Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gudu kowa ya dungule hannu na cin ubanshi yaje ya makale bayan kawu Bala yana Fadin",Kawu ga gansu ko,daga ina musu nasihan hakuri da Kawaici ,saboda dai wanda ya riga ka kwana dole ya rigaka tashi ko mami? yafada yana kallon Mamin Jabir tana Dariya ta amswa da cewa",Hakane Aliyu,babu kuma wanda yakamata yagayamuku gaskiya bayan Shi,yarigaku auren nan,sannan kuma yaya yake agareku Tunda kuna auren kannensa"Suna jin haka sai kawai suka juya suna hararansa,gwalo yake musu yana yar dariya,shi wlh dariya suke bashi in ya kallesu kowani shege ajirace yake da mace🤔Azeema ce tazo ta murdemai kunne ta baya yayi yar kara yana kallonta kafin yace"Pretty mugunta ko? zaki cirema Baban Triplet kunne ko? matse mai gefen ciki tayi tana Fadin"Kabarsu Jabir hakanan don Allah,tunda kai lokacinka babu wanda Yasa maka ido.."Hannuwansa yahada yana Fadin"toh angama Ranki shidade maman yan"uku"Dariya kawai tayimai ta wuce shiko yabita da kallon sha"awa azahirin batu anfara kureshi fa haba,hanya fa ba kyau,tsakani ga Allah yakamata pretty tazo taji dashi Tunkan yafita daga hayyacinsa.


Basu dawo gida ba,sai da sukaga tashin jirginsu,kana suka koma gida cike da kewa,Shashen Azeema ya rage daga Baba Ade sai Gimbiya Razeenah sai Inna Ramatu,hakama Shima Aliyu yaji shuru saboda harda Umar aka tafi zasu koma Asallamesu kafin su biyo jirgin sojojinsu su dawo kasarsu.



**************

Koda suka sauka A Nageria,direct Su goggo kano suka wuce da Safaratu,Awata anguwa mai Suna Tarauni,gidane babban kirarre,sai wanda yagani komai na alatun Rayuwa akwaoshi acikin gidan,babu Abunda zasu nema su rashashi,nan suka kwana sai washegari suka bar kano zuwa kaduna dukkansu,ammh shi kawu tun jiya yakoma kaduna abunshi,da zasu taho sai da goggo ta damkama haisam cheque dinsa na milayan uku,wanda maimartaba yabashi kyauta,tare da albishir din kujeran makka,shida Safaratu,Ummah harda guda da rawa,tana ta godiya balle su madina da sukayi ma Haisam chaa,wai yakowo su ijiyemai kudin,banza dasu yayi,shifa duk ya kosa su watse don wlh arike yake fa😂Karfe 2, da wani abu na Rana suka bar kofar gidan Haisam,suka bar shi daga shi Sai Safaratu sai halinsu sai dai Fatan Allah ya basu zaman lafiya.


Hudu da wani Abu na yammah suka Shiga kaduna direct to barikin Su jabir suka yada zango,shima din dai apartment din na jabir kamar na Aliyu komai ya mallaka,gyare gyare kawai sukayimata da Sauran abubuwa,basu kwana ba,tunda kaduna gidane,dama tuni iyayan jabir suka bi kawu bala,tun jiya suka dawo kaduna abunsu,shima irin kyautar da maimartaba yama Haisam irinta akama Jabir,tare da kujeran makka Shida zafira,Murna kam ba'a mgana basu wani jima sukayimata Abunda yakamata suka barta daga ita sai Halinta kowanne yakoma gidansa,gimbiya Fasilatu da Goggo da ummah mai babban Daki gidan Kawu bala suka sauke gajiyansu sai sungama hutawa ko zasuyi Shirin komawa Niger,saboda atsakanin nan sun yawatu aduniya ba laifi.

