Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

matukar yin kyau fiye da hasashenta har ma ta fi kyau a zahiri fiye da a zanen.
Dukanin su sai yabon kayan suke.
Wani babban bako da Roman ya gayyata ya bukaci da abashi damar fidda design din a kamfanin sa.

Sun yi taro anci an sha kuma an nishadantu sosai da sosai kowa ya ji dadi, tun safe sai karfe hudu aka gama ana gamawa Deejerh taji ba inda take buƙatar zuwa sai gida domin ta yi wanka jikinta na yi mata wani iri duk ta tsargu.
Hakan yasa tayiwq su Daeej sallama ta kama hanyar gida.

Tunaninta ba kowa gidan hakan yasa ta shiga hankali kwance da karfin gwiwarta.
Tana shiga dakinta ta tube kenan zata shiga toilet taji an hankadata ta fada kasa, kafin ta yi wani yunkuri zayd ya fara taka mata ruwan ciki yana dukanta da belt, duk kokarinta na ganin ta janye jiki ta gagara tamkar wanda aka turo dukanta yake da hannu da bulala da kafa kawai, tsabar azaba aman jini ta fara,tana sa hannu ta ga jini ts kara firgicewa tana kuka , "Uncle Please.... please.... Uncle...." Abun da take iya furtawa kenan.

Ya dagata kamar tsumma yana tsayar da ita sannan ya fara tusa hannunsa gabanta.
Yana fara hakan ta rufe idanunta babu abun da take gani sai training din su na MMA ita kanta batasan ya akayi ba sai ji tayi kawai ta saki wata kara ta daidaici daidai marar Zayd din ta dunkule hannunta ta dunga buga masa.
Yana kokarin kare kansa amman kamar ingizata ake ko ince wacce aka sakewa famfom karfi.
Wani bugu da tayi masa a karshe ya yi wani gajeren nishi take numfashinsa ya tsaya caj ya fadi a wajen.

Ta tabashi ta ga baya motsi kuma baya numfashi hakan yasa ta birkicewa da tunanin cewa ya mutu, rigarta guntuwa kawai tasa ta fice da gudu, haka ta dunga tafiya tana haki akafa har gari yayi duhu dare ya yi a kafa har ta isa gidan Nawar.
Tana zuwa masu gadin suka hanata shiga tana ta kuka da shashsheka.
Hanayaniyar da tayi yawa yasa shi fitowa aiko ya ganta yaji mamaki matuka ganin ta cikin dare, kai tsaye ya bada umarnin abarta ta shiga.

Ban da nishi da ajiyar kuka tare da hawayen da ke ambaliya daga fuskarta babu abun da take.
Ya dibo ruwa ya bata tasha sannan ya ce, 'Mene ne? Me ya faru ne?"

Deejerh ta saki ajiyar zuciya ta ce, "Uncle, Uncle Zayd...."
Sai kuma ta yi shiru.
Nawar ya ce, "Zayd? Me ya faru ya miki wani abu ne ko wani abune ya same shi?"
Ta girgiza kai a tsorace.

Rike mata hannu Nawar ya yi,ya na shafa mata kai a hankali ya ce, "ki nutsu ki fadamun gaskiya kinji, ba zan taba bari wani ya cutar dake ba, ni ai abokinki ne ko? Kuma aboki na sadaukar da rayuwar sa ga aboki."

Murya na rawa ta ce, "na...na...na... kashe...shi."
Sai da mamaki ya bayyana a fuskar Nawar ya kalleta ya ce, "kashe shi kuma? Akan me? Garin yaya?"
Da ya ga Deejerh na shirin firgicewa sai ya yi shiru ya ce, "shikenan yanzu ki nutsu ki kwanta kinji gobe da safe za mu yi magana.

