Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

je ba sai na babbalaki cikin gidan nan."

Ta dauka zata sa ya kara fisgewa ganin tana yi kamar baza ta yi ba.
Da kanshi ya cire mata kayan da sauri yana zungureta yasa mata ya dauko turare ya kurma mata sannan ya jata suka fice.
A sit din baya ya ajiyeta duk da cewa ba a ganin mutum in yana cikin motar.

Kai tsaye gidan Nawar ya wuce da ita.
Gida ne da kana shiga zaka fahimce lallai ba abun Alkairi ake aikatawa ciki ba, musamman yanayin mutanen ciki, yawancin su duk bugaggune wa inda basa bigen kuwa suna cen suna wata tabarar ne,ko ca-ca ko dambe.
Duk da kasancewar gidan karami ba wani babba ba,amman haka suke lalatacciyar harkallarsu tsakanin maza da mata,har ma maza da mazan.

Deejerh na fita daga mota gabadaya idanunsu da hankulansu ya koma kanta, musamman matan da suke binta da kallon banza domin a tunaninsu tazo ne ta tuge su daga kan kujerar mulkinsu.

Zasu shige cikin dakin Nawar kenan wata na fitowa ta takewa Deejerh kafa da gangan sai da ta saki kara,kallonta tayi tana galla mata harara kafin ta ce, "Oh Sorry."
Ta wuce abinta.
Zayd kuwa ya fisgeta suka shige.

Suna shiga Nawar ya mika mata hannu,taki mika nata, Zayd ya mata kallon azabar da ya saba mata, haka ta mika masa hannun ya rungumeta.

Zayd ya fita ya bar su adakin.
Nawar ya kankameta kenan Deejerh ta janye jikinta.

"Mene ne lafiyanki kuwa? Kin san ni ba amun rashin daraja kuwa?"

Kan Deejerh na kasa ta ce, "Ranka Ya Dade Sallah nake son yi Don Allah ka barni inyi sai kayi duk abun da kake son yi ma."

Nawar ya ce, "Okay shikenan koma mene ne kiyi ina jiranki."

Tashi tayi ta yi Rolling din gyalenta, tana da wani agogo a hannunta dake iya nuna mata gabas hakan ta duba, ta kalla sannan ta fara sallah.

Idon shi na kanta yana kallonta har ta idar.
Tana idarwa ya ce, "Amman ita wannan sallar tana da mahimmanci ne? Na ga a prison wasu da yawa nayi kuma basa wasa da ita,yadda na ga kinyin nan suma haka suke."

Ganin yadda yake mata magana cikin nutsuwa yasa ta zauna kafin ta ce, "Is the ritual prayer of Muslims, performed five times daily in a set form, one of the Five Pillars of Islam. duk musulmin da ya yi wasa da sallah tamkar ya yi wasa da addini ne gabadaya ko ince ya fita ma daga addinin ne ma gabadaya."

Nawar ya ce, "Umm ni ba damuwana ne wannan ba yanzu tashi muyi abun da ke gabanmu."

Cikin nutsuwa ta bashi kanta domin bai mata kamar yadda sauran ke yi ba.

Kuma ta sake masa Sosai.
Har ya kai ga sun gama abun da suke ma sun zauna suna hira tare.
Tana tambayarsa to meyasa shi baya sallah.

Nawar ya ce, "mu addinimu babu wannan ba ace muyi ba church kawai muke zuwa addua."

Deejerh ta ce, "aiko in baka fara sallah ba za a ƙonaka a huta."

Dariya ya yi yana mamakin furucin nata ya ce, "Da gaske?"

Deejerh ta ce , "Eh mana."

"To shikenan zaki koyamun yadda ake sallah nima kar in shiga huta."