Kowani ango awannan daren ya maida amayarsa cikakkiyar mace,Abun ba ragowa ko kadan da alamu dai sunji maza,Ammh dukkansu sun tsinci kansu cikin wani nishadi mara misalatuwa jabir ne yace aransa"Dama Tuni irin wannan Dadin gayen chan ke kwasa,lalle dole yacemana yara,ammh wlh danasan haka aure keda dadi da Rahama da wlh Tun da na balaga zanyi aure,domin na mori Abun da kyau😂kuji fa jabir daga Shiga sau daya yafara sambatu,shidai Umar Tuni ya wuce sansaninsu,ammh shima kasan Ransa yana Cewa ne daya koma kasarsa zai nemi mata yayi aure,shima ai ba Dutse bane.


Sati daya cur su goggo sukayi suna hutawa kafin sukoma kasar Niger,koda suka koma Tuni yan uku sun kara girma da yau kamar ba yan wata daya ba,Fati itace suke cema Afra,sai suwaiba suna kiranta Afiya,sai Namijin suna kirana Anwar,Azeema kuma na cigaba da samun kulawa sosai gimbiya Razeenah na kokarin saka ido akanta kada tayi danyen jego,shiko Aliyu yayi nacin da bin,ko zai samu ya samu Ritsa Azeema ita kadai babu dama,ko gaishesu yazo yi da safe,su Inna Ramatu na wajen da Baba Ade,kuma Abunda ke bashu haushi suki tashi daga wajen,Abun na bakantamai rai Shiyasa kwana biyu yayi musu yaji,da Azeema taga haka sai dauki waya ta kirashi yana dauka ya balbaleta da masifan ta rabu dashi yaji da Abunda ke damunshi kawai ya yanke kiran,itakuma sai ta zuciya kan mene zai mata tsawa haka alhalin yana sane ba laifinta bane,kuma tayaya zata bashi kanta alhalin jiya jiya ne tayi tsarki,kuma ko samun damar zuwa Shashensa bata dashi saboda Baba Ade bata barinta Fita ko'ina suna tare da ita toh ya zatayi,toh dalilin yasa kowa ya Share kowa kenan harsu goggo suka dawo ana gaba,duk da sai su shafe kwana uku basu hadu da juna ba,don ko Su Afiya sai dai ya aiko jakadiya ta daukan mishi su,ko shashen Azeeman bai kallah saboda takara batamai rai saboda ta rainashi ko zuwa ma tabashi hakuri batayi ba,kuma ya sake kiran wayarta tanagani taki dauka,kwafa yayi aransa yana ayyana yadda zaiyi mganinta.


Su goggo basu Rufe sati da dawowa ba Aliyu yace shifa ya shirya zai koma bakin aiki,Abun yaba kowa mamaki,bama kamar goggo,wacce sukayi mgana yace sai Azeema tagama wankan yara sunyi kwari zasu koma tare da ita,da goggo ta tunamai sai ya bata rai yace ya chanza ra"ayi ne intagama wankan tazo daga baya ganin yadda ya mtsane yasa maimartaba ya amince aka neman masa Visa,Shida mallam lawal wanda maimartaba yayi yayi dashi yadawo masarauta su zauna tare yaki,yace abarshi a inda yake saboda yafi sabawa da chan,kuma ko ahaka babu Abunda zaice sai godiya ga Allah,ta sanadin Suwaiba da Azeema bazai kirga alheran daya samu ba,gashi ayau saboda ita zai je kasa mai tsarki lalle Allah ne Abun godiya.


