Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya saka masa ido akan mu. The guy might have saw you two together and reported to him" Diyam tayi shiru tana tunani, she will have to talk to him about that, hakan kamar rashin yarda ne. Murjanatu ta katse mata tunanin ta ta hanyar cewa "there is nothing between the two of you, is there?" Diyam ta harare ta tace "in kina son shi just say so, sai in hada ku" Murjanatu ta tabe baki tace "bai yi min ba, he is definitely not my type. Daga ganin sa nasan lady's man ne, Allah kadai yasan yawan yammatan sa" Diyam tayi dariya tace "wai dama kura tana iya cewa da kare maye? Ke ma Allah ne kadai yasan yawan samarinki" Murjanatu ta yi murmushi ta fara bata labarin new catch din da tayi a school last week.

Suna tsaye suna jira jirgin ya iso, Diyam tana ta jujjuya hannun ta feeling nervous dan bata san da wacce zai zo ba sannan kuma ga zuciyarta da take neman betraying dinta saboda dokan tuwa da tayi gurin son ganinsa after almost three months of not seeing him. And then suddenly sai idonta ya sauka a kansa, yayi kyau sosai fuskarsa tayi fes gashinsa na fulani da sajensa sun kwanta lufluf suna daukan ido. The freshness of his dark skin alone zai tabbatar maka da cewa he is taking good care of his body, yanayin takunsa kuma da posture dinsa sun nuna yawan ziyarar da yake kaiwa gym. Their eyes locked, and everything in her stopped except bugun zuciyarta da yayi doubling. He walk straight to gabanta ya tsaya one hand inside pocket, his expression unreadable yace "hello Madam".

Ta bude baki zatayi magana amma sai taji duk rehearsal din da tayi na abinda zata ce masa ya gudu ya barta. Yayi mata kwarjini da yawa, and the fact that he called her madam have added to that. Sai ya dauke idonsa daga kanta ya mayar da dubansa kan Murjanatu da take kusa da ita tana mishi murmushin dole, suna hada ido tace "sannu da zuwa yaya, ya flight din?" "Fine" yace mata in short sannan ya zagaye su yayi hanyar fita, Murjanatu taja hannun Diyam da sauri suka bishi a baya. Suna fita suka ga cab tayi packing a gabansa Murjanatu tayi saurin cewa "ga mota munzo da ita fa" ya juyo yana kallon Diyam yace "thank you" sai ya shige suka ja suka barsu a wajen.

Murjanatu ta juyo tana kallon Diyam tace "you kept quiet, me yasa zaki yi shiru?" Diyam tace "he called me Madam. Kin san kuwa yadda nake jin haushi in yace min Madam?" Murjanatu tayi dariya tace "to menene na jin haushi? In yace miki Madam sai kice masa Sir, ba shi kenan ba? Now we have to follow him kuma" suka shiga mota suka bi bayan cab din data dauke shi but sai suka ga sunyi wata hanyar daban ba hanyar gidan su ba, Diyam zata yi magana Murjanatu tace "gidan Papa zashi. Inda muke sauka in munzo gari" sai Diyam ta juya kan motar suka yi hanyar gidansu. Murjanatu tace "ba binsa zamuyi ba?" Diyam tace "we cooked for him, dole kuma yaci abincin da muka dafa".

Suna zuwa gidan Murjanatu ta shiga ta hado kan girkin da suka yi masa ta jera a babban basket sannan ta dawo motar suka kama hanyar wajen gari inda anan ne gidan yake. Suna packing Diyam ta tsaya tana kallon gidan a ranta tace "wow, da gaske dai Umar Mustapha Abatcha ne ya haifi Sadauki" ba mutane a gidan sai security daya bude musu gate suka shigo, amma komai na gidan tsaf yake daga alama ana zuwa aba gyaran gidan akan kari. Kofar da suka hango a bude suka dosa, suka shiga wani palo madaidaici Diyam tana iyakacin kokarinta na ganin bata yi kauyanci ba. A kan dining suka hango shi yana zaune yana kallon kofar da suka shigo. He kept his eyes on them har suka karaso Murjanatu ta ajiye basket din hannunta ta gaishe shi ya amsa tare da tambayarta karatu, sai kuma tace da Diyam bara taje ta dubo wani abu a cikin gidan.

Sai data fita sannan Diyam ta dauke idonta daga kansa ta sauke kan wata baturiya sanye da apron da hular cooks tana ta jera abinci akan dining table din gabansa. Diyam ta tako ta karaso gurin tana kallon baturiyar tace "thank you, I will take it from here" sai matar ta juya tana kallon Sadauki shi kuma ya yi mata alamar ta tafi da hannunsa sai ta juya ta bar gurin. Diyam tabi bayanta da kallo tana jin haushinta ba tare da matar tayi mata komai ba. Sai kuma ta fara tattare abincin kan table din tana ajiyewa gefe sannan ta dauko basket din da suka shigo dashi ta dora akan table din ta fito da abincin ciki ta jejjera sannan ta jawo kujera kusa dashi ta zauna. Tunda ta fara yayi folding hannayensa yake kallonta har ta gama ta zauna sannan ta jawo plate gabanta tace "banyi maka tuwon da kake so ba saboda bani da kayan hadi. Amma nayi maka something da nake tunanin zaka so" still idonsa akanta yace "how is he" ta gane maganar da yake amma sai ta cigaba da hada abincin ta, carelessly tace "how is who?" Sai ta debo abincin a spoon ta kawo bakinsa tace "ha" and she saw his lips curved in a smile amma sai ya juya fuskarsa gefe kar ta gani sai ta sake bin bakinsa da spoon din tace "ha muga ni" sai ya langwabar da kai sannan a hankali ya bude mata bakin ta saka masa abincin a ciki sai ta zauna tana kallon sa with wide opened eyes shi kuma yana taunawa a hankali sannan tace "please tell me yayi dadi. I spent hours ina shirya maka abincin nan kamar yadda nayi spending hour ina yi maka kwalliya amma gashi nan ko yaba wa ba kayi ba" ta karashe maganar kamar zata yi kuka.

A hankali yace "waye yace miki ban yaba ba?" Ta turo baki tace "you called me Madam, kuma kaki shiga mota ta" ya danyi murmushin daya tsaya a iyakacin idonsa yace "to ba Madam din bace ba ke?" Tace "I am not Madam, in ka kara gaya min kuma nima Sir zan ke ce maka" and his smile widen to his lips. Ta sake dauko wata lomar ta kuma cewa "ha" ya bude ta saka masa yana ci ya kuma cewa "how is he?" Ta gyara fuskarta zuwa serious one tace "kana magana akan Bassam ko?" Ya daga kafada yace "bansan sunansa ba and I don't want to know" tace "he was fine as of yesterday, bansan ya yake yau ba. Kamar yadda bansan me yasa kake wani tunani akan sa ba. He is just my friend, department din mu daya muna lectures tare and he is a Nigerian" ya bata fuska yace "shi yasa kuke cin abinci tare?"

Ta saka masa wata lomar a baki sannan tace "and how do you know that? Wani ka saka yake spying on me? Baka yarda dani ba?" Yace "babu wanda na saka yayi spying on you. Akwai mutumin da muka yi harkar admission da registration dinku tare. He saw your pictures then. A lokacin kuma na gaya masa ke matata ce then he saw you with that boy and thought ya kamata in sani. I told him bake bace ba cos I thought you would never do it sai ya tura min da picture of you two together" ta ajiye spoon din hannunta tana kallon yadda fuskarsa take nuna bacin rai, yace "do you like him?" Ta dafe kanta tace "I just told you, Bassam is my friend. Na bashi labarin ka ma na gaya masa zaka zo yau kuma har cewa yayi zai so ku hadu. There is nothing there. Please stop looking for something that isn't there" she saw him relax a little yana kallonta yace "he is handsome" tace "really? Ni ban gani ba. He may be one of the thousands of stars in the sky amma ni duk bana ganinsu, only one star shines brightly a ido na, you. Kai kadai nake gani a matsayin mai kyau sauran duk dusudusu nake ganin su. You are the only star in my sky".

And he smiled. This time genuine smile yayi mata ya lumshe idonsa ya bude yace "I always remember that night duk sanda naga starry sky" ta sunkuyar da kanta kasa tace "me too".

Sai ya saka dogayen fingers dinsa guda biyu ya dago fuskarta yana kallon cikin idonta yace "feed me" ta hadiye wani abu a makogwaron ta amma taji yaki tafiya, sai ta yi sauri ta dauke idonta daga cikin nasa ta dauki spoon with shaking hand ta cigaba da bashi abinci. Bai kuma magana ba sai ido daya tsare ta dasu har sai da ta tabbatar ya koshi sannan ta bashi drink ya sha sai kuma yace "thank you, this is the best food I have tasted for a while. Ko kuma yadda aka bani abincin ne ya saka naji yafi kowanne dadi?"

Sai kuma ta danji kunya ta rufe fuskarta da bakin hijab dinta, suddenly sai taji babu abinda take so irin ta kuma jin wannan kalmar daga bakinsa but as her husband yadda zata ji dadi fiye da na yanzu kuma ta samu lada mai yawa.

Sai ta zame daga kujerar da take zaune ta durkusa a gabansa tana kallon yadda yake kallonta da mamaki tace "Aliyu Umar Abatcha. Will you do me the honor of marrying me?"

Please, duk wanda Allah ya bawa ikon karanta wannan page din ina barar a karanta min surorin Falaq da Nas. Da niyyar Allah ya gina mana katangar tsari tsakanin mu da duk wanda yake neman mu da sharri, Allah kuma ya tabbatar mana da alkhairi tsakanin mu da duk mai neman mu da alkhairi. Allah yayi mana jagora kar ya barmu da iyawar mu dan mu ba zamu iya ba. Allah ya tabbatar mana da alkhairi a kasar mu baki daya.

Nagode
[3/14, 10:49 AM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Sixty Six: The Unbreakable Love 2

Naga adduoin ku, nagode sosai.

For two seconds ya zauna yana kallonta da tsantsar mamaki a fuskarsa sai kuma yayi sauri ya mike tsaye ya kamo hannayenta duk biyun ya mikar da ita tsaye yana kallonta tana murmushin ganin duk yadda yabi ya rude sai yace cikin saurin murya "No! No".

Ta bude ido da mamaki tace "no?" Sai ya saki hannunta da sauri ya dafe kansa yace "ba wannan no din ba, I mean no karki durkusa please, karki bata kayanki" ya fada yana ciwo hanky da sauri ya kama goge mata hijab dinta, sai daya dago sannan ta daga gira tace "so? Yes ne ko No?" Maimakon ya bata amsa sai ya dora goshinsa a kafadarta, tana jin yadda ya sauke wata nannauyar ajjiyar zuciya wadda tasa hawaye ya gangaro daga idon Diyam sannan yace can kasan makoshinsa "Yes Diyam. Of cause I will marry you. You have no idea how much I want to marry you"

Murjanatu ta bude kofa ta shigo, sai kuma ta tsaya tana kallon su sannan tace "wrong room. Ba nan zan shigo ba" sai ta kalli kofa tace "Na'am!" Ta juyo tace "they are calling me so I gotta go" sai ta juya da sauri ta fita. Diyam tayi dariya tana share kwallar idonta tace "she is funny. Babu wanda yake kiranta" ya danyi dariyar da Diyam taji vibration dinta a kirjinta yace "kika sani ko aljanun gidan ne suke kiranta?"

Ta dan matsa baya forcing him to raise his head from her shoulder. Sai ya kalle ta da idon da suka fara chanja color yace "yaushe kika chanja shawara kuma? What about Saghir? Kin fasa fitar dashi din?" Ta zauna a kujera tayi dagumi but fuskarta da murmushi tace "you won the bet, I can't continue to deny myself freedom. Nayi kokari ai ko?" Ta fada da sanyin murya. Ya zauna opposite dinta yace "Subay'a fa?" Tace "in muka yi aure Subay'a ta zama yarka. And I trust you will do everything in your power to make your daughter happy" ya gyada kai yace "you bet. She is going to be the happiest girl ever".

