaba da lallɓa Ammar har suka tafi gurin ɗaurin Auren.

Aka ɗaura Auren Mufeeda da Ammar akan sadaki har Naira dubu hamsin, Mutane sun yi mamaki musamman magulmata, Yaya Fadila ta shigo ɗaki ta samu Mufeeda tace

"Auta buri ya cika an auri Ammar, an zama matan Aure su Mufeeda yanzu nidake mun zama ɗaya fa ko?"

Banza Mufeeda tai mata taƙi ko kallon ta.

Fadeela tace "Yarinya zaki ga abunda muke jiye miki, seki tashi an ɗaura, ki tashi kije za'ayi hotunan ɗaurin Aure"

Kuka Mufeeda ta saka tare da noƙe kafaɗa, Fadila kuwa ta dinga mata dariya tana cewa

"Yarinya da an gayamiki Auren abune me sauƙi? Ai ki adana kukan ki"

Seda Mama tazo tai fama da ita Sannan aka gyara kwalliyar ta fito, Angwaye sun shigo anata gaisawa Mufeeda ta fito.


Tunda ta fito yake kallon ta da alama tana cikin damuwa amma tayi kyau, irin shaddrsa ce ya kawo mata itace a jikin ta, me hoto yazo anata ɗaukar hotuna, dukda haka wasu anayi tana kuka, kallon ta Ammar yake sam kuka ba yamata wahala ko meye na kukan kuma yanzu oho?

Daga cikin abokan Ammar ne wani Faruk yace "haba boss ka rarrashi babyn taka mana, kana kallo tana kuka"

Wata uwar harara Ammar ya watsa masa, ya maze.

Abokan Ammar suka sasu gaba wai za'a musu hoto tare, Mufeeda taƙi tsayawa, Jabir yace

"dan Allah ka rarrashi Amaryar nan taka ayi hoton nan"

Ammar ya ɗanyi ƙasa da muryarsa yace
"wai ba zakiyi shiru ba? Kukan me kike haka waye yace kice kina son Auren? Kidena wannan kukan ko a fasa hoton, maza goge hawayen nan"

Abokan Ammar se ihu suke suna "kunga wani salon Soyayya"

Mufeeda tana kuka amma ta zumɓura baki daidai kunnen Ammar tace "ka bani handkerchief in goge"
"bazan bayar ba in bazaki dena ba kiyi tayi"
"wallahi in baka banba da babbar rigarka zan goge"
Da sauri ya ɗago ya kalleta, babbar rigar sa fara ƙal tasha aiki, Amma tace da ita zata goge hawaye, yanayin kallon da yayi mata ne kaman na soyayya, aka dinga ɗaukar su hoto.

"Ka bani mana Allah zan goge da rigar ka" girgiza kai yayi baya son yayi wani abu daze nuna rashin kyautawa a gaban mutane, amma tabbas yasan zata aikata abunda tace ya ɗakko handkerchief ya miƙa mata ta karɓa ta goge hawayen fuskarta, handkerchief ɗin se tashin ƙamshin turaren Ammar yake.


shi dai Faruk ji yake inama shi ya samu damar da Ammar ya samu, yarinya ƙarama gata me kyau ga shagwaɓa abunda yake matuƙar burgeshi da mace kenan ya samu mace shagwaɓaɓiya.



Nan ma aka dinga surutu 'yan matan layin su Mufeeda da suke ji da kansu su kaita gulma wata tace
"Taɓɗijan wannan yarinyar ya zata yi da wannan mutumin ai yayi mata girma, kalleta' yar mitsitsiya da ita jishi a murɗe kaman ɗan dambe"

Ɗayar tace "ke Amma wallahi ya haɗu koni na samu wannan Auren sa zanyi wallahi yana da kyau, wannan beyi kalar auren 'yar mitsitsiyar yarinya ba, Amma se wani cin magani yake ko fara' ar kirki ba yayi kaman wanda akayiwa auren dole"

"Ke wallahi da na ganshi lokacin da yake zuwa zance ni zanyi ƙoƙari in cusa kaina, amma wannan ai da irin mu ya dace ba wannan fitsararriyar ba"

Ɗayar tace  "Allah ya kiyaye in auri me Napep nafi ƙarfin nan"

"A'a wallahi ni banfi ƙarfi ba, ba gamu a zaune a layi ba, ita kuma tayi wuf dame napep wallahi indai zanci in sha na samu kaman wannan tafiya zanyi gamu a zaune ai yarinyar da aka haifa a gaban mu ta shige muna zaune" haka suka ci gaba da surutunsu da gulmace gulmace

Haka aka gama shagalin biki a wunin ranar, Amma uwar gayya kanta har ciwo yake saboda kuka, bayan magariba motocin ɗaukar Amarya suka zo, maƙota suka dinga cika motocin nan suna tafiya zasu je suga ƙwal uwar daka suje ganin gidan mufeeda.


Kusan duk an watse Mufeeda ake jira a tafi da ita amma ta maƙale a jikin mama tana ta kuka, Mama ta aurar da yara mata amma bata taɓa zubda Hawaye danta aurar da 'ya ba se wannan karon tana cikin yiwa Auta nasiha mufeeda ta ƙanƙame ta tana kuka, kawai se Mama itama ta hau kukan, duk faɗan da suke yi da Mufeeda tana matuƙar ƙaunar' yar tata, suka rungume juna suna kuka, Yayan mufeeda ya shigo yace

"Mama dan Allah kidena kukan nan ki ƙyale yarinyar nan akaita ɗakin ta, tun ɗazu su gwaggo sahura na mota ita suke jira amma kin ƙanƙameta kuna kuka, haba Mama baki taɓa kuka dan zaki aurar da 'ya ba se Mufeeda"

Su Anty Murja sukai tayiwa mama mita, Sosai Mama taƙi saurara su ta ƙara rungume auta.

Seda Baba yazo da kansa, ya zauna ya ƙara yiwa Mufeeda nasiha me ratsa zuciya sannan yace ta tashi ta tafi a raka ta, amma Mufeeda tai mursisi ta sake hayewa kan gado bayan Mama tana kuka, Mama ji take kaman tace a ƙyale mata 'yar ta, Mufeeda tayi ƙanƙanta da fara fuskantar ƙalubalen dake cikin rayuwar aure, Amma tana mata addu'a Allah yasa Ammar ya riƙe ta Amana.


Baba ne yace "yaki Auta na zo da kaina zan raka ki ɗakin ki, duk yayyan ki ba wadda na raka, amma dole in raka auta taho muje"

Baba yasa hannu ya kamo na auta, ta sakko daga kan gadon amma ta riƙe hannun Mama, shi kansa Baba daurewa yake yadda suke kuka gaba ɗaya jikin sa yayi sanyi.

Baba yace
"Sarah dan Allah kiyi hakuri kiyi mata fatan Alkhairi"

Mama ta goge hawayen ta tace

"yi shiru Auta na kinji, kiyi hakuri haka dama rayuwar 'ya mace take, kedai ki riƙe nasihohi da muka yi miki zaki zauna lafiya da kowa a rayuwa Insha Allah, jeki Auta na Allah ya bada sa' a Allah ya sanya alkhairi yasa gidan zamanki ne, Allah ya Sanya alkhairi da haske a rayuwar auren ki Allah ya bada sa'a"

Daƙyar Mufeeda ta saki Mama, Baba ya riƙe hannun ta yasa ta a mota ya tafi kai Autarsa da kansa ɗakin miji.

***************

Ammar ya kammala shiryawa se zuba ƙamshi yake, abokan sa na waje suna jiran sa, gidan su Ammar wasu duk sun tafi gidan Amarya, yayin da wasu ke ƙarasa Wanke-Wanke da gyaran gida, Ammar ya shiga ɗakin Abban sa ya tarar da shi zaune da shi da Ummansa yaje ya durƙusa gaban su yace
"Abba zan tafi"


Abba yai murmushi yace "Ango ka sha ƙamshi, ubangiji Allah ya Sanya alkhairi ya baku zaman lafiya, dan Allah dan Annabi Ammar yadda suka baka 'yar su cikin mutunci ka girmama musu yarinya ka kula da ita, ka sauke dukkanin haƙƙoƙin ta dake wuyan ka, ka rage wannan zafin zuciyar naka da izza da wannan yawan faɗan naka, kaga yarinya ce ƙarama ka kula da ita Ammar "

Ammar ya jinjina kai yace
" Insha Allah Abba "

Umma tace
"to Ammar duk abunda zan gaya maka na riga na faɗa maka a baya, kuma mahaifin kama ya gaya maka, yarinyar nan da iyayen ta sun mana halacci, kaji tsoron Allah ka riƙe musu yarinyar su Amana, sannan ka tuna kaima akwai 'yan uwanka mata dake aure a gidan wasu, idan ka muzgunawa' yar wasu to tabbas kaima za'a cuzguna ma naka, ka riƙe ta da amana sannan kuma kayi haƙuri, kayi haƙuri rayuwar aure gaba ɗayan ta haƙuri ce, Allah ya baku zaman lafiya "

Ammar kasa cewa komai yayi, a hankali yace " Abba a zaman mu daku nasan baza'a rasa abubuwa marasa daɗi da nayi muku ba ina roƙon afuwar ku"

Abba yace "Aini dama matsala ta da kai ɗaya, rashin Aure ga miskilanci, amma duk wannan ba komai bane akan tarin alkhairan ka a gare mu, mun yafe maka Allah yayi maka albarka"

Ya amsa da Ameen, sannan ya miƙe jiki a sanyaye ya fito tsakar gida, sauran 'yan biki suka dinga masa guɗa suna masa fatan Alkhairi, wasu har sunje sunga gida sun dawo.

Yayar sa Maryam wadda ita yake bi ta ja shi gefe tace


"To ɗan uwana ina maka fatan Alkhairi, Allah ya Sanya albarka yasa anyi kenan, sannan abunda nake so in gaya maka shine, ka kula sosai karka fifita matarka akan iyayen ka, sannan karka fifita buƙatun mu 'yan uwanka akan Na matarka, mu a gidan mazajen mu muke, duk wadda tazo maka da buƙatar ta indai bata da wani mahimmanci ka ƙyale namu buƙatar ka sauke haƙƙin matar ka, dan Allah ze tambaye ka akan amanar da ka ɗakko, Sannan Ammar tsakanin ka da iyayenka da mu 'yan uwanka daban, tsakanin ka da matar ka daban, dan haka ka yi wa matar ka abu ba lallai se mun sani ba, haka dan ka yi wa iyayenka abu base lallai ta sani ba, hakan ze toshe kafar samun matsala, Sannan kasan Auren nan naka yana da maƙiya mussman a gurin bikin nan na ƙara gani, kasan Yaya jidda bata son Auren nan, Sannan karka manta ko kuma in baka sani ba yanzu in gaya maka, Fa'izar Kawu Bala tana ɗaya daga cikin masu ƙaunar ka, ƙiri Ƙiri take nuna adawarta tareda kushe Auren nan, dan haka seka kula sosai, Allah ya baku zaman lafiya ƙanina"

Mamakine ya kama Ammar sosai, wai Fa'iza Yarinyar da ko gaisawar kirki ba sayi ace itake sonsa, da yake duk cikin 'yan uwan sa yana jituwa da maryam sosai dan haka yace

"Shikenan Sayyada Maryama, nagode sosai Allah yasaka da alkhairi, Allah ya huta gajiya"

Yai gaba tana ɗaga masa hannu.

Yana fita nan ma abokan sa suka dinga tsokanar sa, daga nan suka hau abun hawa zuwa gidan Ammar.

Mutane kusan duk an watse, suka je suka tarar da Mufeeda da mahaifin ta yana jiran isowar Ammar.

Suna ganin mahaifin Mufeeda suka nutsu suka dena wannan rawar kan da suke, suka nemi guri suka zauna, Ammar da Mufeeda na gaban Baba, Baba yai musu addu'a da nasihohi irin na dattawa, ya kama hannun Ammar yasa na Mufeeda a ciki yace

"Ammar ga Amanar Auta na nan, ayi haƙuri da halin ta yarinya ce ƙarama, tana da tarbiyya daidai gwargwado amma akwai yarin ta, Mufeeda ga Mijin ki nan ki kula da amanar Auren ki banda rashin ji, kinji Autar Baba"

Jinjina masa kai tayi tana goge Hawaye.
Baba yace "Allah ya baku zaman lafiya"

Yana gama faɗin haka ya miƙe ze tafi, yana jiyo kukan auta amma yayi waje, yana jin babu daɗi a ransa yana jin rabuwa da autarsa har cikin ransa.



Aminu yace "haba Mufeeda burinki ya cika Yaya Ammar ɗinki ya zama naki, meye na kuka kuma?"

Faruk yace

" ai da alama wannan Amaryar shagwaɓaɓɓiya ce, Ammar zaka sha daru fa"

Jabir ya katse hirar ta hanyar yi musu fatan Alkhairi suka miƙe zasu tafi, Ammar yayi musu rakiya suka yi sallama Faruk yace

"To Oga Ammar abita a sannu dai Yarinya ce ƙarama"

Haushi ya fara kama Ammar akan wannan zaƙewar da Faruk yake, amma ya basar suka yi sallama suka tafi, Yayin da Ammar ya rufe ƙofa ya dawo, tana nan zaune inda ya barta, tana ta goge Hawaye, tsayawa Ammar yayi yana Kallon Mufeeda dan besan ta inda ze fara ba, kaman shi a ce wannan 'yar yarinyar ce matar sa, wannan sunan yayi aure ne kawai amma shida wanda beba duk ɗaya.

"Ke wai bakya gajiya da wannan kukan ne? Se kanki yayi ciwo"

Shiru tayi masa ta ci gaba da goge Hawayen ta hada sheshsheƙa.

Tsaki yayi yace

"sekiyi tayi ai, in kin gaji ko kin gama ga leda nan ki ɗauka kaza ce a ciki"

Yana gama faɗin haka. ya wuce ɗaya daga ɗaku nan dake cikin falon, yaje ya rage kayan dake jikin sa ya watsa ruwa ya canza wasu kayan.

Fitowa falo yayi da niyyar ya kashe fitilar falon, kawai ya tarar da Mufeeda inda ya barta bacci ya ɗauke ta, girgiza kai yayi tare da jan tsaki 


"ita wannan yarinyar banda yarin ta ma hadda taurin kai na damun ta"

Ya ƙarasa inda take yace "Ke, ke!" amma sam bata san me yake yi ba, hannu yasa ya bubbugi jikin kujerar da take jiki, amma bata motsa ba sema ajiyar zuciya data sauke alamar baccin ta yayi nisa.

Hannu yasa ya ɗago ta amma baccin ta take, bashi da zaɓi illa ya ɗauke ta zuwa ɗaya ɗakin da yake gado biyu akayi mata, yasa hannu ya ɗauke ta kaman wata 'yar shila se wani irin ƙamshin  turare take zubawa.

Yana zuwa ya shimfiɗe ta akan gadon ya tsaya ya ɗan zuba mata ido, fuskarta harta kumbura saboda kuka, ya zare mata mayafin jikin ta, tare da gyara mata kwanciya, idonsa ya sauka akan zara zaran yatsunta da suka sha adon lalle ja da baƙi, zuba mata ido yayi na wani ɗan lokaci yana saƙaa abubuwa daban daban a ransa sannan ya miƙe ya kashe mata fitila ya tafi ɗayan ɗakin.

Mama kam kasa bacci tayi tana ta tunanin koya ya zata kaya wa autar ta? Wani hali take ciki? Kasancewar wannan ce ranar ta ta farko a gidan miji? (🙄🙄 bafa abunda ya faru mama ki kwantar da hankalin ki) Gaba ɗaya ta kasa sukuni bacci kam se ɓarawo ne ya ɗauke ta


Kiraye kirayen salla ne yasa Mufeeda farkawa, tana tunanin koya akai ta dawo nan oho ita dai tasan a falo take tana bacci

Ammar ya je da niyyar ya tashe ta salla ya ji motsin ta a toilet alamun ta tashi dan haka ya fice masallaci.

Tunda Mufeeda ta koma bacci bayan Asuba bata farka ba se bayan ƙarfe tara, ta farka da wani irin ciwon kai saboda kukan da tayi.

A hankali ta miƙe ta dudduba cikin kayan ta ta ɗako brush da toothpaste tayi brush, toilet ɗinta da famfon ruwa dan haka tayi wanka ta saka wasu kayan, Yunwa take ji sosai ga kanta yana ciwo haka ta buɗe ƙofar ɗakin ta fito, Ammar ta hanga zaune akan three seater yana danna wayar sa.

A hankali ta fara takowa inda yake, ya ɗan ɗaga kai ya kalle ta, ta ɗan rame ga idon ta a kumbure saboda kukan da tayi, ta ƙaraso inda yake ta zauna a kusa da ƙafafuwan sa tace
"Yaya Ammar ina kwana?"

"lafiya ƙalau uwar kuka" ya amsa mata yana dannan wayar, ɗan ɗaga kai tayi ta kalle shi ta sauke kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannun ta.

Shiru ne ya ratsa na wani ɗan lokaci cikin shagwaba tace
"nifa Yunwa nake ji"

Ammar Yace "ai na ɗauka ba kya ci, je kitchen ki duba"

Ta miƙe ta tafi kitchen, Tana zuwa ta tarar da kayan tea har ruwan zafi ya dafa, ba tayi wata2 ba ta haɗo tea ta dawo falo, ta zauna tana yin breakfast ɗin ta.

Ta kalli Ammar tace "yaya Ammar ɗina kayi breakfast kuwa?"

Kallon ta yayi yace "ke kici naki mana ina ruwan ki dani?"

Tace "to Allah ya bada haƙuri" ta cigaba da cin Abincin ta.

Daga nan shiru ya ƙara ratsawa tsakanin su, Ammar ya maida hankalinsa sosai akan wayar sa.

Tana cikin cin Abincin, aka kira Ammar a waya bata san waye ba se ji tayi yace
"A'a base kunzo ba bacci take yi, kuyi zaman ku kawai"

Buɗe baki tayi za tayi magana, ya galla mata harara taja bakin ta tai shiru ya kashe wayar sa ya ci gaba da danna waya.

Cikin shagwaɓa tace "Wai su waye za su zo kace kar suzo?"

Shiru yayi mata yaƙi kula ta, ta ture kayan Abincin tana tura baki.

"ni ka wani zauna kaƙi kulani ance za'azo kace baza suzo ba ni gaskiya kace suzo dan Allah"

Wata uwar harara yai mata wanda ya tilasta mata yin shiru.

Ta miƙe ta kai kwanukan data karya kitchen ta ajiye, ta dawo ta zauna ta zubawa Ammar ido.

Har yanzu kanta yana mata ciwo, Ammar ya maida kai sosai akan wayarsa yana game.

Kallon sa take yi yayi mata kyau sosai, inama ze kulata suyi hira a ranta tace "a sannu zan sauke wannan halin naka in dai nice"

Fashewa tayi da kuka, Ammar ya ɗago da sauri yace "Ke lafiya? Meye haka?"

Ta lanƙwasa "Nifa kaina ne yakemin ciwo"



Ammar yace "shine zakimin kuka? Wannan koke koken da kike yi ba dole kanki yayi ciwo ba, kiyi min shiru ni in duba magani in baki"

Yai maganar yana miƙewa, yana tafiya tayi murmushi, bayan tafiyar sa ɗaki tayi kwanciyar ta akan kujerar da ya tashi, ya dawo da magani a hannun sa da ruwa ya miƙa mata

"ni gaskiya bana son magani ka ƙyaleni ze dena"

Haɗe rai yayi yace "kika kuma Yimin kuka sena ɓata miki rai tashi ki karɓa"

Ta tashi zaune tasa hannu ta karɓa, ta ɓalli ɗaya zata ƙara ɓalla yace
"ke baki da hankali, maganin har nawa zaki sha?"

"to manya ba guda biyu suke sha ba?" ta faɗa kaman za tayi kuka

Hararta yayi yace "suwaye manyan?"

Yasa hannu ya karɓe na hannun ta data ɓallo ya raba biyu ya miƙa mata rabi yace
"ungo" tsayawa tayi tana kallon sa tace  "rabi fa ka bani"

"eh rabin, baki kai ki sha guda ba, ƙarama dake zaki sha magani har biyu saboda shirme, da masu chemist sun fito yanzu da na ruwa zan siyo miki" yai maganar in very serious tone yana wani haɗe rai.

Wata uwar dariya ce ta kama Mufeeda, Ammar yayi mugun raina mata hankali itace ya kamata tasha magani na ruwa sekace jaririya ta gimtse dariyar ta a ranta tace

"lallai Yaya Ammar muje a haka, ka shirya ganin ƙuruciya samfur samfur da yarinta zaka gane kacemin yarinya kuma ƙwaila dani kake zancen, zan maka aikin yara kala kala" .




Masu Comment da addua ina godiya Allah ya bar ƙauna
Domin shawara, gyara ko kuma sharhi
Ayshercool
07063065680
✨✨✨✨
        *WATA KISSAR...... *
                  ✨✨✨✨✨

                      ( *Sai Mata* )

         

                        

*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*_A SHORT LOVE STORY_*

*Story and written by*

'''AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)
The experience writer of ABDUL JALAL'''

Na sadaukar da wannan littafin ga Ɗaukacin masoya na, wanda nasani da wanda ban sani ba

Watpad @ Ayshercool7724

What's app 07063065680

Gmail [email protected]

     

ELEGANT ONLINE WRITER'S

             
**Daddy, Baba, Abba, Appa, papa, Yaya, Abee, babi, father, Abbu ❤️❤️❤️*
*I want tell you that we love you 😍😍😍*

*HAPPY FATHER'S DAY*

_Baba kuɗin mota, school fees, nepa bills, saloon, rapper everything father, father, father_

_we rest in your shoulders in every moment,_
__every day is yours but today is special day for you, i will use this opportunity to tell you that we all loves you endlessly our dads we really appreciate your efforts toward us especially in this very period of hardship, on behalf of every female daughter we wish you a very happy moment, we wish you a very long healthy life, more strength, joy happiness and halal money in your account. May Allah_ _subhanahu wata'ala crown your efforts towards us with countless rewards_
_Your female daughter's really loves you 💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃_
_
_For those that thier father's pass away, we pray for them Allah's Rahma and Janna, may their gentle souls rest in perfect peace may Allah subhanahu wata'ala gives them a highest rank in jannatul fiddausi
Ameen
_
_I dedicated this page to all fathers all over the world thank you 😍 😍 😍 for your love*_

*Your female daughters really loves you* ❤️❤️


           

          Page 11


Haka Ammar ya kwanta yana mamakin Mufeeda.
Da gari waye Ammar be tashi da wuri ba, bacci yake har kusan takwas na safe.

