Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

karbeta da gaggawa,likitan yana ganin yadda take yafara Sakamata drip tare da wasu Allurai,domin yace ba Suma tayi ba,jikinta ne babu karfi sam,Jininta aka diba First,aka tafi dashi lab,domin gwadawa,itakuma Dama Ruwan daya samata saboda yataimakamata wajen samun karfin jikinta.

  Gwajin Farko ya Tabbata da Samun ciki Azeema na Tsawon Sati Takwas koda Resuilt din ya Fito Gadanga aka Damkawa murna kamar bakinshi zai zage,Rumgume jabir yayi yana godiya ga Allah,goggo ko mirmishi take na Farinciki,domin dama Tuni Ta Fahimci ciki ne da Azeemar,itako Azeema batasan wainar Da ake toyaba,tana kwance duk jikinta ba karfi,bata dade ba ta Farka tana Fadin"Goggo Ruwa..." da hanzari Goggo ta bata Ruwa,kafin ta taimakamata tatashi Tana tashi idonta na kan Aliyu wanda yakafeta da ido,yana kallonta lokaci daya da mirmishi bisa Fuskarsa,kauda kai tayi tana amsa Sannun da Ni"ima da Munnera suke mata,amsa musu tayi da kai,tana Kara kallonsu,ita Ni"imar nema ke bata Tsausayi,jabir ne yayimata sannu takarba dakai,Aliyu dayake tsaye chan gefe sai ya matso kusa da ita yana fadin"pretty ya jikin?Kura masa ido tayi tana Tuna sanda yayi Shuri da ita,Runtse ido tayi hawaye na kwararomata,kauda kai tayi tana cije bakinta,ganin haka yasa goggo ta Girgiza kai ta saka kai Ta fice,Jabir ma yabi bayanta Ni"ima ce ta karisa gaban Gadon Azeema tace"Zamu Tafi Azeema,Allah ya baki lafiya.."

     "Gyada kai tayi kafin tace"ngd..."Dakyar cikin muryan ciwo,kallon Aliyu tayi kafin tace"Captain zamu Tafi,ina Fata dai An yafemana kuran damuka aikata.."Tafada idonta na cikowa da kwallah,Mirmishi yayi yana kallonta kafin yace"Bakomai Ni"ima buh next time Kada hakan takara Faruwa ko ba akaina ba,ku koyi yaki da zuciyarku don Allah..."

gyada kai tayi kafin ta Share kwallah Tana Fadin"Insha Allahu hakan bazata kara Faruwa ba.."Gyada mata kai yayi yana Fadin"Toh Yayi kyau naji dadin haka,share hawayenki kibar kuka hakanan,komai ya wuce.."Mirmishi tayi batayi mgana ba,sai ta waiga tana kallon Azeema wacce ta Runtse ido ammh kaf Abunda suke Fada akunnanta ne,Dafata tayi tana fadin"Congratulatino Sisto Allah ya inganta.."Daga haka tajuya,muneera dake tsaye itama tayi Fatan samun lafiya kafin su Fice,awaje sukayima su goggo sallama,suka Tafi suna jin zuciyarsu tayi sanyi Tunda komai ya Wuce yanzu.

   Suna Fita ya karisa gareta lokaci daya yana harde hannuwansa bisa kirjinsa kallonta yake dakyau yadda Fuskarta tayi Fayau tabashi Sha"awa,Sunanta yakira ahankali.."Pretty..." Tana jinsa tayi mishi banza harda dan nishinta alamar barci takeyi,yana kallonta yar dariya ta kamashi,sai ya saka hannu ya dan,matse hannun Da aka sanyamata Drip,taji zafi da hanzari tajaye hannunta tana Fadin"Wash.."tafada tana Jaye hannunta bata bude ido ba,ta mirgudamai baki,dariya ta kamashi sai ya Rankwafa yana lakucemata hanci yake Fadin"Matar Sunnah bata Fushi da mijinta,kuma in yayimata laifi yakamata ta Sausautamai,koyasamu damar bada hakuri..",tana jinsa tayi mishi banza,sai ma juyamai baya datayi,Kai ya dafe yana Saka hannu abaki,kafin ya Sauke ajiyar zuciya yace"Shikenan ki Adanamin duka Fushinki pretty har na dawo,nayi alqawarin daukan kowani mataki kika Dauka akaina,ammh i want to u to know one Thing i relly miss u so much,and kinbiyani Tunda kikayi Saurin Cafkan sako na,Adaren Farkomu,Allah ya saukeki lafiya.."Yafada kafin ya duka ya bata kissa Ahannunta,ya saka kai Yafice yana mai jin Farinciki,Sai da ta tabbarta da yafita kana ta bude ido tana Dafe kirji tace"Ina da cikin yaya captain yanzu a wannan cikin? tafada Tana dafa cikinta lokaci daya tana Sakin mirmishin Farinciki,hawaye suna zubomata ta sanya hannu ta Share Tana fadin",Allah na godemaka..Ni nan da wata Tara nazama mama"Tafada kafin ta saka dariya ita kadai,shafa cikin take tana mirmishi ita kadai,kafin chan kuma ta Tura baki tana fadin"Ina Sonka,ammh ina Fushi da babanka,duk da kewarsa da Soyyyarsa bazata taba barina Fushina yayi Tasiri Akanshi,Alhamdulillah Allah nagodema.."take Fada tana mirmishi ita kadai.

