Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Abunda take sakawa Aranta kafin Azeema tajuya tana share kwallah tabi bayan goggo suka fice tana ma gidan wani kallo mai kama dana karshe.

Suna Fitowa ko ganin Azeema tana kuka baisa gadanga ya tambayi ba"asi ba,suka Shiga mota suka nufi gidan Baba Ade,ko da suka shiga cikin gida Goggo ta koramata jawabi,baba Ade guda ta saki tana korama gadanga Albarka tare da Fatan Nasara bata ta bata wani lokaci ba tashiga ciki ta gyara jikinta ta dauko yan kayanta kala biyu ta rufo dakinta tama matar datasa haya agidan makulli suka fito suka Shiga mota,Dakyar Azeema ta yarda ta shiga gaba sai da goggo tamata ta jan ido kana,Shiko Aliyu kalloma Azeemar bata isheshi ba,don mganar gaskiya haushinta haryanzu bai gama sakinsa ba,sakamakon goggo na motar gadanga bai samu damar shararan gudu kamar yadda ya saba basu iso kaduna ba sai after 3:00pm na Rana,kai tsaye anguwan Rimi ya isa dasu wato gidan kawu bala kenan,wani makeken gida mai kama da aljanar Duniya ga security nan tako"ina agidan yadda kukasan gidan wani gwamna ko mataimaki,motoci kuwa baka iya kirga iyakarsu aharabar gidan,bazata ka taba kallon goggo da gadanga kayi Tunanin suna da dan"uwa mai tarin dukiya da mtsayin irin haka ba,duba da inda ita kanta goggo ke rayuwa ammh ko ajikinta donta Fi son gombe Fiye da shigowarta kaduna,don ko banza tanajin kamshi zaria in ta shigota Shiyasa bata kaunar nesa da gombe don koba komai goggo tace garin Shiya Rufamata asirin lokaci da garin na zaria suka nemi su tona mata.

  Hajiya Umaima Sai dai kawai taga baki daga sama,ai bakinta yaki Rufuwa saboda murna a babban Falon gidan aka saukesu,nan da nan masu aiki suka cika gabansu da kayan ciye ciye dana Shaye shaye,Awaya Ummah takira kawu tana Sanar dashi zuwan goggo,farinciki dayake ciki ne yasa bai dau wani lokaci ba yataho gidan,koda yazo bai tarar da gadanga ba,don na yabar su goggo yashiga barrak saboda major na chan na jiransa.

  Kawu yana Shigo falon sanye da shadda riga da wando harda babban Riga,Bakinsa saboda murna yaki Rufuwa,Hannu ya warema Suwaiba yana Fadin"Taho Taho Suwaiba so nake na tabbatar da ba mafarki nake ba.."Dariya goggo take itada Ummah,Tashi tayi ta isa gareshi ya rumgumeta yana dariyan Farinciki yake fadin",Ashe dai da gaske ne,Suwaiba rabon ki da gidan nan Tun Bikin su madina fa..",Ummah tayi karaf tace,",YAu din ma ta rako surukarta ne da kila bazata zoba sai wani lbri mara dadi ya isheta.."Dariya kawai goggo keyi kan tace"ni bazan ce miki komai ba Umaimah dama kin saba min Sharri,ai yaya yasan komai...",gabadayansu dariya sukayi kafin sukarisa cikin Falon tare,nan ya duka yana gaida baba Ade,Azeema ta gaisheshi ya amsa yana ta saka mata albarka,basu samu zama sai da yaje yayi wanka yaci abinci sukuma aka kaisu masauki sukaci abinci suka huta kana Kawu yanemi ganawar Sirri da Goggo,nan take karantamai Duk Abunda yafaru Ummah na wajen sai da ta rike baki tana fadin"Goggo ita wannan yarinyar? koda yake fa ana tsontson bala"i a nono,don Ramatu ba kanwar lasa bane,ammh goggo inagani  mikama Gadanga Azeema yatafi da ita bariki,Ba masalaha bace,tunda yarinyar bata iya komai ba,kinsa fa bariki baruwan kowa da kowa kuma shi gadanga Namiji ne ba lalle bane yasan Abunda yadace da ita ba,kuma goggo a mikata hakanan babu wani gyaran mata.."Tafada tana yar dariya,girgiza kai kawai Kawu yayi yana fadin"Allah Shiryeki Umaimah sam baki da girma sai najikin ki.."Dariya tayi tana kallonasa tace,"Haba Ranka yadade ina girman yake,haryanzu ina cin lokaci na,banda kowani da agabana saboda haka yanzu zankira madina in fadamata kana na tura direba yakai ita Azeemar chan ko sati daya tayimata insha Allahu nasan kafin lokaci komai zai daidaita.."Jinjina kai goggo tayi tana fadin"Mungode Umaimah hakika kin bada gudummuwa wanda yakamata uwa taba yarta Allah yayi miki sakayyah da gidan Aljannah,ammh zaki kira shu gadangan ki fadamai ko? Ummah tace"Eh zamu mgana dashi,yanzu dai bari na fara kiran Madina,goggo ke kije ki sanar da Baba Ade da Azeema yanzu direba zai karisa da ita.."Tana gama fadar haka ta haura sama tana Faman latsa wayar hannunta,da kallo kawu yabita Yana yar dariya,sam umaimah ba ruwanta ko da ya'yanta haka take,ta dauki kanta tamkar wata yayarsu ba uwaba,ballatana Haisam,wanda tamkar kaninta,saboda shakuwar da yaranta,duk duniya basu iya sharing damuwarsu da kowa sai da ita,saboda macece datasan rayuwa tana da ilimin Addini da na bokon duka gabadaya shiyasata take amfani dashi wajen mu'amalarta tayau da kullum,ajiyar zuciya ya sauke kan yadawo da ganinsa kan talabijin yana kallon Tashar aljazeera,domin itama goggo Tuni ta tashi ta barshi nan zaune.

Ummah tana kiran Madina awaya ta labarta mata komai tace"ga Azeemar nan Direba zai kawota,komai suke bukata kawai tayi mata waya,kuma karta sake ya fadama Captain ga Abunda suka shirya ko yakirata tacemai Taje mata kwana biyu"Cikin jin dadi Madina ta amsa ma Ummah suka rabu akan sai Azeemar tazo,suna gama wayar ta sauko ta shiga dakin da'a ka sauke su Azeema ta tarar da ita tsaye goggo na musu bayani,ganin haka yasa tace"Na shirya..? goggo tace "Eh.."Shiga dakin Ummah tayi ta dauko akwatin Azeema tana fadin"Wannan ne akwatun ta ko? amsa goggo ta bata,hanyar Ficewa tayi kafin ta riko hannu Azeema tana Fadin"Zo muje diyata direba na jiranki awaje.."albarka baba Ade tayi ta sakama Ummah,itako Azeema bata wani damu ba saboda jin ance gidan Anty madina,tana santa tana da kirki gashi tana matukar son yaranta yan biyu mata,Hibba da Hidaya,Yarane masu Shiga rai,in suka zo gidan goggo ta dinga hidima dasu kenan,kusan mai da wawa,nan da nan Azeema ta shiga ranta sosai,har alhere suna mata ita da Anty mardiya.

  Ummah ita tafita da Azeema har haraban gidan indan Direba ke jiranta,bata tare da bata lokaci ba,ta bude gidan baya na motar Venza2k19,tare da kayanta tana fadin"Toh diyata ki natsu kinji,ki kuma maida hankali wajen koyon Duk Abunda madina zata koya miki kinji ko? kai Azeema tagyada tana fadin,"Insha Allahu Ummah.."Rufe mata murfin motan Ummah Tayi tana fadin"Allah yayi miki albarka Sai munyi waya kenan ko? kai Azeema ta gyada mata kan Direba yaja mota su danna hon megadi ya wangale get suka Fice da gudu,Azeema tabi gidan da kallo tana jinjina kyau da tsari irin na gidan kawu bala.

