Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta yarda zataje,nan da nan ko akayi musu Visa,kwanan su Goggo hudu da dawowa sukuma suka tafi ita da Gimbiya Razeenah da Baba Ade,sai Ummah mai babban daki,datace wlh bamai barinta sai taje taga halin da maigidanta ke ciiki,sai su Zafira da Safaratu,wadanda suka sakama Sarki kukan sai sunje sunga Yaya captain suma hankalinsu zai kwanta,mirmishi maimartaba yayi yace duk suyi ta Tafiya Allah ya kaisu lafiya.

Koda suka sauka A babban birnin Delhi,Jabir da Umar su sukazo da motar Asibitin suka daukesu Diret zuwa masauki,Azeema tayi ta kalle kalle tana yabawa da kasar ta india,isarsu masauki ba wuya kowa yayi wanka sukaci abinci suka dan huta kafin Su jabir su ce Su Fito su tafi cikin Asibitin,ita azaton Azeema likita zata gani Shiyaasa,bata nuna wata damuwarta ba.


Umar da Jabir suna gaba sukuma suna biye dasu,har dakin da Aliyu yake suka Tura kofa suka Shiga,yana kishiginde,yana motsa hannunsa babu komai ajikinsa sai boxers,yana ganinsu yashiga washe baki,don Su Jabir basu sanar dashi,gasu zuwa ba,gaisawa sukafarayi suna tambayanshi yajiki yana amsa musu da sauki,Ummah mai babban daki ta shafa kanshi tana Fadin"Megidana gawa taki rami.."Dariya akasa,shima mirmishin yayi kafin yace"Kwarai don sai kin rigani wucewa wlh.."Yafada yana yar dariya Wajen Umar takoma ta dafosa Tana Fadin",Da tsohuwar zuma ake mgani ko Na gaban goshina.."Yarfe hanunta yayi yana Fadin"Tabdijam bawani nan,ai da sabuwar ma anayi,banan kika watsamin kasa a ido ba,nima aje gaba wlh bani so.."Dariya suka samata gabadaya ganin yadda Tayi Da Fuska,Aliyu dai sai waige yake yana Jiran yaga ta ina Azeema zata bullo,lura da hakan Da gimbiya Razeenah tayi itace ta waiga tana Fadin"Wai ina Azeema ta tsaya ne?Batare da ita muka Shigo nan ba..? jin Abunda Gimbiya Razeenah tace ne yasa Aliyu saukar da ajiyar Zuciya,yana lumshe ido.

Zafira ce ta fita waje,sai kawai taga Azeema zaune kan wata kujera ta wani hade rai,saboda duk a tsammaninta wajen likita suka kawota shiyasa tayi Ficewarta tana Tura baki,don yanzu wlh haushi kowama takeji,Zafira ce ta karisa garera tana Fadin"princess dinmu kizo Ummah na kiranki.."Kauda kai tayi kafin Tafara kokarin mikewa Zafira tana taimakamata harta mike,rike da hannunta gam suka Shiga dakin,bata direta ko"ina ba sai gaban godon Yaya Aliyu kafin ta kauce tana Fadin"Jita tanawani Fushi da mutane mufa taimakonki mukayi wajen mijinki dakike begen gani muka kawoki.."Tana Fada tanayin gefe gadanga dake kwance ya bayyana agabanta.

