Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mulki masarautar ansamu chanje chanje masu dimbin yawa,ciki harda rushe masarautar zuwa na ginin zamani mai kayatarwaa,kana dumfaru masarautar gininta da yanayin tsarinta zai burgesa yakuma baka sha"awa,uwa uba yadda take da uban dakarin yaki da masu tsaronta,masaurautace babba mai cike da bayi da wadanda suka jibamceta.

A babban shashen dayafi kowani shashi girma da kyau da tsari Wanda ya kasance shashin Ranka ya dade maigirma sarki kenan,wanda yake kwance akan makeken wani mulmulallan gadonsa mai kyau da tsari,wanda yaji Shimfidu Na alfarma Adalin sarkin ne da kansa kwance yana barci kamar kullum mafarkin daya saba yine yau ma yakeyin irinshi na yau ma yaso ya bambamta dana koda yaushe domin Fuskar matar hartaso ta bayyana garesa sai kuma yayi Firgigit ya farka daga barcinsa nasa yana salati lokaci daya zufa na ketomai kota ko"ina,Gimbiya FASILA ce yau aturakar ta Sarki da hanzari ta mike tana kallonsa kan tace"Ranka ya dade Allah kara lafiya meya faru ne,naga ka mike afirgice kana salati..? tafada tana kunna hasken dakin wanda ya gauraye lokaci daya.

  Kallonta yayi baice komai ba,illah zuro kafafunsa dayayi ya sauka daga kan gadon ya zura wani takalmi mai gashi ya dumfaru wani dan daki da gefe,tabe baki tayi takoma ta kwanta aranta tana mamakin meke damun yallabai ne haka,duk kusan matan nasa ba wacce bata fuskartan wannan mafarkin nasa duk ranar girkinta,in baiyi wannan karon ba,wani zagoyowar zai faru,kuma ko kayi tambayan Duniyan  nam baya kulaki ballatana ya baki amsa,Tana kallonsa ya fito Fuskarsa da farin gashinsa na digan ruwa alamar alwarla ya dauro ko kallonta baiyi ba ya isa ga wani dan korido inda wani shimfidaddan cafet yake mai kyau da tsari gefe daya carbi ne,sai daga baya wani cabinet ne,mai dauke da qur"anai da sauran littafai,bai bata lokaci ba ya cire fararan kafafunsa cikin takalmin na sarauta ya isa ga cafet din ya daidai sahu ya tada sallar,sai da yayi raka"a goma sha uku kana ya sallame ya zauna yana lazimi tare yima Annabi salati,aransa yana fatan Allah ya bayyanasa komai miye yake so ya bayyanass masa cikin mafarki Aransa yanaji kamar wani nauyi ne,da hakkin akansa wanda ya rataya awuyansa shekara da shekaru baya saukewa domin da alamun matar dayake ganinta tana bukatarsa cikin mafarkin kuma Abunda yafi daure masa kai yaron dayake tare da ita,wnda kowani lokaci yaron yana so ya iso garesa ammh kuma nisa da tazaran dake tsakaninsu baya barinsu su iso garesu da zarar kuma haske ya bayyana garesa domin ganin Fuskarta sai ya farka daga mafarkin wanda ya dau tsawon shekaru Ashirin da biyar yanayinshi,dayake shi mutum ne mai riko da addini bai yarda da duba ba,babu abunda yasa akayimai ko masu fassaran mafarkin da Ummansa mai babban daki ta sanya ayimai hanata yayi,yace ta barma Allah koma miye Allah zai yayi duhu cikin haske.