Daga Aliyu sai Mallam lawal suka bi jirgi suka koma,domin goggo tace Inna Ramatu ta zauna,in za'a maida Azeema sai ataho tare da ita,Abun bakinciki Azeema batama san Tafiyar Aliyu ba sai washegarin daya tafi taji suna waya da goggo,lokacin tana bawa Anwar nono wlh dawani bakin ciki ya Turniketa batasan sadda ta ture anwar ba tatashi da gudu ta shige daki tana kuka ba,Baba Ade dake wajen tayi Saurin daukansa tana lallashinshi,tunda fizgoshi daga Nono tayi,Abun yama Azeema ciwo,itako mai tayima yaya captain da zafi haka har zaiyi iya komawa batare data sani ba,wato yanzu bata da wani amfani awajenshi Tunda tana jego,tagama wahalan cikin ya"yansa yanzu ta haifemai toh bata ita yake ba wata zuciya tace wama yasani ko saboda shegiyar Ni"imar nan yakoma,Tuna haka sai da tayi kwallah,bata son haka take kishin mijinta ba,sai Ranar haka ta wuni kuka bata kuma ci abinci ba, yara ko nata kuka ammh kota kansu batabi ba goggo ko ko kanzil batacemata ba domin ta fahimci Fushin na gadangantane dama Tunda taga Tafiya ba Shiri,kuma tun sadda suka dawo bata ganin yana shigowa shashen Azeeman tasan akwai wani Abun,sanin datayi daga Azeemar har gadanga yan buhu da rabi ne bamai gayamata Abunda yafaru Shiyasa takawo ido ta sanya musu kawai,chan ta matse musu shirtartu kawai,yara kuwa Ita ta daukesu ta tafi dasu zuwa Turakar maimartaba tana basu Ruwan zamzam da Dabinon makka,nan da nan ko sukayi Shuru da maimartaba ya tambayi Ina mamansu take tabe baki goggo tayi tana fadin"Yau Fushin d'ankane ya Shafesu ko kallonsu batayi ba Tun safe tana daki tana koken koken banza.."Mirmishinsu na manya Maimartaba yayi yana Fadin"Toh toh kice Abun na manya ne,toh Allah daidatasu,kinga ni yanzu kitashi ki maidama Baba Ade yaran nan,tunda nidai bama Fada ba,kuma bakya Fushi da mijinki,kiyi maza ki kaisu kidawo kiji wata mgana.."Dariya tayi mai tana wani kallonsa kasa kasa tana Fadin"Kai Yallabaina baka tsufa.."Farin gemunsa yashafa yana Fadin',Kinji ki da wata mgana ina Tsufan yake Suwaiba,ai a soyayyarki ban mori komai ba yanzu ne ma nakecin lokacina,kedai yi maza ki dawo ki amsa kiran miji kada ki shiga Fushin mala'iku.."yafada harda kashe mata ido,sauri ta kwasa tana dariya tace "Yanzu kuwa Yallabaina'Tafice Shiko yana binta da kallon kauna.


______________________


Aliyu yana komawa bariki tacika da murna da Farinciki hatta Dinner dare sai da aka hada aka ci aka sha,akayi Rawan Sojoji sunayi suna wakensu,dayake Jabir shida zafira suka daukosa daga filin jirgi,washe gari kuwa har nan barikin Chief Amry of Staff yazo,suka gana da Aliyu akuma nan take ya samu karin girma daga Captain zuwa *MAJOR ALIYU ABDULNASEER TAMBARI BUZU* Yayinda Jabir yatashi daga Captain zuwa *CONOLE JABIR*,dukkan sojojij da suka je wannan kwantar da tarzoman sun samu karin girma,Ranar barikin tarude da murna,kwana sukayi kide kide da wake wake,haka suka taru waje daya suna rawa da waka suna Fadin _Lalle mune soja,dama kunun salala gidan wuya aikin soja dama kunun salala..._Abun sai wanda yagani,Ranar hatta su kawo sunzo ciikin barikin sun tayashi murna,harda su Anty madina dasu Anty mardiya sai Zafira da jabir,wanda wani shagalin sai wani satin A abuja inda anan ne za"a sanyama kowa rank dinshi.