Shiko Aliyu achan waje,har kasa ya dukama goggo kafin ma yayi mgana tayi Saurin dagoshi tana fadin"Tashi gadanga,Har Abada goggon gadanga bazata yi Fushi dakai ba,konayi baya zuwa ko"ina na yafema Tunranar da naje mkrantansu Azeema Shugaban mkrantar ke Fadamin kagama biyanmta komai,Tun wajen nace na yafema nayita sakamaka albarka,duk da dai Ja"irin ka batamin Rai ammh kadan.."Tafada tana mangaremai kai,dariya yayi kafin ya Fada jikinta ya Rumgumeta yana Fadin"Nayi kewarki goggo.."Kunnensa ta murda tana Fadin"Karya kayi dai kewar matarka ko? ammh bani ba.."Dagowa yayi yana kallonta Kafin ya Shagwabe yana Fadin"Ni Allah goggona nayi kewa.."Dariya tana fadin"Toh naji Nima nayi kewar gadanga ko Tsiyar damuke ankwana biyu ba"a hadu ba..",Dariya suka saka gabadaya kafin Gadanga yace"Goggo zamu koma bakin aiki.."Jinjina kai Goggo tayi kafin tace"Basai kamin bayani ba,yanzu Jabir yagamamin bayanin komai Kuje Allah ya Tsare yakuma bada Sa"a Azeema kuma zan kular maka da ita har kadawo nayi alqawari.."Da Ameen suka amsata mata kafin Suyi mata sallama Su Tafi,daganan Asibitin hanyar gombe suka dauka,dama tawagar da sukazo Tare Tun Sadda zasu kai Azeema Asibiti suka basu Umarnin juyawa gombe,toh Tuni sun damki hanya kilama Sun isa Tundazu.

  Koda goggo takoma wajen Azeema tayi barci lokaci,tatasata tayi tana ta zuba godiya Ga Allah,har saida Tafitar da kwallah,Allah sarki Gadanga,shifa Tunda yatashi baisan dadin wani Dan"uwa ba,sai Hisham,wanda kusan yanayin aikin banki da Tsanani da Takura gashi ba sakewa so basu cika haduwa ba,sai dai awaya,haduwarsa da Jabir yasa yasamu aboki sosai,gashi Allah ya ba matarsa Ciki tana Fatan cikin ya zamanto Silar Farincikin gadanga dasu gabadaya.

Kwanan Azeema daya aka sallamota ta dawo gida,bayan an kafamata dokan banda aiki mai yawa,ba daukan Abu mai nauyi,kuma anbata mgungunar Kara jini,dana saka cin abinci don goggo tace bataci,sai cika ciki da goriba,ba"a hanata cin kayan kwalamanta ba,ammh ance ta dinga cin Abinci sosai,tadai Samu ishasshen Hutu da Lokaci mai Tsawo,goggo ko duk taji bayanan likita Shiyasa suna komawa gida ta zage tayimata Tuwon Semo miyar Kubewa dayan,wacce aka daka kifi aciki,duk da bataci dayawa ba,ammh taci sosai,daddaren Mallam lawal ya Shigo duba Azeema yadade yana mata nasiha hakuri da rayuwa,tare da mata gargadin ta rike mijinta da Amana,nan yake Fadamusu Inna Ramatu tun jiya take kuka da Hajijiya tana Rokon don Allah asakomata Azeeza tatuba tabi Allah,yacema bayan Tafiyarsu saiga Baba Ade tazo,har yara Sun kaimata lbrin Abunda yafaru tazo da kukanta ni nayita bata baki,gyara zama goggo tayi tana fadin"Allah sarki ai tabar kuka,don ta kusa samun megida ko Amarya kai kuma Mallam ka Shiryafa jika na zuwa.."Washe baki yayi yana saka albarka yana kallon Azeema,itako Rufe Fuska tayi Duk kunya ya kamata,Mallam lawal yayi murna Sosai yayita Addu"ar Fatan Allah ya Raba lafiya.


