Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ο»ΏπŸ’΅πŸ’΄ *AKANKUDI* πŸ’΄πŸ’΅

(A poor lady story)

.... 28th March, 2023

πŸ””πŸ“š *JARUMAI WRITER'S ASSOCIATIONS* πŸ“š

@ *sherntee Ghayu* πŸ₯°πŸ₯°


πŸ…Ώ......... *001*


*KATSINA*

"Ummah Kinga wallahi harna gaji da jiranta ace Idan mutum ya shiga d'aki kamar bokanya" Ummah dake zaune gefen wannan kyakkyawar Budurwar da bazata wuce 17 a shekaru ba tace "hmm Maryam Kenan ai duk Kece kika sangarta ta dayawa ace kullum sekin biyo mata" Ummah ta k'arashe tana tana kallon a gogon y'ar k'aramar keypad din hannunta ta cigaba da cewa "ai gashinan takwas din harta wuce" kyakkyawar Budurwar da aka Kira da Maryam tayi murmushi tace "Ummahmu Kenan ai yanzu zakiga ta fito" ko rufe baki batai ba Sega wata kyakkyawa kuma farar budurwa ta fito fuskarta fayau Babu ko powder natural beautyn ta ya fito tabbas da ace ba'a 9ja naganta ba danace wannan anyi kyakkyawar balarabiya irin quraish dinnan lol 😁
Tanata kiciniyar saka face mask tace "Maryam taso mu tafi kar muyi latti" Ummah tace " *SARAUTA* kofa karyawa bakiyi ba" kyakkyawar Budurwar da aka Kira da sarauta tace "Ummah na k'oshi sena dawo, wai meyasa yau bakiyi waina ba" Ummah na mik'amata kud'in makaranta tace "yau sunan y'ar gidan Badiyya inason naje ne shiyasa" sarauta tace "to kijira Idan na dawo sena rakaki zanje mu muntafi ayi mana addua" Maryam ta amshe dacewa "se mun dawo" Ummah tabisu da addua Har suka tafi.

Highlights college
Anan suke karatu Sanda sukaje anata taron latti dole suka tsaya suka amshi hukuncinsu sannan suka wuce class.

