Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

koka,don ni kika zalunta,ammh wannan kukan dakike sai ki dinga nuna Cewa ke aka zalunta.."Daga Haka yafice daga dakin yana jin kamar ya kwanta akasa yayi ta kuka.

Azeema na kuka,ta mike daga ita sai Rigar barci wata doguwa Fara mai Ratsin pink ajikinta,Wani dogon hijabinta ke jikinta wanda take sallah dashi,Akwatunanta dake kan gado ta Shiga saukewa akasa tana kuka,dama tun jiya tahada komai nata,Daukan akwatunan tayi daya bayan daya tana kaisu Falo,harda da kayan kwalliyanta babu abunda tabari,ta kwashe komai nata kamar yadda yace,Dan kit din dake hannunta Shine na karshe ta juya tana ma dakin kallon karshe kafin ta kada kai Tafito tana zubar kwallah,koda Tafito babu Aliyu afalon,kamar da Farko data ganshi tsaye,sabanin yanzu sai wani Soja tagani yanata jiddan akwatunanta zuwa waje,kasake tayi tana share kwallah kafin tabi bayanshi zuwa waje.

    Tana Fitowa ta iske shi Shida Jabir suna Tsaye suna mgana,ammh dukkanasu Fuskokinsu ba Annuri,balle walwala,baya Taja ta Tsaya tana sadda kanta kasa,Jabir yana ganin ta Fito yatako zuwa gabanta yafadin"Azeema ki taimakeni ki Fadamin Abunda ke Faruwa,tunda shi yaki fadamin,Tun jiya na lura wani abu na Faruwa ammh yamin Shuru yanzu kuma gashi kina kwashe kaya don Allah meya Faru..?"Dago idonta tayi dasuka chanza kala tana kallonsa,hawaye suna kwaranyomata,Wani Tsausayin Aliyu ya Tsirgamata,tana kallonsa tana Jin koba komai yayi mata karamci Tunda ya iya boye wannan Sirri,kasa mgana tayi sama jan kafanta datayi da gudu zuwa wajen motar ta bude gidan gaba Tashiga tana kuka mai cin rai,da ido Jabir ke kallonta yana mamakin wannan al"amari,yana kallo Aliyu yazo ya Rufe gidan kafin ya dawo har zai gotashi sai yadawo da baya ya dafa Jabir yana fadin'Am Srry Dude,bafa wani Abu bane wajen goggo zata koma ta Rubuta jarabawarsu ta candy,shine fa kaga munshiga damuwa,ammh babu wani abu ka kwantar da hankalinka yau insha Allahu zan dawo dazarar na kaita bazan tsaya ba.."Juyowa Jabir yayi yana Kallon Aliyu Shiko yaki yarda su hada ido,Girgiza kai kawai Jabir yayi kafin yace"Allah ya kiyaye hanya..." Daga haka kawai yakada kai ya Wuce,don kwata kwata bai yarda da kalaman Aliyu ba,ammh Tunda yana boyemai bazai kara neman yaji ba.

  Da Hanzari Aliyu ya isa ga motar ya Shiga bayan Sojan ya gama Dura kayan Azeema abayan motar,ganinta Zaune agidan gaba ta saka kanta tsakanin Cinyoyinta tana kuka yasa yayi gaggawar Fitowa yana fadin"Plz ki koma baya don Allah,i don"t want to see u in my Side again.."Tana jinsa tayi Saurin danne kukanta ta Fito da Sauri ta bude gidan baya tashiga tana boye Fuskarta cikin hijabi,Sai da ya bata lokaci kafin ya Shigo motar tana jnsa yana karanto addu''ar matafiya ya Daura Belt suka Sulala,basu bata lokaci ba Suka Fita daga cikin barikin kafin su dauki hanyar Gombe.