Har saida Zayd ya gaji da jira ya nocking masu kofa.
Koda Nawar ya bashi damar shiga dakin yadda yaga Deejerh cikin sakewa da walwala abun ya matukar bashi mamaki kawai tsayawa binta da kallo ya yi....
[11/20, 1:04 PM] Xayyeesherthul-humaerath🥀: *°°°VIXEEN°°°*

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
*https://www.facebook.com/106494781436168/*

_#5Stars/Zeeyter/Yel/Freeya/Vixen._

©️ *XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH*

PAGE-16

Nawar ya ce, "Ah ya ka tsaya kana mana wani irin kallone ni da Amaryar tawa?"

Binta ya yi da harara yana fadin, "Oh No na ga lokaci zai kure ne,ina so mu koma gida yanzu."

Nawar ya kalli Deejerh ya ce, "Girl,kina so ki tafi ki barni?"

Kallon Zayd ta yi,yana zare mata ido,kafin ta maida kallonta ga Nawar da ke sake mata murmushi ta girgiza masa kai alamar aa.

Nawar ya ce, "You see? bata son tafiya anan tare zamu kwana ko?"
Ya fada yana kallonta tare da mika mata hannu.

Ita ma mika masa tayi, tana kara girgiza kai a karo na biyu kan cewa ta eh.

Wani irin takaici da mamaki ne ya kubulu a zuciyar Zayd kamar ya janyota ya buga da ƙasa.

Murya na rawa Zayd ya ce, "O...o...Oga amman hakan zai zai...je mun matsala za a nemeta akwai matsala in aka fahimta."

Nawar ya ce, "Common, duk iya shirya zancen naka akan kankanin abu don na ce kawai ta kwana shine zaka rude,ka je cen ka shirya abun da zaka fada ni bai dameni ba,matsalarka ce."

Zayd ya kara cewa, "Oga Serious akwai matsala kasan da ace babu ban da damuwar hakan ni zan fi so ma."
Ya karasa maganaar yana rike hannun Deejerh.

Ita kuwa da sauri ta kara damke hannun Nawar yana janta kamar batasan yana yi ba tayi mirsisi da ido.

Tana kara janye jikinta.
Nawar ya yi murmushi ya kalleta yana fadin, "Sorry Kinji, karki damu ki bishi ku tafi gobe sai mu ci gaba da hirar mu ko?"

Deejerh dai bata so ba ta sunkuyar da kai kasa.

Nawar Ya kalli Zayd ya ce, "Saura kuma goben karka dawo mun da ita kasan sauran."

"Ah haba Oga kasan bama hakan zai faru ba ai dole na." Zayd ya fada ya riko hannun Deejerh da yi mata murmushiin karya.

Bye-bye Nawar ya fara mata cikin sakin fuska,ita ma ta yi masa har suka fice daga dakin.

Ban da kwafa da tsaki babu abun da zayd yake yana driving har suka isa gida, Deejerh kuwa abun da ya matukar bata mamaki da tsoro da ya gagara dukanta tabbas dole akwai wani abu da ya shirya a ranshi da zai mata.

Dakinta ta wuce da sauri kawai tayi sallar magrib da isha har ta kwanta a gado kamar an mintsineta da ta fara ganin abubuwa na dawo mata tuni ta tashi fara practice din MMA training dinsu neman barci ta yi a idanun ta ta rasa.
Karshe kawai ta ciro Tablet dinta tana dubawa, cikin sa'a kuwa kamar kullum Maestro Ramon ya tura mata da wa'azuzzuka da azkar, shiga tayi ta fara bin azkar din ana karantawa ita ma tana bi tana karantawa, bayan ta gama ta shiga wani video da ya turo mata Islamic words of encouragement da Sheik Umar Sulaiman ya gabatar yana fadin, "Allah Knows you're tired, He Knows You're trying ,He Knows it's difficult for you,But know that Allah will never put you in a situation you can't handle."
Tana saurara sai ta ke ji tamkar Don ita yake furucin nan take taji wani sanyi a zuciyarta yana ratsata.
Murmushi ta yi azahiri tana fadin, "Na sani daman Ubangiji na bai manta dani ba,kuma duk rintsi,duk daren da dadewa bazan taba dauwama cikin wannan halin ba, hakan shine jarabawata kuma ina fatan inci ta da kyakkyawan sakamako."
Ta kara bi ta karanta adduo'in kwanciya barci ma da ya saba turo mata sannan ta kwanta cikin ikon Allah kuwa barci ya yi awun gaba da ita.