At 10:20am
Gaba d'aya d'aliban suna waje sunata wasansu inka cire wasu Daga cikin SS3 students suna zaune class suna fira, su hud'u ne Akan teburin hira suke sosai suna shewa inka cire sarauta dake gefensu tana zane. Acikin firar tasune d'aya ke cewa "amm Yawwa spincy dan Allah kinsiya wannan littatafin" spincy tace "na siya harma na Gama karantawa" da sauri zeena tace "tsakanin da Allah wayyo dan Allah kiban labari wallahi tunda na gama free pages ban kuma ba" Maryam tace "wai wane littatafin?" meelarge tace "auren wata Tara mana" Maryam tace "Kai Nima inason littafin wallahi marubuciyar tasan sirrin love dana rubutun littafi wai ya aka k'are ne tsakanin MD da XAHRA" meelarge tace "Aini Dama Bana siyan littafi sedai na jira na bati dan Allah spincy Idan kinje gida ki turomin" spincy tayi kicinΒ² da rai tace "Allah ya sawak'e insai littafi infitar dashi kinma ja wallahi tunda na gama gogeshima zanyi" Maryam tace "kudai kuka sani nidai fad'amin complete sunan littafin naje na nema" Zeena tace "gaskiyarki Maryam Nasir" Spincy tace " *AUREN WATA TARA WRITING BY HAJARA L SADEEQ MISS HAJJO*" Meelarge tace "Aina Allah base k'arewa seme dan baki turomin ba a banza zanga Yana yawo a group" Spincy tace "oho Dai aje aita karanta littafin Allah ya isa" "mttsswww" dogon tsakin dasukaji ne yasasu juyawa su kalleta tsakin ta k'arayi kafin tace "Allah dai ya kyauta muku madadin ku zauna kuyi tunani Akan yanda zakuyi suna ko kuma kunemi na kanku shine zaku zauna kuna firar banza da wofi" Zeena tace "hmm *MARYAM SARAUTA* Kenan ai gwara mu zauna muyi firar banza da wofi Akan mu zauna muyi tunanin dakike magana akai mufa matane harmu mutu rik'on mu ake Daga iyayenmu Zuwa mazajenmu daga mazajenmu Zuwa y'ay'a yenmu to Akan me zamu zauna mu b'ata lokacin mu " meelarge tace" gaskiyarki yar uwa" Sarauta tace "Aiko kunji haushi niko kunganni nan neman kud'i se inda k'arfina ya k'are kenifa *AKAN KUDI* ba abunda bazan ba raina ne kurum da bazan bayar ba" kafin wani yayi magana sukaji ringing bell alamar andawo aji daga haka kowa ya wuce mazauninshi Haka aka cigaba da darasi har lokacin tashi yayi.
Kallon Sarauta Maryam tayi tace "yakamata mu tsaida napep mu tai ko" Sarauta tace "haba Maryam nan da d'aki Tara shine Zaki wani ce muhau napep Dan Allah ki koyi economizing rayuwa haba ni band nawa kud'in inyaso kekin hau napep din Ohk" ta k'arashe tana mik'ama Maryam hannu Maryam tace "yanzu Sarauta abunda kikeyi kin kyauta Kenan ke kullum bakida abunda ke faranta Miki se kud'i kin fifita kud'i Akan kowa kin maidani kamar ba k'awarki ba wallahi kiji tsoron Allah kud'i fa halaka ne ashe duk fad'an da Ummahmu take Miki a banza" Sarauta tayi murmushi tace "hmm Maryam Kenan kud'i ba halaka bane kyauta ce kuma baiwace tadaban da Allah keyiwa bayinshi ni bance Miki keba k'awata bace kuma bance fad'an Ummah yatashi abanza ba but am sorry to say gaskiya kud'i sunfimin komai kizo mutafi" ta k'arashe tana tafiya wannan ba sabon Abu bane agurin Maryam Tasha sanar da ita kud'i sun fita a gurinta so bazatayi mamaki ba shiyasa kawai tabita suka tafi.
A gajiye taje gida, ta tarar da Ummah harta shirya sedai me cemata tayi taje kurum ita tagaji Babu inda zata, dama Ummah ta tsammaci hakan shiyasa kurum tayi tafiyar ta.



*JIDDA*

*The emir palace*


Ajere motocin suka shigo masarautar a hankali suke tafiya harsu kayi parking da sauri escorts din suka fito tare da bud'emai k'ofar a hankali yasoma fitowa daga motar kafin kuma gaba d'aya ya bayyana (hasbunallahu wani'emal wakeel tsarki ya tabbata GA mahaliccin wannan halintar) saurayine da baze wuce 29 a shekaru ba Yana sanye cikin k'ananan kaya inda ya d'ora alkyabbarshi me adon zinari a sama gashin kanshi ya sauko har gurin wuya ta b'angaren Dama kyawawan red lips dinshi su suka k'ara k'awata fuskarshi eyesbolls dinshi bak'i wuluk yariman nan dai ya had'u ta ko Ina ga kyakkyawar k'ira da rabbi yayi mishi tafiya yake in a classic way harya k'arasa wani kyakkyawan building daya gama haduwa tundaga yanayin building d'in kasan cikinshi zeyi kyau da dad'in kallo Haka kuwa akai Kai tsaye yashiga cikin k'ayataccen palourn komai yaji ba'a magana a hankali yasoma hawa upstairs d'in d'aki d'aya ya bud' e Acikin jerin d'akunan wani kyakkyawa kuma farin dattijo nagani Wanda daka kalli fuskarsa zaka hango dattijon taka da mutuntawa *SARKI LADTEEF* Kenan sarki masarautar jidda murmushi yayi tare da mik'ewa cikin nuna murna da k'auna yace "you're welcome my darling son" shima rungumeshi yayi tare da shagwab'e fuska kamar k'aramin yaro cikin lafiyayyen larabcinshi yace "ai Nayi fushi bakaje d'aukoni Airport ba koma murnar zuwana bakuyi ba" kyakkyawar matar dake tsaye gaban mirror tana murmushi tace "my baby boy Kadai k'i girma ko" kallonta yayi yace "Ummi Kenan aina gode hardake ko" kusa dashi ta dawo tana zama tace "Tohm munji we're sorry Ohk koba Haka ba JARUMINA" ta k'arashe tana kallon sarki murmushi sarkin yayi yace "hakane mana ayi mana afuwa" saman kafad'arta ya kwantar da kanshi tare dacewa "badan halinku ba anyafe" duk dariya sukayi Ummi ta mik'e tasama me martaba alkyabbarshi tare da fesheshi da turare "Abieyna seka dawo" Abiey yace "Tohm Abiey's boy sena dawo" harya fita yadawo yace " *MUHAMMAD SHUREIM*" dasauri ya juyo yace "Na'ammmm" Abiey yace "kome kakeyi karka bari yau ta wuce bakaje Ka gaida su Neenah ba kaji ko" Muhammad Shureim yace "in sha Allah Abiey" daga Haka Abiey ya fice kallon Umminshi yayi yace "meyasa Abieyna yake hakane Sarai fa yasan halin mutanen nan amma shi yafi son ayita wulak'antani" Ummi tazauna gefenshi tare da d'ora hannunta a saman kafad'aeshi tace "kayi hak'uri my son mahak'urci nawadaci wata rana se labari kaje kugaisa kaji Aidai bazasu cinye namanka d'anye ba ko" Kai ya d'aga mata tace "good boy Shureim" murmushi yayi yace "Humm Ummi Bari naje b'angaren *SHUBAI'A* tun kafin tasamu labarin dawowata tad'au fushi me dogon zango dani" Ummi murmushi kurum tayi tace "gaskiya Kam gwara kaje nasan dishes nasan an shirya maka" murmushi yake harya fice daga d'akin cike da shauk'i da d'okin ganin k'anwar tashi............


