Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[1/2, 8:57 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️


By

Maman Maama

To my daughter Haleema, May you forever be blessed.


Bismillahir Rahmanir Rahim


Godiya ta tabbata ga Allah da ya bani damar fara wannan rubuta, ina rokonsa ya bani ikon rubuta alkhairi ya kuma haneni daga rubuta sharri. Allah ya sa wannan rubutu ya amfane ni da duk wanda Allah ya bawa ikon karantawa.

Littafin DIYAM kyauta ne, ina fatan ya zamanto min sadakatujjariya har bayan raina. Na sadaukar da wannan littafin ga masoyana, na fili dana boye.

Diyam is a total work of fiction, in yayi dai dai da labarin ki/ka to coincidence ne ba wai da niyya ba ne.

Diyam littafi nane, mallaka ta ce, duk wanda ya juya min littafi ko ya siyar min ba tare da sani na ba shi da Allah.

Just follow my pen for I assure you, you are going to fall in love with DIYAM.


Episode One


Madaidaicin dakin karatun mai dauke da dalibai 36 yayi shiru bakajin motsin komai sai na takardu, sai kuma very clear voice din lecturer da take gabatar da lecture ga dalibai masu karantar ilimin law a makarantar Blavatnik school a cikin Oxford University. Darasi ne suke yi akan marital laws, inda malamar take yi musu bayani dalla dalla game da dokokin da suka shafi auratayya. Saboda kasancewa daliban sunzo ne daga mabanbanta kasashe, wannan yasa malamar take daukan kasashe daya bayan daya take musu bitar dokokin kasashen da niyyar in sun gama sai su hadu suyi comparing aga wadanne ne sukafi kyau kuma wadanne chanji ya kamata a samar.

A yau ne kuma malamar tashigo kasashen nahiyar Afrika. Ta fara da Nigeria, the giant of Africa. A nutse ta fara karanto wa daliban dokokin da kasar Nijeriya take dasu wadanda suka shafi auratayya. Suna tsaka da daukar darasin ne suka ji snicker, malamar ta dakatar da karatun da take yi ta dago kanta a tare da duk sauran daliban suka kalli sashen da dariyar ta fito.

A extreme end of the class room, sitting alone like an abandoned island, wata kyakkyawar budurwa ce wadda kallon farko in kayi mata daga nesa zaka ce kyakykyawa ce, in ka matso kusa da ita kuma sai kaga tafi yadda kake tunani kyau, as kana cigaba da kallon ta kyawunta yana cigaba da bayyana a gare ka. Da yawa a makarantar ana yi mata kallon balarabiyya amma nigerians suna ganin ta suke fahimtar cewa tasu ce, kabilar fulani ce, kabila mai dangantaka da larabawa. Daga ganinta zaka fahimci ita kanta bata san cewa tayi dariyar ba. Shirun da taji ajin yayi da kuma feeling na cewa ana kallonta ya saka ta dago kanta da sauri, dara daran idanuwanta a bude kuma ta saka su a cikin na malamar da take tsaye a gaban desk dinta. Suka tsaya suna kallon kallo sannan malamar tace mata "why do you laugh? Are you finding this funny?" Ta girgiza kanta da murmushi a gefen kumatunta. Malamar ta koma kusa da podium ta tsaya tana kallonta sannan tace "where are you from?" Still kanta a kasa tace "Nigeria" malamar tace "menene ra'ayinki game da wadannan dokokin na auratayya a Nigeria. Kina ganin sunyi dai dai ko kina da gyara?" Shiru ta sake yi na wani lokaci, sannan tayi karamar dariya tana girgiza kanta, fuskarta na nuna cewa akwai abinda yake damunta, suddenly kuma sai tayi magana "bani da gyara ma'am. Saboda all those laws da kike lissafawa a rubuce kawai suke, maybe for the sake of the likes of you da zasu nema for educational purposes, amma ba wai amfani ake yi dasu ba" malamar looked interested, tace "so, can you tell us the situation of marriage in Nigeria?" Nan take murmushin fuskar budurwar ya dauke, ta hadiye wani abu a makogwaronta sannan ta sunkuyar da kanta tana kallon rubutun da yake gabanta. "You have a very beautiful handwriting kanwata" taji muryarsa a kunnenta as clear as if yanzu yake gaya mata.

Ta dago kanta tace "in Nigeria ma'am, northern Nigeria to be precise, marriage is just like a form of legal slavery" gabadaya hankalin yan ajin ya koma kanta, har wadanda ada suke yan rubutun su yanzu sun juyo suna kallonta. Ta cigaba cikin yaren turanci mai dauke da nigerian accent "tabbas kafin aure akwai kalmomin i love You, amma yawanci a baki suke tsayawa basa karasawa zuciya, daga zarar anyi aure miji will have a feeling similar to feeling din da master yake ji a lokacin daya sayi slave. Like since I pay your dawry it means like I own you, you belong to me. Sai ya manta da cewa shi da matar belong to each other. Wadansu mazan ko first year ba zata wuce ba zasu juye su zamarwa matar like total stranger, like bata taba sanin sa ba a rayuwarta.

"Na sani cewa kusan more than 80% na mutanen mu na arewa musulmai ne, kuma na sani cewa a Alqur'ani ance 'alrijali qawwamuna alan nisa'i' miji shine sama akan mace, amma kuma da ubangiji yayi gaba kadan a Alqur'ani sai yace ya sakawa maza wannan qawwamar ne saboda su ya dorawa nauyin ci da sha da sutura da muhalli. Amma a halin yanzu more than rabin mazan mu basa iya daukan wannan nauyin da Allah ya dora musu. Mata da yawa su suke ciyar su shayar su kuma tufatar da kansu da yayansu wani lokacin ma harda mazajen na su. Mace zata fita ta je office neman kudi ko kuma ta fita saro kayan sana'arta sannan ta dawo ta girka abincin data siyo da kudinta ta, tayi shara da wanke wanke da wankin kayanta dana yaranta da na mijin, kayan kuma da ita ta siya da kudinta, ta taya yaranta yin homework din da aka basu a makarantar da ita take biya musu kudin makaranta, sannan kuma mijin yayi expecting zata kai masa ruwan wanka tayi masa ta shirya shi tayi masa tausa sannan ta biya masa bukatarsa a shimfidar auren su".

"Mace ce zata yi ciki, ta haihu, wata ma hatta ragon suna da kayan fitar suna ita zata siya, ta shayar da dan ta ciyar dashi da komai amma idan rabuwar aure tazo sai mijin yace 'ajjiye min yayana'. Tana ji tana gani, tana kuka yayanta suna kuka, haka za'a raba su mijin ya dauka ko daya ba za'a bata ba, kuma a karshe shi din daya dauka sai yaje ya kaiwa matarsa ita kuma ta azabtar dasu ta bautar dasu saboda ba ita ta haife su ba. Yara da yawa sun rasa ransu saboda irin haka, wadansu sun salwanta, wadansu sun koma almajirai, wadansu yan daba saboda babu tarbiyya, babu soyayyar iyaye". Ta goge hawayen da ya taru a idonta ta cigaba

"That's why am here in Oxford, that's why am studying law. Saboda in tabbatar cewa babu wata mace a Nigeria da zata sake shan wahala a hannun namiji"

"Ohh shut up please"

Duk class din suka juya suna kallon wanda yayi magana. Ta san shi, tana ganin sa a ajin amma basu taba magana ba dan haka ko sunansa bata sani ba kuma bata da interest din sani. Ya juyo yana kallonta yace "just because kin zauna a kusa da wadanda basu ji dadin aure ba bai kamata ki zauna a nan kina fadin maganganu marasa dadi akan kasar mu ba" ta daga gira daya sama tana kallonsa tace "wacce kasa kenan?" Yace "wacce kike magana akanta" tace "you don't look like Nigerian, and definitely not a northerner" yace "ohh but I am" tace "which part?" Yace "Abuja" ta dan rufe bakinta tana dariya tace "but Abuja is not in the northern Nigeria, so you shut up".

Ya kara bata rai musamman ganin dariya a fuskar daukacin yan ajin. Shi dai yasan duk da shi ba dan arewa bane ba amma ba zai bari a zauna a yaga arewa har haka ba, for his mother is from the north, his only sister now lives in the north, his uncle too, dan haka ya san hakkinsa ne ayanzu ya gayawa mutane cewa karyace kawai yarinyar ta shirya musu, maybe dan tayi suna.

Yace "I may not be born in the north, but my mother is a northerner, kuma...." Tace "was she born and raised in the north?" Dan shiru din da yayi yasa ta fahimci no ce amsar sa, ta daga kafada tace "then she too is not a northerner" da sauri yace "her father was" ta sake cewa "born and raised?" Ya mike tsaye, frustrated, yace "what does it matter?" Tace "everything. In kana son sanin halin da al'umma suke ciki you need to live with and study them". Ya sake yunkurowa da niyyar sake kokarin kare mutuncin kasarsa kamar yadda yake tunani amma sai ya zamanto period din ta kare. Yayi kwafa sanda malamar take bayanin cewa zasu dakata anan sai next class zasu cigaba.

DIYAM..........writing


In anyi comments da yawa zanji dadi, kuma zan fahimci ana son in cigaba.
[1/2, 8:57 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Two

Washegari basu da madam Sally, malamar da tayi musu lecture din jiya, a takaice ma lecture din safe kawai suke da ita shikenan sun gama. Wannan yasa suna fitowa kowa ya fara kokarin tafiya gida dan gabatar da al'amuran sa na yau da kullum. Yarinyar jiya ce ta fito a karshe, tana rungume takardu a kirjinta da hannu daya daya hannun kuma tana rike da wayarta, tana ta waige waige kamar me neman wani sai kuma ta fara tafiya a hankali tamkar mai jin tsoron taka kasa.

Daga inda yake tsaye yana hango yadda daliban suke fitowa daya bayan daya. Ya dauko pack din cigarette a aljihunsa da lighter ya kunna yayi mata dogon zuka ya lumshe ido. Deliberately ya riga kowa fitowa saboda yana son ya ga fitowarta, yana son su cigaba da maganar jiya, yana so kuma ya ja mata kunne akan tasan maganar da zata fada tasan kuma a inda zata fada. Ya danyi karamin tsaki. Haka kawai tana neman ta zubar masa da class a cikin mutane dan duk friends dinsa sunsan shi ɗan Nigeria ne kuma zasu dauka abinda ta fada gaskiya ne.

Yana kallonta ta fito, ta danyi dube dube sannan ta taho direct zuwa side din da yake, tana tafiya a hankali tamkar mai kirga takunta wanda hakan ya bashi damar karewa siffarta kallo, 'too beautiful' yayi deciding, 'too beautiful for my taste'. Har tazo ta wuce shi bata ko lura dashi a gurin ba, ya bata dama ta danyi nisa sannan ya yar da cigarette din hannunsa ya bita da dan sauri yace "hey" ta dan tsorata kadan sannan kuma ta kalle shi ta dauke kai ta cigaba da tafiya, ya daidaita takun shi da nata ya sake cewa "hi" ta dakata tana kwallonsa cikin ido ba tare da ko alamar tsoro ba tace masa "Assalamu alaikum" ya dan shafa kansa yana jin duk confidence din da ya ke dashi yana draining. Her eyes makes him uncomfortable. Jin bai amsa ba yasa ta sauke idonta kasa ta cigaba da tafiya. Ya bita a baya yana cewa "my name is Sadiq, Sadiq Abubakar Sadiq" ya sake shafa kansa yace "my God, this is so awkward, I always feel like this duk sanda nake introducing kaina. I hate my name. Na rasa dalilin da yasa iyayen mu suke son lallai sai sun saka wa yayansu sunan iyayen su. I mean, it make the name only circles and remains in the family. I always wish I can change my name" ta daka ta ta tsare shi da ido, ya dauko handkerchief a aljihunsa ya goge fuskarsa duk kuwa da cewa ba gumi yake ba, he obviously looked nervous, duk planning din da yayi na irin maganganun da zai gaya mata ya gudu ya barshi. A zuciyarsa ya gode wa Allah da ya zamanto su kadai ne a gurin. Yayi ajjiyar zuciya yace "I am talking too much, aren't I?" Ta girgiza kai kawai sannan a nutse tace "in my religion, Islam, an bawa mutum damar chanza sunansa in baya so, what you only need to do is ka sayi rago ka yanka da niyyar ka chanza suna, sai ka kira mutane su shaida, shikenan. But I don't know ko naka addinin ya yarda da haka" he was stunned, wato kallon wanda ba musulmi ba take masa, how can she even think that? Ya bude baki zaiyi magana amma ya kasa cewa komai, sai daya hadiye wani abu mai daci a makogwaronsa sannan a karshe yace "I am a Muslim also" ta dauke kanta tace "sorry, my bad" cikin jin zafin maganar ta yace "me yasa kika yi tunanin ni ba musulmi ba ne ba?"