Haka ko akayi A babban headquater su dake Abuja aka sanyama kowa Rank dinshi,wanda kowani gidan talabejin da gidajen radiyoyi,suke yada wannan Abun dake Faruwa life,Cikin masu kallo harda Ni"ima wacce murna ta cikata sosai,nan take ta dauki waya taturama Gadanga sakon taya murna da Fatan alheri,sukuma su maimartaba Atashar CNN suka gani har lokacin da'ake sanyama Aliyu Rank dinshi na zama major,Murna ba"a mgana domin Shima maimartaba biki na musassam ya shirya,sai alokacin Azeema take jin lbrin Tun komawarsa aka karamai girman yanzu taron tabbatarwa ne,Abun yayi mata tsaye arai wato itace mara amfani ko,domin hatta Safaratu da haisam tagani,taga kowa da kowa,ammh ita saboda bata da wani amfani ko bazata jeba agayamata ma ai wani abune,shiyasa bata karisa kallo ba tabar wajen tana dauke hawayen daya zubomata,Anan wajen aka sanar da anyi Transfer din Major Aliyu daga 1 Division Nageria Amry kaduna zuwa Barikinsu na Abuja mai suna *ABACHA BARRAK*...Sai dai kuma yan kaduna sunyi rashi gashi an saba,ammh babu yarda zasuyi Tunda cigabane kamar ma jabir yaji lbri,kuma anan wajen aka karramma Sojojin cameron,da chadi da Niger,bayan Maigirma shugaban kasa ya jaddada godiyarsu garesu,tare da Fatan Alheri,daga karshe gwannatin kasar Nageria tasanar dasu cewa bazata taba mantawa hallarcinsu gareta ba, Allah yabar zumunci,nan da sati daya duka sojojin ,zasu koma kasashensu cike da samun nasara,suma shawagabanninsu sun yaba da kokarin na gwannatin Nageria tare da jajircewa na sojojinta agaskiya tsarin ya burgesu,sun kuma yaba da wannan tsarin gwannatin Nageria nabama mutane tsaro da kare rayuwankan da dukoyoyinsu,sun kuma yi alqawari bada kowacce gudummuwa in bukatar hakan tataso,jawabin daya sanyaya zuciyar yan kasa,sukaji suma yau suna alfahari da kasar su Ta Nageria nan take aka saka Taken Nageria inda kowa ya mike ya kame,yana bin Taken Nagerian daduka muryansu,dayawan sojojin saboda daraja kasa,yadda sukabama Tutar nageria martaba,sunayi suna kwallah😥,Don Allah masu karatu duk wanda yazo daidai wajen nan akaratunsa yatsaya yayi godiya ga Allah(SWA) daya zamo damu daya daga cikin yan kasa Nageria,in zai samu ku gudanar da taken Nageria,nidai nayi nawa kuma na Fada da karfin *AM PROUNDLY TO BE A NAGERIAN*🙋



Haka akatashi taro,kowa yakoma gidansa lafiya,shima Aliyun bai tsaya anan Abujan ba,kaduna yakoma saboda samun damar parking din wasu kayansa,dakuma sallamar Bakinsu,kwana biyun da karin girmansa yasamu ziyara daga Ni"ima da kawarta muneera Abun mamaki harda mami da Cp Ahmed Sidi na iya,saiga Kwamishina yana nemam Dukawa ma Gadanga wai yana rokonsa gafara saurin dago dashi yayi yana fadin"Haba Daddy taya zaka dukamin,nifa kamar dankane,ni wlh haryau a uba nake kallo ka, don Allah bari ni babu Abunda kamin,kuma wlh ban rike ba"Kwamishina yaji dadin kalaman Aliyu har cikin Ransa yana ta godiya,Aliyu har Gidan Jabir ya karisa dasu suka gaisa da kanwarsa zafira inda tarasa inzata kaisu saboda hidima,Ni"ima tatambayi Azeema nan Yake sanar da ita basu dawo ba tana masarauta ammh zasu dawo kwanan nan,Rokonsa tayi don Allah in yana da hoton Triple ya nunamata,nan take yafito dashi ya haskomata,Santinsu Ni"ima tahauyi tana nuna musu Daddy da mami tana fadin"Daddy ku kallesu,suna kama da captain dina'"Kowa yaji Abunda tace itako da iya gaskiyarta take,bata kula da Abunda tace ba haka ta mikama muneera sunata santinsu,Shiko Umar na gefe Shida Jabir,ammh duk motsin da Muneera zatayi a idonshi baisan dalili ba,tunda suka hada ido da yarinyar yaji faduwar gaba itama haka take abangarenta,duk sanda ta dago ido,sai sun hada ido da Umar,tsarguwa tayi da kallon nashi tatashi ta Fito waje shikuma ya biyota da hanzari yana Fadi aransa"oppourtniy comes one in life"Gwara yayi amfani da damarsa kafin ta kubcemai,yana Fita ya ganta jikin motarsu,nan fa ya karisa gareta da gaggawa ya isar ds sakon zuciyarsa muneera can belive itace wannan hadadden gayen ke cewa yana sonta,kuma ma Dan sarki wow..Gaskiya Abunda bata taba tsammani ba,nan da nan tabada kai bori ya hau,nan take sukayi Sharing nombar juna,suna cigaba da Hiransu,suna bama juna lbrin juna,kafin wani lokaci duka zuciyiyon sun yarda da juna,koda su Ni"ima suka Fito nan suka tarar dasu suna zuba hiransu,duk wanda ya gansu sai da ya fahimci wannan ankullah soyayyah mai karfi,Ni"ima Abun yayimata dadi,dama kullum addu"arta Allah yabama muneera miji nagari tayi aure,sai gashi Allah ya bata,kanin gadanga ta yarda ko batada rabon Auren gadanga toh Muneera zata auri kaninsa suyi zumunci na har Abada,Gadanga bai nuna bacin rai ba,saima kallon Ni",imar dayake da tsausayawa,yana yaba halinta na bata hassada da kyashi,ko fada da wani Ni"ima mace ce so simple shidaya zauna da ita shi zai bada lbrinta,cikin mutumci da karramawa suka tafi bayan Ni"ima ta ciko wasu bakaken ledoji da kayan babys dana Azeema tabashi tace abaiwa mejego da Farko kin amsa yayi saida ta nuna bacin ranta kana ya karba,har suka bar haraban gidajen nasu tana dagamai hannu,wlh haka kurum yaji kwallah,yakuma tabbatarma kansa Ni"ima tanayimai So daya ne tak,babu Surki,gida ya Shige dauke da kayan yana mamakin irin Taurin kan Azeema ko Text batayi mai ba,kuma ya tabbatar da taji lbrin komai,umh wlh xata gane bata da wayau ne, don ya lura yanzu pretty bata shakkarsa.


Achan masarauta kuwa Shirya shiryan dawowan Azeema ya kamkama domin wajen kwananta hamsin kenan da haihuwa ta warke tayi garas da ita,kamar ba ita bace mutane uku suka tsagata suka Fito ba,gyara kuwa tashashi kamar ba gobe ita da kanta takejin kewar mijninta yana tasomata ammh tana kokarin dannewa,Su Afiya kuwa sun kara wayau da girma gasu da jiki Tububu kamar ya"yan Turawa,duk wanda ya daukesu bayan son ya jiyesu saboda sha"awa,ana gobe zasu taho Goggo ta kira gadanga ta sanar dashi nan yake sanar da ita su sauka ta Abuja saboda yanzu ma haka yana Abujan ne tun shekaran jiya yabaro kaduna,jin haka yasa goggo kiran Ummah ta sanar da ita,itakuma Ranar da su Azeemar zasu iso Tun safe direba ya wuceta da ita Abujan,Aliyu yazo yayi musu jagora zuwa cikin barikin,wanda kamar ma ba"a Nageria yake ba,ashe na kaduna kauyene,😃Akuma Aranar su Aliyu suka raka rundunar hadakan sojojin camero da chadi da niger,suka hau jirginsu domin komawa kasarsu,ciki kuwa harda Umar,wanda yakoma kasarsa domin cigaba da gudanar da ayyukansu,ammh yace Nigeria tazama gida garesa,Tunda yanzu ma Anan zai dauko mata.



*am srry for d typing error,ban samu damar tacewa ba*


*Janafty*
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

_Special Day..!Special person,..!Special birthday..🍢🍡🍧..! *1/1/2020* May dis Day be d begining of Anoder beutifull year 4u...May there be pleasant,suprises...Loads of joy And infinite happiness...Wish u a very Happy birthday *HEARTBEATDADDY*_😘💃💃❤💕💖

        *Chapter 39*

""Azeema sun sauka A abuja lafiya,ita da gimbiya Razeenah sai Inna Ramatu kadai sukazo,sai wata baiwa mai Suna Lami,dattijuwace sosai wacce zata dinga taimakama Azeema da kula dasu Anwar,inna Ramatu kuma daga nan Abujan gombe zata wuce wajen mijinta.