Kallonsa take,shima yana kallonta daga sama har kasa,tana sanye da wata doguwar rigar Abaya baka,sai Gyalen kayanta data nadashi bisa kanta,ga cikinta nan ya turo yayi kato,kamar gobe zai Fito Duniya bayan ta cika tayi Fam,kamar ba Azeema ba,itako kallonsa take cikin Fitan hayyaci,tundaga Samansa har zuwa inda kafafunsa suke asagale,Tsoro ya kamata tayi baya tana sanya duka hannuwanta ta danne bakinta dake rawa da karfi ta Furta.."Ya..Ya..Cap...tain...",Tafada idonta gabadaya awaje,Mirmishi ya sakarmata mai Sauti kafin yace"Na"am pretty..,Nine cijeni kiji ba mafarki kikeyi ba.."Yafada yana mikamata hannunsa mai lafiya,ai da hanzari ta karisa garesa sai jiyayi Ta fadomai kai tsaye hartana bugemai hannun dake da ciwo,gefe yayi da hannun yana Fadin"Wash pretty bi sannu,kinsan yanzu mijin naki yadawo sai allallaba fa"Yake fada yana zagaya bayanta da hanunsa mai lafiya,kuka kawai Tafashemai dashi tana fadin"Yaya captain Ashe zan sake ganinka arayuwata? nazata ka mutu ne su goggo ke boyemin?Bayanta ya Rumgume yana Fadin"Ban mutu ba pretty,sai dai nasha wuyane kawai.."yafada yana yar dariya dago kanta tayi daga kirjinsa tana kallonsa hawaye shabe shabe Afuskarta tace"Har wani tsawon lokaci kadauka kana cikin wannan halin? tafada muryanta na Rawa,Rausayar dakai yayi yana kallonta kafin yace",Bansani ba pretty wlh bansani ba,Abu daya nasani shine nidai na Farfado na ganni anan wajen"Kuri tayi masa da ido,kafin takoma tana bin Raunikansa da kallo,tana hawaye na Tsausayinshi,hannu ta sanya zata taba kafafunsa yayi Saurin rike hannunta yana Fadin"Pretty ciwo ne da zafi.."Yafada Ashagwabe,dariya tayi tana hawaye,tayi Saurin Shammatansa,ta dan ture hannun dayake da ciwo,baya yayi yana Fadin"Wash pretty .."Saurin Fadamai tayi tana fadin"Srry kaji bazan kara ba.."Tafada tana mai dariya hancinta yaja yana Fadin"kinganki ko,so kike kiga kukana ko,toh bazaki gani ba.."Dariya sukayi gabadayansu yana kara rikota,kiss ya sakarmata bisa kai yana Fadin"I miss u Pretty,i miss u like crazy..."Hawayenta suka karu ta dago tana kallon bakinsa,lebenta ta saka anashi tana tsotsa na kusan minti hudu kafin ta cire tana Fadin"Miss u more and more Mijina.."Shima idonshi ya kawo Ruwa da hannunsa mai lafiya yasa ya Fado da ita jikinsa ya rumgumeta kam,duk da tsinin cikin na hanata isa gareshi ammh haka ya matseta yana Sauke ajiyar zuciya,koda suka waiga daki bakowa,ashe tun Rumguman Farko kowa ya Fice batare da wani ya yi Shawara da wani ba😂


"Cikinta yake Shafawa yana Sauke tagawayen ajiyar zuciya kafin ya fizgo mganar"pretty cikin nan yayi kato da yawa,anya ba yan uku bane na baki,kinsa fa ni akwai lafiyan mazantaka ko? dariya takamata,mintsilinsa tayi AGefen ciki ya zille yana dan ihu,yake Fadin"kefa muguwace wlh daga fadar gaskiya sai muguntarki yatashi haka ake jinya dama"Bata dagoba illah kara lafemai datayi tana shafa kirjinsa da hannunta har zuwa nipple dinsa,salon datakemai ne yashashi Saurin rike hannunta yana fadin"pret..ty.."muryansa ta karaya,bata samu zarafin mgana ba illah"Umh..Umh..Umh..Mmmm.."Datake ta cemai,Mirmishi yayi mata yana kara damke hannunta yace"Bari mana pretty kinji,kinga fa halin danake ciki,karki kwantomana kura,wlh ko kin kwantota babu amfanin da zan miki.."Yafada yana cije baki,da Sauri ta dago tana Tura baki tace,"Ni yaushe nace haka...? Saurin Rikota yayi Yana Fadin"wayace kince,nine naji yanayi na chanzawa dat why am srry kinji pretty bazan kara ba.."komawa tayi bisa kirjinsa tana dauke hawayenta,domin data dago ta ganshi Ko"ina sagale sai taji kuka yazomata,kankame juna sukayi tamkar wani zai kwace musu juna,yana rike da ita yake bata lbrin Kafarsa daya harbin bindiga ne,daya kuma karaya ne,sai hannunsa,shima dake da karayan ammh Alhamdulillah ana samun cigaba.