   Yadade yana addu'oinsa kafin ya shafa gabda gabatowar asuba cigaba da zamansa yayi yana kwaroroma Allah kirari yana kiran anyi kiran sallar farko ya nufi masallaci domin duk sanda yayi wannan mafarkin barci kaurace ma idanunsa sukeyi.,Itako gimbiya fasilatu Tuni takoma barcinta ko ajikinta domin inda sabo sun saba da wannan al"amarin yallabai Adalin sarkin mijin nasu



     #Comment,share,vote...#
      #Janafty.....#
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

*DEDICATED DIS PAGE TO U KHADIJA CANDY❤(Mama)😘*

          *Chapter 8*

     """Karfe 3;00pm na yammah motarsu ta saka kanta cikin kayataccen barikin na sojoji,wanda bariki ne,wanda ke kula da barikokin kaduna,kano,katsina zamfara da Sokoto Shine babban bariki na North a west wato *1 DIVISION NIGERIA ARMY KADUNA*...

     Agaban wasu manyan gidaje daga chan yammah daga cikin barikin suka faka motarsu gidajene jere kamar estate saboda yawansu kuma dukkansu iri dayane komai da komai nasu illah nombobi ne kadai ya rabasu kowani gida dan madaidaicin flat ne mai kyau da tsari dauke da babban Falo da 3 bedroom kowanne da tiolet aciki sai babban kichen dake wajen falo,sai wajen Dining,daga waje Componud kowanne akwai parking space da dan Fili na motsa jiki ko Buga ball,tsakanin kowani apartment akwai dan tazara kadan bada yawa ba,kowani soja an makala masa sunansa da Nombarsa acikin babban kofar part dinshi,ina daga kai naga an saka da manyan baki cikin wani dan anani *CAPTAIN A.A TAMBARI BUZU* naga ansa kenan wannan gidan mallakinsa ne.

    Suna gama Parking Tsirarrun Sojojin dake wayo aharabar wajen da hanzari suka kariso suna rige rigen bude musu mota,lokaci daya suna kame musu ko kallonsu Aliyu baiyi ba,jabir ne,ya daga musu hannu bayan ya nuna musu bayan motar inda kayansu yake,da hanzari suka bude suka kwashi jakukkunansu da hannu Aliyu ya nuna su,kawai sai naga sun rabu biyu,wasu sun nufi Apartment din Aliyu,wasu kuma Sun nufi apartment din dake kusa dana Aliyu dauke da jakar Jabir alamun nan ne barayinsa,Aliyu bayansu yabi duka hannuwansa cikin aljuhun wondonsa yana wata tafiyan takama bayanshi jabir yabi jin alamun tafiya yasa Aliyu ya waigo yana bin Jabir da wani Suprise look,shiko jabir gyara tsayuwa yayi yana fadin"Muje ko.."Akaikaice Aliyu yanuna shi da hannu yana fadin"to go where? dallah mallam kama gabanka,nan din gidanka ne.."? Wata dariya jabir yayi yana fadin"Nifa taimakonka zanyi,naga baka da lafiya,kana cikin damuwa kana bukatar wani akusa dakai..."Rike baki Aliyu yayi yana kallon jabir kafin yadan ware idonsa yana fadin"Don mai garinku nina fadamaka ina cikin damuwa? comon mallam kakama gabanki,yasin karka shigomin gida Ngd da Taimakon..",yafada yana Wucesa da sauri yar dariya jabir yayi kafin ya juya yana fadin"Kai kasani ga damuwa Aranka,ammh tsinannan iskancinka yasa kana wani basarwa chan ta matse maka gara kawai.."

     "Aliyu bai waigo ba,yace"Ta matse maka dai azariyan wandonka banza Dan saka ido kawai.."Yafada daidai lokacin daya dauko dan makulli daga aljihun wandonsa ya zura akofar yana bude kofar falon,Sojan dake biye dashi daga bakin kofa ya tsaidashi ya karbi jakarsa saramai, yayi ammh Aliyu ko daga kai baiyi ba,sai ma shigewa ciki dayayi ya banko kofa,Sojan bai damu,domin duk wani Soja dake barikin yasan miskilancin Aliyu gadanga,shiyasa babu wanda ma ya damu dashi...

Yana Shiga falon bai tsaya ba,ya isa ga bedroom din,jefa jakarsa yayi kan gadon daya mamaye dakin yayi,kafin yafara tube takalmin kafansa,zuwa duka kayan jikinsa,boxers kadai yabari ya fada bedroom din,bai dade ba ya fito kugunsa daure da wani karamin Towel,yana Fitowa wayarsa tafara neman agaji ta wutsiyar ido ya hango mai kira *Swt Ni"ima* yagani wani dogon tsaki yaja yanajin wani daci aransa,wayar bata gama Ringing ba,ya yanke kiran bayan ya shiga ya sakata cikin blacklist,dama kawarta tun safe ya sakata,saboda bayason Takura sam,Shi yanzuma duk Abunda zai Tunamai da wata Ni"ima ma haushi kamasa yake,Da karamin Towel din ya fice zuwa wajen compound din Flask din da goggo tabasu da kulan Fanken ya duba bai gani ba,Rike kugu yayi yana hangen Apartment din Jabir saboda yasan shi ya dauka,kai gayen nan Dan mtsala ne yanzu yajamai sai ya dafa indomie Tunda bazai sake fita ba,ya dade tsaye yana Tunanin wulakancin dazaima gayen chan kafin yakoma ciki,wani guntun wando ya sanya 3quater ko riga bai dashi Ya fada katon kichen din Gas ya kunna ya dora wata karamar Tukunya,ya zuba Ruwa,lokaci daya yabude wani drower ya dauko indomie cherry guda biyu ya farka ya saka,bai fita daga kichen din ba,saima jawo wani Stool da yayi ya zauna yana ajiyar zuciya kamar wanda yayi wani auki,yunwa yakeji bai wani tsaya indomie ta tsotseba,ya sauketa da ruwa ruwa ya juyeta cikin Filet ya bude fridge ya dauko lemon cway ya fito,bisa daya daga cikin kujerun falon ya yada zangon yana daukan Remot bayan ya kunnah Talabijin din,kallon falon yake,yana ganin yadda yayi kura,karamin tsaki yaja aransa yana fadin"yasin ba sharan da zanyi am tired.."Yafada kamar wanda akasashi Dole,hakanan ya shiga Tura indomie har ya kusa cinyewa kafin ya ture filet din ya mike,ya karishe shanye Cway din,bedroom yakoma ya fada bisa gado,yana damke hannusa bisa kirji bayan ya kulle idanunsa,yashiga Tunanin Abunda ya faru daga jiya zuwa shekaranjiya,yana ta mamakin kansa,Ahaka barci ya kwashesa...

    ***********

_Gombe_

  Tun karfe 4:00Am na Asuba Azeema ke tashi sakamakon tasan yau monday Sunada mkranta,kuma matukar bata tsaya tagama duka aiyukanta ba inna bazata taba barinta tatafi mkrantanba,sai ta kammallah komai koda zataje amakare ne,Shiyasa take tashi da wuri tagama duk Abunda takeyi kafin lokaci ya kuremata Tunda Azeeza dama yar gatace bata changal agidan,sai dai taci ta kwanta da Rashin kunya kadai ta iya.

Kafin 7:49am ta kammallah duk Abunda zatayi tayi wanka ta sanya Riga da wando da hijabi kalan Uniform din mkrantan,Madafi takoma ta dibe Tuwonta tazo tazauna tanaci,Lokaci bayan lokaci tana kallon Azeeza take kwance tana jin shesshekan datake alamar kuka takeyi,Gum Azeema tayi Domin tun dazu take mata mgana tatashi tayi sallar tayi Shirin mkranta ammh Azeeza tamata banza,ganin bazata iya barinta haka ba yasa bayan tagama cin Dumamen Tuwonta tamaida kwanon madafi tazo ta wanke hannu takoma dakin tana fadin"Azeeza keko wani irin barci ne,haka takwas fa takusa ammh baki tashi ba,ni harna Shirya zan Wuce mkranta.."Azafafe Azeeza ta tadago kanta daga kwance idanunta sunyi jawur Fuskarta ta kumbura Saboda kuka tace"Wai miye Ruwanki da Rayuwatace Adda Azeema? kin takuramin kin isheni,baza"ayi sallar ba,in kike da aljannar inna tashi shiga ki tare ni karna samu shiga.."Tafada tana mata wani banzan kallo,Azeema baya taja tana daukan jakarta wacce ta kasance ta hannu ne tana fadin"Allah ya baki hakuri...",Tafada cikin sanyin murya kafin ta dumfari kofar Fita,karaf inna Ramatu ta dago labulen dakin tana fadin"Kai Ni wannan bala"in ya isheni wlh,ke dai in da diyar wani Shehi ne,da anga kinibibi,to sai kuma kikayi dace ke diyar mallam lawal ne mai Saida kayan gwari,ina Ruwanki da yata,bakiga bata da lafiya bq ne,in tatashi Uwarki zatayi miki.."Tafada tana zabgamata harara,dukar dakai Azeema tayi kafin tadan Rankwafa tana fadin"Ina kwana inna..."Ko kallonta inna batayi ba,saima karisawa datayi cikin dakin tana fadin"Azeeza tashi,ya jikin ki? take fada tana tarairayota jikinta,Ko kallonsu Azeema batayi ba,ta fice kofar dakin inna ta tsaya tana sallama,mallam lawal dake ciki ya amsa bayan yabata izinin Shigowa,Shiga tayi bayan tacire sandal dinta mallam lawal dake kan gadon mai Rumfa ya sauko daidai lokacin da Azeema ta duka tana fadin"Ina kwana baba.."Ya amsa yana fadin"Lafiya lau diyar albarka,har anyi Shirin mkrantar..? ta amsa da cewa "Eh baba.."aljihunsa ya laluba ya fito da Naira hamsin ya mikamata yana fadin"Kin mkara ki hau mashi ko Keken napep,saura ko ruwa kyasha amkranta.."Noke hannu tayi tana mikewa tace"a"a Baba kabarshi Ban mkraba yanzu zan isa insha Allahu,ruwa kuma akwai fa famfo baba Amkrantar.."Tafada tana juya,Sunanta yakira ta waigo tana amswa mikata yayi yana fadin"Karbi diyar albarka bansanki da gaddama ba.."Hannu ta sanya zata karba taji an warje kudin bayan an Dunguremata kai,Inna Ramatu ne tsaye take kallonsu tana hararansu kan tace"ehe sannu mai diya,ammh yanzu kagama cemin baka da kudi,ammh dayake kan wannan banzar yarinyar ne,ai ka ciro ka bata,kuma dakake kokarin bata kudin ka manta kayi Auren jari da ita,Inashi mijin nata da bai bata ba.."Tafada cikin gatsine,Kallonta mallam lawal yayi yana fadin"Wai ke Ramatu meke damunki ne,koda tana da miji ni ba Mahaifinta bane,bata da hakki akaina ne? "Harzukomai tayi Tana fadin"Bata da hakkin akanka,don yanzu ba"a karkashin ikonka take ba,Azeeza ce ke karkashinka yanzu sonkai ne yamaka yawa shiyaasa baka ganin haka,uhm ayi mugani indai mune muna zaune zamu gani,kowa yana gudun hada zuru"a da bara gurbi ammh kai ka Rumguma yaron da"akace Rikakken Dan"iskane bai da aiki sai tara karuwai Achan kaduna.."Salati mallam ya saka yana fadin"Ramatu ina kika samu wannan lbrin kuma,oh ni lawal,yanzu baki Tsoron Allah yayi miki hisabi akan kazafin dakikayi masa.."Babu kazafi illah gaskiya in ba iskanci ba,ubansa yakeyi achan sai yadau lokaci bai zo gida ba,..."Azeema batagama ji ba,ta fice tana kwallah ko waiwaye batayi ba,ta fice daga gidan zuciyarta na kuna,Hanyarta ta dumfara kawai tana tafe tana lissafin zuci,Kamar ta biya gidan Baba ade Ammh kuma sai taga ta mkra sai tace bari sai ta dawo ta biya,Duk saurinta sai da Seniors suka tsaida ta tayi piciking kafin ta isa ajinsu duk wanda yaga Fuskarta sai ya Fahimci tana cikin damuwa kawai boyewa takeyi.

       #Comment,share,vote....#
      #Janafty...#
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏


_*A big congratulation to u my Sisi of life AISHA ALTO..4Completing ur Special,Amarzing,Fantactis,Adorable and Educated Novel...GIRMAN KAI(Rawanin Tsiya) d Whole book is dedicated to me,JANAFTY...kai am out of Contol fa,don wannnan babbar kyautace wanda bazan taba mantawa da ita ba,Ina mika miki Hannun Jinjina 👍Sisinah domin kin baje dukkan basiranki da Fikiranki wajen Tsara wannan Novel din,hakika kin Fadarkar damu bayan Tarin nishadi da masu karatu sukayi, kin kuma samu nasaran isar da sakonki cikin Hanya mai Sauki,ke Tadambance awajena,Hakika salonki na burgeni kuma yana Tafiya dani,ina rokon Allah yabaki ladan Fadakardamu dakikayi bayan ya duba kuran kuran dakikayi ya yafemiki Duniya da lahira..Kaunarki Araina bata da iyaka..Bazan gaji da fada ba,bakuma zanji kunyan maimaitawa ba Nagode sosai bisa karamcinki gareni My Sisi of life gabadaya shafin na yau mallakinki ne,na baki shi halak malak..Kisani ki kara sani AISHA ALTO KINA BURGENI*_😘

*NOT EDITED*💥

      *Chapter 9*

    

        """Sati uku kenan da Tafiyar Aliyu gadanga ammh baizo gida ba,sai dai waya da sukeyi Shida goggo,ammh ba kullum ba saboda Tunda ya koma yazama yana keeping kansa busy baya zama sosai,akwai wasu bataliyan Sojoji da yake koyama Training bai samun lokacin kansa ma,balle na Tunani,ya tattara komai ya watsar da zarar Tunanin Abunda ya faru ya fadomai zaiyi Saurin Kaudashi ko Afuska baya nuna alama,hatta jabir duk nacinsa,da son gulmansa,sai da ya hakura,shiko Haisam yadai kirasa awaya sun yimagana,kuma duk Akan yayi hakuri da Abunda Allah ya kaddara maine,to ya zaiyi?ai baya da tacewa shikam Tunda haka Allah yayi dashi.

  Ni"ima kuwa sai da ta shafe Sati a asibiti kafin asallameta tadawo gida,Jikin nata da sauki ammh kullum kwana take kuka saboda Rashin Aliyu atare da ita,Maminta ne da kawarta muneera suke kokarin kwantar mata hankali,ammh ina bata ji bata gani,game da Captain dinta zata iya komai,kawai tana kokarin nuna komai ya wuce ne saboda damuwar Maminta da Abbanta da kuma kawarta muneera,ammh taci alwashin bazata bari captain dinta ya subuce mata ba,zataje koda chan kadunan taasan in ya ganta bazai iya kauda ido akanta ba,dole zai tsausayamata su dawo su kara Shirya Auren nasu akaro na biyu,duk da ta san zata Fuskanci kalubale,har zuwa lokacin Ni"ima bata San cewa Captain dinta yayi Aure ba,shiyasa take ganin shawo kanshi mai sauki ne.

  Bangaren Azeema kuwa babu Abunda ya chanza na dangane da Rayuwarta,inna da Azeeza sungama yawo da mganar a anguwa suna fadin Babanta yaga kwadayi ya auramata mara asali,kuma dan" iska,har a mkrantansu saida Azeeza taje da lbrin sai ya zamana Azeema tazama Abun nune da zunde duk sai taji duniyar tayimata kunci da zafi,ko kawayenta na anguwa haka suke kallonta suna fadin kwadayi zai kasheta ita da ubanta,Azeeza na fadn mganganun banza akanta ana mata dariya,mussaman in suka hadu a bohol taje debo Ruwa da kuka take dawowa,wajen Babanta kadai take samun sauki,sai ko wajen Baba Ade kakarta sai wajen uwa gareta goggo wanda tagama guje gujenta ta hakura taje gidan goggon wacce takamata ta Rumgumeta tana mata tsiya,ita goggo ta fadamata cewa ita ba"a Suruka take kallonta ba,a mtsayin Ya take kallonta saboda haka itama Tadauketa amtsayin uwace wacce ta haifi Aliyu da Azeema,dole Azeema ta saki jikinta duk da Nauyin da Goggo ke mata bata da yadda zatayi saboda goggo babu ruwanta hira take da ita kamar ba matar Danta ba,Tuni Azeema ta saki jikinta suka cigaba da yadda suke da goggon kamar da,agidan take Wuni sai yammah take komawa wannan bakin gida,Inna ko babu Abunda ta fasa na muzgunama Azeema sai ma Abunda yayi gaba,yanzu Azeeza Abunta yayi kamari ko mgana Azeema tayi mata tsab zata saka hannu ta shareta da mari bata da bakinn mgana don sai inna ta kusa kasheta lokacinta baiyi ba,shiyasa ko Baba bata bari yaji saboda duk hukuncin dayayima Azeeza akanta inna zata saukeshi shiyasa take hakuri tasha kukanta ta sharbe hawayenta bata da mai lallashinta,duk ta rame ta kanjame kamar ba ita ba,tayi baki,ga wasu kananan kuraje sun Fito mata in ka kalleta bazakayi Tunanin yarinyace yar shekara 20 ba,sai kayi zaton ta haurama talatin30 baya saboda wahalar rayuwa don ma goggo na tsaye kanta,Abun ne ya ishi goggo dole ta matsama Aliyu yazo gida tana son ganinshi don tanaso ya tsamo Azeema daga wannan kangin bautar datake ciki Tunda dai yanzu Shike da iko da ita,kuma tasan duk iskancin inna Ramatu tana shakar captain din.


    *************   

Sai da Aliyu gadanga ya shafe sati Shida baizo gida ba satin ma sai da ya biya gidan kawu bala suka gaisa da Ummah kawu ma bayanan ya tafi Abuja Haisam ma bayanan yana kano wajen aiki,Shiyasa bai dade ba daganan ya kamo hanyar Gombe zuciyarsa duk babu dadi saboda yaasan kiran gaggon bai Wuce mganar sokuwar yarinyarnan ba,wanda gabadaya baya son Tuna komai,Shidai burinsa da Addu"asa bai Wuce Allah ya bayyana mishi Asalin mahaifinsa ba ko zuciyarsa zata daina wannan Nauyin data dade tana fama dashi.

 
Da misalin karfe 2:30pm ya Iso kofar gidan nasu cikin lafiyayyayiyar motarsa din nan 4matic,kofar gidan ya faka motar,bai shiga da ita garejin ba nan ya barta ya bude booth ya shiga jiidan Tsaraban da yayima goggo yara na Jida suna shiga dashi cikin gidan goggo,wacce ke tsakar gida tana jin Radion ta taga Shigowar yara ko bata tambaya ba,Tunda taji dirin mota ranta ya bata gadanga ne,jikinta na Rawa ta mike har zaninta na neman Faduwa ta nufi hanyar waje Sukaci karo da gadanga ya taho jikinsa sanye da Riga da wando Rigar fara ce ammh wandon Nevy blue ce,sai takalmansa rufaffu ne, kansa babu hula gashinsa yasha gyara yana kyalli,Rumgumosa Goggo tayi tana fadin"Oyoyo gadanga..Sannu da zuwa Gadanga kusar yaki,ga soja mazan fama Ah..Soja na Azeema..."Goggo take fada tana Rumgume da Aliyun..