Monday

Da wurwuri ta tashi ta shirya taje ta diba abinci a kitchen ba tare da sanin kowa ba , ta dunga sauri kar Zayd ya ganta aiko ta ci Sa'a har ta fice a gidan basu hadu ba.
6;00 ta kama hanyar skul

Ko da taje babu kowa cikin School din sai ita kadai hakan yasa ta zauna a stairs dinsu.

Tana zaune jigum cikinta ya fara yi mata ciwo,zufa take ta ko ina,cikin lokaci kadan ta fara ficewa a hayyacinta,gashi ita kadai babu kowa Students basu fara zuwa ba, karshe da tayi wani numfashi take ta sume.

Students na fara zuwa duk suka taru akanta anata cecekuce hayaniya ta gauraye School, Su Noha na zuwa suka je suna jijjigata duk sun gama razana a tunaninsu ta mutu,jin hayaniyar bata kare bane yasa Shugaban makarantar ya fito, aiko yana fitowa daidai da zuwan Maestro Ramon tare suka karasa,suna ganin Deejerh kwance haka cikin sauri suka kira waya clinic din school sukazo suka dauketa.
Su Maira kasa shiga class suka yi suka je suka tsaya kofar Clinic din suna ta zarya,sun kasa zaune sun kasa tsaye hankali a tashe.
Maestro Ramon ma hankalinsa ya tashi matuka.

Taimakon Gaggawa suka bata cikin sa'a ta farka,tana farkawa kuwa ta koma barci kasancewar allurar hutu da suka yi mata.

Dakyar Maestro Ramon ya kora su Daeej class kan cewa lallai da ta farka zai sanar da su.

Bata farka ba sai da lokacin tashi ya yi,ana ringing belt din tashi tana farkawa.
Clinic din suka nufa kai tsaye, suna shiga Noha ta ce, "Da kin mutu da munyi fushi da ke, kuma yanzunma ba ruwanmu dake tunda har munata jiranki kinki farkawa."

"Ai rabu da ita,tana kara yi mana irin wannan shikenan ba ruwanmu da ita kawai tasa mutane cikin damuwa,ni Allah class din yau kaf babu abun da na fahimta ciki fa." Daeej ya fada.

Abiel ya ce, "Yoo ba gwara ku ba,ni wani juyi kaina ya dunga yi kamar zai tsaye gashi babu harka bare mutum ya sha ya dan samu sauki."

Sai a lokacin Maira ta yi magana, "Duk naku mai saukine,ni har yanzu jina nake wata iri ban dawo daidai ba."

Deejerh binsu da kallo kawai take, sai da taga sunyi shiru sannan ta yi Murmushii tana mika masu hannunta.
Noha ce ta fara daura nata kai,Daeej ya daura, Hakama Abiel,sannan Maira karshe.

Deejerh ta ce, "Kawancenmu na nan, kun yafe mun ko sai na kama kunne?" Ta fada a shagwabe.

Dariya suka yi duka suna daga hannun sannan suka rugume juna.

Maestro Ramon ya shigo yana dariya, "Ma Sha Allah jiki ya yi sauki hankali ya kwanta ko?"

Daeej ya ce, "Yes Sir yanzu kam hankali ya kwanta."

"Maddallah haka nakeson ji kuma nake son gani,yanzu zan kaita gida a motata zaku iya tafiya."