★★tana fita ba jimawa sai ga momynta da Daddynta sun dawo gidan, basu yi tunanin komai ba kowa ya fara harkar gabansa sai wajen karfe goma Dadyn Deejerh ya ga wayar zayd a palourn su kuma ya tabbatar baya taba barin waya a gida, da mamaki ya dauka yana nunawa momyn Deejerh ta yi Murmushii ta karba tana, "yanzu haka yana nan gaban Daughter tana ta masa rigima shiyasa muka ji su tsit bara in kai masa wayar." Ta nufi dakinsa bata gansa ba sai ta koma na Deejerh.
Tana zuwa ta ganshi kwance warwas batasan lokacin da ta saki wata gigitacciyar kara ba.
Da gudu Dadyn Deejerh ya karasa dakin shima dukan ninsu suka birkice, cikin gaggawa Dadyn Deejerh ya yi jarumtar kiran motar asibiti.
Cikin 10minute suka zo suka daukesu Ban da kuka babu abun da Momyn Deejerh ke yi.
Suna shiga aka fara yi masa taimakon gaggawa.
★★

A takure ta kwanta, idanunta biyu har safiya,
Nawar na hankalce da hakan ya ce mata, "kin gani ki nutsu ki ci abinci yanzu in kika gama sai muyi magana ko? Ki tashi kiyi wanka." Ta girgiza masa kai ta tashi taje tayi wankan sannan ta kara zama a takure.
Abincin ma kasa ci tayi da kyar ta iya shan tea.
Nawar ya ce, "akwai wani da kike son gani ? Zaki yi magana da shi?"

Deejerh ta girgiza kai alamar eh.

Nawar ya ce, "Ok wane ne? Ko in baki waya ki kirashi?"
Ta kara girgiza masa kai.

Mika mata wayar ya yi ta danna number meastro Roman.
Sai kuma ta mika masa.
Bayan sun gaisa Nawar ke sheda masa cewa in babu matsala yazo dalibarsa na da bukatarsa a yanzu.
Babu musu kuwa duk da cewa Roman yasan hadarin da ke tattare da Nawar haka ya amsa da fadin gashi nan zuwa.

Take ya fice daga School ya nufi gidan Nawar.
Yana zuwa ya kurawa Deejerh idanu yana mamakin yadda akai tazo nan din.
Nawar ya ce, "ka kwantar da hankalinka,ka fahimceni, ba cutar da ita zan yi ba hasalima ita ta zabawa kanta wajena a matsayin mafaka,ni abokinta ne kawai kuma aboki mai son taimakon abokiyarsa jiya da yamma tazo nan cikin wani hali wanda kalmar cewa tayi kisa kadai ta iya fadamun daga nan ta gagara kara fadin komai shiyasa na bukaci da ta kira wani makusancinta wanda zata iya sake jiki tayi bayanin meke faruwa?"

Da sauri Roman ya durkusa gabanta murya a sanyaye ya ce, "ki fadamin kinji mene ne ya faru?"

Ta ce, "Uncle Zayd ne yaketa dukana yake mun irin abun da yake mun ni kuma na bigesa a mararsa shine ya mutu." Tana karasa fada hawaye na zuba daga idanunta.

Roman ya kalli Nawar ya ce, "tabbas hakam ta aikata tunda ta fada kuma abun ya kai mata makura ne,iyaye marasa daukan rayuwar yara da mahimmanci da Uncle mai son zuciya."

Roman ya ce, "gaskiya dan zamana da ita na fahimci cewa tana da matsala a tunanina zan iya kareta daga wani abun amman Zayd ya wuce tunanina yanzu dai mene ne mafita?"

"Sai dai afitar da ita daga cikin Kasar nan shine kawai mafitar ko da kuwa zuwa paris ne akwai wata friend dita na aiki acen zan iya hada su don anan innace zan ajiye akwai matsala muddin ya kasance Zayd na raye to zai yi duk abun da zaiyi wajen ganin ya illata ko ince ya hallaka yarinyar nan duk da kasancewar sa karami cikin mu amman kuma tsaf zai iya bawa Kasuwancina ma matsala don babban abun da nake gudu kenan ya iya dadin baki da shirya zance cikin kankanin lokaci." Cewar Nawar

Zayd ya ce, "Tabbas nima na fahimci hakan,amman yanzu ya za ayi a fitar da itan?"

Nawar ya ce, "fitar da ita cikin sauri sai dai mu bi ta gurbatacciyar hanya kasani."