Lalle masu iya mgana sukace Abun namu ne,toh haka tafaru da Aliyu da Azeema,don mantawa sukayi da kowa da komai suna rike da juna,suna hira gefe daya suna shan soyewarsu,har dare dakyar su Ummah mai babban daki suka tara Azeema suka koma masauki,ammh da Farko kuka tafara wai ita ba inda zata wajen Aliyu zata kwana,baki Ummah ta rike tana Fadin"Wai naji yaran zamani,toh in kin kwana,ina zaki kwanta gado dayane dai adakin,kuma yana kwance ko'ina tallabe? ko kallonta batayi ba ta fice tana Tura baki,Aliyu ko baitabajin haushin Rashin kwanan masu jinya ba sai yau,saboda Tafiyar Azeema ranar ko barcin kirki baiyi ba saboda kewa da damuwa,Tun safe ya ke ta kiran Jabir awaya don Allah ya kawo masa prettynsa Jabir sai yayi tsaki ya yanke kiran yana Fadin"wannan gayen Tunda yafara samuwa sai Allah kuma.."daga karshema kashe wayar yayi don yace yana barci bamai tashinsa,itako Azeema tun sallar Asuba bata koma tayi wanka ko karyawa batayi tatafi dakin su Umar tahau kwankwansa musu,Umar ne tafito,tana Neman yin kuka tana rokonsa yazo yarakata cikin Asibitin,ganin zatamai kuka ne yasa ya koma daki ya Shiryo yazo yatafi da ita ko Shiga baiyi ba ya juyo ya dawo yana Fatan Shima Allah yabashi mata wacce zata soshi ta kula dashi kamar Matar Yaya Aliyu.

Gadanga na zaune Yana Tunanin Azeema,ko Shigowanta baijiba,sai kawai yajita ajikinsa ta fadomai tana Fashemai da kuka,rumgumeta yayi ta lallashinta itako Fadi take wlh bazata kara Tafiya anan zata dinga kwana,cikin kunar rai yace"Kwarai da gaske kinanan wlh keda mijinki sai ahanaki kwana dashi,watafi chanchanta tayi jinyata inbake ba,bari likitocin suzo ko susan Abunyi ko kuma su sallameni mukoma gida gabadaya"Yake Fada Ransa bace.

Haka ko akayi Dr kabirkhan na zuwa Aliyu yayi cikiciki da rai ba Annuri,kuma yaki sakin Azeema yana kamkame da ita,Dariya Da sha"awa Abun yabaiwa Dr kabir khan da Sauran likitocin,Yasaketama Adubashi yaki sai Fadi yake,Asan yadda za"ayi dashi ko ayima prettynsa waje ta rinka kwana dashi tana bashi kulawa,ko kuma Shima sallameshi su tafi gida tare,itako Azeema harda dagowa tana Sharbe kwallah,shiko yana lallashinta,Tafi indiyan likitocin suka saka saka musu suna dariya Dr kabirkhan yace cikin Harshen Turanci" Umh very nice LOVE BIRDS..."Yake Fada yana musu Dariya,nan da nan yayi waya daga cikin Asibitin ya bada umarnin kawo wani karamin gado,kafin kace me har an Shigo dashi an kafashi kusa dana Aliyu anyimai Shimfidun alfarma,hardasu blanket da Filo mai kyau kallonsu Dr Khan yayi kafin yace"Is ok ko,mrs Patient ankashe rigimar zamu iya dubashi yanzu?yafada yana dariya tashi tayi tana gyada kai,cikin yar kunya,kuma wai tana wani Share kwallah,suko suna musu dariya kusan fa indiyawa akwai Bama soyayyah muhimmanci,gefe Azeema ta koma har suka gama Duba Aliyu suka fice suNa musu dariya suna tsokanansu da love birds.


Koda su Jabir suka iso,suka iske sabon lbrin baki suka rike,Jabir da bai iya Shuru yace"Wai yau naga bariki umar,yanzu Kaduba gayen nan,duk Wahalan damukayi dashi baitaba nuna damuwarsa ba inzamu koma masauki,ammh yau Azeema tazo harda tada rigiman kota dinga kwana dashi ko asallameshi yadawo gida? hararansa Aliyu yayi yana Fadin",Eh din,to daman ku gardawa dakune zan so ku kwana dani,Allah kyauta kai ni ko yanzu kuka tattara kuka tafi,Ayashe ta gaida Assha ko pretty? yafada yana kallon Azeema,wacce ke kunshe dariya ganin yadda Jabir ke hararansa,Jabir ya yi kuri yana kallonsa kafin yace"Toh ai ba damuwa ba basai ka koremu ba,zamu tafi kuma wlh zaka nemi ni banza mara mutumci kawai.."Dakin ne akasa dariya gabadaya ganin yadda Jabir yaji zafin Abun,Waje yafita yana ta zagin Aliyu shiko hardamai gwallo,Zafirace ta lallaba ta bi bayan Habibitan,Su ummah ko Aliyu sukayita ma Tsiya shiko ko ajikinsa don Abun yanzu ne yayi mai daidai.



Azeema duk da tsohon cikinta bata nuna kiyuwa wajen kula da Megidanta Aliyu,itace bashi abinci,goggemai jiki sabida yaji dadin jikinsa saboda Rashin wanka,akwana hudun da zuwansu garin aka kwance Karayan hannunsa,kuma Alhamdulillah komai yayi kyau masha Allah,sai da kokarin yafara anfani da hannu,wanda wannan aikin Azeema ce,itace keta kokari kan haka kuma yana kokarin motsa hannu,koda daukan Abune na mara karfi,itama Asibitin suna kokarin kula da ita amtsayinta na mai ciki,tunda duk sun saba da likiticin kamar DR khan sun Shaku dashi,inkaga yadda suke hira da Aliyu sai kuce sun shekara aruaru da haduwa ne.


Sati Daya su Gimbiya Razeenah sukayi suka koma,harda Jabir da Umar,Ummah mai babban daki tace ko ba inda zata zata,har sai Azeema ta haihu Aliyu ya warke kana ta biyosu su dawo,saboda itama ta kula dasu,toh ya suka iya dole suka barta sai Gimbiya Razeenah Tabisu suka koma tare,Ita kuma Ummah Dr khan yace ba"a barta ita kadai ahotel ba,gidansa dake cikin Asibitin nan Yakai Ummah mai babban daki,tazauna ita da matarsa mai Suna KAREENA,suna da kirki sosai,duk da Ummah batajin Turanci tana jin labarci,sukuma sun iya saboda sun zauna da larabawa sosai saboda yanayin aikin Shi Dr khan din,itama kuma Azeema aka barta ita da mijinta tana kara kula dashi..



_________________

*BAYAN WATA DAYA*

Sauki tare da cigaba yana samuwa abangaren Aliyu,wanda har an kwance duka aikin da"akayimai akafafunsa,hannunsa kuma Tuni ya yawarke garas,in ka ganshi bazakace yataba samun Rauni ba,Kafafunsa kuwa haryafara koyon Tafiya dasu Duk da tafiyan bata nuna Sosai ba,ammh sakamakon sanduna guda biyu,suna taimakamai Sosai wajen Nunar da Tafiyar nashi,kullum safe da yammah Azeema ke Fitowa dashi suna zagaya Haraban Asibitin,suna tafe suna soyewarsu babu Ruwansu da kowa,Tuni sukebama duk wanda ke asibitin sha'awa ganinsu bakaken Fata,ammh kuma suna mutumta soyayyah da daraja Aure haka,Ba yadda Ummah mai babban daki batayi ba,akan Azeema tadawo tahuta Tunda cikinta ya isa haihuwa ammh fafur taki,wai Tunda lafiyanta kalau ita bazata ta zauna ba,dole ta zura mat ido toh yazatayi Allah ya hadata da yaran zamani.


Awani dare Azeema tatashi da Nakuda,Hankali Aliyu yayi bala"in Tashi ganin halin datake ciki,ko kafin ya danna Madannin kiran likita Azeema tafara Wani irin nishi,ko kafin Nurses din su kariso Azeema tayi wani nishi mai karfi sai ga Kan d'a ya Fito,Allah ya taimake Nurses din suna shigowa Kan Da'n na Fitowa da hanzari suka karisa suka saka hannu suka jawosa,ai basu bar wajen ba,Azeema ta bankare tana salati nishi take mai karfi sai ga wani kan yakara Fito,suka saka hannu suka jawosa,Aliyu dake gefe yahada zufa kota ko'ina yana rike da Azeema,wlh har sai da yayi mata kwallah,ai suna jawoshi,takoma takwanta tana maida numfashi,Ihu suke suna daga ya"yan suna bugasu,nan da nan suka chanyara kuka atare,Azeema dake kwance hannunta kamkame dana gadanga taji cikinta yakara murdawa Nishi take saki tana Fadin"Yaya inaji fa akwai wani acikin cikin?Tafada tana wani nishin mai karfi,Wata nurses ce ta ankare da hanzari ta kariso tana kara ware kafafun Azeema take Fadin"Anoder one..."Take Fadi tana ihu"push oya push..."take Fadamata Azeema ko jitayi kamar zata Shide saboda azaba,dakyar ta iya wani nishi mai karfi,wanda ya Fito da kan Da'n Suka sanya hannu suka jawoshi,suna murna gabadaya dakin ya gauraye da kukan jariran wadanda Nurses din suka dagasu suka zube bisa jikin Azeema suna dariya,jikinsu duk jini ammh haka Azeema ta rikesu tana dariya lokaci daya da kwallah,Aliyu ko kamar yasuma saboda dadi,Dakyar suka koreshi waje suka kwashe mabiyan Azeema suka gyara wajen gefe daya kuma wasu suna kokarin gyaran yaran,duk da asibitin na kashi ne,ammh Nurses din sun san Abunda sukeyi,shiyasa karban haihuwan Azeeman bai basu wahala ba,duk da Abun yazo da Sauki.


Koda gari ya waye sai dai Asibiti ta cika da lbrin Majinyacin Sojan nan da"aka kawo daga Nageri,matarshi tahaifi Tripple,Mata biyu Namiji daya,kuma dukkansu sun zauna amahaifa dayane domin ko Azeema da Aliyu haryanzu sun kasa gane bambamcinsu,duk da kwana sukayi suna kare musu kallo,sun Rumgume yafi sau Biyar suna kara godiya ga Allah daya Basu wannan kyautar,Ummah mai babban daki sai dai Da Safe Dr khan ya sanar da ita haihuwan Azeema,duk da shima baya Asibitin waya akayi masa,jiki narawa suka nufa cikin Asibitin,sai dai suka tarar da Azeema zaune bisa gado tayi Ras da ita kamar ba ita ta haihu ba ga Gadanga a gefe bakin nan kamar zai yage,saboda murna Ummah mai babban daki ita takira Gida ta sanar dasu,gabadaya masarauta ta rude da murna Jikoki uku alokaci daya lalle Allah Abun godiya,Goggo ita ta kira kawu da kanta ta sanar dashi kafin kaceme haihuwan Tripple yazaga Duniya,Haisam na kano yaji lbrin ai sai ya kira jabir yana sanar dashi da zarar komai yayi daidai Aliyu ya dawo gida zasu fadama maimartaba suna so suma ayi bikinsu nan da wani lokaci domin zamowar Aliyu baban yan uku tabbas barazanane ga rayuwarsu😂

kwana biyu da haihuwan Azeema gimbiya Fasilatu da gimbiya Razeenah suka dira a india,murna ba"a mgana,ai gimbiya Fasilatu batayi shawara da kowa ba tayi saranda Taba goggo dama,Domin ta Fahimci tafi karfinta nesa ba kusa,domin tsakaninsu kamar tsakanin sama da kasa ne,duka duka Sati daya suka kara gabadaya aka Rubutama Aliyu gadanga sallama lokacin yana da wata biyu a asibitin,domin yaji sauki sosai koma nace ya warke,domin kafafunsa sun mike da kanshi yake takawa batare da Taimakon sanda ba.



Asibitin sunsha kewa love birds,Azeema da Aliyu ga kuma Tripple masu shiga rai da Ban sha"awa,haka sukayi ta hotuna da likitocin da Nurses,suna bankwana da sabo suka rabu,Azeema harda kwallaar rabuwa ita da Ummah mai babban daki sunji dadin india,sosai Dr khan kuwa sunyi exchanging din Phone number da Aliyu,da cewa da zarar ya shigo Nageria zai nemesa,haka suka rabu da matarsa kareena wacce suka shaku da Azeema da Ummah.