Rikota suka yi duka kamar wata jaririya suna lallabata har suka rakata motar Roman sannan suka tafi suna yi mata Bye-bye.

Suna cikin tafiya ya tsaya ya siya mata kayan fruits da cake da drinks, sai da ya tabbatar ta cinye cake din ta sha drinks din sannan ya ta motar suka ci gaba da tafiya.

Suna isa gidan kuwa lokacin su Dadynta suka dawo daga wajen aiki, Zayd kuwa ya tafi wajen Nawar.

Da Mamaki suka tsaya kallon Maestro Ramon, ya mikawa Dadynta hannu suka gaisa.
Sannan ya ba shi damar binsu shiga gidan.
Momynta ta ce , "Daughter ya na ganki Somehow? What's going on? Fatan dai ba wani laifi kika yi ba."

Shiru Deejerh ta yi bata ce komai ba.

Saida suka shiga bayan sun gaisa Maestro Ramon yake fadin, "Kuyi hakuri na kara zuwa a karo na biyu ba tare da sanarwa ba."

"No problem ." Dadyn Deejerh ya fada cikin sakin fuska.

Maestro Ramon ya gyara zama kafin ya ce, "Yau Deejerh bata ji dadi ba School wanda har ya kai ga sai da muka danganata ga school Clinic sakamakon ciwon ciki mai tsanani da ya taso mata wanda har ya kai ga ta suma."

Da sauri Momynta ta kalleta tana taba jikinta. Tare da fadin, "Oh Sorry Daughter,sannu kinji yanzu da kwai abun da ke miki ciwo?"
Ta girgiza mata alamar aa ba tare da cewa komai ba.

Ya ci gaba da fadin, "Alhmdu Lillah yanzu kam ta dawo daidai amman akwai matsalar da zata iya afkuwa nan gaba muddin ba a nema mata mafita ba, yan gwaje-gwajen da aka mata a School clinic ya tabbatar da cewa Ulcer ce ta rike mata ciki wanda hakan ke bayyanar da cewa bata cin abinci yadda ya kamata hakan ya yi kasa sosai da har ya fara taba lafiyar cikinta sannan akwai yiwuwar ma tana yawan tunani wanda shi ma yana kara taso da ciwon sosai."

Dadynta ya ce, "aikuwa batun cin abinci kam hakan zai iya faruwa ba makawa domin sam bata son cin abinci in kaga ta danci abinci ma to Uncle dinta ne ya tursasata dole ta ci,tana da matsala ta wannan bangaren tunani kuma banjin gaskiya da kwai abun da har zai dameta ta zauna tunani akai tunda babu abun da ta rasa."

Roman ya ce, "amman ranka ya dade mai zai sa ku dunga tursasata da kanku ba sai Uncle din nata ba,na tabbata da cewa Zata fi sakewa kuma ta ci cikin nutsuwa sannan batun tunani ai ba sai mutum nada damuwa ba kila bata samun masu debe mata kewa ne."

Karaf Momynta ta ce, "to ai tafi sabawa da Uncle dinta kuma shi yake yi mata Komai sannan mu bamu cika zama da ita a gida ba,shine yake zama domin ita muna gun aiki kuma bamu da wata matsala yana debe mata kewa dama duk abun da ya kamata."

Roman ya ce, "Amman Madam bai kamata ace aiki zaisa baza ku damu da rayuwar Yarku ba,ko da kuwa Uncle dinta na dawainiya da ita dole tana bukatar iyayenta ma su jata a jiki sosai sannan su samar mata da lokacin su, 'Ya'ya mata rayuwar su na dauke da kalubale kala kala daban daban wanda kuskure kankani kan iya ruguza komai na cikinta."

Ta ce, "hakane Amman Deejerh bata da wata matsala da Uncle dinta kuma na tabbatar da cewa yana yi mata abubuwan da suka dace mafiyin yadda mu muke."

Dadynta ya ce, "Karka Damu Ranka Ya Dade za a kula in sha Allah mun gode sosai."