Kar ku manta labarin *AKAN KUDI* k'irk' irarren labarine danayishi domin nishad'antarwa dakuma fad'akarwa nice taku me nishad'antar daku a kullum da ko yaushe

@ *sherntee ghayu* πŸ₯°πŸ₯°

Sak'on godeeya ta Zuwa gareku a bin alfaharina
~Miss hajjo
~mom Islam
~Daddy's little girl
~zaituna


07064706167


πŸ’΅πŸ’΄ *AKAN KUDI* πŸ’΅πŸ’΄

( A poor lady story)

..... 19th April, 2023


πŸ””πŸ“š *JARUMAI WRITER'S ASSOCIATIONS* πŸ“š


@ *sherntee Ghayu* πŸ₯°πŸ₯°

πŸ…Ώ....... 002

........... Tunda Yafito ake gaishe shi amma gaba daya hankalin shi ya tafi,
Wani kata farin building yashiga wanda kallonshi kurum Zenuna maka bak'aramin kud'i aka zuba a gurin ba daga ganin tsarin building din zenuna maka Bana mutum daya bane,

Babban falo ne wanda yaji kayan alatu da more rayuwa akwai bene a both side din falon wanda yabada wani style na daban upstairs d'in shima akwai falo dakuma bed rooms, hawa uku ne benen kowane hawa akwai falo bedrooms dinning da kitchen, Babban photo frame din dake a falon shize nuna maka Cewa falon nasune duk zaune suke suna dariya akan kujera su ukku akayi hoton, Yarima Shureim, gimbiya Shubai'a dakuma umminsu ba qaramin kyau sukayi ba.

A hanzarce ya k'arasa hawa na biyun, lek'e yafara kafin yashiga gaba d'aya cike dason nuna bazata yace "surprise" a D'an tsorace ta juyo, wow a gaskiya gimbiya Shubai'a bak'aramin kyau gareta ba, cikin yaren kurmanci take nuna mishi yaushe yazo, yana motsi da bakinshi kuma yana Mata nuni da yanzu yazo ba jimawa,
Rungumeshi tayi cike da farin ciki sundau kusan 3mins ahaka kafin ta sakes shi da hannu take nuna mishi tayi kewarshi,
Ahaka suka D'an tab'a hira kafin tasoma jera mishi abinci, iya farfesun kifi kurum yaci tunda yafara cin abincin yake yabamata harya gama don dama yasan lagon k'anwar tashi, haka suka d'au tsawon lokaci kafin yaje yayi wanka ya shirya ya fito domin ta rakashi b'angaren su
Neenah, da farko Shubai'a bata so rakashi ba amma hakanan ta rakashi.