__________________

_Kaduna_

  Yau kimanin kwana hudu kenan da zuwansu barikin baitaba yin nesa daga Sansaninsu ba,iyakarsa Dan haraban wajen,sai jiya kuma da Sukaje bayan bariki sukayi Atisayen Harbi,yau Tunda yatashi yakejin sha"awar zagaye barikin nan duka duk da baisan ko"ina ba yasan baya bata ba,cikin Kakinsu na chan ya Fito yafara Tafiya duk inda yabi yana Daukan Hoto ko video din wajen da Rantsatsiyar Wayarsa kirar Samsumg,Duk inda ya Shiga sai Binsa ake da kallo Abunda yabashi mamaki Wasu Sojojin jahar ta Nageria har kamemai Sukeyi Saboda Su bihakki da gaskiya Dauka Suke Captain Aliyu ne,duk da kuma da bambamcin Uniform din da Suka gani,Abun ya Daureshi mishi kai,sai yakoma daya Hadu dasu yaga sun Kamemai Sun Saramai,kawai sai ya Daukesu Selfe ya wuce yana dariya,suko suyi ta mamaki don Asaninsu Captain Aliyu baya dariya Sai dai mirmishi ko kaga yadan murmusa kumatu kadan.

Yana Tafe yabada baya yana Daukan wani lafiyayyan Titin daya Shararo,wajen ya burgeshi yadda kasan ba"a Nageria ba,kamar akasar Turai saboda Haduwansa gashi so quit,ga wasu Fulawoyi dasuka kawata wajen,sojojin dasuke wucewa kadan kadan ne,sakamakon Lokacin da Safe ne sosai ba'a Fito Training ba.

Jiyayi ya bangaji Mutum harsaida wayar dake hannun Wanda sukayi karo da Umar din,tafadi kasa da hanzari Umar ya sanya wayarsa a aljihu ya duka ya Tattaroma mutumin wayarsa wacce ta watse yana fadin"Am so Srry did know u are coming Srry...",Yafada yana dagowa karaf ko suka hada ido da Jabir wanda ke Tsaye yana karemai kallo sama da kasa kafin ya zaro ido yana Rike baki yace"Kambu Dude,basaja kakoma kuma,yau Abun naka harda komawa Sojan Niger.."Yafada yana Dariya galala Umar yayi rike da waya yana kallonsa bakinsa na motsi yace"ni..Ni..Bansan meka ke mgana akai ba fa? Kafadansa Jabir ya daka da karfi yana fadin"Kai Dude dawo hayyacinka kasan dai ni bazakamin layan zana bako?any why yau fa kasan akwai Atisayen gudu ina kuma zaka naganga ta nan? Umar ya lumshe ido kafin ya bude,baiyi mgana ya Rike hannun Jabir ya damkamsa wayarsa yana fadin"Ba wanda Kake Tunani bane,Ni Sunana Leuitenant Umar Abdulnaseer Tambari buzu ina daga cikin bakin Sojojin da suka sauka Shekaranjiya.."Kuramsa ido Jabir yayi kafin ya warci wayarsa yana Fadin'Kajimin dan iska,Umar kuma kakoma? Toh in bakai bane waye,Nikaga Tafiyata mallam,dama kai baka Rabo da Maida mutane yan iska..",Yana Fadin haka ya juya ya cigaba da Tafiya ko waigowa baiyi ba,Galala sake da baki Umar ke binsa da kallo kafin ya rike baki yana Gyada kai,mamaki yakamashi,ammh sai bai ba Mamakin matsungunni ba,juyawa yayi yakoma,ammh kuma Abunda yafaru ya tsayamai Aranshi.

  Jabir da hanzari yakoma barayinsu yana zuwa kofar Apartment din Aliyu ya ganshi ya Fito sanye da kayan gudu,cogewa yayi agabansa yana kallonsa Abun ya bashi mamaki,toh wannan Aljanine,yanzu fa ya ganshi Aliyu dake tsaye yaga yadda Jabir ke kallonsa Tsaki yaja yana Fadin"Kai fa dan iskane lafiya kawani kuramin ido,bafa wannan kwailar budurwantaka bace"Yafada yana hade rai,Hararansa Jabir yayi kafin yace"Durun uwar kwailar,Ai kwaila bata Wuce Azeema ba.."Dirowa Aliyu daga saman Apartment dinshi ya Naushi Jabir agefen ciki kafin yayi gefe yana fadin"Ai Azeema Ta wuce kwaila Tunda ta iya daukan Nauyi na,har gashi tana Dauke da ciikina,kuma wannan ne last time dazaka kara kiran Sunan matata gatseai ba sakayawa,Tunda ba sa"arka bace.."Jabir dake duke yana rike da gefen cikinshi ya dago yana Fadin"Allah ya isar min mugu kawai,don kaga kai ka fara kokarin ijiye kwanka aduniya Shine ni zakamin mugunta Rasa nawa,ta Allah bata mutum ba.."dariya Aliyu ya saka mai kayatarwa yana Fadin",Au kudai zauna yanzu nagama yima gayen nan Hisham,nace ya zauna aikin banki ya daskararmai da kwan haihuwa,ko kuwa zama waje daya da Wuni cikin Ac,ya Lusarar dashi,sai bayan anyi Aure aji mata ta gudu taga ba bayani"Dashi da Jabir din suka saka dariya atare harda Tafawa Jabir yace"Kai Dude kasan kan Tsiya fa"Yafada yana Fada kadafadansa kafin yace'Kai Dude Seroious Fa,kana aiki da Aljanune,yanzu fa naganka sanye da kakin Sojin Niger,yanzu kuma na ganka da kakin Sojan Nageria kuma banga sanda kadawo harka chanza kaya ba,wai kodai layan zana gareka.."Kallonsa Aliyu yayi yana Fadin"Tsiyana dakai kwakwalwarka bataja,Ni da yanzu Fitowata kenan,kuma banda Abunka meya hadani da Sojojin Niger da har zan sanya kakinsu,..? Rantsuwa Jabir ya jero yana Fadin"Wlh da gaske,wai bakai bane Harfa kacemin Sunanka Umar Abdulnaseer Tambari buzu fa? Har Aliyu ya juya Yafara Tafiya jin sunan da Jabir ya ambata sai dayaji yanayin jikinsa ya chanza,waigowa yayi yana fadin"Ni kuma? kai mallam kafara Rudu wlh,bani bane kaji na Rantse maka ma,yanzu dai duk ba wannan ba kashiryo kazo muje Atisayen gudu da za"a gudanar yau.."Yana gama Fadin haka yayi gaba da dan gudunsa.

Tsaye Jabir yayi yana mamakin wannan al"amarin Hannunsa bisa baki yana fadin"Bashi bane to waye? yafada yana kada hannu Alamar Abun yabashi mamaki,tsaki yaja kafin yace"Mtsewww shege shine fa,so yake yayi Wasa da Tunanina"Fadin haka yasa ya juya yashiga part dinshi da gudu domin Shiryawa domin Atisayen na yau na musamman ne,domin Duka Shuwagabannin kowani bangare zasu Koyar da Atisayen na yau,duk acikin salon Dabarun yakin daza"a koya musu ne, na Tsawon Sati daya duk da su sun dade da kwarewa game da Aikin,ammh dalinlin bakin Sojojin dakuma Turasun da gwannatin Nageria zatayi zuwa wajejen da yan boko haram suka mamaye.



*JANAFTY*😘
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

           

           *Chapter 29*

    ""Har aka gama Atisayen gudun Gadanga da Umar basu hadu ba,sakamakon Filin ya cika da Sojojin Nageria,dana cameron Chadi,da Niger,kuma akallah kowacce tawaga zata kai kimanin Mutane Dari uku,shiyasa ba wanda yahadu da wani acikinsu tunda ba"a Batch daya suke ba,Jabir ko shima yayi Dube Dubenshi baiga ga Wanda yagani dazu ba,sai ya barshi atabbas Aliyun yagani ba wani ba,ko awashegari da"aka Sake maimata atisayen Allah bai hadasu ba,Jabir ya sanya Ranshi kawai Raina masa wayau Aliyu keson yi don yasaba tunda Halinsane,kiri kiri kana Tambayanshi Abu,sai yayi maka banza koda yasani,ko yashiga Raina maka hankali.

*Bayan kwana biyu*

_Gombe_

  Yau Azeema Tafara Jarabawarta ta WAEC sun Fara da Pratical Chemistry,karfe biyu sukaje suka dawo biyar,koda tadawo duk ta gaji,goggo nata yimata sannu,kan kujera ta Jabe tana cije baki,yanzu bata wani karfin jiki tafiya kadan takeyi taji tagaji Tafara haki,taji Sauki sosai karfin jikin ma babu laifi tasamu mganar abinci ma tanaci shima,duk da ba sosai ba,cin goribane sai Abunda yayi gaba kuma don ba raguwa yayi ba.

   Sai dai Abu daya dake damunta Shine Tunda suka dawo asibitin Kewa tare da Son kasancewa da mijinta ke damunta Wani lokacin rasa inda zata saka kanta take,sai dai ta Shige daki tayi ta kuka,tana Jin haushin kanta na yarda ko ada batayi wannan Jarabar ba sai yanzu,kullum dakyar take barci saboda muradi da son kasancewa da Yaya captain ammh Abu yaci Tura,gashi kullum Abun baya raguwa saima gaba gaba yake,haka in Abun ya ciyota zata saci wayar goggo ta Shige Tiolet talalubo Nombar Yaya captain takira,sai Tafara ringing watarana ma harya dauka sai tayi Saurin takashe tana jin haushi datakaicin kanta,yanzu in yadaga sai tacemai miye? Tace yazo tana cikin Tsaninin bukatarsa? haba aiko ba abunda yahadasu bazata iya ba,balle dama Tana Fushi dashi,datayi wannan Tunanin sai tayi Saurin Fitowa tana Share kwallah tayi hanzarin Ijiyema goggo waya a inda ta ijiye,shiko yana ganin kiran goggo,in yana busy ne xai bari daya samu sarara zai kirata,da goggo ta dauka bayan sungaisa sai yace"Goggo naga kiranki,Allah sa bawani laifi nayi ba.."Goggo da mamaki zatace"Kirana kuma? anya bani bace sai dai ko in Azeema ce",Mamaki ya cikasa kullum aka kirasa da nombar goggo daya kira goggo zatace ba itabace to waye"?Azeema ce? Daya Fahimci haka dayagani, zai yanke sai yayi Saurin kira,ammh har takarishi ringing bata dagawa,wani lokacin in yayi sa"a tadauka,ammh mganar Duniya zai mata taki cewa ko Uffan,yarasa meke damun Azeemar,koda ya tambayi goggo sai cemai tayi lafiyanta kalau babu Abunda ke damunta,bai yarda ba,yadai bar mganar ne,zai yi kokarin zuwa koda a asati na sama ne.

Ko yanzu ma datake cije bakin,Abunda ke damunta kenan,Tun amkranta Abun ya isheta,dakyar ta dawo ita wlh tama Rasa wannan Jaraba,ace wai tana Bukatar Namiji Abun kamar wani Asiri,goggo data Shiga kichen ta daukomata Ruwa tazo ta isketa tana yamutsa Fuska tana wani mele baki,kallonta goggo tayi kafin tace"Wai duk gajiyan ne? kwanciya tayi kan kujeran tana Fadin",Eh goggo kaina ke ciwo..'"Tayi karya ijiye Ruwan goggo tayi tana Fadin"Ash sannu,bari na kawo miki panadol bayan kinci abinci sai kisha,sai fa ahankali yanzu keda barin laulayin nan sai ciki yayi kwari,Allah ma ya Soki bakya Miyau da Amai.."Tafada tana komwa kichen,tana Ficewa Azeema taji kuka yazomata ta danne da hannunta bataso goggo tajita ganin kukan yana so yayi karfi,sai tatashi da gudu Ta Shige bedroom ta fada Tiolet kafin ta Fito da kukanta,tarasa wazata Fadama damuwarta,kowani ciwo gareta ne,kodai zata Fadama goggo su koma Asibiti ne? don Tana Tunanin bata da lafiya,ta dade tana kuka kafin ta Tube kaya tayo wanka Ta fito,sai da tafara gabatar da sallar la'asar kafin taci abincin da goggo ta kawo mata Danbun Shinkafa da zogale,yayimata dadi dayake ta bankada yaji,har sai da goggo ta dauke Roban yajin tana Sababi,batasha mganin ba sai da sukayi issha"i kana tasha ta kwanta ammh bawai don tana jin barci ba,cikinta ne juyawa,babu Abunda take bukatar sai lafiyar yaya captain,don Hakurinta yakusa karewa tarasa meya sameta ne,kodai wata Allura akayimata asibitin? gaskiya tanajin da wata kasa😂

Lalle Azeema kina Ruwa😹Toh duk cikin gadanga ne ya jawo haka,ai shi gadanga in yaji lbri Kakarshi tayanke saka😛😂


    •°•°•°••°•°•°•°•°••°•°•••°

   _Babbar headquater yan sanda na garin gombe_

Ababbar Headquater su na nan garin gombe aka kai Azeema aka sakayata,babu fada ba zagi,ba duka sai dai zaman waje daya da Takura,sai kuma Rashin samun barci ga Sauro kamar mutane,ga kudin cizo ga kwarkwata,da suke bin jikin mutane,sai Rashin abinci mai kyau,watarana ma sau daya ake bata Arana,Tun Azeema na ganin Abun Wasa har ya wuce Tunaninta bata yi Nadamar Soyayyar yaya captain datakeyi ba,ammh tafara Nadamar mugun halinta Da Zigan Shedan gareta,domin Tunda aka kawota take Fama da wani ciwon kai mai Tsanani,ga Nauyi da kirjinta keyi,saboda yadda Abubuwa sukayimata yawa,bata da wani aikinyi sai kuka,Tanaji Aranta indai bata samu captain ba,toh sai dai Tarasa rayuwarta don Tun yanzu Tafarajin Alamun Rashin Captain gareta Abu ne da zai iya sawa tarasa rayuwarta.

Haryau da"a kawota aka sakayata bawanda yakara lekota,balle abi ta kanta batama kara ganin kowa ba,sai Wadanda ke kawomata abinci,basu cemata uffan,itama bata ce musu iyakarsu su ijiye Abinci su Rufeta su kara gaba,Abincin ma sai yazamana ba kullum take ci ba,sai dai tatasa Abinci agaba tana tsiyayan hawaye,Tabbas Azeema tafara Nadamar Abunda ta aikata,ammh wannan Soyayyar datakema Captain babu Abunda yaragu saima karuwa.

   ****************

_Kaduna_

Yau dai yawon Umar yakaishi har Wajejen da gidajen su captain suke zaune,hakika wajen ya burgesa balle yadda aka Tsara gidajen ajera komai iri daya babu bambamci,kamar wani Estate,wajen yamatukar burgesa sosai Shiyasa yake ta Daukan Gidajen hoto,Yaji yana kaunar Sojojin Nageria domin Sun Fisu moran Abubuwan yaki da Sauransu,Yau din sanye yake da kayan gida,riga da wando black and white,sai ya sanya bakar jaket kansa babu hula sai Nannadaddan gashinsa daya murde waje daya,kana kallonsa zaka san wannan Buzu ne na gaba da baya.


Ta bayan gidajen ya bullo,shiyasa bai Kawo gidan Aliyu ba,sai da ya wuce na Jabir,gidan Aliyu yana Jerin Farko ne,don Shine No5,yazo ta wajen kenan yana Daukan Hoto,tare da video,tsaye yayi cak yana bin wajen da kallo,lokaci daya yaji yanayin jikinsa ya canza,tsayawa yayi yana waige waige kafin kuma ya dawo ya cigaba da Abunda yakeyi.


Aliyu dayake sanye da kayan Jc Riga da wando ya bude kofa ya Fito,kafarsa sanye cikin wani Farin takalmi,domin duka kayan jikinsa Farare ne,yana Fitowa yaci karo Da Umar ya juya baya yana Daukan Hoto,ta bayanshi Aliyu ke kallonshi ammh sai da gabansa ya Fadi,yayi baya yana laluban wayarsa Jabir ya Turama Text da cewa",_Dude come out..I think na kama wani dan leken Asirinmu_.."

jabir dake kokarin Fitowa Jugging yaga sakon Aliyu da hanzari yakoma daki ya sako karamar bindigarsa ya cogeta abayan wandonsa Ya fito,yana Fitowa yaci karo da Umar,wanda yagama Daukan baya ya juyo ta gaba ta wayarsa yana Dauka karaf ko ta cikin Wayar ya hango Fuskar wani kamar Fuskarshi,mamaki yakamashi sai ya zata ko yamaida Abun Hoton ta gabane,ammh kuma wannan ai ba Kayan jikinsa bane,Kara ware ido yayi yana kallon Aliyu wanda ke Dago kai yana So yaga Fuskar Umar din,Da hanzari Umar ya Jaye wayar Hannunsa Fuskar Aliyu ta bayyyana Azahiri agabansa.

Aliyu dayake leken ganin Fuskar ko waye,Umar na jaye wayar ya Daskare Atsaye yana binsa da kallo daga sama har Kasa,Zuciyarsa na lagude,mai kama dashi yake gani,ammh kuma sanye da wani kaya dabam,Umar ma Kallonsa yake Yana kuma kara Bin kansa da kallo,kamar yadda Aliyu keyi,Jabir Tunda ya Fito idonshi ya Sauka kan Umar,yazata Aliyun ne,yafara Taku zuwa gareshi sai kawai ya hangi Aliyu akofar apartment dinshi,ware ido yayi yana bin kowannensu da kallo bakinsa na Rawa yama kasa mgana,sai ya kafe Aliyu da ido na Tsawon Lokaci sai yakoma ya kafe Umar da ido,nan take ya Fahimci Abokinsa na gaskiya ammh fa sai da ya Sha kallonsu dakyau.

Aliyu da Shiga mamaki yafara daga kafarsa yana takowa zuwa ga Umar,wanda Shima yake takowa zuwa ga Aliyu dukkansu sun kafe juna da ido,kowannen Zuciyarsa na bugawa Jabir dake tsaye gafe sai kawai ya saki baki yana kallonsu sanda suke kusanto juna,bala"i wannan wace irin kamace komai nasu iri dayane hatta da Gashin kansu Wlh hatta Fuskarsu iri dayace babu bambamci,sai dai Shi Umar yafi Aliyu jan Fata sosai,sakamakon Mahaifiyarsa Buzuwa ce,shiko Aliyu ya surka da Fatar goggo shiyasa sai yayi Duhu kadan,Kana Aliyu yafishi Tsawo da murdewar jiki,duk da Shima Umar din ba baya ba.

Da gudu Jabir ya karisa ga Aliyu yana Rikemai hannu yace"Shine Dude wlh Shine...",Da mamaki Aliyu ke kallonsa yana bin kuma inda yake Nunamai da hannu kafin ma yayi mgana Jabir ya rigasa da cewa"Shine nagani Ranar,na zata kaine wlh Shine..."Aliyu bakinshi ma yakasa mgana Illah kurama Umar ido dayayi Shima Umar din agaban Aliyun yaja ya tsaya yana kallonsa kur ko kiftawa bayayi,atare kowannensu yanuna dan'uwansa yana Fadin"Waye kai...? Suka Fada bakinsu na Rawa atare.

Mirmishi kowannensu ya saki ganin sun samu Gamuwar mgana atare,Jabir dake gefe yayi tsalle gefe yana fadin"Wlh Allah Dude har mirmishinku iri dayne,wai kodai Ku yan biyu ne,baka sani ba.."Yafada yana Rike haba Abun fa yabashi mamaki,hannu Aliyu ya saka a aljihu yana Fadin"I don"t Think so Dude ai da goggo ta Fadamin,ammh kuma meyasa nakejin wani Abu game dashi,inajin zuciyata na wani Rawa in ta kalleshi.."Yafada yana kallon Umar din.

Umar yayi ajiyar zuciya yana Fadin"Nima haka nakeji Araina,zuciyata tana gayamin Kai din wani ne agareni,ka taba zuwa Niger ne..?Kallonsa Aliyu yayi yana fadin"Kai daga chan kake? gyada kai Umar yayi yana Fadin"Eh ina daga cikin Sojojin gamayayyar nan,."gyada kai Aliyu yayi kafin yamikama Umar din Hannu yana Fadin"Good ni kuma Sojan Nageria ne,am *CAPTAIN ALIYU ABDULNASEER TAMBARI BUZU* Kaifa..? Umar yaciro hannu da niyar yamikama Aliyun ammh jin Furucinsa na karshe yasa yayi Saurin dauke hannunsa kamar ya razana gabadaya idonsa awaje yana nuna Aliyun.