Karfe goma da wasu mintina Motar Aluyu tayi Parking akofar gidan na goggo,dayake lokacin yayi safe dayawa,shiyasa layin babu kowa,tsit kowa yatafi neman Halali,mataye kuma suna cikin gida,suna Dafa Abun sawa abaka,idonta biyu suka iso,don tunda Suka Fito daga kaduna take kuka,har suka iso gombe,da hanzari Ta bude murfin mota dauke da karamin kit dinta ta Fada gidan goggo da gudu tana kuka,shiko dama bai yi niyyar Shiga ba,waige waige yafarayi kafin ya Hango wani almajiri da hannu yayafitoshi yako zo da Sauri,Yana zuwa ya zura hannu a aljihu ya zaro dari biyar ya mikamai kafin yace"Don Allah kaya zaka Shiganmu dashi Cikin gidan nan..!Yafada yana numa mishi gidan,washe baki almajirin yashigayi yana godiya booth din Aliyu ya budemai yana Fito da akwatunan,shikuma ya fara dauka yana Shiga dashi cikin gidan.

  Goggo na zaune abakin Fomfo tana dauraye yan kayanta taji Fadowar mutum jikinta Ana kuka,ta tsorata ta Waigo da Hamzari tana fadin"Subhannallah waye haka.."?Tafada Tana Rikota Da Hanzari Azeema ta jaye hijabinta kanta tana kallon goggo,Baya goggo taja tana Fadin"Azeema...Azeema,mezan gani haka? keda waye kuka zo?Azeema na kuka tace"Goggo sunyi Nasaran Rabani da yaya captain,Sun rabamu goggo,sunyi Nasara akaina,wayyo Allah na Shiga uku.."Mikewa da hanzari goggo tayi tana Rawan jiki,bata kai ga yin mgana ba,almajiri yayi sallama yana Shigowa da kayan Azeema,da kallo Goggo ke binshi tana kallon Azeema lokaci daya kafin tace"Kedawa kikazo? Runtse ido Azeema tayi kafin tace"Shi ya kawoni yana waje.."Ai goggo ko mayafi bata sanya ba tayi waje da gudu,sai dai tana zuwa Motar Aliyu na barin wajen da hanzari goggo ta Kwalamai kira Tana fadin"Gadanga.."Kai Gadanga.."Ammh ina har Ya kule daga layin.
 

  Baya goggo taja tana dafe kai,Kafin takoma cikin gida,tana bin akwatun nan da almajirin yagama Shigowa dashi da ido,gefe daya kuma tana bin Azeema da kallo wacce tayi zaune akasa hannunta bisa kai tana kuka,duk kammaninta ya chanza bakin goggo na Nauyi tace"Wai Shin Azeema Abunda bangane ba gadanga ya sakeki ne ko yaya,nifa kunsani a cikin duhu don Allah bar kukan nan yimin bayani,naga gabadaya kayanki gasunan meya faru ne? Majina Azeema taja kafin tace"Bai Furta saki gareni ba goggo,ammh yace bazai iya cigaba da zama dani ba..?"

  kusa da ita goggo ta kariso tana fadin"Kam wani dalili..? nace kan wani dalili ko ya dauka aure Shiga jeji ne koko harbin bindigane..?Goggo tafada cikin bacin rai,bakinta Azeema ta dafe tana fadin"Wlh ban aikata ba goggo,Sharri ne,kuma bansan wanda ya aikatamin haka ba,kuma bansan dalilin kowaye ba."Kuri goggo tamata da ido kafin ta sanya hannu ta rikota tana Fadin"Daina kuka Azeema,taso mu shiga daki,ki warwaremin komai,insha Allahu ina tare dake.."Tafada tana rikota suka Shiga daki,Kan kujera goggo ta zaunar da ita,kafin takoma ta rika jido akwatunan Azeema tana Shigowa dashi,gefe daya na zuciyarta tana cike da takaichin wulakancin da gadanga ya yayi mata,ai ko miye Azeema tayimai ya kirata awaya su tattauna ammh dayake wulakanci ya Shirya harda kawota da kanshi,kuma yajuya yayi Tafiyarshi,wlh zai zo ya sameta zai ya gane ita ba"a mata iskanci Ja'irin yaro kawai.