    Gimbiya Razeenah ita takira gadanga awaya ta sanar dashi saukansu,bai dau lokaci ba sai gashi yazo Filin jirgin na Nnamdi Azikiwe international Airport,koda ya iso,wajen da Azeema yafara tozali ya kalleta ta kalleshi lokaci daya suka dauke kai,kowa naji da kansa,cewa shi aka batamawa saboda haka shiza"a bama hakuri,ko su Anwar hannu Baba lami ya karbesu kafin ya daukosu su rankayo zuwa cikin barikinsu dake Abuja,ko zaman motan baya ta Shige ta hade rai sosai,gimbiya Razeenah ne ta Shiga gidan gaba.

Suna isa suka tarar da kyau da tsari irin na gidajen wajen harsunfi na kaduna ma girma,domin na nan din 3bedroom ne,da kuma falo har guda biyu,bayan katon kichen mai hade da store,kuma ko"ina yaji kayan alfarma babu Abunda ake bukata dama sai kayan da mutum zai saka su kawai zai zo dashi koda suka iso Tuni Ummah tagama gyara ko"ina harta Abinci sai tayi musu,suna zuwa Sallah sukayi kafin su zauna suci Abinci ana hiran Duniya da tambayan Mutanen chan,itako Azeema tunda tayi wanka tashige dayan bedroom din ta kwanta ko kara lekewa batayi ba,su Afiya suna wajen Baba lami,suma sunyi barci Tunda sukaji Ruwan zafi,da kuma nono,shikenan aka daina jin motsinsu,shiko gadanga Tunda yakawo su ya fice bai kara waiwayan gidan ba,saboda bayaso su Raba hali Shida Azeema don yaga take takenta so take yau takureshi har yatankanta.

Basu samu tafiya ba sai washegari da safe Gimbiya Razeenah da Ummah sai inna Ramatu suka rankayo sai kaduna suka bar Azeema da Baba lami da kuma mijinta Aliyu gadanga,daga kaduna ko kwana inna Ramatu batayi ta matsa tana son komawa gombe aranar Shiyasa Kawu Bala yasaka Direba ya kaita dauke da sha tara na arziki data samo daga Masarauta,dakuma wanda Kawu yakara mata,Gimbiya Razeenah dai tanan nan sai ta kwana biyu inji Ummah.

Tunda Su Ummah suka Tafi Azeema tashige bedroom din data zaba amtsauyin nata,takarayin wanka ta Shirya cikin Riga da sikat na Atamfa,wanda suka dauketa sukamata cas dasu,Baba lami na Falo tana Fama dasu Anwar yan Rigima itako kichen tafada domin lokacin har 11 ta gota yakamata tadora musu lunch ko badon Shi ba,don cikinta dana Baba lami.

Farar Shinkafa tadafamusu,saboda babu cefane,dama tazo da Soyayyar miyarta wacce taji kaji aciki,daga Niger wanda goggo da kanta ta soya mata shi,sukaci da ita,suna gama ci ta kwashe Abunda suka bata ta kai kichen ta wanke ta kife ta tsabtace wajen kamar ma batayi girki ba,tadawo Falo ta amshi Afra dake kuka tana Shiga bata Nono,Tagama bata kenan Ta karbi Anwar tana bashi ita kuma Afra baba lami ta sabata,tana dan jijjigata nonon ya kwantamata kada tadawo da ita,sai ga Gadanga yashigo da sallama,Azeema na jin sallamansa ta hade rai,tayi kini kini dashi,Baba lami ce ta zube tana jeramai Sannu da zuwa ya amsa yana mika hannu ya karbi Afra dake hannunta yazauna kusa da Afiya wacce ke kwance tana wutsil wutsil da kafafunta,kumatunta ya latsa yana Fadin"Afi Afi yanmata,kina wasa ne..? yafada yana daga Afra dake hannusa,Baba Lami kuwa Tunda ya amshi Afra ta shige dayan bedroom din da Azeema ta sauketa aciiki