Tafe suke suna fira gwanin ban sha'awa harsuka qarasa wani building shigen nasu ne amma nasu yafi haduwa shikuma hawa hud'u ne a ciki
B'angaren Neenah, da b'angaren Hajjo Mubeenah, se b'angaren Hajjo Jumaima, se b'angaren gimbiya Khaleesat,
A Babban falon suka zauna, Hajjo Mubeenah itace ta fara saukowa tundaga kallon da take musu zaka fahimci basu karb'u ba a wajenta, cike da izgili take kallon su kafin tace "Allah yasa lafiya??" Shubai'a ce tayi dariya take Mata nuni da Yarima ya dawo yau shine sukazo gaishesu, murmushi Hajjo Mubeenah tayi tace "toh fa su kurma anfara bada ba'asi" kafin wani yayi magana sukaji muryar Hajjo jumaima na cewa "ah ahh yau kuma su kurma ne a part d'inmu" Neenah dake shigowa part din tare da khaleesat tace "maraba da bak'in k'asar turai yaushe a k'asar tamu" yana d'an murmushi yace "d'azu nazo" Neenah tace "Tohm sannunka da dawowa" ta k'arashe tana zama kusa da Shubai'a, kafadarta ta data tana Mata magana da kurmanci yanda zata fahimta tace "shine se yau ake ganinki kin b'oye" Shubai'a tayi murmushi tana Mata nuni da Babu inda take zuwa, Hajjo jumaima tace "toh dama Ina kurma zeje" Neenah tace "Haba Hajjo dan Allah ki kama girmanki Ina ruwanki ba Allah ya d'ora mata ba Kindai San bada shi aka haifeta ba ko to ki kiyaye" sakamakon suna dan shakkarta yasa suka Ja tsaki duk suka koma d'akunan su, a wayence khaleesat ta gaisa da su kafin ta wuce d'akin ta, kusan minti 20 suka dauka suna fira da Neenah wanda jigon firar itace Shubai'a, Shubai'a akwai son hira da labari, kafin sukayi mata sallama suka tafi.




*KATSINA*

Zaune take daga k'ofar d'akin tana danna y'ar k'aramar wayar Ummah, yayinda Ummah ke kitchen tana girki, wani yarone yayi sallama tare da cewa "a bada kub'ewa" Ummah dake kitchen tace "ta nawa?" yace "ta ashirin" tsam Sarauta ta mik'e ta dauko mishi kubewar ta amshi kud'in ta koma ta zauna, Ummah data fito daga kitchen tace "Kwana biyu Sarauta kamar akwai abunda ke damunki duk kin shiga damuwa" a hankali tace "Ummah Maryam fushi take dani yau Kwana biyu batazo gidannan ba kuma kinga na kirata tak'i dagawa" Ummah tayi murmushi tace "Sarauta ta Maryam Kenan to ai sekije kiji me kikayi mata" Sarauta tace "to ai seta d'auka na wani damu da'ita" Ummah tace "Aikin damu da'ita ne Kinga bansan shashanci ki tashi kibani guri" tana kaiwa nan ta koma kitchen mik'ewa Sarauta tayi ta dauki Hijab dinta tayima ummah sallama ta fita, tafiya take cikin salon burgewa seka d'auka yar gidan wani Babba ce a hankali take tafiya harta k'arasa babban titin tananan tsaye kusa da wata mota, a hankali taji ana cewa "yanzu ya zamuyi mu dauko yaron can duba fa kagani akwai mutane dayawa a gurin nidai gaskiya tsoro ya kamani" d'ayan dake gefen shi yace "Haba Nas sokake ka b'atama komai kawai fa fita zakayi ka jawo hankalin yaron mud'aukai" wanda aka kira da Nas yace "gaskiya bazan iya ba" a hankali ta k'araso gefen motar tare da cewa "me zaku bani in kawo muku shi nan"................