Rowan girgiza kai, "ehwen zanyi kokarin hakan In Sha Allah."
Murmushi Nawar ya yi kafin ya ce, "aa zan yi abun da ya dace karka damu domin kai ba irin da ba bane tunda ka zubda makamanka nasan yin jagaliyanci zai ma wahala a yanzu."

Roman ya yi dariya, "ai da sai in tada sabon liki indai Deejerh zata fita cikin kangin nan burina ya cika."
Suka yi dariya duka.
A wajen Nawar ya kira waya kan ayi ciku-cikun yiwa Deejerh Visa ta samu ta bar kasan."

Nawar ya dafa shi ya ce, "karka damu zanyi bakin kokarina,kasan 15days ne Amman ni zanyi yadda za ayi cikin 5days a kammala komai and kuma kasan in tana gidan nan bata da wata matsala she is save."

Roman ya ce, "hakane kam Allah saka da Alkairi zanna tabaka ta waya kuma kila ma in dawo kafin ta tafin, yanzu zan koma school kar aneme ni."

Daga nan ya tashi ya tafi yawa Deejerh sallama tare da fadin ta kwantar da hankalinta ta zauna gidan babu abun da zai faru.

Su momynta kuwa a asibiti suka kwana har safiya likitoci na kan Zayd kuma basu fada masu cewa yana raye ko akasin hakan ba koda suka yi magana ce masu suka yi kawai suta addu'a don ba lallai ya tashi ba.

Da safe duka suka koma gida, sai a lokacin tunaninsu duka ya koma kan Deejerh suka duba babu alamarta a gidan.
Dadyn ta ya kira school aka tabbatar masa da cewa bata je ba.
Nan hankalin su ya tashi suka fara bincike gidan.
Momynta na kan bincika dakin tana daga pilonta tayi karo da diary book dinta,wanda take rubuta abun da ya shafi rayuwarta ciki.
Da sauri ta dauka ta zauna ta fara bude shafin farko.
PAGE1
"Ban san ko na aikata wani laifi bane a cikin mahaifiyata kafin zuwa duniya da na sani da tun tuni na nemi gafara, domin ban san dadin iyaye ba kuma ban san dadin rayuwa ba ko da kuwa a cikin mafarkine, an danne ni dannuwar da ban da karfin kwatar kaina, jikina ya zama kayan kasuwanci ana kasuwanci dani ana samun kudi, shin momy ,Dady? Idanunku sun rufe ne bakwa ganin rayuwar da nake ciki? Ina azabtuwa matuka."
Daga nan jikinta ya fara rawa zufa na keto mata cikin sauri ta bude shafin gaba
PAGE 2 wanda aka rubuta MOMY da manyan baki tare da jawabai kamar haka.
You say you love me,but you never thought to hear my side of the story.

You never extended your hands when i needed it to hold me.

I hate to admit but you don't even know me and at this point its not a flex neither is it funny.

You say you love me,but you never give me room for change.

I tell one lie growing up you displine me never to repeat such.
And when i decided to put your word in to action you call me a liar.
Because i was one once Why?

You say you love me but you're trying to live your life through Me everything you wanted but couldn't be you want to make me.
I didn't even choose to be here can i at least choose to do me?
You say you love me but you don't understand me.
You don't know how in constantly keeping myself in check because i don't want to get you on my nerves cos that's the last place i need you to be.
You don't know how I cry myself to bed because of that one ward you said.
You say you love me but you don't notice how self conscious I've become because you're too selfish to see it.
You wanted a perfect daughter and unfortunately i got costed for the role had to learn how to act m
Because i know with scene or two then everyone has a pact.
You say you love me but you don't tech me to love me.
Its SAD."

