Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Compiled By Umar Dalha Funtua.

An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



[1/28, 2:58 PM] GOLDEN PEN WRITERS ASSOCI: *JARABTAR MU*

Writing by-Qurrah

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*

*~we write assidiously perceive no pain~.*

*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*

*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pai

Page_1_2

Inama Allah godiya da ya nunaman nafara wannan Book din lafiya,Allah ya nunaman na gamashi lafiya.Ameen

Godiya ta mussam gareki Aunty Nabeelart lady Allah yabar zumunci.Ameen

Bissimillah Rahmanir Rahim.

DEDICATED TO.....MY SISTERS.

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

-----------Subhanallah Matii me ya faru?? Na fadi hakan a cikin tsoro!!

Kallona yayi yace "yar gidan liman kiyi hakuri yau ma motar ta samu matsala " nayi ajiyar zuciya na kalli mutanen dake a cikin motar,kowa sabgar gaban shi yake, daga mai shan rake sai mai cin kosai sai mai rike da biredi.

Walkiya naga ana yi gashi motar a bude take,ga hadari dake haduwa.

Matii dan Allah zaka isa kauyan mu??

"Kiyi hakuri yar gidan liman bazan samu isa chan ba iyaka ta nan saboda babu yan kauyan ku a cikin motar ke kaɗai ce"

Hawaye ya cika idona ganin zai zubo nayi saurin daukar fanteka ta da gammona,daman gefe nike na dire " Mati yace ba zaki jiraba na ida? "nace a'a hadari ke akwai a garin na mika mashi Murtala biyu "yace nagode kiyi ratse ta cikin gonakai yanzu zaki kai "nace to.

Yan Matan cikin motar su kallona suke sai suka kwashe da dariya,na juya na kallesu cikin bacin rai "nan naga wata na nunani wai taje kauyan mu biki ta ganni duk kauyan mu bamai sona guduna ake "shine suke dariya mai bakin jini "na kalleta kamar nasanta??Nan na tuno kawar Ma'u ce kenan Ma'u ta Fadi mata.

Ganin hawayen dake makale zasu zubo,yasa nayi saurin barin wajen.

Tafiya nike ina goge hawayen dake bin fuskata,bana ganin gabana tafiya nike cikin gonakai,sauri nike harda dan gudu,walkiya ake hakan yasani jin tsoro ga duhu sai kara sakkowa yake gari na baki.

Gashi babu ko fitila a tare dani.

Ina cikin tafiya ruwa ya sakko,kasancewa cikin daji nike ga dare babu wajen fakewa hakan yasa na kara azama.

Koda na shigo kauyen mu,ruwa ya dauke nayi ajiyar zuciya nace Alhamdulillah tunda na iso lafiya.

Jikakken Hijab dina na jawo na dan rufe fuskata saboda gudun kada wani ya ganni,da naga ana haskani saina boye,har na isa gidan mu.

A hankali nayi sallamar, Subhanallah!!

Na ambata tare da dafe girji "Bakar munafuka mai bakin halii jinin tsiya da bakin jini shigo yau ni naga sheɗaniya kenan??"

A hankali na iso inda take "Barikin naki har ya kai ki da kikai dare haka "Wallahi Innah wallahi tallahi kinsan kullun sai motar Matii ta lalace yauma lalacewa tayi a kafa na taho tun daga Tudu kinga ma ruwa ya jikeni.

Kallona take tun daga sama har kasa "tace inma gaskiya kika fada matsalar ki dan kin kwaso shege ai ba komai bane tunda kema shegiyar ce"

Kuka ya kuɓuce man "tace kukan mi zaki yi sharri nayi makii?? Ke ba shegiya bace idan ba shegiya bace fadaman uwar ki da ubanki a garin nan? Malam fa a chan wajen yawon shi ya tsinto ki dadin bakin banza ne da yake ce maki diyar shi har yana fifitaki akan jinin shi "kuka nike sosai wai mizan ma matar nan na samu sauki wajenta??

"Assalamu Alaikum "muryar Baban mu naji,cikin sauri na juya tare da jin dadi nayi saurin goge hawayen dake bin fuskata duk da dare ne,Amman akwai fitila a hannun shi.

Tace mik'o man kudin nace.

Na warware gefen zanena na kwance daurin na mika mata kudin, dai-dai lokacin da ya iso wajena.

"Subhanalillah "ya ambata yace ke yaushe kika fita ina kika je ruwa ya dokeki haka??

