Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tare data kalleta ba tace "sure. Wani abu ne" Diyam tayi tsaki tace "Will you please stop telling him duk abinda nake yi? I need some privacy and some space" Murjanatu dai bata ce mata komai ba har ta yi mata banging kofar ta tafi, sai kuma tayi murmushi a hankali tace "hypocrite". Sai da Diyam ta gama duk abinda zata yi ta yi shirin bacci sannan ta dauko wayarta ta tura masa reply

Thanks

Ta jima tana kallon kalmar, tana so ta kara rubuta wasu kalaman no matter how small wadanda zasu nuna masa irin yadda take ji a zuciyarta a game dashi amma ta kasa. Bata so tayi giving up, not now, not ever. Haka ta tura masa kalmar guda daya ta koma ta kwanta tana jin ranta babu dadi.

Bassam kuma ranar kasa bacci yayi, yayi ta tossing akan gadonsa. Abu na farko daya ke ransa shine sabon aikin daya samarwa kansa, yaji dadin aikin nasa sosai dan shi tunda yake bai taba aikin neman kudi ba, komai yi masa ake yi. Yanzu yasan at least bashi da fargabar running out of money. Abu na biyu kuma da yake ransa shine Diyam, ya rasa dalilin da yasa yarinyar ta tsaya masa a ransa tun encounter dinsu ta farko, he just can't stop thinking about her. A haka har bacci ya dauke shi. Cikin dare ya farka idonsa ya sauka akan hoton Khausar dake kan bedside dinsa, ya saka hannu ya kife hoton ya juya ya cigaba da baccin sa.

Ranar Monday ya rigata zuwa hall dinsu. Sai ya zauna akan kujerar da take kusa da wadda take zama koda yaushe ya dauko littafi yana bubbudawa kamar mai karanta wa amma sam hankalinsa baya kai, hankalin sa yafi karkata zuwa ga kofar da students suke shigowa zuciyarsa tana kara dokanta da son ganinta. Can ya ganta ta shigo, suna hada ido tayi masa murmushi and all his problems melted away. Tun kafin ta zauna lecturer dinsu ya shigo dan haka basu yi magana ba suka mayar da hankalinsu kan lecture. Amma Diyam tana lura dashi yafi mayar da hankalinsa gurin kallonta maimakon gurin lecture, and her heart sank.

Lecturer yana fita ya juyo gaba-daya gurinta yace "so, miss Nigeria, you are from Yobe state, right?" Ta dan bata rai tana kallonsa tace "Yobe kuma?" Yace "eh, rannan kince min sunan ki Haleema Usman Kollere, and I know Kollere is in damagum local government, yobe state" tayi dariya tana rike baki tace "you are amazing" yayi murmushi proudly yace "I know my geography" ta mike tsaye tana zuba kayanta a jaka, shima ya mike, tace "You surely do, but I am not from Yobe. Kamar yadda na fada ranar nan ni yar kano ce, yes, my grandparents na uwa da uba duk fulanin Kollere ne amma ni a kano aka haifeni, kano ne a birth certificate dina dan haka kano nake amfani dashi" suka jera suna fita daga ajin tace "so you are from Abuja, where in Abuja are you from?" Yace "somewhere" ta tsaya a waje tana kallonsa tace "wayo ko? Wato ni na bude baki na gaya maka daga inda nake shine kai kuma zaka wani ce min somewhere ko?" Yace "a,a ke fa kawai kince min ke yar kano ce, kano ai tana da girma" direct tace masa "Municipal. Yakasai. Kai fa?" Ya sosa kai yana kallonta, taga bashi da niyyar fada tayi gaba tace "ohhh, I hate stingy people" ya biyo ta da sauri yace "I don't want to lie to you, kinfi karfin haka. And I also don't want to tell you yet" tace "saboda me?" Ya sake yin shiru. Ta karkata kai tana kallonsa tace "someone as shiny as you must have come from the Villa, not less" yayi dariya yace "You are wrong, ko kusa da Villa ban kai ba" tace "where then?" Ya kalli surrounding din gurin yace "ina zamuje ne naga mun fito waje" ta gane so yake ya chanja maganar tace "cafeteria, yunwa nake ji, I over slept har na makara kuma munyi fada da Murjanatu taki tashina" yayi dariya yace "me ya hadaku?" Tace "girl's stuff, you won't understand" ya rungume hannunsa a kirji yana kallonta yace "stingy, are we?" Tayi dariya tace "ba zaka gane ba fa" yace "okay, let's go. Nima banyi breakfast ba".