*Intelligent writer"S Asso*
*Janafty..*
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

      *Chapter 26*

    *After 1 week*

    Bayan Sati daya da dawowar Azeema gombe,har kuma yau basu ji wani mgana daga bakin Gadanga ba,koda goggo ta gaji da Fushinta ta kirashi wayarsa bata Tafiya,Itako Azeema bata gayama Goggo Abunda yafaru Tsakaninta da Azeeza ba,saboda batasan taya zata kama lbrin ba,ammh tabi Shawaran goggo ta maida lamarinta ga Allah Shine zai warware komai cikin Sauki,Azeeza kuwa Aranta tana mata Fatan shiriya,Yanzu ta rageyawan kuka da damuwa ammh ba kewa  Tare da kaunar gadanga bai bar Ranta ba,kullum dashi take kwana take tashi,gashi Tunda tazo take Fama da zazzabin dare,dakuma gari yawaye sai ta nemi zazzabin Tarasa,gashi bata cikin kwanciyar Hankali ammh taKara haske sosai Fatarta tayi kyau,Kullum sai dai Tasha paracetamol ta kwanta,itama goggo Abun na damunta ammh Sai Azeema tashashantar da zencen Zuwa asibitin,mganar cin abinci kuma bata cika ci ba,sai da yanzu Tafi kauri wajen kayan kwalama,irinsu goriba,wainar Fulawa ta manja,da kuma Danwake wanda kullum cikin yinshi take,goggo dai kallonta kawai take ammh kasan zuciyarta tana zargin wani Abu,Allah yasa hasashenta yazama gaskiya,Shiko mallam lawal kullum zai Fita kasuwa sai ya Shigo sun gaisa da goggo yaga kwanar Azeema,in ko yadawo sai ya Shigo yakawo mata Sakonta nasu goriba da dan Ta matsitsi tunda ya lura tana so sosai,Sune yanzu Abun shanta da Tsamiyar biri,Daga goggo har Mallam lawal sun tabbatar da hasashensu kan Azeema domin alamomi dadama sun bayyana zarginsu.

Ranar Asabar sai ga Kawu bala Shida Ummah suka diro gombe,Murna wajen goggo ba"a mgana tarasa ina zata sakasu saboda murna,kawo musu Wannan kawo musu wanchan,Sai da suka huta sukaji abinci kafin su shiga tattauna Abun yakawosu Goggo tana Fada tana gayama Kawu bala cewa gadanga bai kirata ba,kuma takirashi akashe,mirmishi kawu yayi yana fadin"Kiyi hakuri Suwaiba komai zai Wuce,ninaje wajenshi har cikin barikin na sameshi,kwance baida lafiya abokinsa na kula dashi,ammh yaji Sauki sosai,yace aiki ne yayi musu yawa,tunda Sojojin hadin gwiwan da"a ke sa ran zuwansu gobe ko jibi su zasu bi Tawagar Cheif Army of Staff,suje Abuja su Taho dasu nan barikinsu Tunda kinga babban bariki ne,mai wakiltan Arewacinmu na Nageria,shiyasa ,kuma komai fa Ahankali zamu bi Suwaiba Har Allah ya warware komai"Jinjina kai goggo Tayi kafin tace,"Shikenan yaya Allah ya Shigemana gaba.."Da Ameen suka karba kafin Kawu yace"Suwaiba kiramin Azeeman nayi mgana da ita.."Tashi goggo tayi tashiga ciki takira Azeema wacce ke zaune ta zabga Tagumi,koda Tafito sanye da dogon hijabinta kasa ta durkushe tana kara gaishesu domin sun gaisa sanda sukazo,hakuri ya Shiga bata tare dayimata nasiha mai Shiga jiki,Tare kuma da Umartanta datayi hakuri tadauka wannan Jarabtane daga Allah,gyada kai Azeema ketayi tana Tsiyayan Hawaye,Ummah dake kusa da ita,tajata kan jikinta tana lallashinta kawu ya kalli Goggo yace"Suwaiba mganar jarabawarta zan baki kudi Ranar monday Ki dauketa kuje tare,kiyimata Rigistration Din,Allah ya Rufamana Asiri yakuma bada sa"a.."Da Ameen goggo ta karba tamai godiya,Itama Azeema tashiga mai godiya,yana girgiza kai baice komai ba.

Basu Tafi Aranar ba ,sai washegari da safe suka koma,bayan ya cika goggo da kudi da kayan Nau"in Abinci kala kala,Mallam lawal ma yasamu nashi kason,don daya dawo daga kasuwa yaShigo nan suka hade da kawu,suka Shiga hirar yaushe gamo,Tare sukaci abinci sai wajen goma ya Shiga gida,Aljihunsa cikeda kudin da kawu ya bashi,koda inna Ramatu Tafara Tsiyarta yana gayamata inda ya tsaya da kudin da kawu yabashi harda kayan abinci,washe baki Inna Ramatu tayi tana Murnan sun samu kudi,domin dama idonta fa Anaira yake,Dubu biyu yabata harda dari biyar,sai kaji baki ya mutu ta kalmashe kafa tana mai Hira harda Cemai in Azeema zata koma zata bita taga dakinta,jinta kawai yake yana jinjina son Abun Duniya irin na Ramatu sam bata iya boye kwadayinta.

Ranar monday Tun karfe 8:00am tayi masu goggo a office din principal din mkrantar su Azeema,koda tafadi Abunda ke tafe dasu,Har an bude Littafi za"a Rubuta sunan Azeema,aka Tambayi Sunan dalibar, Azeema tace"Azeema lawal bature.."Cike da mamaki principal ke kallonsu kafin yace"Ai Yayanta yakirani awaya mun gama mgana dashi,haryama Turo da kudin Rigistratin din na both WAEC AND NECO,gashi ma Monday mai zuwa zasu Fara WAEC,gama Time dinta.."Yafada yana zaro wata paper agefensa ya mikama Azeema,Tasa hannu biyu ta karba,Mirmishi goggo tayi kafin tace"Ayyah dana ne,munyi mgana dashi,toh nazata baisamu lokaci bane,dayake yana chan kaduna yana aiki ne,kasan Soja ne.."principal din ya gyada kai yana Fadin"Allah sarki.."Kafin ya gimtse Fuska kadama goggo taga damar kara wata mgana,dariya takusa kama Azeema,da hanzari ta riko goggo suka Fice tana fadin"Tanque Sir..."Goggo ko ajikinta tana tafe tana sakama gadanga albarka harda Fadin da tanajin Haushinsa ammh yanzu ya wankemata Ranta Fes ta yafemai,Azeema ta hadu da yan class dinsu suka tsaya suka gaisa,cikin kulawa wasu kuma sunata mata murnan Aurenta duk da bata gayyacesu ba,goggo ce ke karbewa da cewa",Ai Abun ne yazo a kurarran lokaci,..."Dahaka take kashe bakinsu basu bar mkranta ba,sai wajen goma,sai da suka biya kasuwa goggo ta siyo ogun da alayyahu,wai yau miyar ogun takejin ci,itako Azeema Goriba ta siya da uban yawa,har goggo na mata Fadan yayi yawa,kada fa hakoranta su Mauje Saboda cin Goriba,dariya kawai tayimata kafin suhau Adaidaita su koma gida,Ranar Azeema Wuni tayi cin goriba,sai danwake wanda goggo tayimata,itadai Tuwon Shinkafa tayi da miyar ogun dinta,Azeema ko warinshi bataso sai dai ta shige daki tana Toshe hanci,goggo na dariya tace"Topha Shikuma wannan Audin da Tsirfar dayazo kenan,aiko sai da yayi hakuri don Tuwon kwana uku nayi wlh.."😹

   ••°°••°°••°°••°°••°°••°°

_Nnmadi Azikiwe International Airpor Abuja_

   "Misalin karfe 5:30pm na Ranar Laraba,Jirgin gwannati wanda ke dauke da Sojojin Cameron,chadi,da Niger ya yada zango a babban Filin jirgin Na Nmandi Azikiwe dake Abuja,acikin masu Tarbansu akawai mataimakin Shugaban kasa *PROF. YEMI ASINBANJO..*sai Shugaban Army Of Staff na Nageria gabadaya Wato *LT.GEN.Y.T BURATAI..*,tare dashi akwai *BRIG.GEN. S.U KUKA SHEKA..* Bayansu akwai wasu manyan Sojiji daga Tawaga Tawaga ciki harda Manyan Sojijin da kananun dake *I DIVISION NAGERIA ARMY KADUNA..*Domin suke da alhakin jagorantansu zuwa Kaduna chan barikin,acikin wadannan Sojojin akwai Irin su Captain Jabir da Captain Aliyu Tambari buzu,wanda kowa yasan kwarewarsu wajen aiki da kawoma kasa cigaba,cikin bakin Sojojin da suka sauka harda *LIEUTENANT UMAR ABDULNASEER TAMBARI BUZU..*yarima mai jiran gado.,daganan Filin jirgin sai da suka isa Fadar Shugaban kasa Wato villa, mai Girma Shugaban kasanmu *GEN. MUHAMMADU BUHARI* yayi musu jawaban barka da zuwa tare da mika godiya sosai zuwa garesu mussaman ma Shugabanninsu daga kowani yanki,an Shirya liyafar ban girma acikin Villah fa,wlh anja kaya sosai ba karya anyi Shaye shaye na lemuka kala kala,abinci kuwa anyi yafi na kala dari,kundai san Villa babbar waje ne,so dole ayi babbar Harka,yan TEAM AZEEMA GADANGA Kuwa da suka biyoni Tuni Security suka hanasu Shiga nima din dakyar na samu rabawa,Allah sarki suna waje suna raba ido 😂😹😛Srry in zamu Masarautar Tambari buzu a sakaya ku😂Nan suka kwana sai washagari Suka sake hawo wani jirgin zuwa Kaduna.

 
__________________

    inda suka Faka motarsu wanchan karon,wannan ma anan suka ijiyeta,wato gaba da gidan goggo da kadan,Sun Fito daga motar suna waige waige neman wanda zasu Tambaya don lokacin wajen sha biyun Rana ne,babu kowa alayin,sai ga wani dan yaro wanda bazai Wuce shekara goma ba,da kayan mkranta ajikinsa da alama dai daga mkranta yataso,harya gota su Muneera tayi Saurin kiransa.

"Kai yaro zo nan.."Waigowa yayi kamar bazai zo ba,ganinsu yan gayu sai kuma yaje,ammh sai ya tsaya daga baya baya,mirmishi Muneera tayi kafin ta bude Yar karamar jakar dake hannunta ta zaro Naira dari tamikamai Tana fadin"Karbi dama tambayarka zamuyi.."Da hanzari ya karba yana washe baki,muneera tace"Gidansu wata yar budurwa mai Suna Azeeza,zaka ganta wata mai kiba Fara,idonta asama.."Shuru yaron yayi kafin yace"La Anty Azeeza kanwar Adda Azeema wacce ta auri yaya sojan nan gidan.? yafada yana nuna gidan goggo da hannu,Faduwar gaba ya ziyarci Ni"ima da Muneera atare,Suka kalli juna kafin su kalli yaron Muneera tace"Au dama yayartace ta Auri sojan nan gidan? yaron ko yawashe baki yana fadin"Eh mana gama gidansu Anty Azeezar nan,innansu kawar innanmu ce fa.."Zaro ido muneera tayi kafin tace"Toh mun gode jeka.."

  yako zura aguje yana murnan kudin da suka bashi,Hannu muneera ta saka bisa kugunta tana Fadin"Sweetheart anya ba gadar zare yarinyarchan ta Shiryamana ba,kiji fa ance yar uwartace ta Auri captain fa,? ni zuciyata na bani wani Abu dabam..'ajiyar zuciya Ni"ima ta sauke kafin tace"Nima Abunda ya Dauremin kai kenan,ammh karmu yanke hukunci mu Shiga gidan mugani,ammh da mamaki ace in har yar"uwantane kuma taso ganin bayan Aurenta.."Muneera batayi mgana ba,tayi gaba Ni"ima tabiyo bayanta suka Rafka sallama acikin gidansu Azeeza,wanda suka samu inna Ramatu tana Tsakar gida tana gyaran Shinkafa suka Shigo koda ta amsan sallaman tadago tana kallonsu da mamaki don ganinsu yan gayu dasu,mikewa tayi tana musu maraba bakinta duk abude,taga irin Naira,Sannu da zuwa take jera musu Suko suna binta da gidan gabadaya da kallon banza,Tabarma inna Ramatu tashiga daki ta daukomusu Tana kokarin Shimfidamusu Muneera ta dakatar da ita da Fadin.

"No barshi baiwar Allah ba zama yakawomu ba,don Allah mahaifiyar Azeema muke nema matar captain.."Bata Fuska Inna Ramatu tayi ganin Irin yadda suke kallonta tace"Au ita taturo ku kuzo kumin Rashin arziki? kokuwa kunyi batan kaine,ni ba Uwarta bace,uwarta tadade da mutuwa,ni matar ubantace uwar Azeeza,in wajenta kukazo to ku juya ku Shiga wannan gidan na gaba nan take zaune wajen Uwar mara Asalin.."Tafada tana zaro musu ido,Mirmishin Takaichi Muneera tayi kafin tace"Ai dama Azeeza muke nema munyi batan Sunane.."Tafada tana kallon Ni"ima wacce Tun yanzu Nadama suka dirar mata.

Azeeza dake barci adaki sama sama takejin hayaniyar Inna Ramatu,tsaki taja kafin ta Fito daga ita sai wata doguwar Rigar Atamfa bako kallabi,tana hammah da mika atare ta bude labule tana Fadin"Kai inna waike dawa kike Masifa da Rana tsa...."Bata ida mganarta ba idonta ya sauka kansu Ni"ima da Muneera wadanda ke jifanta da wani kallon banza nazakici ubanki din nan.

  Inna Ramatu tace"Nida wadanan yan Rainin arzikin ne,wai da Farko sunce wajen Azeema sukazo,sai da sukaji na balbalesu kana suka dawo sukace wajenki sukazo,kiji fa rainin Hankali ina kika sansu ma.."Tafada Hankalinta kwance,Azeeza wacce ta Razana da ganinsu Ni'ima ammh sai ta boye Razanarta Ta Fito tana fadin"kyalesu inna Wajena sukazo na sansu yan sch dinmu ne.."Inna Ramatu ta washe baki tace"Oho ai sai kuyi bayani,kuyi hakuri fa,ke Azeeza kishiga dasu ciki mana sannunku da zuwa.."Tafada tana mikewa zata kawo musu Ruwa,yake kawai Azeeza tayi kafin takoma daki tana fadin"Ku Shigo.."Ai bata gama Rufe baki ba Muneera ta bankada dakin da Sauri Ni"ima tabi bayanta suka tsaya cirko cirko suna kallon Azeeza wacce ke tsaye tana jifansu da wani kallon uku saura kwata,suna tsaye sai ga inna Ramatu ta Shigo da Jug da Ruwa hade da kofuna ta ijiye tana fadin!ku zauna ga Ruwa kusha.."yake kawai Muneera tamata tana Fadin"Toh...Inna bata kawo komai Aranta ba,ta Fice zuwa waje.

   Muneera ce ta katse kallon da Azeeza ke binsu dashi tana Fadin"ke baiwar Allah nasan kinsan meke Tafe damu ko,and wht all dis ya akayi kika samu aiki,kuma alhalin Azeema matar captain yaya take gareki,and abubuwa dayawa da bamu gane ba plz u need more explanation fa"Tafada da kakkausan murya,Baya Azeeza taja kafin ta tuntsire da dariya harda dukewa Ni"ima ta kalli Muneera idonta na cikowa da hawaye,itama muneera ita ta kallah,kafin ta maida hankalinta kan Azeeza tace"Lafiyanki kika tasamu kinamana dariya..? tafada tana bin jikinsu da kallo,dariyan Azeeza takara kecewa kan ta tsagaita tana fadin"oh don Allah kiyi hakuri,wlh ba Dariyan komai nake ba,sai dariyan gaku ridaridan yan mata,ga kyau ga iya wanka,ga kudi ga ilimi ammh sam kwakwalwarku bata aiki daidai ko nace ta wawaye ne wlh.."Tafada tana Tafa hannu tana cigaba da dariya,Zaro ido sukayi suna mamakin Furucinta Ganin yadda sukayine yasa Azeeza tacigaba da cewa"Yo eh mana banda Wauta da Saunanci daga ganin mutum yace,kayi Abu kaza,kaikuma dayake gabo ne,sai kayi jiki na rawa,koda yake duk acikin son dakikema captain din ne ko,?don naga Tun kwana hudu da mganarmu Aka sako Azeema tadawo gida duk da ba"a Fallasa Abun ba,inaji nace lalle kinyi kuskuren yarda dani,domin wannan Abun dana sakaki kika aikata na saki ne saboda nakara nesanta yaya captain dake,bayan kin kashe auren Azeema kinga na jefi Tsuntsu Biyu da Dutse daya kenan.."Tafada tana daga musu gira,Muneera da Ni"ima sukayi wani slow suna bin Azeeza da kallo yarda karamar yarinya ta iya Wasa da hankalinsu Ni"ima ce bakinta na Rawa tace"Toh sa..saboda mene...?

  Daure Fuska Azeeza tayi kamar ba ita ke dariya ba tace"Ko baku Tambayaba,dama yakamata kuji koda jin bazai muku amfani ba,Yaya captain nawane nikadai,nafi kowa sonshi harda da uwarsa nafita sonshi,Duk duniya bani da wani buri sai na yau na ganni amtsayin matar Yaya captain,nasoshi Tun banso mai ake kira soba,Na rayu da Sonshi na girma da Sonshi,kullum mafarkina na Aureshi,sai gashi kwatsam Adda Azeema tafim Shigar Sauri,saboda shi na tsani yar"uwanta naji bana  kaunarta balle nakaunar ganinta da Abun kaunata,Tunda akayi Auren naketa Shiryamata gadar zare,ammh yana Tsallakarta da ita,tadalilin haka ya dauketa daga garin nan ya maidata kaduna,ganin haka yasa na Rasa mafita ammh duk da haka ban hakura ba,kwatsam sai Allah ya jehomin ku,,naganku kuna neman agaji,sai naga kema ai kina son Abunda nakeso ne,nikuma bana barin watama ta rabi yaya captain Shiyasa Na ce ki kashe auren Azeema sabida bani da halin zuwa kaduna,ko kulla wani makirci akanta,nayi hakane kema na gama dake,Bayan ki kullah Abunda kika kullah,daga karshe zan kashe Azeema da hannuna,sai na fadama Goggo cewa kice kikayi sanadiyar mutuwar Auren Azeema bayan nan kuma kika aiko har gida aka kasheta,kinga daga Yaya captain yaji lbri zai makaki kotu a yanke miki hukunci kisa,nikuma yazo ya Aureni ya tattarani mu koma kaduna Duniya Ta budemana Sabuwa..."Tafada harda daga Hannu tana tsallen murna kamar Abun ya tabbata.

Ni"ima da Muneera sunyi matukar shock dajin wannan lbrin,kasa motsi sukayi,Muneera da Ranta ya baci tadaga hannu azuciye zata wanke Azeeza da mari Ni"ima ta damke mata hannu tana girgixamata kai hawaye na kwanroyomata Kallonta Muneera tayi kafin  tace"Meyasa kika hanani? kibarni na Sauyama jaka kamanni,Tunda ta iya sakamu muka aikata Abunda ba Halinmu bane.."Danne kukanta Ni",ima tayi Tana fadin"Barta barta Sweetheart bakiji metace ba,zata kashe yar"uwarta da suke uba daya saboda Captain,to mu suwaye da bazata iya kullah mana Sharrin dayafi wannan ba,kyaleta kizo mutafi insha Allahu Allah bazai barta ba.."Tafada tana jan hannun Muneera wacce ke hararan Azeeza,itako Tana musu dariya kamar taga mahaukata,inna Na madafa taga hucewarsu Ni"ima da hanzari,tana musu mgana, ma ko kallonta ba wanda yayi,baki ta rike kafin ta cigaba da aikinta aranta tana fadin"Azeeza duk kawayenta irin tane.."itako suna Fita tafada gado tana murna harda tsalle.

Amota haka Ni"ima ke kuka Wurjajan Tana fadin"Mun bani Sweetheart yanzu ya zamuyi da hakkin marainiyar Allah,wlh nayi Nadama,shedan ne ya zugani da kuma soyayyar Soja wlh.."muneera na driving Tana fadin"Ai komai ya Faru keki kaja,banyi Gardama ba,ammh kika nuna amincewarki game da yarinyar,nidama Tunda naga idon yarinyarnan Atsaye Nasan za"a rina Shegiya zuciyarta kamar ta kafaran Farko.."Tafada tana cije baki,dafe kai Ni'ima tayi tana kuka,kafin tayi zaraf ta dauki wayarta dake kan motar tana fadin"Kafin tafadama Captain Abunda Ta shirya nidakaina zan sanar dashi gaskiyan Abunda ya Faru  Sweetheart shine mafitanmu yanzu.."Tafada tana danna wayar,Fizge wayar Muneera tayi tana Fadin"Ke kina da Hankali kuwa,yaushema zai Saurareki balle harya gane Abunda kike nufi,kwabe waje kawai zakiyi kibari mukoma gida sai musan Abunyi kinji ko.."Gyada kai Ni"ima tayi tana kara Damke kanta kamar wacce akace Uwarta ta Rasu.

*****************

*1 DIVISION NAGERIA AMRY KADUNA*

An Sauke Baki abbban sashen dayake cikin barikin,sakamakon al'amarin dayafaru da Captain Aliyu,Toh daga lokacin baida Sakin jiki,ko achan Abuja ma,yana baya baya ne,ko achan villa gefe yakoma shiyasa baima Shiga cikin bakin Sojojin ba,kamar yadda wasu sukayi,Shiyasa Jabir shima duk bai saki jiki ba,ganin Abokinsa kuma Amininsa haka,Yayi alqawarin bazai kara Tambayanshi ba,shiyasa yamai Shuru sai dai baya barinshi yazauna Shuru zai zo ya zauna yana jansa da Hira koda bazai Tankanshi ba.

Shiko Yarima Umar Tunda suka sauka Abuja yake video call da gida yana nuna musu Yadda Nageria take da kyau da Tsari,gabadaya iyalan mai maimartaba zakaga an Taru ana mgana da Umar,har Zuwanshi Villa ma haka,kannensa,Safaratu da Zafira sune yan kwakwan Nageria suna makale da yawa bini bini kadan su kira suna  fadin"yaya yarima muyi Video call muga a inda kake yanzu,shiko jiki na bari zai kira,har saukansu barikinsu Aliyu ma Da sukaga kyan wajen,harta maimartaba ba"a barshi abaya ba,dashi ake kallo,shiko yana mgana dasu yana Nuna musu Wajewaje,duk da bai yarda yayi nisa ba acikin barikin don baisan ko"ina ba.

*After 1 day*

Bayan kwana daya da isowarsu Yarima Umar,Da yammah da misalin karfe biyar na yammah Aliyu ya shiga gidan Jabir yace yazo ya rakashi cikin gari gidan kawu,zaije su gaisa sun kwana biyu basu hadu ba,baiyi gardama ya Shirya cikin irin Shigar Aliyun na Riga da wando White and blue,na kamfanin Armani,Suka Fito Ras dasu,amotar Jabir aka Fita,shiyasa shike Driving din motar,Har suka isa gidan kawu bala,Basu waji jima ba,don sun samu kawu agida,Tunda Abun yafaru sai Yau yataka kafarsa zuwa gidan,kuma kawu bai mai mgana ba,sai dai yayimai Nasiha tare da jirwaye,akan yadinga binciken Abu kafin ya zartar da Hukunci,zasu Tafi Ummah ta matsa sai sun Tsaya sunyi Dinner,sai da sukaci suka koshi kana suka baro gidan,ta wajejen Anguwar Rimi din nan,sun kawo kenan sai Danja ta tsaidasu sun tsaya,kamar ance ya waiga gefensa yaga wani Namiji bisa mashin yasaka hulan kwano dayake motar Tinted ne,ba"a ganin na ciki,har zai kauda kai,kawai sai yaga ya cire hular kwanon,kara kallonsa yayi yana Tuna Fuskarsa wanda ko Barci yakeyi Tana mai gizo Tsabar yadda ya haddaceta ido yazaro yana Fadin"Shine..."Da hanzari Jabir ya kallesa yana fadin"Shine wa? shima yana bin gayen da kallo,ganin danja ta saki ne,har yamaida hulan kwanan yafara Tafiya cikin hargitsi yace"Plz Jabir Follow dis bike...."Yafada da karfi yana nunamai Shi,da hanzari Jabir ya bi Mashin din wanda yakara gangarawa cikin anguwan Rimi Da gudu,shima da gudun yatakemai baya.



*Comment and Share...*
#Janafty..#
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏


        *Chapter 28*

     Aliyu da kanshi ya dauki Azeema da hannunsa ya sakata acikin mota goggo ta Shiga baya,jabir na Driving,su Muneera ma Motarsu, suka Shiga suka Mara musu baya,Mallam lawal Bai bisu ba,yadai bisu da addu"ar Fatan samun lafiya,general Hopital suka kaita,suna zuwa aka

Please Login or Register in order to submit comment