Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wata rayuwar.

But with who? Wannan wata tambaya ce for another time. Maganar da Subay'a ta fada ta dawo masa zuciyarsa "zan kawo maka ziyara gidan ka" wanne gidan? Shi fa yanzu ko gidan kansa ba shi da shi, wayake ma maganar gida, shi ko kwandala bashi da ita. Bashi da komai sai freedom dinsa, kuma ya dauki freedom din nasa ya zama another chance at life. Chance din kuma da insha Allah zai yi amfani dashi sosai yadda har sai mutane sunyi mamakinsa. Yadda har sai iyayensa sunyi alfahari da shi. Iyayen da a wancan lokacin ya wofantar ya wulakanta, abinda yake tunanin shine dalilin zuwansa inda yaje ba wai Diyam ba.

Maganar mai napep ce ta dawo dashi hankalinsa, yace "yallabai munzo" ya leko dakansa yana kallon gurin yace "nan ne?" Mai napep yace "nan dai yayi min kwatance, yace jaen layin shago tara, gashi nan kuma har mun kusa fita daga layin tunda mun fara hango diga. Sai dai ka sauka ka tambaya" Saghir ya sauka yana kallon gurin, not that bad. Mai adaidaitan ya miko masa dari biyar yace "dubu biyu ya bani, ga dari biyar ka sha ruwa kai ma" Saghir ya karba harda yi masa godiya sannan ya tafi gurin wasu mutane su uku da ya hango a kasan bishiya ya gaishe su yace "dan Allah tambaya nake yi, gidan Alhaji Babba, bai dade da dawowa unguwar nan ba" duk suka ce basu sani ba, yayi gaba ya cigaba da tambaya amma babu wanda ya sani sai ya juyo ya fara retracing ta inda suka shigo yana yi yana tambaya, ga rana gashi dama jikin sa duk babu karfi.

Da kyar ya samu wanda yace "inda akayi biki watannin baya?" Da sauri Saghir yace "eh" sai aka hada shi da yaro suka koma can inda ya baro, suka je har gaban wani gida sannan yaron ya nuna masa ya juya. Ya tsaya yana kallon gidan, a tsahon rayuwarsa bai taba tsammanin duniya zata yi juyawar da har nan gidan zai koma shine gidan baban shi ba, gidan ma kuma gidan haya, gidan hayar ma kuma Diyam ce ta ke biya masa.

Ya shiga soro yayi sallama, Hajiya ya hango ta fito daga wani guri daya ga kamar kitchen tana amsa sallamar hannunta rike da wuka tana goye da wani yaron da bai sani ba a bayanta. Ta yarda wukar tana kiran sunan Alhaji, Alhaji ya fito, Hajiya yalwati ta fito, sai ga yaran gidan suma sun fito daga wani daki duk suna binsa da ido. Shi ya karasa shigowa, ya tafi gaban mahaifinsa ya durkusa amma sai ya kasa gaishe shi sai kuka ya kwace masa. Alhaji ya sunkuya gabansa ya jawo shi jikinsa ya rungume shi shima yana hawayen yace "bansan yau zasu fito da kai ba Saghir, da ko ba zan iya zuwa da kaina ba da sai in gaya wa mahaifiyarka ta je ko ta tura aje a taho da kai" Saghir ya goge hawayen sa yace "Mr Abatcha ne yaje ai, dashi da Diyam da Subay'a" ya fada yana jin dacin zuciyar dazu yana dawo masa. Alhaji yace "madallah dasu. Allah yayi musu albarka ya jikan Usman".

Nan fa gida ya rude da murnar dawowar Saghir, dan ma yanzu duk yaran babu saura kadan. Hajiya Babba ce ta kama shi ta kaishi daki, Hajiya yalwati kuma ta dora masa ruwan wanka, alhaji kuma ya aika a siyo masa nama da lemo kafin a gama abinci. Babu laifi suna cikin rufin asirin su duk da cewa alhaji har yau bai kuma gwada kasuwanci ba amma matansa suna yan sana'o'in su sannan yayansa mata da suke aikin gwamnati suna kokari gurin taimaka musu sosai, haka ma surukan gidan lokaci zuwa lokaci suna aiko musu da kayan abinci ko kuma suttura.

A dakin Hajiya ya huta, naman da Alhaji ya siyo masa sannan yayi wanka ya chanja kaya zuwa wanda Hajiya ta ajiye masa akan gado. Sai ta kunto yaron bayanta ta mika masa. Kallo daya yayi masa yasan waye, sai kawai ya ajiye shi a gabansa ya sunkuyar da kai, tace "sunan babanku ne dashi, Jawad ake ce masa" yaron ya rarrafa da sauri yabi bayan Hajiya yana kuka alamar bai san shi ba.