"Kallo yabi Innah dashi yace "ba nace kibar aza mata tallah ba?? Kuma tallah har ta wuce cikin kauyan nan da kauyu kan kusa damu har Katsina,ina laifin konan tashar Ado takai ai za'a saya,diya mace ce kuma zamani ya sauya yaran binnin ynxn basu da tarbiya sam ga karancin kunya,idan ta kwaso wa'innan halayyan fa,kuma acikin maza zata zauna akwai hadari sosai mata cikin maza hakan yake sa mace karancin kunya "ni dai dukar da kai nayi ga kyar mar sanyi inayi.

Kuka Innah ta aza "yanzu Malam duk abinda nike ma diyar nan baka ganii? Yanzu fa fada nike mata ta kai dare wannan wace irin tallah ce har dare "lallema Innah Rakiya gori fa ta gama yi man ,amman ta chanza magana.

"Yace ba haka nike nufi ba "tace kai dai kawai dan ba Ma'u bace ita da na haifa cikin cikina "Baba yace ya isa haka muje yace danii.

Nabi bayan shi ya bani fitilar hannun shi .

Dakina na shiga cikin sauri na jawo buhun da nike saka kayana,na dauki wasu riga da zani na saka naga zanen duk ya kode ba kamar rigar ba kallon su nike,ni da Ma'u ke da atamfar masaya tayi man kenan, kuma idan nayi magana a zageni har da duka tunda ubanta ya ɗin ka.

Na saka rigar taman yawa saboda Ma'u ta fini kiba,amman tsawan mu guda.

Na cire su, dama su kaɗai ne da basu yage ba a cikin kayan nawa sai na jikina da suka jike.

Haka nan na hada riga daban zane daban.

Baba ne ya shigo da kaskon wuta a hannu.

Nayi saurin mikewa na amsa nace sannu Baba "yace yawwa Nana bari na kawo maki abinci "na daga kai.

Jim kadan sai gashi da abinci nasan na shine dan kusan kullun abincin shi nike ci ba zai ci abinci ba sai naci hakan ya kara wutar kiyayya tsakanina da Ma'u da Inna.

Ya aje a gabana "kici nasan kina jin yunwa " jikina har kyarma yake saboda yunwa,na saka hannu ina ci har na gama ya mik'o man ruwa.

Baba!!

Jin yadda na kira sunan yasa yayi saurin ɗagowa.

Nace Baba wai menene sunana kaga *NANA* laƙabi ne kamar Nanah Fatima,khadiya,Maryam,Aisha,kaga kamar Ma'u Nana Asma'u ina son na sani ko dan koyi da mai sunana.

Shiru yayi har na wasu lokutta.

Ganin yadda fuskar sa ta chanza yasa nayi saurin cewa yi hakuri Baba bazan karama wannan tambayar ba.

"Babu komi yace,idan kin gama ki iskeni daki da littattafan ki ya kamata nayi maki sadaka idan kin gama Bulugul marram kuma nayi maki kyauta,sannan akwai tambayoyin da zan maki a cikin iziyyah "na ɗaga kai.

Shiru nayi ina tunanin bazan kara tambayar mahaifina sunana ba zan cigaba da amsa NANA amman naso nasan sunana,nace kila saina kara girma kana ya fada man , nasan Baba mutun ne mai ilimi zai sa man suna mai ma'ana.

Lumshe ido nayi ina tunanin maganar wani malami cikin littafin sa,idan yace *Ana sanin* *mahaifin ka da sunanka* sauri nayi na mike na shiga Bandaki nafito nayi alwala.

Bayan nagama sallah na dauki jikata nayi dakin Baba nace yau sanyi ya hanamu karatu a zaure kenan.

Sallama nayi ya bani izinin shigowa na shiga na iske Ma'u yana mata fada,muka hada ido ta wurgo man harara,na samu gefen ta na zauna.

"Yace haka kika ga yar uwar ki nayi?? Idan zata shigo sai na bata izini sannan yau insha Allah zata gama Bulugul marram a cikin babi na karshe take "ya dago ya kalleni yace koba a zikiru waddu'a'i kike ba "na daga kai.

"Yace amman ke har yanzu arba'una kike shima har yau ba kiyi rabi ba "cikin hadisi arba'in,yar uwar ki nada sama da Hadisi dubu biyu littafin Hadisi nawa ne a kanta ba zaki iya lissafawa ba.

Ran Baba ya baci sosai yadda yake mata fada kamar zaiyi kuka.

Kuma dan naje dakin Mahaifiyar ki nace kizo muyi karatu shine zaki banko man daki har kofata ta cire to da a kaina ta faɗo fa?

Sai a lokacin naga babu kyauren dakin.

"Yace buda inda kike kuma kibiya na jiya ko kuma naimaki yadda na saba kullun sai an maidoki baya "ta bude tana tura baki"

Kallon Ma'u nike nima ta so saman rai saboda yadda takema Baba kullun sai ranshi ya baci inde zamuyi karatun "Tace na manta "shiru yayi yana kallon ta "yace ba nace kije yar uwar ki ta ringa koya maki ba?? "tace Allah ya kyau amman bai ji ba.

Ta kalleni ta wurga mani harara kamar idon ta zai faɗo, kana tace "Batanan tallah take zuwa kuma sai dare take dawowa "yace kefa??

Kai tsaye tace "Niban tallah" shiru nan ma yayi ya girgiza kai.

Ya biya mata kana na bude ya ida biya man nawa, yayi addu'a yace yanzu tunda kin gama wannan kuma kinyi mukkutarur hadis kuma kinyi Riyadus salihin yanzu saura muwadda imam Malik.

"Ma'u ce ta mike a fusace ta fita "yabita da kallo ya safke a jiyar zuciya.

Ya gama yi man tambayoyi muka yi sallama.

Duk da maganganun Inna naman ciwo akan cewa ba Baba ya haifeni ba wai ni yar Zina ce shiyasa duk garin nan babu mai Sona.

Shiru nayi ina tunanin maganar ta zata iya zama gaskiya,amman kuma kullun Baba sai yace ni ne na haife ki shiyasa nafi kowa sonki,son da Baba ke man idan bashi ya haifeni ba bazai man wannan son ba.

Amman kuma banda dangi amman shima Baba ai ba dan nan bane Inna kawai ce yar nan.

Toko minene gaskiyar labarin??

*************

Zaune yake a cikin wasu Royal din kujeru Milk colour ya lumshe ido jin karar tafiya yasa ya bude runan nun idon shi da suka kada suka yi jawur tamkar garwashi.

"Asslamu Alaikum" a hankali ya bude idon shi cikin wata kasalalliyar murya marar sauti ya amsa ya kalli mutumin nan yace.

Please Dad help me!!

Bayan ya zauna ya kama hannun shi "yace *Annuwar* mike damunka?"

Dad Abie ne yayi maganar tamkar zaiyi kuka "Abie? "wayar shi tayi kara yasa hannu ya ɗaga, bayan sun gaisa sun dade suna waya shi dai Dad hakuri yake badawa.

Bayan sun gama ya kalli Annuwar yace "Mai Martaba ya fada man komi yanzu kaine baka da gaskiya "Dad wallahi bazan iya son wata mace ba bayan Princess.

Shiru Dad yayi nawani lokaci"haba Annuwar ya kamata kamanta da ita yarinyar da tadade da rasuwa"wallahi Dady bata mutuba"Dady yace a tareda kai muka kalli videon da suka aiko inda suke chaka mata wuka"sai kuma yayi shiru saboda yadda shima abin ya soshi ranshi.

Kayi hakuri kaje wajen Kursim yarinyar mahaifin ta nada kirki kuma tana sonka kayi hakuri kaje Katsina gobe.

Dady daman kaima dake goyan bayana a koda yaushe yau kuma kabi bayan Mai martaba Why Dad??

Ba haka bane inason ka bazanyi abinda zai zamo maka takura ba ko cutar wa, shekarun ka ya kamata ace kanada iyali Mai martaba yana cikin damuwa dalilin rashin iyali,magana ake a garifa ana cewa shiyasa baka zama kasar kowa da abinda yake cewa a kan ka,a shekarun ka ace bakada iyali kaga dole a zarge ka shi kuma Mai martaba dole abin ya dameshi.

Shiru yayi bau magana ba Dady yasan halinshi shiyasa bai damuba dan yasan bazai yi magana ba.

"Yace yanzu bari naje na kwanta dare yayi zuwa gobe zanje dakaina bama maganar waya ba akan ya karama lokaci ku faminci juna kaida yarinyar"sai a lokacin ya kalli Dady yayi murmushi"Murmushi Dady yayi shikade yasan halin dan nasa tunyana primary yake tareda shi har zuwa yanzu.

Fita yayi shi kuma ya mike ya nufi bedroom dinshi zama yayi bakin bed dinshi yana bin photunan su da kallo murmushi yayi yace banji a jikina baki cikin wannan duniyar ba.

Tashi yayi yaje bakin window yana kallon cikin Villah mtsww yayi tsoki yace duk akan wannan mulkin narasaki.

Kunnen shi yayi saurin rufewa tareda da idonshi.

**********
Asuba nayi na mike naje na zubama kowa ruwa a butarsa nayo alwala nayi sallah bayan nagama addu'a sai kuma na mike naje nakaima tumakin Inna abinci na share wajen,na cika ko ina da ruwan rijiyar dake tsakar gidan mu.

Ma'u ta fito tana mika tareda hamma tasa kafa ta ture ruwan butar dana zuba mata.

Ina hada wanke wanke ta iskeni babu magana ta mikoman buta nace mizan yi da ita??

Kallon banza tayiman tace"ruwa zaki saman saboda ban alwala da ruwan sama sanyi garesu"zanyi magana Inna ta fito daga daki ta tsaya tana bina da mugun kallo"tace idan bakiyi yadda nace kamar yadda kikayi dalilin zubar hawayen ta jiya da daddare kema yanzu zaki zudda naki"na amsa na mike naje na jawo mata ruwa na mika mata.

"Ta harareni tayi gaba"na koma na zukunna ina aiki.

Alwallah take amman ba ruwanta da hagu ko dama,shiru nayi ina wani tunani wai nan yar Liman ce, gidan karatu take,tosu sauran matan garin fa ya suke ibadar su??

Inama zasu yadda su daukeni nima tamkar diya irinsu,danashiga na koya masu yadda zasuyi ibadar su,Ma'u a cikin abokanta tafi kowa ilimi haka a garin tafi kowa ilimi shiyasa dan Mai Gari kesonta.

Kaf naji anjefoman buta nayi firgigi!!

"Kada kicinye man diya bakar mayya kallon ya isa haka"ashefa Ma'u nike kallo ina duk wannan tunanin.

Cikin sauri na Ida ta mike tace"ga buhu chan Yau ma zogala zaki dafa dan ta kawo kudii jiya buhu biyu zakiyi harda Rama zaki debo gonar Baban ku ta gefen gari"Jim nayi Ina tunanin dauko buhu biyu akwai wahala"cikin tsawa tace koba zakijeba ne!!"nayi saurin dauka nafita.

Yauma ratse na kamayi banson shiga mutane dan gudun wulakan ci.

Ina isa na iske su Shatu suna wasa kawata ce bafulatana ce ga gonar su gata Baba kuma tare muke tallah ita nono ni kuma fura, baban su yanada mutunci shiyasa suke mutunci da Baba rugar su babu nisa.

"Tace lah Nana"duk duniya bayan Baba dakeso na sai ita kade ta taba nunaman soyayya shiyasa nikesonta"baki na washe nace Shatu mai nono"tace yau ban fita tallah kiwo nazo"nayi murmushi"tace muje na tayaki"tare muka dibi Zogalan da Rama,koda muka gama mungaji bakin wata bishiya muka zauna cikin gonarsu ga rana ta tafara dan goma ta kusa,kosai ta mikoman"tace gashi mucii dazun jabe ya siyoman shi a kauyan ku"na amsa naci taban ruwa nasha najini dai-dai.

Nace bari naje kada na makara zan gyara zogalan tallah zan fita"tace muje na kama maki tunda jabe na wajen shanun"Nace lah barshi na gode"tace wallahi sainaje cikin Hausar ta dabata fita,na dauki guda ta dau guda,muna tafiya muna fira har muka isa bakin kofar gidan mu,tace bata shiga nace ai nagode saboda nasan dalili.

************

A hankali ya bude idonshi jin ana huramashi ido, kan fuskar wata yar matashiyar budurwa ya sabke idonshi wadda shekarunta zasu kai goma sha biyar itada kanenta shima zai kai shekara sha biyu,dariya suke ganin ya bata fuska yasa suka kalli juna,sai suka kama kunan su cikin shagwaba suke"ohh sorry Broth Annuwar Dad ne yace kafito ayi Breakfast dakai Momy ma is waiting for you.

Hannu ya daga su duka sukabar wajen.

Kallon yakai akan photunan dake kusa dashi daya ya dauka shida wata yar yarinya jikin photun zatakai shekara tara,kiss yakai a saitin fuskar ta yace I love you My princess.

Toilet yanufa yayi wanka yazo ya shirya cikin kananun kaya ya fito.

A parlon Momy ya iskesu"Dad yace tahonan My Son"kusa da kujerar Dady ya zauna suka gaisa da Momy yamaida kallon sa ga Dady suka gaisa daga haka baice komi,abinci aka zuba mashi kalar wanda akasan yana chii.

Bayan sun gama har ya mike"Momy tace Anty Amina tana bukatar magana dakai tace kakirata"kai ya daga ya juya"tace Annuwar yau Momyn ce kake fushi da ita??