  
Dariya yake yana Rike da goggon yake fadin"Oyoyo goggo ta....Nayi kewarki sosai mamata.."Dunguremasa kai tayi tana fadin"bakayi kewata ba gadanga Tunda sai da nayi ta magiya kafin ka dawo.."Tafada tana Amsan jakar kayansa dake hannunsa,dariya yayi kafin ya saka hannu ya zagayo da hannunsa kan kafadanta kamar wasu kawaye suka jera zuwa cikin gida yana fadin"Haba goggo..Kefa kika haifi gadanga..Kinfi kowa saninshi ko zan manta da kowa wlh banda Uwar Ali gadanga.."Yafada yana wani lamgwabemata nishadi ya kashe goggo tana dariya,ahaka suka karisa daki,tana mai maraba,saboda murna ma goggo bata bashi Ruwa ba,saida tagama kawomai abinci kafin ta tuna,dariya ya dinga mata yana jin dadin zama da goggo sosai haka suka zauna sukaci abinci tare suna hira da dariya in ka kallesu bazakace mahaifiyarsa bace sai ka dauka Kaninta ne saboda yadda take yar daidai da ita.

Azeema data dawo daga kai nikan Alalan da inna ta Aiketa tunda tadawo mkranta ta bata nikan ko Uniform bata cire ba,tatafi kai nikn,,gashi ta tarar da layi sai da tadade bata dawo ba,tana ta sauri ta iso kofar gidan goggo gabanta ne ya fadi dataci karo da Motar yaya captain bakinta har rawa yake tana karkarwa,tana leken gidan ta yi Saurin Wucewa jikinta na rawa saboda tsoro,koda da takaima Inna nikan sai da ta mareta tace ta dade ta tsaya iskancinta bata dawo da Wuri ba,ita duk wannan bai dameta ba,duk fargaban Dawowar yaya captain ya dameta ammh ta godema Allah dayasa taga motarsa da sai ta shiga su hadu da juna,rike baki tayi tana Tuna karonsu dashi,kayan mkranta kawai ta cire tazo ta hau sharan gida,wanke wanke ta hada,ta duba rijiya babu wani Ruwan kirki,tunda rijiyar taja baya sosai babu Ruwa shiyasa take wahalam Aiki yanzu Tunda ga debo Ruwa ya karu,karamin hijabinta ta sanya Domin Riga da sikat ne ajikinta kayan ma sun mata kadan domin sun matseta,rashin wadatattcen kayan ne,yasa take sakasu har yanzu,botikai uku ta diba ta fice zuwa bohol din dake gaban gidan goggo da kadan,sai da ta leka ta tabbatar da kofar gidan goggon babu kowa kana ta fito ta wuce tana waigo koda taje wajen layi yayi yawa sosai,dayake anfara mtsalan Ruwa,idonta ne yakawo Ruwa data tuna da Abunda inna tace,tace in tawuce minti goma bata dawo ba,sai na lahira ya fita jin dadi,jikinta na Rawa ta shiga rokon yan matan dake wajen su bata da diba ko botiki daya ne,kallonta sukayi shekeke kafin su sheke da dadariya suna fadin",Ahhyyyye...Sannu isassa...Kije sojan da kwadayi yakaiki aurensa yazo ya kwatan miki,an dai ji kunya mutum yazama matar aure,ammh kullum ko karen layi bai kaishi Arha ba.."Kallonsu Azeema takeyi hawaye na zubomata domin dukkansu kannen bayanta ne,kawayen Azeeza ne,batace komai ba,sai takoma gefe tana sharan hawaye tana jiran layi ya kawo kanta ta diba.

Inna Ramatu taga Azeema ta dade bata dawo ba ga kullin Alala zai kumbura bata dawo ba,Ranta ya baci ta kwalama Azeeza kira,wacce ke daki tana kwance tana hutawa,tana kuma saka yarda zata zama mallakin Captain taji kiran innar,tana fitowa inna tace"Taje wajen bohol ta kirawomata Azeema tace in bazata kawo mata Ruwan bane ta sani.."Tura baki Azeeza tahauyi don ita ta tsani aike,Dakyar ta shiga daki ta sawo hijabinta ta fice afusace,Bagazan bagazan take tafiya Ranta bace Shikuma yana kokarin Fitowa daga motarsa ya bude gareji zai sakata yaga Wucewar Azeeza kamar wata jaka,baima ganeta ba,yadda yaga ta wucene ya bita da kallo,don shi ya zatama inna Ramatun ce,tsaki yaja kafin ya Rufo motar yana kokarin komawa cikin gida kamar an ce ya daga kai sai ya hangi Azeezar tsaye gaban Azeema domin Tazaran kadan ne da gidan goggon,yana hange bohol din da duk Abunda yake faruwa.

  Tana zuwa batayi watawata ba ta ture Azeema datayi nisa cikin Tunani, sai da takusa faduwa tayi Saurin dafa bango,dagowa Azeema tayi tana fadin"Haba Azeeza baki da hankali ne,kikamin wannan bangazan..",Wani kallo Azeezar ta wurgamata kan tace"Anyi miki Din,ba inna ta aikeki ba,tun dazu kinzo kin tsaya kina bin Mutane da kallo,kamar wata sakarya.."Tafada da alamar raini,gabadaya wajen suka kecemata da dariya,Azeema ta karisa wajen kawayenta suka tafa suna dariya suna nuna Azeema dake hawaye,wani saurayi ne,dan kasan layinsu ne,sunansu sulaiman Ya tsawatar musu ammh sai suka buge damai Rashin kunya,Yana ganin haka dama layi yazo kanshi botikin daya diba ya mikama Azeemar yana fadin"Karbi ki Tafi dashi gida,ni zan jira sai na kara diba.."Azeema da hawaye ya cikamata ido ta kalleshi tana fadin'Nagode.."Tafada Hawaye suna kwararomata,Daukan Ruwan tayi ta juye adaya botikin nata ta Cicciba zata dora akanta,sai ta kaasa sai Sulaimam din yasa hannu ya taimakamata ya dora mata ammh duk da haka sai da Ruwan ya jikata,har hijabin jikinta ya lafe bisa jikinta,albarkatun kirjinta duk sun bayyana waje,hawaye na zuba ajikinta ta dago tana fadin"Nagode sosai.."mirmishi yayi mata bai ce komai ba,tazo zata wuce su Azeeza suka kwashe da dariya suna nunata sai ta zargu tafara hardewa ganin haka yasa Azeeza tahowa gabanta batai wata wata ba ta sanya hannu ta tura Azeema baya ji kake chambal...!Azeema ta fadi cikin katuwar kwatamin kwatan dake wajen botikin Ruwan ya watse bisa jikinta itakuma tayi tsamo tsamo cikim kwata,gabadaya wajen ya dau ihu,Shiko sulaiman baki ya rike cike da mamaki ganin tsabar mugunta wajen Azeeza.

Takaichi Tare da bakinciki sukayima Azeema dirar makiya tana zaune cikin kwata take bin Azeeza da kallo Tana zubar hawaye,itako Azeza banda nunata tana dariya ba Abunda takeyi tana fadin"Tabdijam lallema Adda Azeema kina nufin Ruwan botikin wannan kazamin zaki kaima na gida,wlh da sake kima sake Tunani.."Tafada tana Wurgama sulaiman din wani kallo dama ta tsaneshi saboda sam ko a anguwar baya daukan Raini baya sakarmata Fuska sam.

Yanajin Abunda tace ya nufeta yana fadin"Lalle yarinyar nan baki da kunya yanzu zan koya miki hankali..."Ya fada yana karisowa,kusa da ita baiyi wata wata ba ya daga hannu zai mareta sai yaji ance daga baya cikin wata kakkausan murya..'Hey Leave her...'"Sukaji an fada daga bayansu gabadayansu suka waiga suna kallon mai mgana.

Dukkansu sai da suka Razana hadda Azeema dake zaune cikin kwata tana kuka,yana Tsaye hannayensa gabadaya ya zuba su cikin Aljihun wandonsa,Fuskarasa Murtuke babu Annuri ko kadan har wani ja tayi saboda bacin rai,Azeza da kawayenta yake bi da wani wulakantattacen kallo,wanda Tuni suka Tsorace kamar

Please Login or Register in order to submit comment