Shi yayi musu order abinci, bacon and eggs, da coffee. Suka fara ci sannan yace "so, how did a Fulani girl daga rugar Kollere ta samu kanta a Oxford?" Ba tare data kalleshi ba tace "luck" yace "hmmm?" ta ajiye chokalin hannunta tana kallonsa tace "you talk about kaddara ranar nan ko? To ita ta kawo ni nan, I was destined to be here and here I am. How about you? How did a guy from somewhere in Abuja find himself here" shima yace "luck" ta daga gira daya sama tana kallonsa sannan yace "okay, I was lucky to be born into a wealthy family" tayi murmushi tace "Villa?" Yace "definitely not" sukayi dariya baki daya.

Ranar kusan tare sukayi komai, har suka tashi daga school suka kuma tafi tare, sai daya rakata har bakin block dinsu sannan yayi mata sallama ya tare cab zuwa gurin aikinsa. Yana jin zuciyarsa fari kal kamar takarda, duk wani bacin rai da stress duk ya gushe daga ransa. He is finally finding happiness.

Diyam kuma tana shiga parlon su ta yarda jakarta ta kwanta ta lumshe ido, tana jin Judith ta shigo parlon tana yi mata magana amma sai tayi pretending kamar bacci take yi nan kuwa idonta biyu, lissafi kawai take yi a ranta. Most of the time shi yasa tafi son zaman makaranta saboda in tana can tana mantawa ne da duk wasu problems dinta amma tana zuwa gida sai taji kamar damuwowinta jiranta suke yi a bakin kofa. Jiya da daddare sukayi rigima da Murjanatu, kuma ita tasan Murjanatu gaskiya take gaya mata, tasan yaudarar kanta kawai take yi taki admitting hakan. Ta dauko wayarta tana kallon hoton dake kan screen din tana murmushi, sai kuma ta shiga cikin ta fara kallon pictures tana ta dariya ita kadai. She missed Nigeria sosai, but wannan zaman da take, wannan karatun da take, shine kadai solution dinta a yanzu. Me yasa mutane including Murjanatu suka kasa fahimtar hakan?

Sai bayan la'asar Murjanatu ta dawo. Kafin nan Diyam ta shirya musu pasta saboda tasan Murjanatu tana so duk dan su shirya. Tana shigowa kallo daya tayi wa Diyam ta kara tura baki gaba ta wuce daki, sai da tayi wanka ta shirya cikin riga da wando budaddu kalar ruwan toka da suka kara wa bakar fatar ta kyau sannan ta dawo parlon ta tsaya ta rike kugu tace "shine kika taho kika barni ko? Kuma na tambaya ance min tare da wannan tsinannen Bassam din kuka taho" Diyam ta mike zaune tace "ayyah Fanna, karki tsine masa, kinsan bakin ku dafi ne dashi, kar kisa ya tambade shi da baiyi miki komai ba" Murjanatu ta zauna ta dora daya kan daya tace "tunda yake kula matar yayana ai yayi min laifi, kuma wallahi daga ke har shi ku shiga hankalinku idan ba haka ba yana zuwa next week sai na gaya masa, kuma kunsan sauran" Diyam tace "oh oh, to gaya masan mana, an gaya miki kowama tsoronsa yakeji kamar ke, ni kinsan daga ke harshi dai dai nake daku. Naci nasha tsumin fulani barebari sai dai su ganni su barni" nan kuma suka koma wasan fulani da barebari, sannan suka ci abincinsu tamkar ba sune jiya suka yi fada ba.
[1/6, 10:32 AM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Seven : The Phone Call

Tun daga ranar Diyam da Bassam suka hade, kullum a school suna tare duk ya daina kula friends dinsa ita kuma dama bata dasu, daga school kuma zai wuce gurin aikinsa, anan zai samu kudin kashewa gobe. Sosai yake jin dadinsa hankalinsa kwance as if bashi da wani problem.

Ranar Thursday suna lunch a cafeteria kamar kullum, Diyam ta tambaye shi "can you tell me about that not laughing situation da kace kana ciki? Because I can see yanzu kana dariyar" dariyar yayi sannan kuma ya hade rai yana jujjuya abincin gabansa yace "I got fired" ta zaro ido tana mamaki, fuskanta cike da concern tace "daga gurin aikinka? When?" Yace "no, ba daga gurin aikina ba, I got fired from my family" ta hade rai tace "your family? Ta yaya za'ayi familyn mutum su kore shi? Me kayi Bassam? What happened?" muryarta tana breaking kamar zata yi kuka ta tambaye shi, ba tare daya kalleta ba yace "nayi laifi, babban laifi, maimakon in tsaya in fuskanci hukunci na kuma sai na gudu na kama daki a hotel nayi zamana. When I did that na saka ran kwana biyu ba zasu wuce ba mami na da Daddy na zasu zo kasar nan, nayi tsammanin zasu zo har dakin da nake, nayi tsammanin karbar wadansu kyawawan mari daga Daddy na kuma yi tsammanin in samu nasiha daga mami amma shiru, basu zo ba ballantana su fada min cewa nayi ba dai dai ba ballantana su kaini gurin Aunty na da nayi wa laifi su saka ni in bata hakuri" ya dago ido yana kallonta cikin ido yace "basu zo ba ba kuma su kira ni ba, they just cut me up, basu zo ba ballantana suyi min maganin problem dina, at least ko shawara ce su bani". Tana kallonsa tace "wanne problem ne kenan? Your smoking problem?" Ya girgiza kai yace "basu san wannan ba ai" sai kuma ya bata labarin feelings dinsa for Khausar, da kuma yadda ya tarar tana dating cousin dinsa Ayan, tun daya fara bata ce komai ba har sai daya gama sannan tace "how old are you Bassam? You know nothing about love, do you? That girl doesn't love you, cigaba da jan magana tsakanin ka da ita ba abinda zai yi sai bata zumuncin dake tsakanin ku. Kuma ni a fahimtata familyn ka ba wai cutting dinka off suka yi ba, suna keeping tabs on you tabbas tunda su suka haife ka and they love you. They just want you to grow up, they want you to make the right decision by yourself daga nan sai su san hukuncin da zasu yanke maka. Kafin Mami da Daddy su zo su baka shawara ni ga tawa, ka koma gurin auntyn ka wadda kayi wa laifi kaje ka bata hakuri on your on ba wai sai ance maka kaje ba, ka bawa cousin dinka hakuri kuyi shaking hands kabar maganar Khausar, you don't know what God has planned for you".

Yayi murmushi yace "I guess you are right, maybe wadda zan samu nan gaba tafi Khausar komai" ya karashe maganar yana kashe mata ido daya. Tayi saurin dauke kanta tana jin zuciyarta tana bugawa da karfi. A take taji abincin ya fita daga kanta, ta ture plate din ta mike tace masa zata je class in ya gama ya same ta a can, ya bita da kallo har ta fita yana mamakin me ya chanja mata mood.

A ranar haka ta wuni tana jin ranta babu dadi, kar dai abinda take tunani akan Bassam haka ne, kar dai he is developing feelings for her, kar dai abinda Murjanatu ta fada rannan gaskiya ne, cewa she is playing with fire. Tana zuwa gida ta tarar da abinda yafi wannan daga mata hankali. Murjanatu ta gani zaune ta zuba uban tagumi, ya yarda jakar hannun ta ta zauna a gabanta cike da concern tace "Fanna? Lfy?" Ta dago tana kallonta tace "yaya ya kira yanzu, wai in gayawa Judith ta hada kayanta ta bar gidan nan kafin weekend" Diyam ta mike "au wai har yanzu bai bar maganar Judith ba? Me ta tsare masa? Akanshi take zaune? Ni ba zan iya korar Judith ba tunda babu abinda tayi min, dama baki gaya masa sakona na ranar nan ba?" Murjanatu tace "ni na ce miki bazan iya gaya masa ba Diyam tsoro nake ji" Diyam tace "mala'ikan mutuwa ne shi da zaki ke tsoronsa?" Daga haka ta figo wayarta daga cikin jaka and for the first time tun zuwan ta kasar ta danna number dinsa, bugu daya ya dauka, bata ko saurare shi ba ta fara zazzaga bala'i "wanne irin mutum ne kai wai? When will you stop playing god? When will you stop making decisions a rayuwar mutane? This is my life and I asked you to stay out of it" I nutse yace "Diyam...." Ta katse shi "kar ma ka gwada yimin dadin baki, bazan kori Judith ba and that is final" yace "am sorry dear, I was just trying to.." tace "trying to protect me? To kayi hakuri but I don't need your protection" ya sake cewa "I was just trying to.....to provoke you into calling me" sai ya kyalkyale da dariya. Ta tsaya tana kallon wayar da mamaki, sannan ta kalli Murjanatu taga ta durkushe a kujera tana ta kyalkyala dariya harda rike ciki, sannan tayi realising abinda ya faru.

Ta jefar da wayar kamar wadda aka ciza sannan ta dafe kanta da hannu biyu tace "oh God, Murjanatu what have you done?" Da gudu Murjanatu ta mike ta shige daki tana dariya ta rufo kofa. Diyam ta zauna akan kujera ta dauki wayar da har yanzu take a kunne tace "this is cheating" har yanzu da dariya a muryarsa yace "kin tuna abinda kika ce min ranar da zaki bar Nigeria? Kin tuna alkawarin da muka yi dake cewa in dai kika dauki waya da hannunki kika kira ni to nayi winning, zan yanke duk hukuncin dana ga dama" ta sake cewa cikin raunanniyar murya, "but this is cheating" yace "in life, my dear, cheating is allowed once in a while" sannan ya kuma dariya yace "see you on Saturday" ya katse wayar.

Ta kife kanta a kujera tana jin hawayenta yana jika kujerar, sai da tayi kukanta ta gama sannan ta dago ta dauki wayarta ta tura masa message

"You always claimed that you play your games fair and square, but this is not fair"

Bayan yan mintina reply ya shigo mata

"Nothing is fair my dear, life in itself is not fair, you just have to be smart and have eyes like an eagle's so that you won't get cheated on. My regards to your lips".

Comments dinku suna kadan, shi yasa typing yake kadan
[1/6, 8:19 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Eight : The Numbers

Ta jima a kwance a gurin, har Judith ta dawo ta shiga kitchen ta fara hada musu dinner, sannan ta tashi ta shiga daki tayi sallar magrib ta kwanta, ita ba bacci ba ita ba ido biyu ba tana ta saka da warwara. Allah ya gani bata son wannan zuwan nashi dan tasan ba zasu kare da dadi ba, zuwa zaiyi suyi ta rigima kuma rigimar da babu inda zata kai su. A nesa nesa dai sai sunfi samun kwanciyar hankali, wannan shi yasa ta zabi tahowa karatu nan kasar dan tayi baya dashi har abubuwa su warware. She don't want to keep hurting herself and she don't want to hurt others. Bassam ne ya fado mata a rai. Poor innocent Bassam, daga ganinsa tasan is from a wealthy family amma duk da haka bata son involving dinsa a wannan drama din, kuma she is afraid that he is already involved saboda irin kallon da yake mata kwana biyun nan. Kar dai ace ya fara son tane. She will have to put a stop to their relationship.

Har daki Judith ta kawo mata dinner kuma ta matsa mata sai data ci, tana ta tambayar ta abinda yake damunta amma sai tace mata family issue ne kawai.

Washegari tana shiga class ta hango Bassam a seat din kusa da inda take zama, sai tayi sauri ta dauke kanta ta samu front seat ta zauna. Bata jima da zama ba taji kamshin turarensa a kusa da ita, bata dago kai ba yace "Are we changing seat?" Still bata kalle shi ba tace "I am" ya koma baya, ana jimawa sai gashi ya dawo da takardun sa ya zauna a seat din kusa da ita. Bata ce masa komai ba ta dauko littafi tana karantawa, shima ya dauko nasa yana flipping through the pages, can ya ajiye yace "can we go and eat? Ni fa yunwa nake ji" bata kalle shi ba tace "you can. Am okay" yace "me kika ci?" Sai ta mike zumbur ta rataya jakarta, yace "ina kuma zakije?" Tace "somewhere quiet" ya bita da kallo baki bude har ta fice daga ajin. Ya ajiye littafin hannunsa yana tunanin a inda yayi laifi.

Har aka fara lecture bata dawo ba. Sai a lokacin yayi realizing cewa bashi da number dinta, dan haka hankalinsa gaba-daya yana gurinta har akayi lecture din aka gama. She never misses her lectures tunda ya santa sai yau. Ya fara tunanin ko bata da lafiya ne? Lecturer din yana fita shima ya fita ya fara nemanta, duk inda suke zuwa tare sai daya je amma bata nan har lokacin wata lecture din yayi sannan ya dawo wai ko zata zo wannan amma itama shiru har aka gama. Ana gama wa ya tafi department din su Murjanatu ya tarar yau sam basu da lecture ma dan haka bata zo ba. Yana futowa ya tare cab sai block dinsu. Ya hau lift har apartment dinsu yayi ringing bell, daga ciki ya jiyo muryar Diyam ta amsa "who is there?" yace "thank God. Bassam ne, Diyam?" shiru tayi bata bude ba, har yayi kamar zai sake danna bell din kuma sai ta bude, fuskarta a hade ta tsaya tana kallonsa kawai bata ce komai ba, ya tsafa kansa yace "You skipped your class and I was worried and thought ko baki da lfy ne" direct tace masa "lfy ta kalau as you can see" tana ganin yadda expression din fuskarsa ya chanja, daga gani tasan bai ji dadin abinda tayi masa ba amma sai kawai ta juya zata koma ciki ba tare data kara cewa komai ba, yace "Diyam?" ta dakata amma bata juyo ba, yace "in kina so in daina kula ki ne just say so ba sai kin tsaya kwana kwana ba, but please don't skip your classes because of me" daga haka taji motsin tafiyarsa. Ta juyo tana kallon kofar duk ranta babu dadi, sam bata ji dadin bata wa Bassam rai da tayi ba but wani abun ya zama dole ne, laifin tane tun farko data fara zama involved with him amma ai a lokacin bata yi tunanin zai yi attaching wasu strings a relationship din nasu ba. Ta dawo ta rufe kofar sannan takoma ta kwanta a doguwar kujera ta rufe idonta tana lissafin yadda next weekend din zai kasance. Haka ta ringa jera tsaki ita kadai a kwance har taji motsi a hanyar corridor din dakunansu, ta daga kai taga Murjanatu a tsaye tana kallonta, nan take ta kara bata rai ta juya bayanta. Murjanatu ta karaso ta zauna a gefenta tace a hankali "Diyam" Diyam ta mike ta dauki wayarta ta shige ciki ta barta a zaune.

Bassam tunda ya bar gidan su Diyam ya saka hannayensa a cikin aljihunsa ya fara tafiya, wani irin zafi yake ji a ransa yana jin zuciyarsa tana kara karyewa, tambayar da yake ta maimaitawa kansa itace me yayi mata? Duk iya tunanin sa in ya dawo da hirarrakinsu baya sai yaga babu inda yagaya mata ko da kuwa wata magana ce marar dadi. Shi akwai wanda ya samu power over him a rayuwarsa irin Diyam? Tun farkon haduwar su baya iya mayar mata da magana, to me ya faru? Babu abinda ya kai ayi maka hukunci ba tare da kasan laifin me kayi ba ciwo. Yana isa kofar hotel dinsa sako ya shigo cikin wayarsa. Ya dauko yana dubawa, for the first time in weeks ya samu sako daga gida, daga brother dinsa, yaji heart dinsa tana racing kafin ya bude amma yana bude wa sai ya tarar babu ko kalma daya a cikin sakon sai hoto, hoton flight ticket.

Yayi ajjiyar zuciya ya jingina da bango, wato babu wata magana kenan a tsakanin su sai yaje gida. Abinda suke bukata dashi shine ya kai kansa gida ya karbi laifinsa. Yayi ajjiyar zuciya ya mayar da wayar aljihu a ransa yace "not now brother" dan bayajin zai bar kasar har sai yayi straightening tsakanin sa da Diyam. Ya tuno da shawarar da Diyam ta bashi na cewa ya je gurin Aunty Hafsat ya bata hakuri sannan ya tafi gida ya kai kanshi. Wani tunani ya fado masa a game da Diyam, anya ba wannan ne dalilin da yasa ta juya masa baya ba?

Washegari Friday, da sassafe Diyam taje school dan ko breakfast bata tsaya tayi ba saboda bata ma son abinda zai hada ta magana da Murjanatu har sai tayi deciding inda zatayi placing dinta. Ta jima a class tana duba takardunta amma a can kasan zuciyarta tana duba ta inda Bassam zai bullo. Tana nan a zaune har aka zo aka sanar cewa lecturer din ba zai samu zuwa ba, a dai dai nan Bassam ya shigo, suna hada ido tayi saurin dauke kanta amma ta kasan idonta ta hango shi straight ya taho gurinta, ta fara kokarin harhada takardunta pretending to be busy har yazo daf da seat dinta ya tsaya, da dan karfi yace "why? Menene dalilinki na cutting dina off? Laifin me nayi?" Bata ce komai ba amma sai taji wani abu ya rike a tsakiyar cikinta kamar mai jin yunwa, nan take jikinta ya kama karkarwa har takardun hannunta suka zame suka zube a kasa, ta sunkuya tana kwashewa shima ya sunkuyo yana taya ta, sunkuyon da tayi yasa rolling din veil dinta ya kunce gashinta ya zubo ya rufe mata fuska ya sauka akan hannayensa. Still yayi yana kallon tsaho, baki da santsin gashin, ya daga hannunsa ya mayar mata da gashin bayanta tare da bude mata fuskarta, a lokacin ya lura da how red fuskarta da idonta sukayi, sai kawai yaji tashi zuciyar tayi melting, yaji kamar bai kyauta ba da ya daga mata murya har ya bata mata rai. Ta mike ta warce papers din hannunsa ta ajiye a gefe tana gyara veil dinta yace "am sorry Diyam but dan Allah ki gaya min abinda nayi miki" ta dauki takardun ta ta zagaye shi zata wuce ya rike jakarta yace "saboda na fada miki am in trouble da family na shine zaki juya min baya?" Da sauri ta juyo tana sauke manyan idanuwanta da suka yi ja a kansa, she looked shocked, bata taba zaton zai yi linking wannan abin da labarin sa ba, ta warce jakarta tace "is that what you are thinking? tunanin da kake yi a kaina kenan?" Ya daga kafada yace "then tell me otherwise, me nayi miki" tace "babu abinda kayi min Bassam" ta danyi shiru kamar mai tunani sannan cikin karyayyiyar murya tace "am just not who you think I am. Am sorry" ta juya da sauri saboda hawayen da taji yana taho mata. Kafin ta kai kofa ya kuma rike jakarta, ta juyo ta zuba masa jajayen idanuwanta yace shima da raunanniyar murya "ko ba zaki cigaba da kulani ba, at least give me your number yadda zan ke jin halin da kike ciki ko a waya ne, ko physically ba zamuyi magana ba at least....."

"Number?" Ta katse shi "wacce number zan baka Bassam? Ohhh I have so many numbers a cikin wannan kan nawa" ta fara lissafa masa da yatsun hannunta "kaga na farko 24 itace number din shekaru na, 3 itace number adadin yayan dana haifa a duniya, 2 itace number of times I was divorced, 8 itace shekarun yar karamar yarinya ta, infinity shine number of times my heart was broken and 0 is the tolerance I have for other hear breaks. So tell me, wacce number zan baka a cikin wadannan?"

A hankali jakarta ta zame daga hannunsa saboda yadda gaba-daya jikinsa ya saki, tamkar numfashin sa aka zare gaba daya. Ta tako zuwa dai dai fuskarsa tace "like I said, am not who you think I am".

Har

Please Login or Register in order to submit comment