Ranar da suka baro india zuwa Masarautar Tambari buzu,sukowa ana chan ana gudanar da shagulgular murnan dawowar Aliyu da kuma murnan haihuwan yan"uku ,wanda ba"a tabayi ba tun sadda aka gina masarautar,Mutanen Nageria kuwa Sun dade da isa zuwansu Aliyu kawai suke jira,Hatta da jabir wanda yazo Shida Maminsa da Daddynsa,da Haisam ba"a barsu abaya ba domin sunce wlh wannan karon bazasu koma Nageria ba sai da matansu sun gaji suma,suna bukatar gwada karfin mazantakansu😂 wannan karon ma kawu da duka iyalansa,harda su Anty madina sunce wlh suma baza"a barsu abaya ba,tab uwa uba kuma ga shi Sunan yan ukun za"a hadashi ne da bikin gwagwaran biyu Wato Jabir da Haisam,kawu ya roki alfarman kuma Maimartaba baiyi gaddama ba,sakamakon yadda yake cikin Farinciki na dawowar Aliyu,ga kuma wani kyautan daga Allah.



*Ina godiya sosai masoyana ina ganin duka comments dinku daga mabambamta group dadama,bana samun binku daya bayan daya na yi muku reply,saboda ina cikin busy ne ko Typing din ma kokari nake mu kareta mu huta hakanan Shiyasa,ngd sosai kujigaba da hakuri dani Allah ya bar zumunci Ameen*


_*Sisinah Aisha Alto,keda Sahibata Hafsat Hafan ina kai gaisuwa🙋 Alherin Allah ya lullubeku aduk inda kuke*_


*D'IYATA LADINGO GA SAKON JINJINATA👍Allah yayi ma Rayuwarki Albarka can love u less diyar kwarai*



*Janafty*
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

      *Chapter 38*

   "Koda suka isa Masarautan, ta dinke babu masaka tsinke,haka aka yayyabe Aliyu da Azeema kamar za"a cinyesu saboda murna da Farinciki,Triple ko sunsha dauka sai da Gimbiya Razeenah ta daukesu ita da Azeema kwacokam zuwa shashenta,inda ta sanya Jakadiya ta saka wata baiwa ta saka mata katuwar gawar da Ruwan zafi ta shiga da Azeema tiolet ta gasata dakyau sosai ita kuma Baba Ade ta wanke yaran tas,aka Shiryasu cikin kayan sanyi masu kyau,aka kaima maimartaba su,shida kawu suka daukesu suka sanya musu albarka,shiko Aliyu bayan gaishe gaishe shashensa ya wuce,shida amininnasa,yasamu yayi wanka yaci abinci ya kwanta domin Hutu,suko Su Zafira da Safaru,suna dawowa goggo ta damkama Anty madina su tace amanar gyarasu na hannunta nan da nan ko tashige dasu Shashen goggo chan kurya domin cika Umarnin goggo,Ummah ko ita dasu gimbiya Fasilatu suna Shashen Azeema suna zaune suna hira cike da Farinciki da Annushuwa,Azeema kuwa tana gama cin abinci suka kulleta cikin daki wai ta kwanta ta huta,tana kwanciya kuma sai barci.

Tako'ina masarauta ta dinke da jama"a daga mabambanta wajeje a kasar Niger,dama kewayanta harda mutanen wasu yanki,domin samun damar amsa gayyatan Da maigirma Sarkin Agadez yayima jama"a na Murna haihuwar jokokinsa har guda uku,tare da Daura Aure tilon ya"yan nasa guda biyu,dole Abun ya Wuce hasashenmu,domin fa ashirya taro ne na azo agani,Hatta da Mallam lawal da Inna Ramatu sai da maimartaba yasaka akayi visa suka taho,domin yace har abada inna Ramatu tana mtsayin mahaifiya ne ga Azeema,sai ga Inna Ramatu zaune cikin masaraurar Tambari buzu rike da ya'yan Azeema,lalle duniya Abun tsoroce kuma hausawa na Fadin Abunda yabaka Dariya watarana Shizai sanya ka kuka,Sai kuma alokacin Aliyu ke jin lbrin Rasuwar Azeeza yaji ba dadi,ammh baiwani nuna damuwarsa ba,kawai yayi jim ne,saboda kada Azeema tace yana murna da Rasuwar yar"uwanta,ammh harga Allah ya manta da wata hallita Azeeza,Fatan dacewa wajen Allah yayimata,ammh akasan Ransa Yana fadin an rage mugun iri.