Kar ku manta labarin *AKAN KUDI* k'irk'irarren labarine danayishi domin nishad'antarwa da kuma fad'akarwa, nice taku me nishad'antar daku kullum ako yaushe

@ *sherntee Ghayu* πŸ₯°πŸ₯°


Sak'on godeeya da fatan alkhairi ga jarumata
*Zeinerb Ibrahim momy*



07064706167


πŸ’΅ πŸ’΄ *AKAN KUDI* πŸ’΅ πŸ’΄

(A poor lady story)

......... 22nd April, 2023

πŸ””πŸ“š *JARUMAI WRITER'S ASSOCIATIONS* πŸ“š


*Story & writing*
*By*

@ *sherntee ghayu* πŸ₯°πŸ₯°

πŸ…Ώ......... 003 & 004


................... A razane suka juyo suka kalleta cike da tsoron ko jami'ar tsaroce Nas yace "to ked'in Wacece eye??" cikin halin ko inkula tace "ba damuwar ka bane " Rabiu yace "to shikenan wancan yaron dake tsaye k'ofar makarantar can zaki dauko mana" juyawa tayi ta kalli yaron kafin tace "a nawa?" Rabiu yace "20k" Kai kurum ta d'aga ta juya ta tafi, Nas yajuya Yana fuskantar Rabiu yace "amma gaskiya ba k'aramin wauta kayi ba Haka kurum daga ganin yarinya bakasan ko y'ar Sanda bace ba kawani kama ka yarda da'ita toni Dai babu ruwana ehe" Rabiu yayi murmushi yana dafa kafadar Nas yace "Nas kenan daga ganin wannan kasan ba yar Sanda bace irin y'ammatan nanne da babu Abun da bazasu iya ba AKAN KUDI saboda Haka ka kwantar da hankalin ka kaji" tab'e baki kurum Nas yayi Rabiu yayi murmushi yace "Nas sarki tsoro"


Gefen yaron ta tsaya tare da fiddo snacks chocolate tafara sha kallonta kurum yaron yake, seda ta kusa cinyewa sannan ta kalleshi tace "zaka sha?" Kai ya d'aga Mata yace "Ehm amma Idan dadna ya siyamin" Kai ta d'aga tace "ya sunanka?" seda yad'anyi Jim sannan yace Mata "Abbakar" Kai ta gyada tace "nice name" kafin tacigaba da cewa "kozan zama Auntyn ka?" Abbakar yace "Ehm amma se munyi magana da dadna sannan" tana jinjina ma k'ok'arin mahaifin Abbakar tace "me yasa komai zakayi seka sanar da dad d'inka?" yayi murmushi yace "to ai shikad'ai nikeda Banida mom" ba k'aramin tausayin shi taji ba ji take inama zata iya kyaleshi amma Kash AKAN KUDI Babu abunda bazatayi ba kallonshi tayi tace "eyyah sorry, please ungo nan kaje gaban motar can ka siyamin chocolate kaji" amsa yayi ya juya ya nufi inda ta nunamishi Yana kaiwa Rabiu ya fito ya d'auke shi, Anan suka aje Mata kud'in da gudu suka ja motar suka tafi, xuwa tayi ta d'auki kud'in ta k'arasa gidan su Maryam Nasir.


Sun D'an jima suna fira da Maryam kafin Sarauta tabata labarin duk a bunda ya faru hankali tashe Maryam tace "Nashiga ukuna ni Maryam yanzu Sarauta abunda kika aikata kenan baki tunanin ko kashe yaron nan zasuyi wayyohni yanzu me kika aikata Haka Sarauta baki...." bata k'arasa ba Sarauta ta katse ta da cewa "na shiga uku Haba Maryam miye ne Haka eyeh wani abunne kuma Nayi gaskiya kidena min irin Haka dan kinga Bana iya rufa miki sirrina shysa kike min Haka ko kinsan dae ke kadae kurum Nike sanarma da sirrina ko toki cigaba ki cigaba damin irin Haka Aikin Banza kurum nikinga na tafi gida ga dubu 10 kema kiyi amfani dashi zan sanar da Ummah a gunki na samu sae anjima " ta ajiye kud'in ta wuce, ajiyar zuciya Maryam tayi tace" Babu abunda zanyi dasu amma zan aje miki " " oho" shine kurum abunda Sarauta tace tafice a tsakar gida ta tadda Maman Maryam sukayi sallama ta wuce.



*JIDDA*


Yarima ne zaune shikad'ai a d'aki bazaka tab'a cewa ga halin dayake cikiba saboda shi mutum ne me sauk'in Kai da iya sarrafa fushin shi shysa bazaka iya cewa ga halin dayake cikiba saboda kullum fuskar shi cikin annuri take,

A hankali ta shigo d'akin tana sanye ta alkyabba me kyau a jikinta kusa da d'an nata ta k'araso a hankali ta d'ora hannun ta saman kafad'ar shi, da sauri ya d'ago daraΒ²n idanunshi ya sauke a Kan fuskarta murmushi ta sakar Mai kafin ta zauna gefen shi, dafaffar madarar dake gefen shi tazuba mishi ta mik'o Mai a hankali ya amsa ya soma sha, almost 10mins Yana sha kafin ya Gama, juyawa yayi ya kalleta fuskar shi cike da annuri kamar Koda yaushe yace "shukran ya Ummee" ajiyar zuciya Ummee tayi ta d'ora hannu ta Saman kyaklyawan gashin kanshi, cikin lafiyayyen larabcinta tace "meke damun Yarimana" kallonta yayi kafin yace "Ina cikin damuwa Ummee na" matsowa takuma yi kusa dashi tace "Akan P. A d'in da KHAMEEL yasameki maka ne ko?" Kai ya d'aga Mata yace "Ummee Kindai ga irin abunda ke faruwa ko kullum Abu d'aya baya k'arewa shikuma Abiey Sam baya fahimta ni bansan abunda Nayi musu ba haka" ya k'arshe Yana rik'e hannunta, cike da tausayin d'an nata tace "ka kwantar da hankalin ka SHUREIM d'in Ummee kaji komai zezo k'arshe yanzu yaushe P. A d'in taka zata fara aiki?" Shureim yace "next week zamu had'u a KOREA" Ummee tace "Tohm Allah ya kaimu Kadai kiyaye kaji, Allah yasa hakan shine alkhairi kaji my boo" besan Sanda murmushi ya kwacemai ba Jin ta kirashi da sunan datake kiranshi lokacin yana yaro, yana murmushi yace "Ummee na kenan ta kaina Ina k'aunar ki wae Ina wannan madam surutun ko tayi barci ne" Ummee tace "ah ah tadai bi Abieynku wani taro ne kasanta dason Hidima shysa kullum firar ta itace BIKIN AKHIEY gashi AKHIEY yak'i fiddo Mata" dariya yayi domin antab'o mishi farin cikin shi Wato SHUBAI'A yace "Ummee zanyi aure amma ba yanzu ba sena samo mata daidai da zamanin mutanen nan wacce ko yatsa bazata yarda su d'aga ma mijinta ba" Ummee ta dungure mishi Kai tace "ja'iri kawai to Allah ya zab'a ta gari" da "Ameen" ya amsa kafin ya mik'e domin rakata, a main parlour suka had'u dasu Shubai'a kasantuwar ta gaji yasa ta wuce b'angarenta domin watsa ruwa, kallon Muhammad Shureim Abiey yayi yace "Yarimana yadai " shagwab'e fuska Yarima yayi sosai yace "shine kaje da AMEERAH ni banda ni" ya k'arashe maganar kamar k'aramin yaro, Abiey yayi dariya Har hak'oranshi suka bayyana yace "JARUMA TA kinga d'anki ko shi kullum be girma" murmushi kurum tayi, Shureim ya k'ara shagwab'e face yace "Ummee kin ganshi ko" Ummee tace " kyaleshi shalelen Ummee " Abiey ya matso kusa dasu ya d'ora hannunshi Saman lallausan gashin Kan yarima daya sakko har wiyanshi yayi baya da gashin kanshi Yana k'arema kyakkyawar fuskar d'annashi kyau yace "munyi magana da Khameel inaga ai kasan komai ko my boo" Kai ya d'aga mishi kurum kafin ya d'ago ya kalleshi yace "amma Abieyna meyasa kafi son Khameel a kaina?" Ummee na cire mishi alkyabbar jikinshi yace "bawai nafi sonshi akan ka bane shine yake mutuk'ar k'aunarka kabuda fa ka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment