Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nema..? bakinta na rawa tace"Az...Azeza.."bata Fuska yayi kafin yace"Wai Shin tsaya na tambayeki Azeezar nan ita ta haifeki ne? kokuwa dai ke Sakarcin ki haryanzu bai nuna miki kina zubar da kanki bane come get in kafin ki bani haushi.."dago kanta Azeema tayi idonta sun ciko da hawaye kafin taji kawai taji baki ya bude tace"Ban da kowa fa,ita kadai ce wacce zan daki kirji na nunata amtsayin yar"uwanta ba sakarci bane yaya captain kulafuncin yanuwantakane..",Tafada hawaye suna gangaromata,kuramata ido yayi baisan dalili ba,sai yaji kalamanta sun sanyarmai da jiki kallonta yake cike da tsausayi kafin ya jinjina kai yace"it ok wipe ur tears..Kije kidawo daga mkranta zamuyi mgana kinji.."yafada cikin sanyin murya gyada kai tayi tana Share hawaye kafin ta shiga adaidaita din Hannu ya sa aljihu ya ciro 1k yamikamata kin amswa tayi illah nuna mishi Hannunta datayi tana fadin"Goggo ta bani.."Kallonta yayi yadda idonta suka cika da ruwa sam baiji dadi ba juyawa yayi yana fadin"Ok Tunda kinfi son ta ringa baki da hannunta zan barmata sai ta baki..Take care of u self.."Mirmishi kawai tayi tana bin bayanshi da kallo har suka bacema ganinshi,har takai mkranta tana Tunanin yaya captain ita kadai sai sakin mirmishi take in ta tuna da wani Abun.
 

Itako Azeeza bata hakura ba Domin Tana Shiryawa tana Fitowa daga gida tazo gidan goggo,daga kofar gida ta tsaya ta faman leke,hango yaya captain tayi ya fito tsakar gida yana waya bayi da riga dagashi sai dogon wando gabadaya Sirrin jikinsa ya bayyana awaje,Azeeza dake labe Tuni taji ta manne da bango saboda shauki kirjinsa ta kurma ido lokaci daya tana wani lashe baki tama manta damai tazo yi Shiko yajuya baya ta jikin kofar goggo ya hango Azeeza ta leke bayan yajuyamata baya dayake kofar tanada glass daga samanta ne,mamaki yacikasa bai yanke wayar ba ya juyo yafara taku zuwa wajen yanayi yana dan kallon gefe Azeeza batama Fahimci cewa gadanga ya taho ba daga kanta kawai taji ance"Ke..."Cikin tsawa firgigit tayi saboda razana tasaka kafa zata zura da gudu gadanga yayi Wuf ya riko hijabinta yajawo ta baya ya watsar da shegiya kasa yana binta da wani banzan kallo,ammh mayyar hankalinta naga kan Suran jikinsa tana wani kifkifta ido nunata yayi kafin yace"ke ubanwa kike nema da kike ma Mutane labe..? bakinta na rawa tace"Adda Azeema.."tabe baki yayi kafin yace,"Oh yanzu kikasan da Adda Azeemar yaushema ta zama Addarki mara mutumci,ke nifa ban ma yarda dake ba gayamin waya Turoki ko Uwarkice taturo kizo ki cutar da Azeema..? yafada yana dukawa daf da ita baya Azeeza taja tafara tsorata da yaya captain din tsawa ya dakamata yana fadin"Zaki gayamin kokuwa sai na Fasa kanki da bindiga.."Jin zencen bindiga yasa Azeeza Saurin cewa"Armmm..A"a ba wanda ya Turoni.."Tafada idonta kyam akan kirjinsa sai alokacin ya fahimci inda idonta ke kai,mikewa yayi lokaci daya yajefa wayarsa cikin aljihun wandonsa yana jinjina kai yake fadin"Oho Yanzu na ganoki ke ashema ba iya rashin kunya kika tsayaba harda bin maza ko?  Saurin girgiza kai tayi zatayi mgana ya dakamata tsawa yace,"Rufe min baki don ubanki zan miki karyane,kina kafe ne da ido kamar kin ga wani tsohon customer dinki ko? shegiyar daga ganin yadda kike kallona tsab aka kyaleki watarana zaki iya zama magajiyar karuwai,wlh tallahi kinji Rantsuwar dan musulmi in nakara kama idonki cikin nawa sai na fito da kwakwalwar kanki,Uselless kawai.."Yafada kan yasa kafa ya shureta yana fadin"Ur way out..Kar in kara ganin kafarki agidan nan.."Yafada yana nunamata kofa da Azama Azeeza tamike zata fice hawaye sun cikamata ido,Harta kusa Fita yace"ke tsaya..,kinga ko Azeema naga wani chanjin dabi"a awajenta ko naji wani lbrin wani Abu yafaru wanda ba halinta ba i swear daga ke har mahaifiyarka karnuka zasuyi watanda da Naman jikinku.."Yafada yana kadamata hannunsa,Azeeza tayi waje da gudu saboda kukan daya tasomata mkrantan data fasa zuwa kenan Inna Ramatu Ganinta kawai tayi ta shigo tana kuka,kuma tayi tambayar Duniyanan ammh Azeeza tayimata banza Kyaleta tayi,Saboda Yanzu kwata kwata tadaina gane kan Azeezar yanzu,itako kuka take da Duk Abunda tashirya sai Yaya captain ya Ruguxamata shirinta Kuka take da takaichi sai taga alamun Nasara sai kuma komai ya kwacemata.

  
Jabir da Aliyu suna cikin karyawa jabir ya samu waya daga Amminsa tana Fadamai mijin kanwarta dake jos Allah yayimai Rasuwa sakamakon hadarin mota yanzu hakama chan zata wuce yayi kokari yazo ya samu jana"iza Babu ko bata lokaci suna gama karyawa suka Shirya suka kama hanya Aliyu yayima Jabir din rakiya goggo tabisu da Fatan alheri tare da Addu"ar Allah yajikan wanda ya Rasu..Suna tafiya ba dadewa sai ga kawu bala ya zo,dayake ya shigo gombe yazo wani taro ne na Siyasa sai ya biyo nan wajen Suwaibar suka gaisa nan take fadamai yanzu su gadanga suka Dauki hanyar jos,Fatan isa lafiya yayi musu,Nan ya zauna sunata hira har bayan Azahar,har sai da Azeema tadawo mkranta ta tarar dashi,nan goggo ke koramai bayanin Duk Abunda ke Faruwa hakika ya tsausayama Azeema kuma yayi jinjina ga hikimar gadanga nan yayita ma Azeemar Nasiha tare da Shimata albarka da zai Tafi 30k yabama goggo Azeema kuma 10k yabama goggo 10k ta ijiyema mallam lawal saboda bazai iya jiransa har yadawo daga kasuwa ba,sallama sukayi cikin so da kauna tare kewa kafin su dau hanya shida tawagarsu goggo na bada sakon gaisuwa ga Umaima.

  Aliyu kwana daya yayi ajos yadawo gombe yabar Jabir achan,shigan yammah yayi don bai shigo gombe ba sai Wajen biyar na yammah koda ya shigo gidan Azeema kadai ya tarar agidan wai goggo batanan Tatafi gidan kakarta Baba Ade bata da lafiya itama wainar Fulawa ta tsaya soyawa Goggo ko tace wlh bazata jirata ba,in tagama tazo daga baya toh tana kichen tana ta Faman Sauri taji shigowar yaya captain gabantane yayanke ya fadi Ras..,Sai da ta dafe saitin zuciyarta dakin goggo ya Shigo yana mamakin jin babu alamun mutum Agidan Motsin dayaji akichen ne yasashi Nufar nan Yana shiga yacikaro da Azeema tana tsaye tana kwashe wainar Fulawan Tsaye yayi yana kallonta itako ganinshi ya sata ta Rude bakinta na Rawa ta Furta.."San..nnu da zuwa.."Yamutsa Fuska yayi kafin yace"Baki amsa sallama ne?ina goggo..? ya jehomata tambayoyi  fiki fiki tahau da ido kafin tace"Banji bane,goggo kuma tatafi gidan Baba Ade..."juyawa kawai yayi yana fadin!Taimakeni da Ruwa don Allah.."daga haka yafice daga kichen din.



_Allah yayi ma Rayuwarki Albarka Diyata LADINGO IKON ALLAH...Akullum ina alfahari dake Endless of love Dota_😘


    *Comment..And share...*
    *Janafty...*
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

       *Chapter..15*

  ""Da Sauri ta kwashe wainar Fulawan ta kashe gas din,Fridge ta bude tadaukomai Ruwa mai sanyi sama ta taka tahau ta bude drower din dake kichen ta dauko wani filet mai hade da kofuna da hanxari ta daurayesu ta dora Ruwan bisa kafin ta jeramai kofuna guda 2 Ta nufo Falon tana Faduwar gaba.

Yana Zaune kan daya daga cikin kujerun Falon  saboda gajiya ko Takalmin kafansa bai cireba ya kishingida da cussion din kujeran idanunsa alumshe kamar mai barci,Tana isowa falon taja Center Table din dake tsakar dakin Ta dora Ruwan akai,ganin idanunsa alumshe yasa Tamike salaf salaf zata fice taji yace"ok ni kikeso na zuba Ruwan dakaina kenan ko? haka kika ga goggo na min..? kyam ta tsaya tana sauke ajiyar zuciya kafin ta waigo still dai haryanzu idanunsa alumshe suke Tahowa tayi tazo ta durkusa ta Bude Ruwan ta zubamai cikin kofin data hado dashi mikamai tayi tana fadin"ga Ruwan yaya captain.."Bude idanunsa yayi karaf ko suka hada ido,jikinta ne yafara rawa tana neman Mai bari da Ruwa yayi Saurin Amsan Ruwan yana fadin"ke shin wai meke damunki ne?ji yadda kikeneman min barin Ruwa ajiki.."Sunkuyar dakai tayi batayi mgana ba,bai sha Ruwan dayawa ba ya mikamata ta karba Mikewa tayi zata maida Farantin kichen taji yace"Jeki dawo yau dai naji menene mtsalarki.."yafada kai tsaye gabanta ya fadi tayi Saurin kallonshi shima ita yake kallo kauda kai tayi kafin ta Shige kamar zata fadi,bin bayanta yayi da kallo yana Tunanin anya yarinyarnan bata da Shafan Aljanu.


  Sai da tabata lokaci kafin takoma,ita duk ta tsargu saboda bata da hijabi Sai wata doguwar Rigar Atamfa cikin wanda goggo ta dinkama ne,chan nesa dashi taje tazauna kanta na duke tana wasa da gefen dankwalinta kamar wata yarinya,kallonta yake yana Tunanin wani abu kai tsaye yace mata"Taso ki dawo nan mgana zamuyi kuma ba'a mtsayin mata da miji  amtsayin Yaya da kanwa.."jin haka yasa tadago tana kallonsa gyadamata kai yayi alamar tabbatarwa tashi tayi ahankali ta isa kujeran dayake zatayi kasa yayi Saurin riko hannunta yayi ya zaunar da ita agefensa yana fadin"Sit here.."Jikinta ne yahau rawa lokacin da hannunsa yatabi nata balle da kafadanta ke dukan nashi,ganin yadda Ta rudene yasashi dan matswa Shidai baiji komai ba,kodon baisaka Abun aka bane baisani ba.

  Yadade yana karema Surarta kallo Azeema ba Farace ammh tana da, hasken Fata sosoi wahalace ta maidata baka Tana da doguwar Fuska mai dauke da kyawawan idanuwa,hancinta bai cika tsawo ba,ammh yadace da kyakyawan Fuskarta tana gashin gira hade dana ido Masu kyau da Tsari bakinta dan karami ne,ammh leben sama yafi na kasa girma da kadan,in ta tsuke bakin sai ya birgeka yakuma baka Sha"awa doguwa ce bata da jiki,ammh tana Fadin kugu da kirji mai kyau kirjinta ba"a cike yake ba,sakamakon nonuwanta basu da wani girma na azo agani ammh Suna tsaye cur dasu,zarazaran yatsun hannunta yakoma yanabi da kallo kawai lokaci daya yaji ya tsaida kallonsa kan dokin wuyanta yadda wasu kananun gashi suka kwanta awajen,cikin kankanin lokaci tsigar jikinsa tafara tashi lumshe manyan idanunsa yayi kafin yakira sunanta.

  "AZEEMA...."Cikin Sanyin murya da muradi bata amsa ba,ammh sai tadago tana kallonshi saboda jin muryan dayayi amfani da ita wajen kiranta idanunsa ya bude fess akanta yana kallonta sadda kai tayi kasa kafin ta amsa.

  "Na"am..."gyara zama yayi kafin yace"Don Allah tambayanki zanyi waht i want is to tell me,d truth kinji ko.."Gyada mai kai tayi kafin tace"Toh insha Allahu."good yafada kafin yaciga ba da cewa,"Ina so kifadamin hakikanin meke damunki?mekike bukata?me kika nema na Halin Rayuwa kika Rasa Azeema,in mganar Gidanku ne,yanzu kin dawo nan buh ammh har yanzu abubuwanki basa raguwa sai karuwa don Allah kifadamin meye ke damunki kokuma miye matsalarki? kudi? mkranta kikeson achanza miki? kokuwa baki son zama da goggon ne natafi dake kaduna ai zaki zauna abariki ko? Duk Abunda yake fada tanajin sa,wani tsausayin kanta ya kamata tare da Tsausayin yaya captain,jin Abunda yace na karshe ne yasata dago kanta tana mirmishi ammh hawaye sun cikamata ido kai tsaye ta girgiza kai batayi mgana ba,Hade naman goshinsa yayi kafin yace"To meye? kifadamin meke damunki kinganni nan banda yawan mgana i know ahaka halittata take buh ur own Azeema yayi yawa baki da sakewa ko kadan.."Yafada da alamar Abun ya dameshi.

  Dago kanta tayi tana kallonsa kafin tace"Hakika in nace nayi rashin wani Abu toh na zama butula babu Abunda na nema na rasa kuma ni babu Abunda ke damuna,in akwai Abunda na Rasa arayuwata abu dayane yaya captain..'kallonta yayi kafin yace"Maza fadamin meyeshi nikuma nayi miki alqawarin mgance miki duk wani Abunda ke damunki.."tadade kanta asunkuye kafin tadago idanunta na fitar da amon hawaye tace muryanta na Fitar da amon kuka.. *UWA...UWA..* ita na rasa yaya captain na rasa uwa wacce zata nunamin banyi daidai ba in gyara! na rasa uwa wacce zatamin fada ko tabani shawaran in wata mtsala ta sameni!,na rasa uwa wacce zan kwanta bisa kafadanta nayi kuka ta lallasheni!na rasa uwa wacce zata kalle ni ta sakamin albarka,duka na rasa wannan yaya captain na taso arayuwata nikadai nake gudanarshi,babana yana Sona ammh tsoron inna ramatu baya barinsa ya kebe dani ballatana har yasan damuwata na kasance duk wani damuwa da zan Shiga sai dai nayi kuka adaki ni kadai na lallashi kaina bani da dan"uwa ko wani Shakiki da zan Fadama damuwata yabani Shawara haka nake rayuwata nikadai,toyaya kewa tare da damuwa bazasu taru sunman yawa ba,ka fadamin yaya captain Tayaya...?Tafada tana Rushewa da kuka kamar zata shide.

Gabadaya kalamanta ya Sakashi jin wani tsabar tsausayinta ya kara mamayeshi kallonta yake tana kuka lokaci daya Shima damuwarshi ta dawo sabuwa,yasani shi mahaifi ya rasa ammh Goggo da kawu bala basu taba bari yayi kukan maraici ba,koda aboye koda asarari ne,itafa bata da kowa ba uwa ba,ba uba mai kula ma dangi ba wani dan"uwa sai da wanda Allah yaduba ya tsausayamata tabbas tafishi jin dacin rashin Abun Aranta fiye da yadda yakejin nashi Aransa.

Saboda tsausayinta baisan sadda ya mika hannu ya rikota ba,ya kwantar da kanta bisa kafadanshi yana bubbuga bayanta yana fadin"shiiiii....am srry kinji Stop Craying i promise i won let u down insha Allahu..."Yake fada yana sharemata hawaye da hannusa,gyara mata zama yayi suna facing din juna yace yana riko hannuta"Yanzu Firstly do u luv me,zaki zauna dani duk da ana ce nidin bani da cikakken asali wasu ma cewa suke bani da uba..? dago kanta tayi tana kallonsa dan hararansa tayi kafin tace"injiwa..? haba dai suma wasa sukeyi.." karkatar dakai yayi yana fadin,"Eh mana ko,kin manta dalilin haka aka hanani Auren Ni"ima Shine ma dalilin dayasa Auren yakoma kanki.."yafada yana cije lebe,kallonsa tayi kafin tace"Kayi hakuri haka Allah ya kaddara itadin ba matarka bace,..Kayi kokarin cire sonta aranka sai kaga komai ya wuce.."Zuru yayimata da ido kafin yace"who told u cewa haryanzu am in luv wit Ni"ima.."Sadda kai tayi taki mgana girgiza hannunta yayi yana fadin"Kiyi mgana waya fadamiki.."Kai tsaye tace"Azeeza ce..."Ware ido yayi kafin yace"Ohh i seee... wato ita ta zaunar dake ta tsaramiki haka,to kila ni nafadamata ko.."?yafada Fuskarsa na chanzawa saurin cewa Azeema tayi"A"a ni batace kai kafadamata b..."Toh meyasa kike yarda da duk Abunda tace miki,kina zaton ita da mahaifiyarta suna kaunarki ne,kinga dole fa in kinaso tamu tazo daya dake Azeema u should learn how to respect ur self,kiwani zauna yarinya karama na zana miki zence kawai don ta maisheki mara wayau.."yafada cikin Fushi Saurin Sadda kai tayi kafin tace"Kayi hakuri baza akara ba.."tafada tana Kwace hannunta ita tsoronta kada ya zuciya ya kaftamata mari.

  

    Sakinta yayi yana fadin"it ok kikiyaye gaba,komai ta tambayeki as From today karki bata wata fuskan da zata sake sanin Sirrinki kina gaba da ita,ita din kanwarki ce so be carefully...'Yafada yana kauda kai shuru tayi tana wasa da hannunta kafin bazato yaji ta jehomai tambayar

  "Toh in kadaina son Ni"ima wakake so..? saurin kallonta yayi yana hade naman goshinsa Cike da mamaki saurin sadda kai tayi,cike da kunya Dan dariya yayi kafin yace"Ada nasota lokacin danake Tunanin Ita zatama abokiyar rayuwata buh tun lokacin da mahaifinta yanemi cimin zarafi naji tafita daga Raina,any way kobana sonki Azeema kinada wani babban mtsayi Araina keda mahaifinki domin kun sharemin kasan da mahaifin Ni"ina ya watsamin.."Yafada yana kallonta kur da ido,kallon ne yabata kunya tayi Saurin tashi ta fice waje da gudu,da wani kallo yabita yadda kugunta ke kadawa rausayar dakai yayi yana cije baki,nan take mganar Jabir ta fadomai Aranar da"aka daura musu aure....

  _Yarinyar tayi zaka samu duk Abunda kakeso wajen mace,tama fi Ni"imar komai..._Tuna haka dayayi ne yasashi shan mur yana kunkuni shidakai na yadda har jabir yarigashi gano Abunda shi yakamata yafara ganowa.

  Azeema na Fita waje tacikaro da goggo daga gefe zaune kan wata kujerar roba dake wajen tana cin gyadanta soyayyiya hankalinta kwance baki Azeema ta rike kafin tace!la..Goggo yaushe kika dawo.."Kallonta tayi kafin tace"Na jima Azeema.."Karisawa Azeema tayi tana fadin"wlh goggo bamuji shigowarki ba.."Goggo tace"Ai bazaku ji ba,na Shigo ina ta rafka sallama har daga makota anajina,harfa leka dakin nayi naga ko barci kike sai na samu ana zantawa tsakanin mata da miji,shine nace toh toh..Bari nayi baya har kugama kada na katseku.."Tafada tana dariya kunya takama Azeema sai ta labe bayan goggo tana yar dariya.
 

  Gyadar goggo ta nunamata tana fadin"kega Abunda baba Ade tabani tace sai kinzo zaki karbi naki.."mikewa Azeema tayi tana fadin"la gyada goggo,yanzu kuwa zan mata dirar makiya sai tabani nawa.."tafada tana fadawa daki,koda ta shigo sai taga kamar gadanga na barci sai ta shige kurya tadauko Abayarta ta fito harta kai kofa zata fita taji ance daga bayanta.."Ina zaki..?"Saurin waigowa tayi still idanunsa na kulle,cewa tayi"Gidan Baba ade zani.."lalle yarinyarnan to ki koma ki cire hijabin sai gobe yanzu yammah tayi.."Ya bata amsa.

  Tura baki tayi da jin Abunda yake cewa,bude idanunsa yayi karaf ko suka hada ido dashi ga gudu ta kariswa bedroom din goggo tana dafe kirji,shiko mamakinta ne yacika ashe ta iya tsiwa dama,mirmishi yayi shi kadai kan yamike agajiye ya fice nan waje yaga goggo suka gaisawa alwala ya daura yafita sallar mangariba,itama goggo tayi nata ta shiga ciki tayi sallarta ita da Azeema wacce goggo kema gwalo da dariyan hanata fita da gadanga yayi sai mata kwalelen gyadan takeyi itako duk Haushi ya cikata sai da goggo tagama jan mata rai kana tabata gyadan,shiko gadanga a massallaci ya zauna har akayi issha,"i kafin yakoma gida,kuma bai ma koma barayin goggo ba yashige daki yayi Shirin kwanciya saboda gajiya.

      ****************

  "Oh my god Sweetheart don Allah kibar wannan kukan,bai da wani amfani juz keep praying in Captain mijinki ne,ko duk duniyanan zasu hadu wlh basu isa suhana ba,kuka bai da wani amfani..."Muneera take fada tana Riko Hannun Ni"ima,Share hawayenta Ni"ima tayi kafin ta dago idanunta jajir Tace"Ya zanyi Ya kikeso nayi Sweetheart..Wlh i love Captain Bazan iya hakurin rashinshi ba,bakiji menake fadamiki bane,he told me bazai taba Aureba Sweetheart,yayi Aurensa ya barni."Tafada wasu hawaye suna kwaranyomata, Rumgumeta muneera tayi tana lallashinta tana fadin.

  "Nidai ki daina yawan kukan nan Sweetheart..Wlh banijin dadi,insha Allahu captain Sai yazama naki da yardan Allah..."tafada tana bubbuga bayanta Lamo Ni"ima tayi tana Shesshekan kuka ahaka Mami tazo ta samesu Tana tsaye tace"Kingan ta nan Muneera haryanzu kukanta yaki karewa,Ni narasa wannan bala!in,sai kace Aliyun ne, kadai Namiji aduniya ko Rasashi Tamkar rasa rayuwace gabadaya,Allah tun inajin Tsausayinta hartakoma bani Haushi,ai sai kiyita kece keda wahala.."Tafada kafin tafice Cikin Fushi da nuna Abun ya dameta.

  Bayanta Ni"ima tabi da kallo hawaye suna kwaranyomata,Zame jikinta tayi ta mike Tafada bedroom dinta tana sharan kwallah,bayanta Muneera tabi da kallo tana mamaki wani irin sone Ni"ima kema Captain data kasa hakura dashi Tunda yayimata nisa,gabadaya ta rame ta dishe ta lallace kamar ba ita ba,Abun nacimata Tuwo akwarya ammh babu yarda zatayi domin hartagaji da ba Ni"imar baki tahakura takoma ta zuramata ido saboda al"amarin nata yawuce duk yadda bawa zaiyi tsammani.

   ______________

Azeeza ko alama bata ja da baya ba,Abunda yakara bata tsoro ko School Azeema bata nemeta ba Abun ya matukar Dauremata kai,tafara Tunanin kodai ta ganotane ammh duk da haka bata ja baya,ba washegari dataje mkrantar agaban idonta maikeken yazo yayi Dropin din Azeema kuma Abunda kowa bai sani ba Duk motsin Azeemar a idonta domin tana labe akofar gidansu tagazuwam mai keken yazo Daukan Azeema,batayi mamaki ba,tasan kila aikin yaya captain ne,don taga He is very smart yana da Saurin Ramfo mutum tana ganin Azeema ta Shigo cikin mkrantar ta nufi ajinsu sai ta chanza shawara sai tabaro ajinsu ta ratso ta tsakiyar mkranta kamar zata office din Principal nan sukacikaro da Azeema wacce ke kallon Azeezar Tunda daga nesa tasha mur tana kallonta ammh ta kauda mata kai.,Kiran ta Azeema tahauyi ammh Azeeza tayimata banza kamar bataji ba,da hanzari Azeema tatake mata baya da dan gudunta sai gashi tasha gabanta tana fadin"Haba Azeeza mgana fa nike miki ke man banza.."Wani kallo Azeeza ta maka mata kafin ta raba ta gefenta zata wuce,ammh sai Azeema taki bata damar haka Ta hanyar riko hannunta.

Cak Azeeza ta tsaya ammh bata waigo ba,juyo da ita Azeema tayi tana fadin"Wai Azeeza duk miye ya faru ne ? nine fa Addanki Azeema ai yaci komiye nayi miki bai dace nayi mgana acikin mutane ki tsinka ni ba.."Yamutsa Fuska Azeeza tayi kafin tace"Dole na Tsinka Adda Azeema naga kin zabi Namiji,Namijin ma bare akaina,kinga ai sai naja baya.."Ware ido Azeema tayi kafin tace"lala..Injiwane Duk duniyar nan ina da kamarki ne.."Bata Fuska Azeeza tayi kafin tace"ba gashi ba,Tunda har wanda aka lakaba miki amtsayin mijinki ya iya cimana mutumci dagani har ke da baba ba wanda ya ragamawa.."Tafada harda matso kwallah Zuramata ido Azeema tayi kafin tace"Shi yaya captain din? da hanzari Azeeza tace"eh mana Ranar dana biya miki yayi min kaca kaca hardacemin wai daga gani na watarana magajiyar karuwai zan zama..'Takarishe fada harda fashewa da kukan karya.