Matar dazu ce ta shigo ta fara gyaran dining table sannan ta zo gurin su tana tambayar Sadauki in akwai abinda yake bukata in babu tana son tafiya. Ya sallameta ta tafi ya juyo yana kallon Diyam da take bin bayan matar da harara yayi murmushi yace "what?" Tace "fire her. Ita da wannan secretary din taka ta Kano" ya bude ido da mamaki yace "why?" Ta turo baki "ni bana son su" yayi dariya yana shafa kansa yace "and you accuse me of being heartless" ta bude hannu tace "sai ka basu wani aikin ai. Kai kuma ka samu maza suke yi maka irin wadannan aiyukan" yayi tagumi da hannu daya yana kallonta yace "yarinyar nan anya kuwa Baffa bada A'isha yayi miki huduba ba? Kishinki yayi yawa. Yanzu suna min aiki kince ba kya so, so tell me idan kuma kika gan mu tare muna cin abinci a cafeteria mai zaki yi? Hmm?" Ta gane inda ya dosa sai tayi saurin cewa "kayi hakuri, an gama ba za'a kuma sakewa ba" bai ce komai ba sai kallonta da yake tayi fuskarsa da murmushi. Ta jawo fuskar hijab dinta ta rufe fuskarta tace "ni kunya kake saka ni in kana kallona" sai ya koma ya jingina a jikin kujerar yace "kinsan tunanin me nake yi?" Ta bude fuskar ta tace "no" yace "tunani nake yi in koma airport a yau in koma Nigeria, gobe inga Kawu Isa jibi a daura mana aure in dawo gurin amaryata a jibin" tayi saurin mayar da fuskarta ta rufe tace "kai dan Allah. Ka dai bani lokaci in shirya dai ko?" Yace "wacce shiryawa kuma? Nasan a gida zasu ce zasu shirya wani abu amma koma menene sai dai su jira sai bayan na tare da amarya ta" sai ta mike da sauri tayi hanyar waje tana hada hanya tace "sai dai ka tare kai kadai" ya biyo bayanta yana cewa "dama ai ni kadai nake tarewa ta kullum on my empty cold bed, it is about time I get some warmth" ta karasa kofar da sauri tana hoping ba irin ta office dinsa bace ba. Tana murdawa taji ta bude ta fita tana raba idon inda zata hango Murjanatu, sai gashi nan ya fito shima ya rufe kofar ya jingina da jikin kofar ya harde hannayensa da kafafuwansa yace "run run little girl. Duk inda zaki je you will come back here" ya fada yana nuna kirjinsa yace "cos that's where you belong. A heart belongs to the chest".

Ta juya suka hada ido, feeling like yau ta fara ganin sa. She couldn't help but look at chest din daya nuna, very broad and very strong, sai taji babu abinda take so irin ta jita a gurin feeling the warmth and the strength that she so much miss. Ta hadiye wani abu tare da saurin girgiza kanta a kokarin ta na goge image din daga kanta tace masa "uhmmm. Lokacin Sallah. Murjanatu" yayi mata murmushin gefen baki sai ya nuna mata wata kofa da hannu" ta juya da sauri ta tafi can. Sai data bude kofar ta shiga sannan ta rufo kofar ta jingina da jikinta ta yi ajjiyar zuciya. Sai kuma tayi murmushi tana girgiza kanta.

Daga gefenta taji ance "hmmm. Wato da can anaso ana kaiwa kasuwa akeyi ko?" Ta juyo ta harari Murjanatu tace "ke nifa yayarki ce, bana son rashin kunya". Anan tare sukayi sallah tare sannan suka fita Murjanatu tana zagayawa da ita gidan Diyam tana ta kashe kwarkwatar idonta. Komai na gidan abin kallo ne, exact lissafin da Diyam take yi na abinda ake cewa aljannar duniya. Suna cikin zagayen suka hadu dashi, yace da Murjanatu "thank you Fanna, zaki iya komawa daki" ta turo baki tana buga kafa amma yana yi mata wani kallo ta juya ta koma. Diyam tace "kai kuwa ka barta mana mu karasa" yace "a gabanta zanyi hira dake? Kina sone ma ta raina ni kenan" suka jera suka cigaba da tafiya tare, but ba kallon gida sukeyi ba hirar su kawai suke yi suna jin dadin iskar da take kadasu.

Ta rungume hannunta tana jin sanyi amma bata son nunawa dan tana jin dadin hirar da yake yi mata, sai ya cire top dinsa ya saka mata, ya cigaba da bata labarin irin yadda ya yi ta kokarin ganin ta kira shi dan yayi wining amma taki. Yace "har halucination fa nake yi. In wani ya kira ni sai inga kamar ke. It was hectic. I almost lost it" tayi murmushi tace "kasan me? Wani lokacin sawa nake Murjanatu ta saka min kai a handsfree" ta fada tana rufe fuskarta, yace "laaa ila, that was cheating" ta bude fuskarta tana hararar sa tace "har zaka yi maganar cheating?" Yayi dariya yace "bature yace 'nothing is fair in love and war".

A lokacin suka kai karshen gidan sai suka juyo suna retracing steps dinsu sai yace "sanda zaku taho Papa cewa yayi ku zauna a nan gidan, but sai na nuna masa cewa yayi nisa zaku ke shan wahalar transportation. But ni personally ba wai dan haka na samo muku wancan gidan ba, ni a ganina you are my responsibility kuma nan ba gida na bane ba bana son matar gidan ko sauran siblings dina suzo gidan suyi miki wani kallo, gwara can nawa ne babu mai daga miki kai" tayi murmushi tace "bansan sauran ba amma Murjanatu tana da kirki sosai" ya gyada kai yace "tana da kirki, suma duk basu da problem amma hausawa sunce maganin kar ayi kar a fara".

Sai da sukayi sallar isha sannan suka bar gidan. Zuciyoyin su tas kamar takarda. Suna zuwa gida sukayi wanka suka yi shirin kwanciya saboda duk sun gaji. Diyam ta kwanta tana bitar maganganun su da Sadauki. Yes, ta karbi shawarar Bassam, Sadauki baya son tana maganar Saghir dan haka ta daina amma bawai ta bar maganar bane ba, zata jira taga if he will come around and do the right thing da kansa.

Watarta tayi kara ta dauka tana murmushi. Bai gaji da hirar ba kenan. Ta dauka da sallama yace "so nake in taho nan kin yarda?" Tace "nan kuma? Me zaka yi anan din?" Yace "hira zan yi miki kadai" tace "to kayi min a wayar mana, ai ina jinka a haka" yace "nafi son inke ganin ki as ina miki maganar. Nafi son in yi miki joke kiyi min murmushi in gani. Nafi son in tsokane ki ki harare ni in gani. Nafi son in fada miki sweet sweet words inga kin rufe fuskarki kina jin kunyata" sai taja abin rufa ta rufe fuskarta. Tace "ni dai kar kazo zuwa zakayi kayi ta sakani jin kunya" sai kuma tace "amma bada gaske kake ba zancen daurin aure jibi ba ko?" Yace "in da zan samu yadda nake so da ko gobe nema ina so. But nasan ba zan samu ba, Papa zai ce abokansa da sauran mutanen sa, Mama zata ce zasuyi biki, and you, I want you to have all the wedding things da baki samu ba ada. So, I will wait. Kinsan ni am a patient bird. Yanzu ki gaya min duk abubuwan da kike so for the wedding" ta lumshe ido tana tunanin childhood dreams dinta, but those are only dreams kuma yanzu sun zama past, dan haka tace "ni bana son komai fa. Sai dai ko in kai kana son wani abu" yace "ni ke nake so. I want only you, and that's the only thing that matters" taji ta tamkar tana narkewa tana shigewa cikin katifar da take kwance. Is it possible to love someone this much?

Suka cigaba da hirarsu mai ratsa zuciya, tana bashi labarin makaranta da yadda tayi adapting, shima yana bata labarin lokacin da yake tasa makarantar. She told him about Bassam abinda ya hada su da yadda rayuwar su ta kasance tare but sai taki gaya masa cewa Bassam ya fara sonta. She told him yace ya taba ganinsa yaje daurin auren brother dinsa. Sai a lokacin yace "Abuja? Last year you said?" Tace "eh" ya danyi tunani yace "naje daurin auren gidan sarki. Maybe can yake". Sai da yaji alamar ta fara jin bacci sannan yace "kiyi addu'a ki rufe idonki. I will talk to you sai kinyi bacci saboda ina son kiyi mafarki na"

Took my hand, Touched my heart, Held me close. You were always there, By my side. Night and day, Through it all. Baby, come what may.
Swept away on a wave of emotion, Oh, we're caught in the eye of the storm. And whenever you smile, I can hardly believe that you're mine, Believe that you're mine.
This love is unbreakable. It's unmistakable. And each time I look in your eyes, I know why.This love is untouchable. A feeling my heart just can't deny. Each time I look in your eyes, Oh, baby, I know why This love is unbreakable.
Shared the laughter, Shared the tears. We both know We'll go on from here. 'Cause together we are strong. In my arms: That's where you belong.
I've been touched by the hands of an angel. I've been blessed by the power of love. And whenever you smile, I can hardly believe that you're mine.
This love is unbreakable. Through fire and flame. When all this is over, Our love still remains.
This love is unbreakable. (Lyrics by Westlife)
Washegari Sunday, Diyam tayi baccin safenta sosai sannan ta tashi. Tana mikewa ta jawo wayarta ta tura masa message cewa tana gayyatarsa breakfast. Ta fita ta tarar duk su Murjanatu suma babu wanda ya tashi dan haka ta zarce kitchen ta fara shirya abinci. Tana cikin aikin Judith ta shigo suka cigaba tare har suka kammala sannan ta tafi ta tashi Murjanatu ita kuma ta shiga tayi wanka ta shirya sannan suka fito kusan a tare da Murjanatu. A palo suka hadu suka baje kayan breakfast suna yi sai gashi ya shigo. Suka gaishe shi gaba-daya ya amsa da sakakkiyar fuska tana bude warmers din gurin. "Me aka shirya mana ne?" Murjanatu ta tashi tana serving dinsa yayinda Judith tayi musu sallama ta fita. Ya jingina da kujera yana shan tea yana kallon Diyam yace "kin yi kyau sosai" ta sunkuyar da kanta tace "thank you".

Ranar wuni sukayi tare, ya dauke su a motar Diyam suka fita yawon zaga gari. Sai dare suka gama suka dawo gida ya ajiye su shi kuma ya tafi da motar. A daren Diyam ta kira Inna dan rabon da suyi waya tun sanda ta kira ta suna tare da Bassam. Inna ta dauka suka gaisa suka kuma gaisa da Asma'u da Subay'a. Sannan Inna ta karba tace mata "ya bakon naku?" Diyam tace "lafiya lau Inna" Inna tace "ya gaya miki abinda yayi? Naji bakiyi mana magana ba" Diyam taji gabanta ya fadi, me kuma yayi? Sai ta dake tace "me yayi kuma Inna? Ni bai gaya min komai ba" Inna tace "nasan dama bai gaya miki ba, na dauka zai gaya miki yanzu da yazo. Ya kwashe dabbobin nan daga gidan Alhaji Babba ya mayar dasu bayan gari tun kusan sati biyu da suka wuce. An buge katangar tsakiyar gidan Alhaji yace ya bar masa gurin kyauta".

Ga breakfast, ayi enjoying tare da oga.
[3/17, 12:15 AM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Sixty Seven: The Inheritance

Diyam ta ajiye wayar tana tunani, sati biyu da suka wuce Inna tace anyi relocating gidan gonar, sati biyu da suka wuce lokacin Sadauki bai ma yi winning bet dinsu ba. This means yayi abinda yayi ne on his own account ba wai dan yayi winning bet din ba. Shin hakan yana nufin Saghir yana da hope?

Washegari Sadauki ya koma Nigeria. A airport Diyam ta marairaice masa kamar zatayi kuka shi kuma ya rikice. "Ki taho mu tafi. Sai ki dawo next week" tace "school kuma fa?" Yace "share school din nan, ai baku fara

Please Login or Register in order to submit comment