  Daga Nageria Aliyu ya samu waya dadama,ciki harda waya daga Babban headquater su na Abuja,sukayimai ya jiki,bayan nan ya samu waya daga abokan aikinsa dadama,cikin wayar data tsayamai arai itace wayar da Ni"ima tayimai tana kuka,tace tayita nemansa so ba adadi bata sameshi ba sai yanzu,tadamu sosai Allah yasa ya warke babu Abunda ke damunsa,Mirmishi kawai yayi mata kafin ya sanar da ita ya warke yanzu hakama yana Masarauta nan yake sanar da ita haihuwan Azeema,da kuma Aurensu Jabir,Ni"ima taji hawaye sun taho mata tayi Saurin dannewa tana fadin!"Allah ya raya su bisa sunnah Congratulation,"Lokacin datake Fadin haka yana jinta kuka takeyi,sai ya basar yana tambayanta yakamata su Fito da miji ita da muneera Suyi Aure saboda Shine mutumcinsu,Dariyan kuka Ni"ima tayi kafin tace"Muneera zatayi Aure in Allah ya bata miji na gari,mgana na kuma bata don bazan taba yarda na auri wani namiji ba sai mutum daya,in ban sameshi ba,sai da nakoma ga Allah banyi Aure ba.."Saurin katse kiran tayi tana Fashewa da kuka,Aliyu Tunda sukayi waya da Ni'ima ya koma wani Sukuku ranar,saboda kalaman Ni"ima,hakika in yace bayason Ni"ima yayi karya,kuma in yace baya tsausayinta tabbas yasan karya yakeyi,kawai Shi ra"ayin Aurenta ne bayayi,saboda Shi mutum ne,mai zuciya da tsayawa kan Ra"ayinsa tunda yarasa Ni'ima da Farko komai na plan din Aurenta ya Rushe,sai gashi Azeema dabaitaba tsara Rayuwa da ita tazo tazama kaddaransa,gashi yau an wayi gari bayan goggo bai da wata sanyin idaniya daya Wuce Azeema yanamata Sonda baisan iyakarsa ba,saboda kirkinta da sadaukarwanta gareshi,hakadai yayita tunane Tunane har ya kareta baisamu mafita ba.