Jabir da Aliyu suka bisa da kallon mamaki kafin Aliyu yace"Lafiya kuwa...?Bakin Umar na Rawa ya nuna kansa yana Fadin"ni...Ni..Ma Suna...na *UMAR ABDULNASEER TAMBARI BUZU* kuma Tambari buzu masauratarmu ce,mukadai keda wannan Sunan ta masaurata,kuma mahaifina Shine *SARKI ABDULNASEER TAMBARI BUZU MAI MULKAN MASAURATAR TA TAMBARI BUZU WACCE KE YANKIN AGADEZ*...!

gabadaya daga Jabir har Aliyu daskarewa sukayi Aliyu dayaji wani Abu ya wucemai ta makogaro,yayi Saurin Riko kafadun Umar yana Fadin"Da gaske kake yi? yafada kamar yafita hankalinsa Umar ya gyadamai kai,kafin ya samu zarafin mgana Aliyu yace"Mahaifinka yataba zuwa Nageria achan baya,ma"ana katabajin lbri..? Shuru Umar yayi kafin yace"Eh Tabbas Abbah ya Fadamin shima yayi Rayuwa A Nageria,ammuh bazai iya Tuna a ina ya rayuwa ba,balle ya Tuna da Wasu Ahali yayi Rayuwa ammh Tabbas koda zan Taho din nan ya jadaddamin shima yayi Rayuwa A Nageria.."

Aliyu da Wasu hawaye masu dumi da sanyi suka wankemai Fuska,yayi Saurin Rumgume,Umar yana Kuka Muryansa abude yake Fadin"Wlh Dan"uwa ne,dan"uwa ne yau naga wani nawa yau na hadu da jinina,yau nazama kamar kowa yau zanji lbrin mahaifina,wanda banta gani ba Tunda nazo Duniya Allah na godemaka Alhamdulillahi..',Yake Fada yana kuka da duka muryansa yana kara kamkame Umar.

Umar dake tsaye,yaji Shima hawaye sun kawomai,ya kamkame Aliyu shima hawayensa na diga bisa bayansa yake fadin"Hakika zuwana Nageria yana da Babban Sanadi,da kuma sila,ammh babban dalilin Shine,domin na warwarema Abbah mafarkinshi na Shekara da Shekaru,hakika Kana da nasaba da damuwar da maimartaba ke Shiga na mafarkin wata mata da Da'n ta suna halin Neman Taimakonsa da bukatarsu,kaine Wannan Fassarar mafarkin kai ne wlh.."Yake fada yana kuka Shabe shabe,Aliyu yana jin Abunda Umar yace sai wasu hawaye suka kara gudunmai bisa kuncinsa yana Dariya da kuka ya dago yana Fadin"Kai dan"uwa ne yanzu? Ashe zanga wannan Ranar? yafada yana kara kamkame Umar din Shima kam ya rikesa yana Fadin"Ba Dan'uwa kadai gareka ba,kana da kanne da iyayye bayan mahaifa da wasu Ahali masu yawa" Kukan Farinciki Aliyu keyi kamar wanda akace zai Shiga aljannah.

Jabir dake gefe shima Sharen kwallah yake yana dariya,kawai baisan sadda ya saka hannu yana basu Tafi ba Raf raf,Aliyu ya dago yana kallon Jabir,yadda yaga yana hawaye ga Dariya yana yi lokaci daya Hannun ya mika masa yana Fadin"Taho Dude taho,Katayani murna nima yau naji lbrin Ashe nima da,ne kamar kowa ina da uba.."Yafada yana dariya da hanzari Jabir ya isa garesu Aliyu ya hadasu ya Rumgume yana Ta hawayen Farinciko,kafin ya sakeshi ya Riko hannu Umar yana Fadin"Taho muje cikin gida mganganun bana Tsayawa bane.."Yafada duka hakoransa na waje,Rikesa Umar yayi yana Fadin"Toh *YAYA..*...."Wani Farinciki ya lulllube Aliyu wanda baisan sadda ya jawo kafadan Umar ba yana mai mirmishi mai

Please Login or Register in order to submit comment