Karantawa take tana kuka har ta gama wannan fejin ma taje na gaba.
PAGE3
"Wanda kuke kira da jigo gareni shine ya tarwatsa mun rayuwa,wanda kuke kallon shine farinciki gare ni shine babban bakin ciki gareni, ku yarda da cewa Uncle zayd zai kula dani zai kaunaceni baku taba damuwa da sanin shin cewa ina jin dadin rayuwa da shi ba, ban san meke faruwa ba amman ina ji a jikina cewa dole akwai wata rana da zata zo, kuma zakuyi nadamar barin rayuwata a tarwatse kuna nufin ban da amfani ga rayuwa kenan? "
Gagara karasa karantawa tayi tana kuka na fitar hayyaci ta tashi ta fice aguje....
[12/14, 11:14 AM] Xayyeesherthul-humaerath🥀: *°°°VIXEEN°°°*

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
*https://www.facebook.com/106494781436168/*

_#5Stars/Zeeyter/Yel/Freeya/Vixen._

©️ *XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH*

PAGE-24

Tana fita Dadyn Deejerh ya rike ta yana fadin, "Mene ne ya faru? Ina take? Kin ganta ne?"

Cikin muryar kuka ta ce, "Aa ,aa Zayd ya cuceni,ya cutar mun da rayuwar 'Ya ban san inda take ba, shikenan,muje gunsa ya nemo mana ita, muje ya nemota."

Take suka tari taxi suka nufi asibitin.
Suna shiga Zayd na farkawa kenan.
Dakin Momyn Deejerh ta kutsa kawai taje ta cakume Zayd tana fadin, "Ina Deejerh? Ina ka kai mun 'Yata? Ka fitomin da 'Yata, na ce ka fitomin da 'Yataaaa." Ta karasa tana kara fashewa da kuka mai tsuma zuciya.

Tsaki Zayd ya yi duk da cewa jikinsa ba wani karfi amman haka ya hankadata gefe saida dadyn Deejerh ya riketa
"Kun bani ajiyarta ne? Ko ina take ma ku zaku fito da ita kuma Na rantse da girman Ubangiji idona idonta sai na kasheta ba ma ita ba hatta ku sai na kasheku."

Wani kallon mamaki Momyn Deejerh ta yiwa Zayd ta ma kasa cewa komai kawai abubuwa ne kawai ke mata yawo cikin zuciyarta arai tana sakawa, "Tabbas ni ce na cutar da 'Yata da kaina,ni na nuna mata cewa shine bangon da zai tallafi rayuwarta, ashe shine makamin da zai rusata?"
Karamin suman tsaye ta yi.
Ganin ta kame kam Dadyn Deejerh ya riketa .
Kara rugumesa ta yi cikin muryar kuka tana fadin, "Kana gani? Kana gani ko? Wai Dan Uwana ne zai tarwatsa mun rayuwar 'Ya? Ashe ba son mu yake ba? Ashe duk abun da take nunawa da gaske ne? Har abun da ta fadamin ranar?" Ta kara fashewa da kuka.
Jan hannunta ya yi suna fita daga dakin, "Duk ki bar batun nan,ki nutsu mu nemeta yanzu,ba komai ya ja mana hakan ba illa sakaci da son zuciya ganin cewa yana da arzikin da muke mora."

Cikin muryar kuka tana kara daga sauti ta ce, "Wallahi in banga Deejerh ba sai na kashe Zayd sai na kashe shi kafin ya kashe mu zan kashe shi gwanda duk mu mutu."
Tana maganar yana janta.
Kai tsaye police station suka je shigar da cikiyarta.

Suna Fita Dr yazo kan Zayd da takaddar sallama.
Zama ya yi gefensa yana fadin, "To aboki jiki ya yi sauki Alhmdu Lillah kuma mun sallameka yanzu ruwan nan na karewa Shikenan,amman kafin nan ina so muyi wata 'Yar magana,fatana dai ka fahimceni kuma ka karbi kaddara mai kyau ko mara kyau."

Zayd ya kalle shi ya ce, " kaddara kuma? Wacce kaddara? Ni ai banjin akwai abun da ya sameni lafiyata lau nake jina."

Murmushi Dr din ya yi ya dafa kafadarsa yana fadin, "ba abun da ya sameka kam Alhmdu Lillah amman an samu yar tangarda kadan kuma...

Kafin ya karasa Zayd ya katse shi,"wacce irin tangarda? Kamar ya? Zaifi kyau kamun magana kai tsaye Dalla Malam."

Dr Ya sunkuyar da kai kafin ya ce, "Ahto gaskiya ka samu matsala a testicle dinka ma'ana 'Ya'yan maraina wanda in aka samu matsala abu ya dokesu har ya kai duka akan samu matsala wacce hakan kai haifar da rashin haihuwa ma'ana atakaice baza ka taba samun haihuwa ba a rayuwa....

Fincike abun ruwan zayd ya yi yana kafawa Dr din mari a kumatu ya ce, "banza matsiyaci makaryacin karya, sai dai ka ga rashin haihuwa a kwaryarka ba dai tawa ba,ita kuma wacce Annamimiyar yarinyar duk inda take sai na nemo ta na kasheta na yi sanadin." Ya fice.

★★★Anyi neman Deejerh har an gaji Momynta da Dadynta sun sadakar sun koma gida tsawon kwana shida dan takaici ko aiki basa iya zuwa Momynta ma na kwance kullum cikin jinya.

★★Nawar ya gama hurda hurdar sa saidai ya tabbatar ya sama mata Visa zuwa Paris
Ta Cruise ship su zai tashi karfe shida na Yamma shi kuma lokacin Zayd yaje bakin ruwan yana ci gaba da nemanta.

Suna fitowa a mota yana juyawa daidai saitinsu.
Idanunsa idon Deejerh.
Tayi saurin razana tana komawa bayan Nawar.
Daga kan da zaiyi ko shi ma yaga Zayd amman kuma ga dukkan alamu idanunsa ne kawai ke kallon wajen amman zuciyarsa na wani bangaren.
Hakan yasa Nawar ya yi saurin shigar da ita ship ya mika mata wani bargo ya rufe ta da shi sannan ya tsaya agefen.

A dube dubensa ya je ya tsaya gaban nawar inda ya tsaya yana kallon Deejerhn
Zayd zai juya kenan Nawar ya yi saurin sunkuyar da kai kasa.
Har ya wuce nan yaje ya ci gaba da lalubensu bai ga ko alamar ƙeyar Deejerh ba.

Ajiyar zuciya Nawar ya yi ya daga kai yana yi mata magana, "Duk inda zaki kasance ina fatan ki yi kokarin inganta rayuwarki kada ki dubi bayan ki,ki duba gaba da tunanin haskaka ta Kinji wayar dake gunki kuna sauka ki kira sona zata zo ta dauke ki, in kin huta muma ki kira mu kinji Allah tsare hanya."

Yana tafiya kuwa suka tashi.

PARIS
★★sai da suka isa Ta fito daga ship din kenan ta laluba jakarta don daukan wayar da Nawar ya bata ta kira Sona,waya ta ce daukeni a hankali babu ita babu dalilinta.
Ta daga kai
Ga mutane kowa na harkar gabansa ba wanda ke yi da wani kawai kowa damuwarsa yake, suna neman hanyar shiga cikin gari kawai.

Bata san lokacin da hawaye ya fara zuban mata daga idanu ba ganin cewa ta rasa makafa da hanyar bi.

Tafiya ta fara yi kawai ba tare da tasan hanyar da take bi ba.
Har ta fita cikin jama'a ta fara shiga gun da ba mutane sosai.
Can gaba kuma ta ci karo da wani team din maza kallo daya za a masu a fahimci cewa tantirai ne na karshe.

Suna ganinta kuwa suka yo kanta suna kokarin bin jikinta
Duk kokarinsu na sai sun aiwatar mata da abun da bai dace ba sai kara kaucewa take ganin hakan suka hadu duka tare suna so su jata na karfi.
Da kyar ta samu ta bigesu gefe ta fara gudu,tana yi suna binta tana yi suna binta har jini ya fara kwaranya daga jikinta.
Haka ta ci gaba da gudun duk da cewa ta jima da ficewa a hayyacinta haka ta ci gaba da gudun a karshe har suka gaji suka daina binta ba tare da ta sani ba ita dai gudu take har ya kai ga ta shiga cikin wani karamin kauye.
Jirine ya dibeta yayin da wani gudun halita ke fita daga jikinta take ta fadi,jini sai babbala yake kamar ruwa ga wani irin guda kuma shi ba na jini ba.