Maestro Ramon ya ce, "Nike da godiya na barku lafiya."
Yana fada ya fita daga gidan.

Motar sa na fita ta Zayd na shiga.
Sai lakewa Zayd yake yaga wanene amman ina har Roman ya wuce.

Zayd na shiga ciki Momyn Deejerh na mita, "wannan mutumin ya cika shishshigi wallahi nufinsa kenan Dan uwans baya kula da ita ko ya? Tsabar gulma da munafurci."

Dadyn Deejerh ya ce, "ke ko kiyo shiru ki bar maganar mana ba dai na amsa masa ba ai Shikenan."

Zayd ya katse su da fadin, "mene ne yake faruwa ne? Naga wani ya fita yanzu gashi kuma kuna ta hayaniya."

Momyn Deejerh ta ce, "wannan Maestro Ramon dinne yazo wai ba a kula da Deejerh yunwa ya sa mata Ulcer, naga ma ai mutum na iya ciwon ciki kawai yanzu haka munafurcinsa ne kawai ke cinsa."

Zayd ya zauna yana kallon Deejerh da ta tashi ta shige dakinta ya ce, "wannan mutumin ai kasurgumin munafuki ne,ni tun zuwansa na farko bai mun ba,shiyasa na je nayi bincike a kasansa, Da ya yi rashin ji sosai baya jin magana kuma yana da kudi sosai tsabar munafurci da son sawa 'ya'yan mutane idone yasa shi fara koyarwa a makarantar nan,tunda ance albashinsa na makarantar shine na mai gadin gidansa fa."

Momyn Deejerh ta ce, "No wonder, aiko Deejerh na kammala high school dinta bazata ci gaba Anan ba sai yaje can ya ta munafurincinsa."

Zayd ya ce, "nima abun da nake tunani kenan."

Ya fada yana tashi ya shiga Dakin Deejerh.
Yana tura kofar......

08103080717

*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
08089965176
07084653262
[11/20, 1:04 PM] Xayyeesherthul-humaerath🥀: *°°°VIXEEN°°°*

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
*https://www.facebook.com/106494781436168/*

_#5Stars/Zeeyter/Yel/Freeya/Vixen._

©️ *XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH*

PAGE-17

Zaune take rike da Tablet dinta tana danna karatu yana yi tana bi.
Wayar ya fisge ya jefar gefe, sannan ya ce, "kin dage sai kin sanar da wancen munafukin malamin naki sirrinmu ko? Ko ince atakaice kina son numfashi ya bar jikinki dana iyayenki ko?"
Ta girgiza kai kafin ta ce,"Na rantse ni ban fada masa komai ba,na je School dinne ban da lafiya shine daga Clinic ya kawo ni gida,kuma ni bance masa komai ba."

Wani kallon banza ya mata yana daga kai tare da fadin, "Really? kenan haka kawai yake kokarin sa mana ido da bin diddigi ba tare da kin bashi kofar yin hakan ba? U are very stupid taya ma zan yarda da hakan? U think am idiot as u?"
Ya karasa maganar cikin daga murya yana daga hannu zai mareta.
Kafin hannunsa ya kai fuskarta ta kauce.
Hannun ya sauka kan karfen gefen gado.
Wata azaɓa ce ta ratsa hannun take ya canja kala abun ka da farin mutum.
Cikin takaici ya daga hannun na rawa yana kallonta.

Radadin da yaji ya sanya shi gagara yin wani kwakkwaran motsi bare tunanin daukan wani mataki.
Ita kuwa saurin sunkuyar da kanta ta yi,ta yi tsuru jikinta na rawa.
Kara binta ya yi da razanannen kallo yana cizon yatsa ya fice cikin sauri.