  Bisa hanya haka Azeema ta saki baki da hanci tana karema Kaduna kallo,ashe haka take kyau da tsari,gidaje kerarru sai wanda yagani,Nan da nan Abun ya Shiga burgeta ko"ina suka wuce sai wasu classic mata take gani kowacce na harkan gabanta,wasu su suke tuka kansu cike da ilimi da wayewa,wasu kuma Direba ke tukasu suma din cike da wayewa,lokaci daya Azeema tagane Kaduna ba na zaman irinsu bane,don in baka da wayewa tuni za"ayi baka,nam da nan ta kudirta aranta zata cire komai takoyo duk Abunda aka koyamata domin nan Duniya bata wanda yafiyemata Yaya captain da goggo da Ahalinta,babanta kadai gareta,shikuma baida wani iko akanta inna Ramatu kuma bata da wacce ta tsana sama da ita,ga yar"uwanta kwaya daya datake kallo taji Sanyi Azeeza da bakinta ta Furta bata da wata makiyiya kamarta,Tundaga lokacin ta farka daga Nanannauyan barcin daya kwasheta Ta fahimci mutanen datake kokarin yima butulci sune nata ba wasu ba.

  Gidan Madina yana anguwar Sarki ne,mijinta Controller ne,yana lagos yana aiki,Suna zuwa mamaken get din gidan suka zuba hon maigadi ya budemusu,suka rankaya cikin gidan,Madina na haraban gidan da kanta tazo taran Azeema,tunda ummah ta sake kiranta ta Fadamata Azeemar na bisa hanya,tana sanye da wani leshi mai Ruwan hot,ta karya daurin Zahra buhari,fuskarta dauke da simple makeup kallo daya zakamata kasan yes ta amsa sunanta na mace,domin madina macece mai wayewa da sanin duniya,shiyasa Mijinta Ahmed kallo Sauran mata yake matsayin basu san komai ba

  Da hanzari ta karisa ta budema Azeemar murfin motan Tana fadin"Maraba da Antyn Hibba da hidaya,yau in suka dawo mkranta zasuyi ihun murna in suka ganki.."Take fada tana mata dariya,Fitowa daga motan Azeema tayi,tana kokarin dukawa tagaisheta,tayi Saurin rikota tana fadin"Sannu da zuwa Azeema,kona ce matar yaya ko? Sunne kai Azeema tayi tana mirmishi Rikota tayi tana kwalama yar aikinta kira,tana fadamata tazo ta dauko akwatin Azeema,takai mata dakin dake kallon nasu hidaya.

   Suna Shiga babban Falon gidan sai Azeema tazama yar kauye balle da kafarta ta nutse cikin lallausan Chinese capet din dake malale afalon,Haka ta saki baki tana bin Falon da kallo,kan daya daga cikin Royal chairs din dake falon ta zaunar da ita,da kanta ta kawomata Ruwa da drinks,tasha kafin ta rakata dakin da"aka kai akwatinta,shima dakine nagani na Fada,gado da wardrope sai madubi da tiolet,shikanshi gyare tsaf,Madina ta Shiga toilet ta hadama Azeema Ruwan wanka ta fito tana fadin"Matar yaya,shiga Tiolet ki watsa Ruwa,kizo kici abinci ki kwanta ki warware gajiya kafin anjuma mu fara Aikin namu ko?"Mirmishi Azeema tayi kafin tace"Ngd Anty madina..."Itama mirmishin tamaida mata tana fadin"Ah bakomai,yayana fa zan gyaramawa,to meye namin godiya hop dai u are ready..? kunya takama Azeema sai ta Rufe fuska Ficewa madina tayi tana fadin"Wai kunyata kikeji,dankari,toh kinga kima daina Tun Wuri,don kunni zaki bude ki kwashi lacra yarinya.."Ta fice tare ds jawo mata kofa,Hijabinta ta cire tana bin dakin da kallo,kafin ta fada tiolet din,chan ma bakauya ta zama ashe bayin gidan goggo bakomai bane,akan wannam,dakyar dai Azeema tayi,wanka,ammh kusan Rabin wanka duk takareshine wajen kallon kanta amadubi,kafin ta fito,tana Fitowa daga Anty madina adakin tana Bude mata wani lotion tana ganinta tace"Yauwa kinfito,ga mai kishafa,bari na dauko miki wasu kayan ki chanza,ki Fara daukan karatunmu Tun yanzu kowani wanka to danashi sabon salon Dreesing din,kinji ko?gyada kai Azeema tayi kafin ta karisa Fitowa,jikinta dauke da kayan jikinta data Shiga dasu,Akwatinta dora bisa gado ta bude ta zazzage kayan ciki,tsaki taja tana daga kayan tace"Gaskiya muna bukatar kudi,domin chanjin kayanki,Lalle ne su goggo nan toh da Nufinsu da wannan kayan da zaki gidan miji,bari na kira Ummah yanzu sakawanan kila anjuma mu fita kasuwa ki zabi kayansawa,daganan mu biya ki wanke kanki ko? gyada mata kai Azeema tayi tana ansam doguwar rigar abayar da Anty madina ke mikamata,ficewa tayi da hanzari Dakinta takoma ta dauki waya ta kira Ummah.

Ummah na tare da kawu bala,kiran Madina ya Shigo mata cike da zumudi ta dauka tana Fadin"Makka da madina ya akayi ne? Tura baki Madina tayi kafin tace"Toh ku Ummah kuna nufin haka zaku kai diyar taku babu kayan kirki,yanzu na bude akwatinta wlh babu kayan kwalliya na mata ko kadan.."Ummah tace"Topha to yanzu yaza'ayi Hajiya madina.."Madina tace"Kudi muke bukata Ummah,da zan Shiga kasuwa nayi mata siyayyah,sai sauran kayan gyaran da zan Hada mata,da wanda zatayi amfani dashi anan harda wanda zata tafi dashi"Ummah ta jinjina kai tace"Ok tom ba damuwa bari nayi miki Transfer din 2 hundred Thousand yanzu ai zasu isa ko? Madina tace"In ma basu isa ba,Ummah zan yi ciko,ai Matar yaya ne,so antytin for him aie.."Tafada tana dariya,kashe wayar Ummah tayi tana fadin'"Allah ya Shiryeki Madina.."Kawu na gefe yace"Harda uwar Madinar itama Allah ya Shiryata.."Dariya Ummah ta kece dashi batayi mgana ba.

  Kawu yace"Naji ana mganar kudi ne,babu bukatar taimako na.."girgiza kai Ummah tayi tana Fadin"Babu bukatar Taimakon yallabai anan,kai kagama naka,Tunda ka biya sadaki kuma ka karbo Auren,barmu da Sauran mu makarisa Abunmu.."Gyada kai yayi yana fadin'Hakane.."Tace"Eh mana.."Maida kansa yayi kan kujera yayi yana fadin"Allah bada sa"a ammh a sassautama Dana don Allah.."Wani kallo Ummah tayi kafin tace"Toh yallabai..."Tafada tana dariya Shima yar dariya yakeyi,nan take tama Madina Tranafer din kudin datace,kawu bai damu ba domin yasan halin Umaima indai tana dashi toh babu Abunda bazata iyayimai ba,balle ma ita Aliyu tamkar uwa da Danta ne.

  Shiko Aliyu tunda ya Shiga bariki abubuwa suka mai yawa,sai zuwa darene,ya samu kiran Ummah tana Shaidamai Azeema tana wajen Madina zatayi sati awajenta kafin Su kawota nan Barrak din,Ummah ta fake ne da cewa akwai wani dan gyare gyare da sukeyene,bai damu ba yace Bakomai,dayake Aliyu Namiji ne,kuma Soja,so kwakwalwarsa bata kawomai wani gyara akema Azeema ba,yafi bada kila lalle za"ayi mata da kitso,kowani Abu dabam😂Shiyasa bai damu ba,bai samu komawa gidan kawu ba yabari sai dai da safe,in jabir ya dawo suzo tare dashi Tunda shi bai samu dawowa Aranar ba sai washegari.

Suko Su Azeema basu tafi kasuwa Aranar ba saboda yammah tayi,gashi su hibba sun dawo daga sch nan fa suna cin karo da Azeema sukayita ihun murna kamar su maidata ciki sun hanata sakat,itako tana biye musu Ranar ko Maminsu basu bi ta kanta ba,hatta cire musu uniform da saka musu kaya na Azeema sukace suna so tayi musu,wanu homework ne,harda yar goye goye duk ita kadai,dayake kuma ta saba da yaran,kuma kunsan Aduniya babu aikin da zai gagari Azeema sai dai in ba"a kirkiroshi ba,Karshenta dai Ranar dakinta suka tattara sukace wlh chan zasu kwana har jan madina tayi musu suka makale su Tare Anty Azeema zasu kwana,Azeemar ta roki,Anty madinar kafin ta kyalesu su kwana,aiko sun kai wajen 11 suna hira,kafin su kwanta,ta Shege tsakiyarsu kaunarsu na Ratsata tana fatan kada Allah ya Dau Ranta sai ta haifi mace ta sakamata Suna FATEEMA..,Niko nace karki damu Azeema very soon Aliyu zai baki kwan haihuwa🙈🙈

  Sai washegari suka samu Tafiya,bayan yaran Sun tafi mkranta,kasuwa suka Shiga Madina ta darzomata Atamfofi Masu Rai da lafiya super,holland,swices less,codde less,material dogayen Rigana,masu sikat da masu wando,Mini sikat da mini wandunan,bras,pants,kayan kwalliya komai da komai da kayan mata sai da ta siyamata harda takalma masu Tsini da Flat,sai kananun jaka,dan kunne,masu sarka da Fashion Bands,da sauransu kafin su wuce shagon dinkinta,tabada dinkunan kayan,wata in yamurace bosse,ta gwada Azeemar tace jibi ta aiko direba ya karbi dinkunar,bayan madinar ta ijiyemata kudinta cash,suna Fitowa dagana shagon salon takaita aka wankemata kai harda gyaran kafa sukayimata,wajen harda gyaran jiki sunayi,ammh sanin itama madinar sana"arta kenan basu mata tayi ba,domin sun santa tun Tuna budurwa suke gyaramata kai,ta yarda da shagon sun san aikinsu sosai,basu dau lokaci ba,suka kammallamata sai ga gashin Azeema ya mike sosai yayi kyau kamar ba ita,ba kudinsu tayi musu Transfer ta banki suka Fito suka wuce,daganan anguwan Rimi suka biya gidan wata kawarta SALAMATU FODIO SG GUMBI..Ta amshi wasu tsimi ahannunta tare da Wasu garin magani cikin wasu robobi,dayake sana"arta kenan itama,basu wani jima ba,daganan suka koma gida,suna komawa gida,madina ta shiga tiolet ta hadamata Ruwan Turaruka masu tsada hadin yan maiduguri ne,ta umarceta data Shiga tayi wanka,ita kuma ta sanya wani kasko ta kunna Hurashi ta watsa Turare,tana Fitowa da digon Ruwan ta Umarceta data tsugguna hayakin Turaren ya dinga shiganta,ba gaddama Azeema tayi yarda Madina tace,sai da ya sike kana tace tatashi,wani hadin mai shima cike yake da wasu hadin Turaruka tabata tace daga yau yazama man shafawanta,karba tayi ta shafa,kayan da suka siyo ta zazzage pants dinta ciro mata kafin ta miko mata wata kwalba tana fadin"Rike wannan almiski ne,zaki dinga digama wandunan ki kafin ki sanya kinji ko? amsa Azeema tayi tana fadin"Naji Anty.."wani riga da Sikat Madina ta mikamata tana fadin"Karbi ki sanyasu,wadandan Dressing din,duk bayan kin daidaici lokacin dawowar yaya captain ya kusa zakiyisu,ammh bayan kin tabbatar da Dinner dinshi is ready kinji ko.."kai Azeema ta gyada tana Fadin"Naji Anty.."kada kai tayi tana fadin"Shirya bari baje na hada miki Sauran magungunar ga Turaran wankan chan a tiolet sau biyar akowanni Rana,Kowani wanka Murfin jarka Uku zaki sanya,na sati daya ne,bari na kawo miki Sauran na garin akwai na karin Ni"ima kana kuma akwai na mganin infection ma"ana Sanyi..."Gyada mata kai Azeema tayi alamun ta Gane ficewa tayi tana fadin"In mun gama da wadanan kingane sai mu dora da lacran mu,munayi lokaci daya kuma muna Shiga kichen tare,domin kinsan Duk wadananan Abubuwan basu tasiri,sai Mace ta kasance ta iya sarrafa mai gida ta hanyar iya girki,balle nasan Sojiji da son cin Abinci mai dadi.."Tana fada tana yar dariya kan Ta fice daga daki.

Yar Dariya Azeema tayi tana bin Tulin kayan da suka siyo wadanda ke zube bisa gado,kayan da Anty tace ta saka take bi da kallo,Tana mamakin yadda zata sakasu,sai da bazata iya bama Anty madina kunya ba,da hanzari ta sakasu,kayan roba ne sai suka lafe bisa jikinta gashi sun kamamata,hips dinta ya fito tana tafiya suna rawa,duk da ta saka pant,sai kirjinta wadanda suka cika fam,suna bin bayyana,gashinta ta daure da band,kayan baida dan kwalli,Sai ta samu wata hula ta saka ta isa gaban mirrior tana kallonta sai da tayi mamakin ganin yadda kwana daya tadawo gawani Fitinannen kamshi na binta da ko"ina,duk inda ta Shinshina ajikinta sai taji kamshi,ita ta kanta take lumshe ido in ta Shaki kamshin jikinta,shafa fuskarta tayi taji wani Santsi Mirmishi ya subuce mata lokaci daya hawaye sun ciko idanunta ta furta ahankali

  _Thank you,Yaya captain,Thank you goggo,Thank you Ummah and Thank you too Anty madina.._ take fada tana goge kwallar data zuraromata bisa kumcinta    

  Madina dake bayanta ta bugamata tafi tana fadin"Weldon matar Yaya da alamun zaki Saurin dauke komai kafin sati dayanmu ta cika,.."Tafada bayanta yar aikinta ne,ke ta Shigo dawasu jarkunan magunguna dawasu arobobi sai madara Sajet sajet,sai Zuma awata katuwar gora sai gumba mai yawa,gabanta tasaka aka zube haka ta zauna ta tankwashe kafa itama Azeemar ta sauko daya bayan daya take maata jawabi,da wanda zata sha da madara,dana sha da zuma,komai dai tayi mata jawabi,harta Fahimta,nan kuma ta ake ta shiga hadamata ta mikamata tana Sha,duk da wasu suna da bauri,ammh hakanan take Daurewa Tunda ba laifi takan danci karo da mai dadi har dawani hadin Dabinon makka mai dan karen dadi,Azeema taji dadinsa sosai,shida wani garin Aya shima da madara ake sha Duk sun mata dadi sosai,Tana gama sha madina ta kwashe ta sanyasu gefen gado tana fadamata Sau daya zata dinga sha Arana,ammh Turaren Tsugguno sau biyu arana safe da yammah Ficewa tayi ta barta tana fadamata cewa gobe zasu Fara lacra su,da safe Allah barshi da yammah sai sudinga Shiga kichen domin koyar da ita girke girken zamani wato Akushi da Rufi😂Tuni Azeema ta amsa da toh domin Ta fahimci Rayuwarta ta yanzu tafikomai dadi,koba komai itama tanaso ta waye tazama irin Anty madina da kawayenta,zaka gansu so classisc mallam babu Raini ko kadan.

            

*Intellenget writers asso..*
*Janafty..Aka Shakira*💇
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

_*Kyakyawan Shafi lokaci Daya da kyakyawan sadaukarwa,eh mana domin Duka Shafin yau na ALIYU GADANGA.,Kacokan Dinsa sadaukarwane ga Daukacin malamai da Shugabannin dake mkrantar primary U.B.E. KOFAR KIBO ZARIA..,Gaisuwan Fatan alherin zuwa gareki ne mai gayyah mai aiki,headmistrees HAJIYA BINTA UMAR ABUBAKAR(Momy)Allah yaja kwana👍😂,Tare da uwar gayyah Assitances,HALIMA IDRIS(Goggo balaraba)😹 Allah dai ya biya,bazan yi toya na manta da albasa ba,jinjinar ban girma zuwa gareka lantarkin zuciyata,kuma malami na,kuma uba yake awajena,lalle na kasance mai sa"a Tunda Allah yahadani da gwarzo kamar ka,UMAR BELLO SADIQ(Uncle me)😘,Soyayyarka gareni sai dai nace A kinda masha Allah,Kulawarka akaina sai da na kirashi da Alhamdulillah Allah nake roko daya iya maka Abunda kagaza,Kafin na wuce zuwa wani ajin yakamata nafara Farawa da gida ne,gaisuwa tare da Fatan alheri gareku MALAMA RUKAYYAH(Maman Suhailat)sai MALAMA AISHA(mmn Fuad)sai MALLAM ABUBAKAR(mallam Ammar),Bazan manta daku ba dole ne nayi jinjinar ban girma gareku iyayan dakina,ANTY HADIZA,tare dake MALAMA AISHA,Bazan manta dake ba kawata abokiyar Cin mushe,😂😛,kuma malamata ba wato ANTY JUWAIRRIYAH,Son so Fisabillillah,kai zan yi Abun kunya ban ambaci uwata ba takaina ba MALAMA ZAINAB(Anty Ummi)tare dake Malama Hafsart,malama jamila,(Namecy),sai malama Harira,Anty hauwa,Malama Asiya dake da malama Hafsart,ban manta dakai ba Mallam Aminu tare da wadanda ban ambataba,gaisuwan Ban girma gareku Allah yabar zaman Tare Ameen..Ku sani ku kara sani JANAFTY AKA SHAKIRA,na Sonku Fisabilillah*_😘😍❤💕💖💞💘🔐






      *Chapter 18*

    """Koda garin Allah ya waye,Kafin Anty madina tagama Shirya yara zuwa mkranta Tuni Azeema hartayi wanka,takumayi Turaren Tsugunnonta,takuma sha mganungunanta wanda Anty madina ta nunnuna mata,koda Anty madina ta Shigo Azeema ta cakare,cikin Wata Atamfa mai blue da ja,cikin wanda goggo ta dinkamatane,simple make up ne Afuskarta,ta taje gashinta tayi baya dashi ta saka band ta daure,tsaye take gaban madubi tana cikiniyar Daura dan kwallin Anty madina ta Shigo kallonta tayi tana rike baki kafin tace

  "Matar yaya,Allah kinyi kyau kinganki kuwa chanchadi.."Tafada tana dariya Rufe Fuska Azeema tayi kafin tace"Ina kwana Anty madina.."Ta amsa da lafiya kalau matar yaya,yakika tashi..? tafada tana karisawa kusa da ita ta karbi dankwalin tana fadin"Laccan Mu ta farko zata Fara daga Dauran dankwaline,Tunda Shi na tarar kinayi.."Gyada kai Azeema tayi tana kallon yadda ta dankwasa dankwalinta,Kafin ta Dauramata bisa kai,Daurin Maryam babangida tana yi tana mata bayanin yadda zatayi bayan tagama sai tace ta kwance ta daura da kanta,nan da nan kuwa ta aza abinta yayi kyau sosai Tafi Anty madina tayi mata tana fadin!Good matar yaya da alamun, dai zaki Saurin dauke komai,yanzu taho muje mufara dora karatunmu lokaci na kurewa.."Tafada tana jan hannunta zuwa kan gadon,tsakiyar gadon madina ta hau tana fadin"Hayo nan matar yaya..!Hayowa Azeema tayi suka zauna Suna Fuskantar juna bayan Dukkansu sun tankwashe kafafunsu Riko hannunta Madina tayi kafin tafara da cewa.