Juyowa yayi sai kuma ya tsaya"tashi tayi ta iskeshi inda yake tsaye"Dady yace inada meeting zamuyi magana anjima,shima ya fita.

Kamashi tayi suka shiga Bedroom din ta zaunar dashi.

Yace Momy please kinsan banason hayaniyya banason ayima rayuwata kutse,miyasa lokaci guda ku duka zaku juyaman baya saboda Kursim??

Inason nayi rayuwata batareda an takura man itaba inason na zauna nikade.

Shiru tayi tace"kayi hakuri Anty tace ka budewa wayar ka kuyi magana amman kayi kokarin cire MANAL a zuciyar ka"jin jina kai yayi ya wuce.

A parlo ya zauna ya runtse idoo yana tunanin tayaya zai cire Manal a ransa??

Miyasa gabana ke faduwa a duk lokacin da aka ambaci Katsina???

Qurrah

Share and comment plx
[1/28, 3:02 PM] GOLDEN PEN WRITERS ASSOCI: *JARABTAR MU*


*Writing by-* *Qurrah*

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/



*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*




*~We are bearer's of so golden pen🖊~*

*~we write assidiously perceive no pain~.*

*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*

*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*



DEDICATED TO...MY SISTERS😘



Page-3&4



*~Abin Da Ake Fada idan aka firgita~*



لاَ إِلَهَ إِلاَّ الله


La ilaha illal-lah
Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.




-----------------Innahlillah kawai yake ambata, saboda yadda zuciyar shi ke bugawa akai-akai.

Wayar sa ya kunna, yana kunnawa sunan Abie ya bayyana yana kiran shi, har ta kusa tsinkewa ya kasa dauka, sai chan yayi saurin dauka yayi sallama, dayan bangaren Abie yace, "Yarima me kake nufii dani, na zama karamin mutum nace za kazo yau shi ne ka koma Abuja!?".

"Abie kayi haku.....!!".

Tsawar da Mai martaba yayi yasa Yarima toshe kunnenshi, daman Bluetooth ne a kunnen shi da shi yake waya. Runtse ido yayi yana jin zafi a zuciyar shi, wannan wace irin Jarabta ce yake so ya shiga tsakanin shi da Abie har da tsawa.

Yau ita ce tsawa ta farko a tsakanin su, kullum Abie cikin tattalin shi yake da nuna so da kauna.


Kashe waya Abie yayi, Annuwar yayi zaune bakin gado wani irin zafi mai radadi yake ji a zuciyar shi, maimakon ya saduda sai ma kara tsanar Kursim da yayi a zuciyar shi.

Maimakon sati daya, mai martaba ya maidashi wata daya a Katsina, ta yaya zan zauna inda ban sani ba har tsawon wata daya??

Gashi na tsani garin, koya aka ambaci Katsina sai naji wani irin faduwar gaba.



****************


"Wash!", nace tare da zama ina lumshe ido, na gaji sosai. Inna ce ta fito tace, "zaman mie kike anan??".

Nace; "Na gaji ne Inna".

"kin gaji inma dan dumamen da nayi kike mawa to ki daina, dan an cinye idan kin dafa zogala zan dan dan maki, shi ma dan kiji karfin yin tallah".

Na mike na samu wani buhu na joluye zogalan na gyara.


Koda na safke zogalan rana tayi nace Inna zanyi wanka, "tace wanka kuma? daman neman maza kike zuwa ba tallah ba?? shi yasa kike saidawa"!.

Nace, "wallahi Inna masu saye sunfi son mai tsafta, shi yasa ake sayen nawa da wuri".

Tsaki tayi tace, "sai kiyi sauri dan a kasa zaki, banda kudin mota". Ido na zaro cikin mamaki. "Kas.....?!!".

Kallon da tayi min yasa na kasa ida maganar, nayi saurin daukar bokiti nayi bandaki, ina fitowa naje daki na shafa mai, d'an sauran turaren da Yaya Maimuna ta kawo min na balle inda ake sawa na goge ga kayana, sunsunawa nayi na lumshe ido a duniya Ina matukar son kamshi yana sani farin ciki,Yaya Maimuna ita ce Babba wajen Inna, sai Yaya Auwalu dake neman kudi Abuja, ita Kuma Manii take aure duk zata zo turare shi ne tsarabar mu, amman Inna bata sani ba ta dade bata haihu ba sai akan Ma'u, shi yasa duk wani tanadin ta Ma'u dai komi.

Na mike na saka silifas dina da suka sha wanki
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment