Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

exams ba" sai ta tuna sanda yake hanata zuwa islamiyya, tace "so kake ayi min bulalar fashi ko?" Yace "waye zaiyi miki bulalar? Gaya min shi in fara yi masa tun kafin yayi miki" tayi dariya kawai tana tuno jibgar da ta sha a gurin Saghir, sai tace "ni yanzu mai duka na ai sai dai ruwan sama, ruwan saman ma sai na tsaya" yayi kasa da murya yace "in kin tsaya din ma I will shield you from it, like an umbrella" sai ta tuno sanda Inna ta kama su suna saukowa daga sama tazo zata dake su ya kare ta shi akayi ta dukan sa. He had been shielding her all his life. Ya katse mata tunanin ta ta hanyar langwabe kai yace "Please kizo mu tafi" ta makale kafada tace "naki, sai dai ka zauna anan" yace "ai kinsan maganar da zata mayar dani Nigeria. So nake fa ayi lokacin hutun ku sai mu dawo tare" ta rufe fuskarta da hannunta tana murmushi, sai kuma tace "Inna ta gaya min zancen Alhaji Babba. An gode madallah Allah ya kara arziki" yace "ameen" sai kuma ya dauke kansa gefe kamar yana tunani yace "ina yammatan gidan? Su Murja kawarki wadanda kika yi min maganar su rannan akan har yanzu basuyi aure ba?" Diyam tace "suna nan. Muna waya da Murja ma. Wani abin ne?" Yace "ya maganar auren nasu" tace "suna jira dai. Last wayar da muka yi tace min zata tura saurayinta gurin Baba Sa'idu (mijin anty Fatima)" yace "idan kun sake waya kice mata zakiyi musu kayan daki, ita da sisters dinta" ta bude baki tana kallon sa yace "ke ba yayarsu bace ba, ke zakiyi musu kayan daki ai" ya dauke kai yace "in place of their brother".

A kano bayan Sadauki yaje gurin Mama yaje ya gaya mata sun daidaita da Diyam, sai kuma ya nemi shawarar ta akan abinda ya dace yayi next. Sai ta nuna jin dadin ta sosai tace "ko ku fa, ai hakan yafi muku akan wannan zaman jiran da da kuka ce zaku yi" ya shafa kai yana murmushi. Tace "to yanzu abinda za'ayi shine zanje ni da kaina in samu Alhaji Babba, in yaso sai ya fadi ranar da za'a je a same su kai kuma sai ka fada a can gida sai su zo" yace "da nayi tunanin ko Kawu Isa, saboda kar a samu matsala da Alhaji Babba" Mama ta girgiza kai tace "babu matsala insha Allah. Shine Babba dan haka dole a bashi girman sa in ya karba shikenan in bai karba ba in yaso sai a je wani gurin a nema" suna cikin maganar sai Mukhtar yazo, suka yi hannu da Sadauki, Sadauki yace "ka yar dani Mukhtar, ko nema na bakayi" Mukhtar yayi dariya yace "ai ka zama yallabai ne yanzu, ka zama hukuma sai da lallashi" Sadauki yayi murmushi yace "sharri zaka yi min kenan ko? Zan samu time zaka ganni har gidanka".

A Oxford da Diyam taje school sai taji babu dadi saboda ganin seat din Bassam empty. But sai taji dadi dan hakan yana nufin ya tafi gida kenan, ya tafi yaje ya gyara tsakanin sa da family dinsa. She just hope ba zai dade sosai ba saboda kar karatunsa ya samu matsala.

Kamar yadda Mama tayi alkawari, washegarin da Sadauki yaje ya same ta sai ta tafi gidan Alhaji Babba. As usual, bata ji dadin yadda ta samu gidan ba duk da dai a yanzu matan gidan sun fara yan sana'o'i, Hajiya Babba tana siyar da ruwan sanyi, lemo da kankara. Hajiya Yalwati kuma tana yin snacks, da wannan sana'ar suke kokarin ciyar da kansu da yayansu dan Alhaji Babba har yanzu kusan dashi da babu duk daya a gidan sai ma jigilar asibiti da suke tayi dashi, shi bai mutu ba shi kuma bai cigaba da rayuwa normal ba.

Taje suka gaisa da matan gidan sannan ta tafi dakin Alhaji. Yana nan har yanzu a dakin da Inna ta zauna bai koma part dinsa ba duk kuwa da cewa Sadauki ya saka an gyara part din tas batan an kwashe kajin. Ta gaishe shi ya tashi daga kwancen da yake ya amsa mata yana tambayarta lafiyar family dinta, kafin ta gabatar masa da abinda ya kawo ta sai cewa yayi "Hafsa ina Diyam, har yanzu bata zo gari ba?" Mama tace "bata zo ba. Basu samu hutu ba ai" ya mayar da kansa ya kwantar yace "Diyam yarinyar kirki ce mai son zumunci. Fatima ta gaya min abinda tayi wai taki auren shi wannan yaron da take ta nacin so tace lallai sai ya fito da Saghir tukunna zara aure shi. Banyi tsammanin haka ba, na dauka in ta juya bayanta ta bar Saghir a prison ba zata sake waigen inda yake ba, na dauka in ta samu cigaba a rayuwa ba zata sake tunanin halin da muke ciki ba. Ina so inga Diyam Hafsa, ina son in roki gafarar ta tun kafin lokaci na ya kare a duniya. Ina kuma son in roki gafarar Saghir. Ko ma menene Saghir ya zama ko ma menene Saghir yayi ko ake zargin yayi to laifi nane, nine na lalata rayuwar dana mafi soyuwa a zuciyata duk a tunanin soyayya ce nake nuna masa. Ina sane, ina sane da duk abinda Saghir yake yi nasan yana yi din amma sai in rufe idona in nuna tamkar ba zaiyi dinba saboda ina so in gaya wa kaina cewa ba zaiyi din ba. Banyi nadama a bisa tarbiyyar da nayi wa Saghir ba sai da na je gidan yari na ganshi tukunna" yayi shiru yana kokarin saisaita muryarsa saboda kukan da yaji yana neman ya kwace masa. Mama ta fara bashi hakuri "sai hakuri Alhaji, komai mukaddari ne komai rubutacce ne" yace "haka ne, amma komai yana da sila. Silar lalacewar Saghir kuma shine rashin tarbiyyar dani da mahaifiyar sa muka gaza bashi. Ba kuma mu tashi ganin sakamakon abin ba sai da ya zama babu abinda zamu iya yi akai. Bani da yadda zanyi in fito da Saghir daga inda yake, bani da kudi ko hanyar samun kudin da zan biya yaron nan kudinsa sannan bani da karfi na jiki dana aljihu da zan samo wannan yaron daya lika masa wadannan kwayoyi"

Yayi shiru yana tunani sannan yace "Hafsa, idan kunyi waya da Diyam ki nemar min gafararta dan ban tabbatar da zanyi tsahon ran ganin ta in roke ta da kaina ba, sannan kuma ki ce ina rokon alfarmarta akan ta janye waccan maganar ta kin cikawa kanta burin zuciyarta na auren Sadauki, ta aure shi indai tana sonsa, shi kuma ruwansa ne ya yafe wa Saghir ko kuma yaki yafe masa wannan zabin sa ne".

Sai Mama taji dadi, dan haka sai ta rufe maganar sasantawar da aka samu tsakanin Sadauki da Diyam dan tana son alhajin ya ji dadi a ransa ya dauka tamkar shi ya sasanta su din, dan haka ta ki shigar masa da maganar auren da niyyar sai bayan kwana biyu sai ta dawo ta sake shigar masa da maganar. Ta kuma yi masa alkawarin kiran Diyam ta gaya mata sakonsa.

Sai dai tana mike wa sai ga Kawu Isa ya shigo dakin hannunsa rike da jariri. Ya wuce ta yaje chinyar Alhaji Babba ya ajiye masa yace "ga sakon Saghir nan. Nayi masa huduba da sunanka dan haka ina yi maka murna ka samu takwara" ya juya da sauri ya wuce Mama ba tare da ya kula mai take cewa ba ya fita. Ta juyo ta dawo gaban Alhaji tana kallon jaririn da take kwance kan cinyarsa yana ta jujjuya kai da alama abincinsa yake nema. Ko ba'a yi mata bayani ba ra fahimci cewa Suwaiba ce ta haihu kuma wannan shine dan gaba da fatihar data haifawa Saghir. Ta saka hannu ta shafi kan yaron tana kallon fuskarsa mai kama data Subay'a. Tace "Allah yayi maka albarka" Alhaji ya dago kansa daga kallon yaron shima yace "ameen. Ki kira min Hajiya Saratu a ciki". Ga dai jika nan namiji Alhaji da Hajiya sun samu amma kuma shege.