Baki Azeema ta rike tana kallon Azeeza,Zuciyarta takasa gasgasata,Saboda Duk kalamanta babu gaskiya,ganin haka yasa Azeeza tashiga jerama Azeema rantsuwa hartana fadin yace kema wani Shiri kawai yake akanki da zarar yacinma burinshi zai baki takardanki,nidai don Allah Adda Azeema karki kuskura kiba dan iskan sojan nan kanki saboda bai da wani buri,illah ya maidaake karamar bazawara ya sakeki kuma Allah duk Abunda kikaga yanayi Duk shawaran uwarsace goggo..."Ai Sai Azeema tazama out of control zuciyarta tashiga zafi lokaci daya wani bangare na zuciyarta na amincewa da kalaman Azeeza wata kuma na kwabarta,Zuciyarta ta bata cewa in mganar Azeeza gaskiya ne,to ai yaya captain bai taba nuna wani zalama akanta ba asalima basu taba zaman Fahimta ba sai jiya,kodai kodau duk cikin plan nasa ne,Goggo kuma bazata taba cin amanarta ba,itace makwafin mahaifiyarta ta ci kashinta da fitsarinta goggo ta goyata da bayanta duk Abunda uwa zatayi ma danta shi goggo take mata,gaskiya bazata taba yarda da goggo za"a cuceta ba,to ammh mganar Azeeza Abun dubawane,domin akankantar Shekarunta bazata kitsa mgana kai tsaye ba,itako Azeeza ganin yadda Azeema tashiga Rudani Shiya bata damar kara mata famfo tana tsaro mata wasu mganganun wanda ita da kanta ta tsarasu,nan da nan Azeema ta amince da Azeeza ,100% harda kukanta tana fadama Azeeza ita yanzu yazatayi batasan ya rayuwarta zata je ba,shawara Azeeza tabata kan daga mkranta ta wuce gidan Baba Ade koda goggo taje ta tubure tace wlh bazata koma gidan goggo ba,bayan kwana biyu kuma ta bijuro da zencen sai yaya captain ya saketa.

Azeema ta yarda da shawaran Azeeza saboda yadda hakalinta yake atashema nan take tace Azeezar tazo ta rakata,Bakin Titi ta hau Abun hawa takoma gidan Baba ade,murna fal cikin Azeeza ta hanzari suka tafi office din principal,sukayi report kan Azeema bata da lafiya zata koma gida,nan da nan aka bata permission Azeeza ta rakata bakin Titi ta hau Keke tawuce gidan Baba Ade bayan Azeeza ta jaddadamata komai tambayan da za"a mata kada ta fadi dalili kawai tadai tada kayar baya,amsa mata tayi da cewa zatayi duk yadda suka tsara,Azeeza na dagamata hannu har suka bacema ganinta wata dariya ta kwashe dashi tana fadin,"Bye bye Adda Azeema i wish wannan karon bazaki tallakema tarko na ba..Yaya captain am coming iin to ur life Soon..."Tafada tana yar dariya kafin tajuya takoma cikin mkranta tana Dariyan Farinciki da nishadi.



   _*Topha bala"i...Gaskiya my Fans sai yanzu nake ganin wautar Azeema dakuke tafadi,yarinya kamar kwalkwalarta ba Ta wani Tunani sai na Shirme,yanzu goggon zata gujema saboda dambala,...🤔🤔🤔Lalle Azeeza yanzu kika Fara wasan naki,toh bari mugani Shin gadanga zaifiki zama player ko yaya? Hmmmm i don't know..,Sai mun hade a next page,love u all my Fans*_

               *Comment,share and vote...*
               *Janafty..,AKA...SHAKIRA..*💇
 *ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

         *Chapter 16*

  _Am srry For d typing errors ban samu na editashiba_✌

      "Aliyu yasha barci domin sai wajen karfe daya na Rana ya farka wanka kawai yayi agurguje ya sanya Shadda fara Dinki Muhammed riga da wando,da hula yatafi masallaci saboda ya samu jam"i,,koda aka idar da sallar bai Shigo gida ba,kofar gida yazauna yana waya da Haisam bayan sungama kiran Jabir ya Shigo wayarsa nan fa yazauna Sunata Fira,sun dau tsawon lokaci suna mgana kafin suyi sallama Akan sai sun hadu akaduna don kowannensu jibi yake san Ran komawa bakin aiki.

    Sun yanke kiran kenan sai ga KekenNapep din dayake Kai Azeema mkranta ya iso Faka keken yayi ya fito ya nufo Gadanga wanda yake binsa da kallon mamaki karisowa yayi yana mai sallama lokaci daya ya bashi hannu sukayi musabaha,bayansa Aliyu ke kallo yaga kota ina Azeema zata bullo ammh shuru,da kallon

Please Login or Register in order to submit comment