Ta kalle shi tun daga kan brown wind tossed hair dinsa, his cigarette stained lips, katuwar head phone din dake kunnuwansa, shirt dinsa da take dauke da katoton hoton Lady Gaga, wandon sa da yake tsatstsage daga guiwa, zuwa takalminsa da yafi kama dana sojoji, sannan ta daga gira daya sama tace "na farko you don't dress like a Muslim, na biyu nayi maka sallama baka amsa ba, na uku muslims don't complain about their parent's choice of name, Abubakar Sadiq suna ne mai dadi kuma mai daraja" he was speechless, tunda yake ba'a taba yaga shi irin yau ba, me wannan yarinyar take tunani? Wacece ita? Babu abinda yake so a lokacin irin ya hada wa kyakkyawar fuskanta jini da majina. Ya dunkule hannu amma sai jikinsa yayi betraying dinsa har ta juya ta barshi a tsaye, instead, sai yaji bakinsa yana furta "baki gaya min sunanki ba" ta juyo tace "why?" Ya maimaita "why? I just told you my name that's why" tace "I didn't ask you for it" daga haka bata kuma cewa komai ba sai ma kara sauri da tayi.

Ya dunkule hannunsa ya naushi iska, ya rankwashi kansa yana jin haushin kansa sai kuma ya shafa gurin daya rankwasa alamar yaji zafi, gaskiya ya fara sanyi da yawa, har shi mace zata yiwa haka? Who is she?

Daga bayanshi yaga wata yarinya tazo ta wuce shi da sauri tana kira "Diyam!! Wait for me" yaga ta tsaya ta jirata ta karaso sannan suka cigaba da tafiya tare. "Diyam" ya maimaita, how can someone name his child water? Me parents dinta suke tunani? sai kuma ya koma gefe ya samu guri ya zauna, ya dauko sigari ya kunna, ya gyara zaman headphone dinsa ya zuki tabarsa ya lumshe ido yana lissafa hanyoyin da zai rama abinda Diyam tayi masa.

*****. *****. *****

Diyam taji kiran da akayi mata, ta juya suka hada ido da kawarta Judith, kawarta ce tun a Nigeria suka hadu lokacin suna shirye shiryen tahowa UK, a lokacin da suka yi registration ne Diyam ta fahimci cewa Judith tana neman gidan zama sai kawai ta jata suka zauna tare a nata gidan, tare da Murjanatu. Tayi mata murmushi lokacin da Judith ta karaso suka jera suka cigaba da tafiya a tare. Judith tace "if you don't mind me asking, were you talking to that guy?" Diyam tace "yes I was, what about it?" Judith ta danyi dariya tace "it is just that you never talk to anybody" Diyam ma tayi dariya tace "believe me, it wasn't such a good talk. Am sure that guy is never going to talk to me again" suka yi dariya baki daya, Diyam ta dafa goshin ta tace "God, am so boring, how do you guys manage living with me?" Judith tace "it is never easy" haka suka cigaba da tafiya suna hira akan halayen Diyam.

A kafa suka tafi estate ɗin da gidan su yake, suka je block E suka hau lift zuwa fifth floor inda apartment dinsu yake. Judith ta fito da key din hannunta ta bude kofa. Suna shiga a parlor duk suka zube a kasa saboda gajiya. Murjanatu ta fito daga kitchen da spatula a hannunta tana kallonsu, black beauty ce, mai dan karamin jiki, manyan idanuwa da cikar gashin gira. Kana ganinta zata yi maka kama da irin shagwababbun yaran nan wadanda suka taso cikin naira, tace "shi yasa naki zuwa yau. Haka kawai akan lecture daya bazan sha wannan wahalar ba" diyam ta kalleta tace "kinyi missing, alot" Murjanatu ta karkata kai gefe tace "at least ai nayi muku girki ko? So what you should be saying is 'thank you'" Judith ta mike tayi pecking Murjanatu a cheek dinta tace "thank you".

Suna cikin cin abincin, wanda Diyam chakula kawai take kamar mai cin magani tana ta complain din how much she misses abincin gida. Tace "I can give anything, I mean anything, dan in samu tuwo in ci" Murjanatu ta tabe baki tace "niko ko missing tuwo banyi ba, sam dama ni ba sonshi nake yi ba" Wayar Diyam tayi kara ta kalleta kawai ta dauke kai. Judith ta dauka tana kallon sunan mai kiran har ta katse sannan ta ajiye tace "ban taba ganin marar zuciya irin mutumin nan ba, wulakancin da kike masa Diyam ya isa haka" Murjanatu ta daga hannu tace "hey, yayan nawa kike cewa marar zuciya?" Tana yin shiru wayar ta tana yin kara, ta langwabar da kai tace "Please Diyam, kinga ya kira a wayata. Please just for today" Diyam ta harare ta bata ce komai ba, Murjanatu ta daga wayar ta gaishe da wanda ya kira tana kallon Diyam tace "lfy lau take, yanzu muka dawo daga lecture wallahi duk mun gaji yaya. Eh bata zuwa da motar wai exercise ne zuwa school din. Eh shikenan for today. Gata nan tana cin abinci. Bata ci da yawa wallahi yaya, wai tuwo take so. Ah ah ni ban sani ba wallahi. Yaya ni Wallahi ban iya tuwo ba. Okay, sai anjima" ta ajiye wayar tana turo baki fuskarta kamar zata yi kuka tace "wai inyi miki tuwo yau da daddare ince with love from him" duk suka yi dariya, Diyam ta tashi tana rawa tana yiwa Murjanatu gwalo ita kuma ta dauki pillow ta bita da gudu suka shige corridorn da bedrooms dinsu suke.

Diyam.......... writing
[1/2, 9:01 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Three

Bayan tafiyar su Diyam, ya jima zaune shi kadai, yana ta sakawa yana kwancewa yana kuma zukar hayaki zuwa hunhun sa. Sai da ya ga kwalin ya kare sannan ya jefar da shi ya duba agogon hannunsa yayi tsaki ya mike. Cab ya tare zuwa hotel din da ya ke. Yana shiga dakin ya zauna akan gado yana kare wa dakin kallo kamar yau ya fara ganinsa, idonsa ya sauka akan hoton wata yar kyakkyawar budurwa akan study table dinsa tana murmushi. Ya lumshe idonsa ya bude. She have been the reason for everything daya ke ciki a yanzu, for all his pain and his agony. Ya dauko wayarsa yayi dialing number dinta for the hundredth time amma yanzu ma kamar ko yaushe bata dauka ba. He wandered me yasa ba tayi blocking dinsa ba dan gwara ya kira bata shiga ba akan ya kira ba'a dauka ba, meaning ta gani kenan, meaning tasan all what he is going through but she just doesn't care.

Fatima sunanta, Khausar suke kiranta, he had been in love with her for as long as he can remember, maybe tun da yasan menene love din but he failed to tell her. Daga baya kawai sai yaji labarin wai zata auri brother dinsa, that has been the beginning of his agony, wannan ne asalin dalilin fara shan sigarin sa. Yayi iyakacin kokarinsa tun a lokacin dan ganin cewa ya cire ta a ransa and he succeeded a little, but then sai auren baiyi da brother din nasa ba and his brother ended up marrying another. Wannan turn of events din ba karamin faranta masa rai yayi ba, he saw it as another chance na auren wadda yake so.

Shekara guda kenan da faruwar hakan. A cikin shekarar ne kuma yayi failing terribly in his course of study a Abuja, amma sai ya alakanta hakan da cewa dan baya son course din ne, yace yafi son yabi footprints din maternal grandmother dinsa

Please Login or Register in order to submit comment