Ta gefen ido yake kallon Azeema,ammh Abun mamaki ko kallo bai isheta ba,balle yasa ran zatacemai sannu da zuwa,itakuma abarayinta ta dojene Tayimai banza,saboda ita ganinta shiyakamata yafaramata sannu da zuwa saboda itace ta sha hanya kafin tazo inda yake,ammh saboda Wulakanci jira yake tamai mgana Shikuma ya tsinkata,aiko tace wlh ya bushe indai itace wlh.

  Ganin yadda tawani hade rai kuma ta dauke kaine yasa Shima ya tattarata ya watsar ya cigaba da wasa da ya"yanshi,ganin haka yasa Azeema ta mike tana gyara rigarta kusa dashi taje ta ijiyemai Anwar Tajuya ta Shige daki tana wani Taku,wanda har aran Aliyu yaji wannan Tafiyar,baki ya rike yana binta da kallo wai ma yaushe Azeema takoma hakane? Abun fa mamaki yake bashi,ya"yansa yayi Ta biyemawa yana wasa dasu yana kuma mgana kamar ya samu wasu manya,suko kamar sun sani suyita washe baki suna bangala dariya,yadda bai nemi abinci ba,shiyasa itama batayimai Tayi ba har sai bayan la"asar kana ya bar gidan,bayan ya kira Baba lami ya dankamata su Anwar yayi Ficewarsa.

Koda ya dawo bayan issha'i,ko takan Azeemar bai bi,yayansa kadai ya dauka yayi musu wasa kafin ya mikama Baba lami su,yayi Shigewarsa daya Bedroom din da kayansa ke ciki,itako Azeema tana jin adawowarsa taki Fitowa dama abincin dazu da Rana daya ragu sukayi Dinner dashi,saboda taga alamun bayan ita harta Girkinta ma baya Ra"ayi,shiko Abun ya dameshi na kyaluwan da Azeema tayi dashi,wlh bai zata ba,kuma tana sane itace bata da gaskiya kowa na ganin laifin kowa kenan.

Washegari Tun Safe Azeema tatashi ta tsaftace ko"ina kafin lokacin Tuni Baba Lami ta wankesu Anwar ta shiryasu cikin kayansu na alfarma,ita kuma Azeema harta Fada kichen tana kokarin nema musu breakfast,ganin duk babu cefanan Abinci yasa kawai ta dafa musu macaroni,Suka sake ci da miyar jiya,domin yadda takejin kanta bazata iya bude baki tace yayo mata cefane ba,toh Shi da baya cin abinta yaushe zai yomata cefane,🤔kaji mata kin bashi ne kikaga baici ba?

  Wanka tayi cikin Riga da wando na wani pakista,mai kalan pick,yayi mata kyau sosai,sai ta daure gashinta ta baya ta zuboshi ko dankwali bata sanya ba,tafito falo bayan takoma kichen ta sanyo musu macaronin ita da Baba lami ta kawo mata,ita kuma tazauna kan kujera tana tsakuran Abuncin kamar ansata dole,gefe daya kuma hankalinta na bisa talabijin tana kallon wani Shiri A Mbc2,Saiga Aliyu ya Fito sanye da bakar jallabiya alaman yanzu tatashi,gaisuwan Baba lami yake amsawa ammh idonsa na kan Abincin da suke ci,macaroni da miya dasafe kuma? ya tambayi kanshi kafin yakalli Azeema yace"ki Rubuta dukkan Abunda kuke bukata,in na Fiti nayo cefene"In kun tanka Azeema ta tanka,don saima tatashi ta Shige kichen tana wani takun dai dai kamar wata wahainiya,Girgiza kai kawai yayi yakoma daki,yayi wanka ya Shirya ya Fito,ko takanta baibi ba yafice,ammh bayan ya Shiga dakinta ya iske tana tiolet,kan Gadonta ya ijiyemata ledojin kayan da Ni"ima takowa yayi Ficewarsa,sai da Tafito taga kaya akan gado,zazzagewa tayi tana dubawa kafin tayi kwafa,ta maidasu cikin ledojinsu ta ijiyesu nan tashiga harkan gabanta,shiko bai dade da Fita ba sai gashi ya dawo dauke da cefane niki niki,duk Abunda take bukata sai da ya siyomata,Shida Baba lami suka dinga jindan kayan suna kaiwa kichen hakima Azeema na daki tana jinsu taki Fitowa,saima gyara kwanciya datayi Abunta.