Kafin Mama ta baro gidan sai data yi ta zarya zuwa gidan Kawu Isa akan ayi hakuri a mayar da yaron nan hannun uwarsa amma Kawu Isa yace sam bai san wannan maganar ba "ba zata shayar dashi ba" ya fada ya kuma maimaita wa. Ko samun ganin Suwaiba Mama bata yi ba, daga baya ma ta tabbatar bata gidan dan haka ta hakura amma tace "yaron dai jikan mune gabaki daya, kuma shi bashi ne yayi laifi ba dan haka bai kamata a hukunta shi akan laifin dashi bai san ma sanda aka aikata shi ba. Rashin shayar dashi ba zai goge cewa Suwaiba ce ta haife shi ba".

Sai taje ta siyo baby formula da feeder ta dawo ta kawo wa Hajiya Babba. Ta tarar da ita ta goya dan jaririn da ya rare baki yana ta kwarara kuka. Ta mika mata tayi mata barka sannan ta koma tayi wa Alhaji sallama, sai yace "ki turo min Amina dan Allah" daga haka sukayi sallama.

Bata koma gida ba kuwa sai da ta je gurin Inna, ta fada mata duk yadda sukayi da Sadauki da kuma yadda suka yi da Alhaji da kuma abinda ya faru a gidan alhajin. Inna duk ta tayar da hankalinta nan take washegari ta dauki kudi ta shirya ita da Asma'u da Subay'a taje tayo siyayyar kayan babies sukaje gidan Alhaji Babba, ta kaiwa Hajiya Babba ta kuma yi mata barka ta dauki yaron da yasha madarar sa yana ta baccinsa tayi masa addu'a sannan taje gurin Alhaji.

Bayan sun gaisa yace mata "Amina idan kun yarda ke da yayanki ina so za'a zo a raba gadon usuman" Inna ta kalle shi da mamaki tace "wanne irin rabon gado kuma Alhaji?" Yace "an raba ne? Ai har yau ba'a raba ba. Kuma taba kudin da nayi ne ya haddasa min duk masifun da suka same ni. Tun da na shigo kano na fara neman kudi nake samun sa'a da nasara a rayuwata ban taba cin karo asara ba sai dana bi son zuciyata na taba kudin gadon nan. Kuma har yau ban biya ba, wannan shi yasa duk abinda nake dashi bashi da albarka, duk harkar neman kudi bana tarar da komai a ciki sai asara. Wannan kuma a duniya ne kadai, idan har ban biya ba to azaba tana can tana jirana a lahira. Na sani sarai, ina sane da duk abinda nakeyi son zuciyata kawai nake bi shi yasa na kasa gyarawa amma yanzu alhamdulillah rayuwa ta bani wata sabuwar damar gyara kurakurai na guda biyu. Zan fitar da hakkin usuman da yake kaina sannan kuma zan gyara kuskure na na tarbiyyar Saghir akan wannan yaron da aka haifa masa".

Inna tace "mu ai Alhaji mun riga mun yafe maka rabon mu ni da yara da yake cikin abinda ka dauka, shima kuma Sadauki yace ya yafe kason mahaifiyarsa, sannan kuma ai kaima da sauran yan'uwa kuma da rabo a ciki sannan....." Yace "muna dashi, hardo yana dashi, hatta yaya ladi mahaifiyar Zainab tana dashi. Yanzu bayan mutuwar hardo matar daya aura kafin rasuwarsa tana dashi. Mutanen da suke da hakki suna da yawa, wannan yafiyar ba zata sauke min nauyin nan ba".

Tayi shiru tana lissafa maganar sa, sai yace "ina so azo ayi rabon gadon a bisa ka'ida. Zan bayar da complete kudin dana dauka, sai ayi wa gidan da kuke ciki kudi sannan a raba a bisa tsarin da addini ya tsara a bawa kowa rabonsa ko zan samu rayuwa ta dan sassauta min kafin in bar duniya kuma in samu sassauci a lahira" tayi tagumi tace "to a ina zaka samu kudin nan Alhaji?" Yayi murmushi yace "nan gidan da muke ciki shine kadai abinda ya rage min a duniya. Shi zan siyar. Kollere zan koma in cigaba da rikon sarautar da hardo ya mutu ya bari muka ki karba. Sauran abinda yayi min saura kuma sai in samu sana'ar yi a can wadda zata rike min iyalina a can din".

Inna ta girgiza kai tace "ba zai kai ga haka bama Alhaji, insha Allah ba zai kai ga haka ba".

Wasa wasa abu ya tabbata. Inna ta kira Diyam da Sadauki ta gaya musu abinda duk ake ciki, farko Diyam ta nuna rashin yardarta amma sai inna ta gaya mata cewa hakan shine dai dai "shima marigayin wannan wani sauke nauyi ne akayi masa". Aka yiwa gidan Baffa kudi, a take Sadauki ya siya. Aka kuma yiwa gidan Alhaji Babba kudi aka siyar, ana siyarwa Diyam ta aiko da kudi tace a kama musu ko rent ne su zauna kafin komai ya zama settled. Sannan Alhaji Babba ya ware kudin garejin Baffa daya siyar aka hada da kudin gidan Baffa aka raba kudin cash, kowa aka danka masa nasa a hannunsa hatta amaryar da hardo yayi kafin rasuwarsa sai da aka fitar mata da nata a cikin kason Hardo aka aika mata dashi har Kollere.

Babu yadda Alhaji Babba baiyi ba akan son komawa Kollere amma yaya da yan uwa suka saka shi a gaba akan lallai ba zai koma ba. Dole ya zauna a gidan da Diyam ta aiko da kudi aka kama masa haya a unguwar Jaeen, suka koma gabaki daya shida iyalinsa. A lokacin ne kuma Diyam daga can ta aiko da kudurinta na son yiwa kannen Saghir su hudu wadanda suka isa aure kayan daki. Sai Alhaji Babba yace "ku gaya mata tazo sai a hada auren tare da nata".

A bangaren Sadauki, yana ta son ya tunawa Mama da maganar da suka yi amma kunyar ta yakeji, sai yayi ta cewa Diyam wai ita ta kira Mama ta tuna mata, tayi dariya tace "wato nice marar kunya ko? To babu ruwana, tunda kaji tayi shiru tana da dalilinta".

Sorry for keeping you guys waiting. Biki things. Enjoy your week.
[3/18, 11:02 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Sixty Eight : Save the Date
Yace "eh nasan tana da dalilin ta shi yasa ni kuma na kasa zuwa in tuna mata. Am just scared Diyam, tsoro nake yi kar a sake hana min ke a karo na biyu. Bansan me zanyi ba wannan karon" tace "babu wanda zai hana mu juna Aliyu. In har kaga ba'ayi ba to kuwa tabbas Allah bai rubuta za'ayi ba. Waliyai na ne su amma basu kadai bane waliyai na in sunki zamu iya zuwa Kollere mu......" Yace "no, no Diyam. Ba su kadai ne waliyan ki ba amma sune shakikan Baffa, kamar yadda kika fada haka ne Baffa zaiji dadi idan muka sasanta tsakanin mu da su. Kuma ni ba zanzo in zama sanadiyyar rabuwarki da yanuwanki ba but am not going to give you up, not now not ever. Dan haka zamu jira in ta kai ga cewa ni zan kuma durkusawa Alhaji Babba zan durkusa din" sai ya dan yi dariya yace "the table have been turning so past yanzu kuma na dawo ni nake nema a gurinsa" ta taya shi dariyar sannan tace "in lokacin durkusawar yazo, call me sai mu durkusa tare ni da kai because we are in this together".

Washegari sai ga wayar Mama. Ta gayawa Diyam duk abinda sukayi da Alhaji Babba tace "na bashi wannan damar ne saboda naga yadda yayi nadamar abinda yayi, so nake ya nemi Sadauki da kansa ya gyara kuskuren da yayi da kansa. Yanzu yace yana so kizo gari dan yana son neman yafiyarki, sannan kuma yace kice da Sadauki ya turo, in yaso sai a hada dana su Murja ayi gabadaya"

Diyam ta lumshe idonta tana jin wani irin farin ciki marar misaltuwa a zuciyarta wanda har sai daya saka hawaye ya taru a idon ta. Mama tace "kinyi shiru kuma, me zance masa?" Ta dan goge hawayen idonta tana jin zuciyarta fari kal kamar takarda, rabon data ji wannan feeling din tun Baffa yana da rai, tun tana carefree teenager, tun lokacin da Sadauki yake zuwa gurinta a school suyi ta bayyana wa junansu abinda yake zukatan su.

Amma sai taji kunyar Mama tace "mun kusa fara exams yanzu Mama, ba zan iya tahowa gida ba amma muna yin hutu zan taho sai in samu alhajin, duk da dai ni na riga na yafe masa tuntuni" Mama tace "to Allah ya bada sa'a. Maganar Sadaukin fa?" Diyam tace "duk yadda akayi Mama" Mama tace "ki gaya masa ya tura gurin Alhaji Babba, sai asa rana tare daba su murjan. Yaushe kuke so a saka?" Diyam ta sake yin shiru sai da Mama ta maimaita sannan tace "duk sanda aka ce dai dai ne" Mama tace "in aka saka lokacin hutun ku ai yayi ko?" Diyam ta sake yin shiru tana murmushi amma a ranta tana lissafa kwana nawa ya rage ayi hutun.Mama tace "shikenan tunda ba zakiyi magana ba, shi bara in kira shi in tambayeshi" s

Suna yin sallama Diyam tayi saurin kiran Sadauki ta gaya masa yadda sukayi da Mama, yace "tare dana su Murja kika ce?" Tace "eh, haka tace min" ya girgiza kai yace "I don't like that. Nafi son ranar bikinki ya kasance all about you not you and someone else, nafi son in an ganki ace 'ga amaryar can' kar ace 'ga daya daga cikin amaren nan' nafi son ki samu cikakkiyar kulawa daga kowa ba wai ki samu divided attention ba. Dan haka zan gaya mata ayi nasu first, later in an huta sai ayi namu"

Tun da ya fara magana take murmushi har sai daya gama sannan tace "I don't need attention din mutane, attention dinka nake so, in nayi kwalliya ban damu da a yaba ko ayi comparing dina da wasu ba as long as kai ka yaba as long as a gurinka babu wadda ta kai ni. Besides, ni ba biki zanyi ba, daurin aure kawai za'a hada da nasu, ni a gida zanyi zamana kawai sai wanda ya shigo aka gaisa kawai shikenan. Ban damu da having a big wedding ba as long as kaine angon that's all that matters, tunda nasan a gurinka zan samu more than abinda na samu a wancan auren" a can kasan makogwaron sa yace "more of what?" Tace "everything" yace "like?" Tace "caring" yace "and?" Tace "tunda nace everything ai ina nufin everything ko? Sai na lissafa maka?" Yayi dariya yace "so nake ki fada da bakin ki, yadda in lokacin yayi zan tuna miki cewa ke nema da kanki" ta bata rai tace "abinda kake nufi fa ni ba shi nake nufi ba, we are not talking about the same thing" yace "zaki sha kwana ko? To gaya min ni abinda nake nufi" tace "ni ban san me kake nufi ba fa" yace "to in baki sani ba ya akayi kika san ba abu daya muke nufi ni da ke ba?" Tayi rolling eyes dinta tace "good night Aliyu" yace "ashe tsoro na kike ji tunda zaki gudu, ki tsaya mana" tace "ba tsoro nake ji ba bacci nake ji, ina da school gobe" yace "hmmm okay, Allah ya tashe mu lafiya, but I will still demand to know that 'everything' da kika fada, ko ba gobe ba ko watarana I will get the words out of you".

Suna gama wayar Sadauki ya ajiye phone din yana kallonta, sai kuma yayi murmushi sannan ya lumshe idonsa ya kwantar da kansa a bayan kujerar office dinsa yana dan jujjuya wa a hankali. Sai kuma ya mike zaune sosai ya jawo system dinsa yana duba calendar, yasan ranar dasu Diyam zasu fara exams ya kuma san ranar da zasu gama sannan yasan ranar da zasu koma school, sai ya duba dates din da suke tsakanin hutunsu da komawar su school yana neman weekend mai perfect date for their wedding, sai idonsa ya sauka akan date din, his birthday. Ya dafe kansa yana fadada murmushin sa. He is going to have a perfect birthday gift for his 30th birthday.

Mama ta kira shi kamar yadda tace zatayi, ta kuma maimaita masa abinda already Diyam ta gaya masa sai ta tambaye shi shima akan date, sai ya maimaita mata abinda Diyam tace mata "duk sanda aka saka dai-dai ne Mama" ta tabe baki tace "ai shikenan, idan manyan sunzo ayi magana dasu".

Washegari ya hau jirgi daga kano zuwa Maiduguri ya samu Alhaji Babagana wanda yake kani ne a gurin Papa kuma shine dai wanda shekaru goma da suka wuce yazo ya nema masa auren Diyam aka hana shi. Yanzu ma shi zai sake dawowa tare da Alhaji Bukar su karasa abinda suka fara. Nan take shi kuma ya kira Papa ya gaya masa sannan ya bashi izinin ya dauki sauran yan'uwa suje su hadu da Alhaji Bukar suyi duk abinda ya dace. Sai da suka gama wayar sannan Sadauki ya gaya masa date din da ya keso a saka. Sai shi kuma ya tambaye shi "kana ganin ba za'a samu matsala ba? Kar azo ayi irin ta wancan karon" Sadauki yace "babu matsala in sha Allah, tunda wannan karon ai sune da kansu suka nemi azo din".

Daga Maiduguri sai yayi branching a Yobe yaje damagun gurin yaya ladi wadda take zaune a gidan cousin dinta da Sadauki ya gyara musu shi tas ya zuba musu kayayyakin more rayuwa kuma ya daukar musu yan aikin da zasu ke kula dasu. Bayan sun gaisa ta gama loda masa tuwo da fura sai ya sanar mata da duk abinda ake ciki, yana maganar yana murmushi. Sai ta rike baki tace "Diyam din dai Aliyu?" Ya dago kai yana kallon ta yace "Diyam din dai. Ko kina kishi ne?" Ta tabe baki tace "ni dai daka hakura da Diyam din nan da nafi jin dadi, kazo ga yammata nan birjik ka zaba ka darje in ma hudu kake so a tsakanin yau da gobe sai a samo maka su amma kai ka nace sai yarinyar da yan'uwanta suka wulakanta ka, suka wulakanta mahaifiyar ka, suka wulakanta ni kakarka?" Ya daga kafada yace "ita nake so, ita ma kuma tana sona kuma in anyi auren da ita zan zauna bada yan'uwanta ba" Hajiya Dije, cousin din Yaya Ladi tace "amma duk da haka Aliyu, ko bayan anyi auren ne ya kamata ka samu budurwa ka kara da ita" sai ya mike tsaye yana daukan hularsa a hannu fuskarsa da murmushi yace "kar ku damu, bayan anyi auren da sayi daya zan dawo nan sai in aure ku duk ku biyun a rana daya" yaya ladi ta tabe baki dan tasan shirishitar da maganar yake yi, tace "to ai shikenan, uwarka ma haka nayi ta fama har sai dana hakura" ya durkusa a gabanta yace "kisa mana albarka kawai ke dai. Kiyi mana fatan alheri" ta dafa kansa tace "Allah ya sanya alkhairi a ciki, Allah ya baku zaman lafiya ya kuma kade duk wata fitina da zata taso sannan ya baku zuri'a mai albarka" yayi kyakykyawan murmushi yace "yanzu kika yi magana. Karki manta, ke ce uwargida ran gida a gurina, ita kuma amarya ta sannan kuma zuciyata".

A gidan Baffa aka sauki bakin da suka zo daga Maiduguri, aka bude musu part din Baffa inda Inna ta zauna da, Mama tazo da yammatan ta suka hadu suka shirya musu abinci mai rai da lafiya wanda duk da kasancewar su masu hannu da shuni amma sun tabbatar cewa an karrama su. Sannan Alhaji Babba yazo, Kawu Isa ma yazo sannan abban su Rumaisa shima yazo suka zauna suna ta hira ta wasan fulani da barebari suna ta dariya kamar sun saba. Sai a lokacin ne su Alhaji Babba suka san asalin waye mahaifin Sadauki, jin hakan ba karamin girgiza su yayi ba, ba kuma karamin nadama ya saka musu ba. Lallai rashin sani yafi dare duhu, wanne irin gorin arziki ne basu yi wa Sadauki ba? Wanne irin wulakanci ne basu yi masa ba shida mahaifiyar sa?

Sai da suka nutsa sannan Alhaji Bukar ya gabatar musu da dalilin zuwan su cewa suna nemawa dansu Aliyu Umar Abatcha auren yarsu Halima Usman Kollere, sai Kawu Isa ya gyara masa yace "dan mu dai. Sadauki ai dan mu ne kamar yadda Halima take yar mu. Ku kawai zuwa

Please Login or Register in order to submit comment