Haka ta baje yashe agefen wani karamin rafi tamkar gawa.

Kusan awa guda tana haka.
Wata tsohuwa dake kauyen ta fito diban ruwa a rafin kawai ta ci karo da ita.
Da farko sai da ta razana har tana komawa baya kafin tayi jarumtar zuwa ta tsaya tana kallon Deejerhn.
A hankali ta kai hannunta ga hancinta ta ji tana numfashi kadan kadan , hakan yasa ta ajiye tulin ruwan nata a gefe ta fara kokarin daga Deejerh da taga baza ta iya ba,da dabarata ta jata zuwa karamin dakinta na jinka, ko daga wajen dakin kadai mutum ya gani zai fahimci cewa akwai tsantsar talauci anan bare kuma a shiga ciki ita kanta katifar ta kara ce kuma duk ta cinye ta gama sakewa.

Haka ta kwantar da Deejerh kan shimfidar ta fita cikin kauyen ta tsinto wasu ita ce , sannan ta kara komawa cen inda ta dauko Deejerhn ta rufe gudaji da jin da kasa.

Bayan ta koma dafasu tayi kan huta, ta dan diba ruwan kadan tasawa Deejerh a goshi.
Cikin minti biyar ta farfaɗo idanunta sun bude amman bata cikin hayyacinta.
Tsohuwar ta dagata ta dura mata ruwan maganin.
Take ta fara wata irin zufa gabadaya ta jiƙe, ga jini na kara zuba ta sankare take ta kara sumewa.
Da gudu tsohuwar ta fita ba inda ta nufa sai gidan Dr Ali
★★Dr Ali Tsohon babban likitane a birnin Paris da ya yi ritaya hakan yasa ya dawo kauye da zama domin taimakon mutanan karkara da ke shan wahala.

Tana zuwa ta sanar da shi cewa tayi bakuwa kuma bakuwar bata da lafiya tana bukatar taimakon Gaggawa da saurin sa kuwa ya bi bayanta suka je gidan.

Bayan sun shiga ya fara duba Deejerh kuma ya tambayeta yadda akayi ta samota da yanayin da take ciki.
Ta fada masa komai.
Ya kara dubata kafin ya ce, "a yanzu gaskiya bazan iya gane meke damunta ba sai anyi scanning tukunna."

"Ehto Don Allah ayi aceci rayuwar baiwar Allah."

Kai tsaye ya tashi yaje ya kira sauran yaran da ke tayasa aiki suka kaita karamin dakin da tanada domin yin duk wani abu da ya shafi kiwon lafiya.
Ba bata lokaci ya mata scanning bayan ya yi yake sanar da tsohuwar cewa


."Ectopic pregnancy ne."
Tsohuwar ta ce, "kamar ya kenan?"
Dr Ali ya ce, "Ciki a bayan mahaifa ke nan, shi ne pregnancy outside the uterus.Ciki ne da ake samun shi a bayan mahaifa a maimakon a samu ciki a cikin mahaifa wannan shi kuma a bayan mahaifa yake zama.
Amma mafi akasari idan ya fashe ne ko mu ce idan ya yi rupturing shi ne ake samun ciwon ciki mai tsanani da kuma zubar jini sosai.Ana yin theater a cire shi wanda ake cewa Ex-lap, aiki ne da za a buɗe cikin gabadaya sannan a fito da abin da ake son fitowa, saɓanin Cs da mafi akasari an san a inda yaro yake kwance ana buɗe cikin direct za a tafi cikin uterus ne a ciro ɗan.Amma shi na Ectopic yawanci sai an buɗe cikin ake lalube a gano a inda cikin ya maƙale dama ne ko hagu, sama ne ko ƙasa. Shi ya sa ake cewa aikin Ex lap So yanzu akwai bukatar yi mata aiki cikin gaggawa domin tseratar da rayuwarta in hakan bai samu kan lokaci ba zata iya rasa rayuwarta duk da cewa yin aikin ma ban da tabbacin samun lafiyarta a yanzu amman adai gwada fiye da cewa an zauna."
Rawa jikin tsohuwar ya fara tausayin Deejerh ya gama mamaye zuciyarta.


Gadan-gadan ya fara yi mata aikin yana kokarin cetonta duk da cewa ya mata allura amman sai wani irin numfashi take sama-sama yana ta sauri har ya kammalawa kenan numfashinta ya tsaya cak.....


08103080717


[12/15/2023, 6:42 AM] Xayyeesherthul-humaerath🥀: *°°°VIXEEN°°°*

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
*https://www.facebook.com/106494781436168/*

_#5Stars/Zeeyter/Yel/Freeya/Vixen._

©️ *XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH*

PAGE-25

Jiki a sanyaye ya fita ya tarar da wannan tsohuwar na kai kawo ta gagara samun nutsuwa ya ce, "Ma'am Am Sorry to say wannan da mai rayuwa ba ce,ga dukan alamu ta sha wahala sosai kuma ta zubar da jini Sosai."

Gabanta ne ya yi mummunan faduwa ji ta ke tamkar jinin ta ce Deejerh.
Za ta yi magana kenan wani ya fito yana fadin, "Papi tana motsi numfashin ya dawo."
Da sauri dukan su suka shiga ciki.
Cike da mamaki kuwa Deejerh ta dawo numfashi.
Dr Ali ya ce, "Alhmdu Lillah an tsalleke rijiya da baya tabbas Ubangiji shi kadai ya barwa kansa sanin da yasa Numfashin wannan baiwar tasa ya dawo."

Gyarata ya yi, ya duba jinin jikinta sannan yasa yaransa su bincika ko suna da irin jinin.
Cikin sa'a aka samu jinin ba bata lokaci kuwa aka sa mata, wani irin barcin wahala take.

Sai da Deejerh ta kwana uku cir tana barci.
Kullum sai Ma'am ta je ta dubata ta yi mata Adduo'i kafin in dare ya yi ta koma gidanta.
Karfe tara na safiya Ma'am na zaune ta kurawa Deejerh idanu
Kamar wasa ta fara motsawa tana kokarin bude ido.
A hankali ta bude idanunta babu abun da ta fara cin karo da shi sai hangen kanta tayi lokacin da mazan nan suke binta.
Zubura tayi tana rike kai tare da kokarin gudu.
Da hanzari ta tashi ta riƙeta tana fadin, "Aa zauna ki nutsu ki nutsu kinji."
Sai a lokacin ta dawo hayyacinta ta idanunta kan ma'am kafin tayi ajiyar zuciya ta koma.
Ma'am ta gyara mata kwanciyar tana, "karki tashi kinji babu abun da zai sameki ina zuwa ko."
Tana fita gun Dr Ali papi ta nufa ta sanar da shi Deejerh ta farka, ba bata lokaci kuwa yazo ya dubata sai da ya tabbatar jikinta ya yi kyau kafin ya ce, "za ku iya tafiya gida yanzu amman ga magungunanta nan wa inda zatana sha saboda cikinta zaina dan mata ciwo kafin a hankali ya daidaita."
Deejerh kam bata cewa komai binsu kawai take da kallo.

Godiya sosai ma'am ta yi masa sannan ta kama Deejerh tare suka tafi .

Suna zuwa ta gyara mata waje ta shingida sannan ta haɗa mata ruwan tea mai zafi ta bata ta sha.
Deejerh ta ce, "nan ina ne ? Waya kawo ni?"

Ma'am ta ce, "Tsintarki nayi bakin rafi shine na kawoki nan ina zakije?"

Deejerh ta ce, "na rasa wayata da jakata bayan na sauka daga jirgin kasa kuma anan ne zan kira wacce nazo gunta."
Murmushi Ma'am ta yi kafin ta ce, "karki damu zaki ci gaba da zama anan har ki samu wacce kika zo gunta, ni daya ce anan ban taba haihuwa ban da 'Ya kuma mijina Allah ya yi masa rasuwa zaki zama kamar 'Ya gareni?.

Deejerh ta yi shiru batare da ta ce komai ba, ganin cewa tana cikin yanayi

Please Login or Register in order to submit comment