  ""Abu na farko kafin mufara dora karatunmu yakamata kifara sanin menene Aure,Aure dai wani Nau"i ne na bauta,gabadayanshi bauta ne na ubangiji,kuma duk Abunda akace Bautane na ubangiji toh sai fa mutum ya dage kuma ya zage damtse,Abubuwa guda biyu da suka kasance ginshikin bauta ma Aure sune LADABI DA BIYAYYAH..Matukar kinaso,kiyi bautar Aure,sai kin kasance,kina da ladabi da biyayyag,kibi mijinki Sau da kafa,yi nayi bari na bari,kiyi amfani da Umarninsa kiyi hani da Abunda yahanki,karki tsallake Umarninsa ko alama,ki kuma bisa don yana gaba dake,tsakaninki dashi tamkar tazaran kasa da Sama ne,Aljannarki,tana karkashin digadigin sane,sai yalamuncemiki zaki Shiga Aljannah,Abubuwa masu muhimmancin dayakamata kisani bayan Ladabi da biyayyah wanda suka kasance ginshikin,ki kasance mai HAKURI.. Hakuri wani babban Tsani ne,Azeema matukar babu hakuri Da juna Da Auren mutane dadama ya mutu acikin Duniyan nan,domin ko harshe da hakori,suna sabawa balle zaman mutum da mutum,Namiji yana son agirmamasa sosai balle ke mijinki yana da son abashi girma bayason Raini ko kadan,kuma yana da isa da takama,toh dole sai kin zama mai hakuri domin zaki dinga ganin yana yi miki komai cikin isa,duk da ya isan ne,domin Shi Shugabane gareki,ki ka sance mai kauda kai,banda yawan korafi kigani kikigani kiji kuma kikiji,Toh in kikayi haka Aurenki zai zauna lafiya kuma zaku Fahimci juna Sosai,abu nagaba danikeson fadamiki,Shine Kisance mace Tagari wacce take maida damuwar mijinta nata,Farincikinshi shima naki ne,ki kasance kina kokarin rike Sirrrinki dana mijinki,domin bayyanar da Sirrinki ga kowa,koda ga goggo ne,ko kakarki ke ko ni kaina,in bawani abu bane wanda yazama dole sai iyaye sun Shiga ba,Shima din ki bari sai dai in Shi yafara furtawa,yin hakan ba karamin karama mace daraja yakeyi ba,kinga duk sanda Namijin yasan baki da Sirri shikenan ya ranmiki Daga ranar zai Fara kokarin Rike Sirrinshi bazai taba bari ki sani ba,Ki sance mai yawan Fara"a ga mijinki Azeema,karki bari ko alama ya zauna cikin Damuwa kiyi amfani da baiwarki ta diya mace ki hillaceshi har ya manta damuwarshi,ki sance mai ba mijinki shawara,ta wajen aiki ne,na game da yan"uwanshi ne,ke nakomai ma,ki zama mace jaruma wacce zata dinga karafafama mijinta gwiwa aharkan komai,kinga in kika cika wadan nan sharudan kin gama cika Sharudan zama MACE TAGARI.."Fatan kina Saurarena da kunnen basira.

  Jikin Azeema daya gama yin sanyi tagyada kai tana fadin"Eh ina Sauraranki Anty madina.."gyara zama madina tayi kafin tace"good to kinga duk wannan karatun danayi miki toh matukar baki cika Wadandan Fa"idojin da zan gayamiki ba,toh duk abanza ne,domin kamar kayi wanka ne kayi kwalliyah ka koma kayi ma kanka wanka da Kasa ne,"Kallonta Azeema tayi tana Sauraren mai zata cemata Madina ta cigaba da Fadin"Fa"idojin Sune, *KWALLIYAH,GIRKI,IYA SALON MGANA,SALON KWANCIYA.*Kinga duk wanda kika saki acikin hudun nan Toh ina mai tabbatar miki kin samu nakasu"Zaro ido Azeema tayi madina tace"Yes..Matukar baki iya girki toh yakamata ki daina amsa sunanki na mace,ko baki iya kwalliyah ba,da yadda zaki dau dressing din da zaki dau hankalin megida ba,kema Sunanki Sauna,kana matukar baki iya Salon mgana ba,da yadda zaki Rikita mai gida da salon mgana na jan hankali ba,kema Sunanki sakara,uwa uba baki iya salon kwanciya balle sanin yadda zaki sarrafa maigida ta hanyar rikitashi da salolin kwanciya toh wannan Sunanki Dussa,duk matakan baya,kin gama zubar dasu,don sai wadannan sunyi kyau hasken wadanchan ke bayyana"

  gyada kai Azeema tayi kafin tace"Toh Anty kimin bayaninsu daya bayan zan Fi ganewa.."Anty madina tace "Yanzu kuwa matar yaya.bari

Please Login or Register in order to submit comment