Tana jin fitarsa ta dago kai sai da ta tabbatar ya fita kafin ta fara zanga uban dariya harda rike ciki don mugunta,bata ankare ba har ana jiyo sautin dariyarta, taba kofarta alamar shigowar da za ayi yasata saurin gimtse dariyarta ta koma tamkar ba ita ke yi ba.
Dadynta ne ya shiga yana fadin, "Daughter kina lafiya? Na ji kamar wani sauti daga nan dakin?"

Deejerh ta ce, "Dad ba komai ni banji wani sauti ba, oh inaga karar Tablet din cen ne da ta fadi a hannuna." Ta tashi tana dauko wayarta.
Murmushii ya yi mata ita ma ta maida masa sannan ya fice ba tare da ya ce komai ba.

Ci gaba da bin karatunta ta yi,har ta gama,ta ajiye wayar kenan kamar an zabureta ta tashi ta fira zuwa kitchen,a hancinta ji take kamar an bar gas a kunne,taje ta duba taga a kashene,ba ta yarda da hakan ba ta danna ta kunna sannan ta kara kashewa.
Har ta fita zata koma dakinta ta kara juyawa zuwa kitchen din kwakwalwarta na tiriyomata cewa ai yanzu ba ta kashe gas din ba ta na zuwa ta gani a kashe dafe kanta tayi kawai ta koma dakinta.
Tana shiga ta kulle kofarta.
Can koma zuciyarta ta fara rayo mata in kuma gobara tazo fa ta kulle kofa babu mai iya shiga bare ataimaketa,da sauri ta tashi ta bude, tana budewa ta ci gaba da jiyo warin gas a hancinta.
Wani karamin gyalenta tasa ta rufe hanci da shi.
Ta daina jin wari amman kuma da kyar take numfashi,yana yi sama-sama kamar wacce zata bar duniya.
Tuni gumi ya rufe ta, da sauri ta janye gyalen sannan ta shige Toilet ta wanke fuskarta.

Magungunan da maestro Ramon ya bata tasha,ta dan kara shan sauran kayan fruits din kafin ta kwanta.

★★★ HOPEFUL ENDEAVORS ORGANIZATION

Yau dai kam Deejerh sai da ta nemi izinin gun Momynta kan cewa zata gidan su Maira akwai Assignment din da zasu hadu suyi, kasancewar Zayd baya gida ta barta ba tare da ko tsananta bincike kan lallai can din zata ko akasin hakan ba.

Ko da suka je Ranar ba ayi masu wani lectures ba, wassanni suka yi sosai suka samu nishadi da karsashi kafin Ajeef ya sanar da su cewa zasu hada karamin shagalin nuna fasaha na gargajiya.
Sunji Dadi sosai kowa sai murna da dariya suna nuna farincikin su.
Roman ya kalli Deejerh yana fadin, "akwai bukatar a zana mana yanayin kayan da ya kamata asa kuma Deejerh kece zaki jagoranci wannan bangaren ina fatan babu matsala."
Da sauri Deejerh ta amsa, "Yes Sir." Dadi taje aranta Sosai an tabo bangaren da tafi so da kwadayi arayuwarta.

Daga lokacin suka fara shirye-shirye fannin drama wacce Ajeef ya hada masu kan fito da illar shaye-shaye kan iya harfarwa ga kwakwalwa wanda ya kasance Su Daeej da Abiel ne kan gaba wajen jagorantar dramar.
Tun daga farkon yadda aka fara masu bayani kan matsalolin da shaye-shaye kan iya haifarwa ya shafi kwakwalwar Dan Adam jikin su gabadaya ya yi sanyi dukaninsu sai kallon kallo ji suke aransu tamkar donsu aka shirya hakan.
Wanda kuwa kusan hakanne Domin Maestro Ramon ne ya tsara domin nusar da su cikin sauki ba tare da jin cewa antakura masu ba.
Kowanni bangare sunyi rehearsal sosai kan abun da aka basu na cewa zasu gabatar akai hadda kalubalen da 'Ya'ya mata suke fuskanta in sunyi ciki ba tare da Aure ba, wasu koda ace ba da son ransu aka masu ciki ba,indai cikin ya bayyana Shikenan sun fara fuskantar tsangwama wajen al'umma wanda har hakan yakan iya haifar da babbar matsalar da zuciya ke iya ingizasu su fada ga babbar halaka.


Bayan sun gama suka hadu duka wajen cin abinci ranar traditional food dinsu aka yi, Nacho and tacos,sai da suka ci suka koshi Kowa ya fito Deejerh da su Daeej suka tsaya kamar yadda suka saba sai sunyiwa juna sallama kafin su rabu.

Jiki a sanyaye Maira ta ce, "Guys wai anya kuwa zamu iya ci gaba da shan harkar cen? Kanmu muke wa illa fa tunda dadin na dan lokaci ne."

"Gaskiya nima yau abun ya sake mun jiki matuka,kinga mu muke abun amman sai nke ji araina kamar muna hasaso abun da zai iya faruwa damu a nan gaba ne." Abiel ya fada.

Dafe kai Daeej ya yi kafin ya ce, "Duk yadda za ayi ma kawai ayi mu daure mu hana kanmu shan wannan abun inaga shine mafita ni kaina jikina a mace yake Gaskiya in mukace zamu ci gaba ba karamar illa zamuyi wa rayuwarmu ba, zaifi kyau in muka danne,kila muma watarana mu iya hana wasu."

Sai a lokacin Noha ta yi Magana, "ni yanzu kullum addu'a ta Allah ya ban zuciya irinta maestro Ramon in zama mai son taimako da gyara al'umma, kunga kenan dai dole sai mun fara gyara kanmu kafin mu iya gyara wasu."

Deejerh na binsu da kallo bata ce komai ba.

Maira ta ce, "Oyaa to daga yau muyiwa juna Alƙawari Duk rintsi duk bacin rai kuma duk tsanani ba za mu kara attempting shan kowanni drugs ba sai dai wanda aka bamu daga hospital in ya zama ba ma da lafiya." Dukan su suka hada baki wajen fadin Yes harda Deejerh.

Hannunta tasa suma suka sa sannan suka daga tare suna dariya yadda suka saba,kafin suka rabu suna Kewar juna.


Tana shiga gida kuwa ta ga Zayd zaune da Momynta a palour suna hira.
Ya bita da harara sannan kuma ya fara murmushin gulma yana mika mata hannu, "Oyoyo Daughter an gama Assignment din kenan? Na yi kewarki fa tun tuni nake jiranki baki dawo ba."
Kin mika masa hannun ta yi Momynta ta kalleta rai ɓace ta ce, "Miye haka? Baki ga ana miki magana bane?"

Zayd ya cafko hannunta yana zaunar da ita gefensa ya ce , "Am so sorry Daughter kina fushi dani? Chocolate dinki jiya da ban siyo ba, kiyi hakuri ko sai na kama kunne ne?"

Ya fada ta gefe yana sa hannunsa yana murɗa mata fatar cinya.tare da harara.
Haka dan dole ta saki fuska tana girgiza masa kai.
Momynta tayi guntun tsaki tana, "ku dai ai ba a shiga tsakanin ku, za ma ku shirya ne." Ta karasa maganar tana tashi daga palourn.

Yana tabbatarwa ta tafi ya dakawa Deejerh tsawa yana fadin, "Wawiya kazamiya kawai tashi min da gani anan."
Sai da ta zabura ta tashi ta shige dakinta abun ta.
Tana shiga tayi wanka,tayi alwala sannan ta yi sallah,tana idarwa drawing book dinta ta dauko da colours tana fara tsara irin customs din ya kamata su sa maza da mata.

Tun bayan magrib har aka kira isha taje tayi ta ci gaba da yi gabadaya duka biyun sai da

Please Login or Register in order to submit comment