Yana gama Shigo dakomai yayi Ficewarsa hatta Baba lami ta Fahimci tsakanin ma"auratan babu zaman lafiya Aranta tana Fatan Allah ya daidaitasu,tana jin Fitarsa tafito da hanzari Taja ledojin daya ijiyemata ta kaimishi daki ta dungurar kan gadonsa tayi Fitowarta kichen Ta fada tana dudduba Abunda ya siyo,nan da nan ta saka masu lalacewa cikin Fridge,sauran kuma ta sakasu cikin ma"adana,bata koma daki ba,ta kunna gas,don yau wlh Tuwon semo takejin ci,shi ta dora da miyar Kubewa danyan,don ta ganta acikin Cefane,don Ta lura ko agidan goggo Bata Rasa danyan Kubewa saboda Yaya captain.

Bata dauki wani lokaci ba,ta kammallah ta mulmule Tuwon aleda ta zubasu cikin wasu sabbin kololin nan kichen din ta bar komai bayan Baba lami ta taimakamata da wanke wanke Tunda su Anwar sun samu barci,ita tabar gyara kichen din,itakuma takoma daki ta Shiga wanka,ta Fito kenan Taji Mganarsa Afalo,yana ma Baba lami Fadan meyasa aka bar Afiya su kadai adaki,hakuri tayi ta bashi,tanaji yayi Fuu ya Shige dakinsa baki tatabe kawai tacigaba da Shafa manta,tagama kenan ta isa gaban Wardrope din ta na neman kayan dazata sanya ya Fado dakin Afusace dauke da lodejin dazu yana Shigowa ya nunota dasu yana Fadin

"Meye haka Pretty naga kin dawomin da kaya? aiko wani Abu ne kya jira nazo ki tambayeni nayi miki bayani..? yafada yana kafeta da ito,banza dashi tayi saima juya masa baya datayi tana Cigaba da Abunda takeyi,wani Abu yazoma Gadanga wuya ya jefar da kayan kan gado,da sauri ya isa gareta sai dai taji an wani Fizgota tatafi kamar zata Fadi,ya riketa da kyau har Suna gogan Numfashin juna,Kallonsa take ammh batayi mgana ba,ganin yadda yake wani Huci,shikadai yace"Ina miki mgana Saboda wulakanci kina min banza..?

Kokarin kwace hannunta take ammh takasa harara ta sakarmai tana Fadin",Ina ce kunne keji ko,don Allah mallam ka cikani"Tafada idonta ya kwallah Tsuramata ido, yayi Fushinsa na Sauka kafin ya sausauta rikon dayayi mata yana Fadin"Ki kwashe kayannan, danaki danasu Afra ne, Ni"ima ta kawo tace na baki.."Yafada yana Sakinta yakama hanya zai Fita ta waigo tana Fadin"Au kace Tsohuwar budurwanka ta kawo,ai dole ta kawo Tunda bayan dawowarka ta maye gurbina,Kaga don tayima abokin Shasha......


  "AZEEMA.....""!!!!Aliyu ya katseta da karfi da kuma wata tsawa mai gigitarwa wanda sai da tayi baya jikinta na Rawa,taku yafarayi zuwa gabanta idanuwansa sun chanza launi,kafa daya yadora bisa gado yana kallon Azeema yace"Kinfi sanin Ni"ima ne?kokuwa na riga saninki kafin ita,in inason yin iskanci da ita ai ba sai kin Fada ba,datun Farko da mahaifinta

Please Login or Register in order to submit comment