Ranar Da Azeema ta cika Sati biyu da haihuwa da misalin karfe 10:00am na safiyar Ranar jumma"a Duban mutane da sarakai,suka Shaida auren Haisam da Safaratu sai Jabir da Zafira kan sadaki mafi daraja, afarfajiyar Fadar maimartaba Sarkin Agadez Sarki Abdulnaseer Tambari buzu,Daurin Auren daya amsa sunansa,wanda ba"a tabayi ba masarauta tacika makil da yan gida da yan waje,busan algaita kadai kakeji da kade kade da raye raye na Masarauta,abinci ko tako"ina kawai afitowa dashi ake,daga cikin masarauta kuma Yau din ne ake Sunan Triples,wadanda suka ci Sunaye masu daraja Daya taci Sunan goggo SUWAIBA ,Dayan kuma FATIMA,Sai Namijin yaci Sunan Maimartaba wato ABDULNASEER,Wanda ada sunan kawu akaso yace,kawun da kanshi yace maimartaba yafishi chanchantan samun takwara da farko,shima inda rai da rabo,mai sunanshi na zuwa,sunsha wanka cikin kayan alfarma,suda Mahaifiyarsu Azeema,wacce ke sanye cikin wani leshi,mai tsada da yarari,kunnuwanta da hannuwanta gabadaya Sanye da zinarai suna daukan ido,Hakama ango karni sanye da shadda fara riga da wondo harda babban Riga Shida aminan nasa,guda biyu duka shiga iri daya sukayi harda cikon Umar na Hudunsu,Ana gama Daura auren suka nufa shashen Aliyu suka gudanar da wata yar kwakwaryan walima,bayan la"asar nayi aka Fito akayi wata kayatattacan kilasa,mai ban Sha"awa Da dadin kallo,haka duka zaratan maza su hudu ke bama doki wuta sunajan limzami,kowa da kowa yafito kallo,harda maimartaba,Amare ma suna gefe,kowacce ita tarike ma mijinta limzaminsa kafin afara kilasan,Hakama Azeema tayima Aliyu gadangan kusar yaki,daga karshe maimartaba da tawagansa suka Rufe kilasa,yau hatta da kawu Bala Da mallam lawal da sun hau dokuna,Atawagan Sarki,itako inna Ramatu Tunda sukazo take Shashen Azeema ta karbi su Ummah ita ke kula da ita da Triple,Tayi nadama sosai in kuka ganta kamar ba ita ba,Abun jin dadinta ma babu wanda ya riketa da Abunda ta aikata kowa amasarautar yana bata girma amatsayinta na Uwa ga Azeema,Gadanga ne dai haryanzu bai saki da ita sosai ba,don shi mutum ne mai Ra"ayin bala'in in baya Ra"ayinka Tun Farko Abu ne mai Wahala yayi Ra"ayinka daga baya,kawai mazayewa yake saboda Uwar mata Azeema,don ya lura Tunda ta haihu takoma masifaffa,mgana kadan sai ta hau Fushi,shiko yanzu Aduniya in akwai Abunda ya tsana to yaga Fushi Afukar pretty yanzu nan zai Rasa natsuwarsa,shiyasa in gaya su Jabir na Rawan kafa kan su Zafira mamaki suke bashi,dariya kawai yake Aransa yana Fadin"Yarinta haryanzu na damun su Jabir,Allah ya kaunda Fitina,tunda daga su Jabir din har Su zafira shegen Rawan kan tsiya😂


Wajen kwana biyu aka Dauka ana gudanar da shagulgula Amasauratar Tambari buzu,saboda jiran Visan su jabir ta Fito,Ranar kwana uku da Daura Aure visan ta Fito sai haraman komawa,Haisam gidanshi na kano zai wuce da Safaratu,itako Zafira cikin Cikin barrak zasu zauna ita da jabir,sai fa alokacin ne koke koke ya tashi suna kuka sun rike gimbiya Razeenah akan su sun Fasa aure,Abun ma dariya yabama Azeema,sai da taje ta kira Aliyu yazo,tsawa daya ya daga musu kowacce ta Shiga natsuwarta.


Goggo ce da Gimbiya Razeenah zasu raka Amare,Ummah mai babban daki tace wazai zauna tab,wlh dole ne aje da ita gwara tayi amfani da lafiyanta kafin karfinta ya kare tazaga duniya😂Sai su Ummah dasu Anty madina da zasu koma,Inna Ramatu dai tana nan sai Azeema tagama wanka sukoma Tare hakama Shima Aliyu ko Shirin Tafiya baiyi ba,su suka raka Amare da angawaye har Filin jirgi,inda suka sha tsiya wajen gadanga yanata musu iskanci yana Fadin"yaga Sai rawan kafa suke,toh ko sau dari zasuyi Arana bazasu taba kamoshi ba,kuma wlh duk wanda yayagamai kanwa da yawa Allah ya isa😂🙉Jabir ya bashi amsa da cewa"Wlh tallhi yage yagema mallam,kai don Ubanka daka yaga kanwar wani wayamaka mgana,kajimin dan iskan Yaya"Dariya Umar ke tayi Shiko Aliyu hade rai yayi yana Fadin'"Yau ga surikin zamani,yanzu ni kake cema Dan"iska ko,ke Zafira zo nan"Yakira zafira wacce ke tare da goggo,ganin haka yasa Umar ya taresa yana Fadin"Allah huci zuciyar magajinmu rabu dasu,ai kowa ya sani ba wani babban Sai Baban yan ukun mu.."jin haka yasa ya washe baki yana Fadin"Allah yaso ku da na kirata nace ko kazo ta matse kafa🙈🙉"..Dukkansu baki suka rike suna kallon Aliyu shiko gwalo yayi musu yana dariya,daga Haisam har jabir binsa sukayi da

Please Login or Register in order to submit comment