Mufeeda ta shiga kitchen ta dafa tea tun dare Ammar ya shigo da bread, tayi amfani da ƙwan nan da albasa da kuma naman jiya da suka kasa ci ta sarrafa bredin nan ta gasa, har ta gama Ammar be tashi daga bacci ba.

Ɗakin ta tafi domin tayi wanka kafin ya tashi, amma harta fito ta kintsa jikin ta bacci yake, ɗakin sa ta tafi, tana zuwa ta tarar yana ta baccin sa.

Kan gadon ta hau ta ɗan tsura masa ido a fili tai murmushi tace

"Masha Allah mijina yafi na kowa kyau"

Ta ɗan daki fulon da yake kai, tana faɗin "Mijin So, ka tashi haka baccin ya isa fa"

A hankali yake buɗe idon sa har ya buɗe su duka ya sauke akan Ƙwailarsa, bakin ta raɗau da jan Jambaki, tayi ɗare ɗare akan gadon sa, ƙura mata ido yayi ba tare da yace komai ba ga ƙamshin turaren ta me daɗi yana ratsashi, se sake lumshe ido yake.

Murmushi tayi tace "good morning Baby, na dafa ruwan wanka, in kayi seka fito mu karya"

Yadda ta fita daga ɗakin sa a zuciye daren jiya beyi zaton zata kulashi ba, wani ƙarin mamakin wai har tasan ta dafa masa ruwan wanka.

Yanayin kallon da yake mata ne yasa ta tsarguwa, dan haka Ta juya ta sauka ta bar ɗakin, ta koma falo tana jiran sa, koda ya fito falon ƙamshi ne daban daban yake dukan hancin sa, ya samu guri ya zauna harta jere komai na breakfast ɗin.

Ta kalle shi a shagwaɓe tace "Nagaishe ka amma kaƙi amsawa ko"

"to sannu, lafiya ƙalau" ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin janyo flask ɗin shayi.

"No tsaya in zuba maka"

Ta haɗa masa tea, gurin zuba Madara tana zuba spoon ɗaya yace "Ya isa haka"

"taɓ spoon ɗaya, gaskiya ni spoon ɗaya yayi min kaɗan" shiru yayi ya fara shan tea ɗin sa ya kalle ta yace "Ina bredin ne?"

Plate ta miƙo masa ɗauke da bredin da ta sarrafa, ya kalli bredin yace "meye Wannan?"

"kaci kaji mana"

"bredin kika wulaƙanta ya koma haka?"

"ni ban wulaƙanta ba, kaci kaji da daɗi"

Girgiza mata kai yayi yace "bazan ci ba"

Hannu tasa ta ɗakko bredin ta matsa kusa da Ammar ta kwantar da muryar ta sosai tace

"dan Allah Yaya Ammar kaci, na yadda idan babu daɗi na wulaƙanta maka Abinci kamin duk hukuncin daya dace dani, dan Allah"

Yadda tai maganar ne cikin sanyin murya yasa ta bashi tausayi, hannu yasa ze karɓa, ta ɗan girgiza masa kai ta miƙa masa bakin sa, ya buɗe baki ta saka masa.

Ai ba ƙarya bredin nan ba ƙaramin kaiwa Ammar yayi ba, dan yayi test sosai a bakin sa, Mufeeda tasan idan tayi magana ze iya mazewa ya fasa ci dan haka ba tace komai ba ta ƙara miƙa masa wani, ba kunya ya amshe abun sa ya taune ba tare da yace komai ba.

Zata kuma gutsurowa yace "banni inci da kaina,

Please Login or Register in order to submit comment