Dakin da yake soro, wanda kuma yake da kofa a waje shi dama Alh yasa aka gyara tun sanda yaji labarin dawowar Saghir gida. Aka shimfida carpet aka saka katifa, wardrobe, da kuma standing pan. Nan ne ya koma dakin Saghir.

Kwanan Saghir biyar ya warware, duk da dai babu inda yake fita sai yan'uwa da suke ta zuwa yi masa murna. Inna ma tazo ita da Asma'u da Subay'a, suka kuma bar Subay'a anan tayi weekend tare da mahaifinta da kakannin ta. A ranar ne Alhaji ya kira shi dakinsa. Suka zauna sai ya dauko wata leda ya miko masa, Saghir ya karba ya bude sai yaga kudi a ciki, ya zaro ido "Alhaji kudi ai, kudin menene wannan?" Alhaji yace "kudi na ne, sauran kudin gida na ne da kuma abinda na samu daga gadon Usman, su nake ta ajjiye dasu da niyyar duk ranar da ubangiji ya sake baka dama a rayuwa ya saka ka fito daga prison nima zan sake baka dama in baka su kayi jari" Saghir yayi saurin girgiza kansa hawaye yana bin idonsa yace "Alhaji kar kayi haka, ka bani kudi sau ba adadi ina salwantar wa, kai ma kana bukatar kudin nan alhaji, kana da iyali kaima. Ka rike kudinka alhaji ka kula da kanka da matanka da kanne na" Alhaji yace "da wanne karfin Saghir? Ni ai tawa ta kare, karfi na ya kare, dan haka kai na dora wa wannan nauyin ka juya wannan kudin ka kula da kanka sannan ka kula dani da iyayenka da kannenka, kuma ka cigaba da kula dasu ko bayan rai na ne".

Saghir ya karbi kudin ya rike yana jin nauyi a zuciyarsa "anya kuwa akwai soyayya sama data iyaye?"

Alhaji yace "akwai kuma wata magana da nake so muyi. Ina so ka kawo karshen rashin jituwar da take tsakani na da danuwana, ina son ka auri Suwaiba" ya dago kai yana kallonsa, Alhaji ya gyada kai yace "ta inda ake hawa tanan ake sauka. Tunda kuka bata dan haka ku zaku gyara". Sai Saghir yaji Fauziyya ta fado masa a ransa. Bayan ya bata takardarta sun rabu, daga baya sai ta koma tana gaya masa cewa tana da cikinsa, ta kuma ce zata haifi cikin za kuma ta jira shi as long as bata samu miji ba har ya fito sannan kuma yana da sha'awar mayar da ita. Bayan ta haihu kuma ta kai masa babyn ya gani. And after seeing Subay'a rike da hannun Sadauki, baya jin zai kuma barin wata yar tasa a wani gidan. Dan haka indai Fauziyya bata yi aure ba to sai dai ya hada su ita da Suwaiba.

Wata daya bayan nan Diyam tazo yi musu sallama zata koma Oxford, England. Washegarin zuwanta kuma alert ya shigo masa. Ya bude ido yana kallon kudin cike da mamaki ya tafi da sauri ya nunawa Alhaji. Alhaji yayi murmushi yace "Diyam ta gaya min jiya, kudin da Kabir ya gudu dasu ne aka dawo maka dasu. Zabi kuma ya rage naka kasan me zaka yi dasu".

Abinda Saghir ya fara yi shine ya dauki kudin da Alhaji ya bashi ya sayi gida madaidaici amma me kyau. Ba shine ya tare a gidan ba, Alhaji Babba da iyalin sa ne suka tare. Sai kuma ya sayi karamin fili a kusa da gidan a matsayin nasa "sai in zauna a kusa daku yadda zanfi jin dadin kulawa daku" next sai yaje har gidan Kawu Isa ya durkusa ya bashi hakuri sannan ya nemi ya bashi auren Suwaiba. Sai kuma ya tafi gidan su Fauziyya itama ya nemi auren ta. Amma duk kan su yace sai shekara mai zuwa idan ya samu nutsuwa sosai.

Daga nan sai ya tafi kantin kwari, tsofaffin shagunan Alhaji wadanda wuta ta cinye babu komai sai ginin, shima ginin duk ya mutu an sace kwanukan. Cikin kwanaki kadan ya tayar da ginin su, yayi komai ya saro kayan duk da yasan Alhaji yana siyarwa ada da kuma kayan da yasan zamani ya zo dasu ya zuba a ciki. Sannan ya nemo tsofaffin yaran Alhaji wadanda suke kular masa da shagunan a da ya dawo dasu dan su suka san kan kasuwa, shi kuma ya zauna cikinsu dan shima ya fahimci harkar.

Watanni kadan abubuwa suka warware wa Saghir, ya hada kudin neman aure ya kai gida biyu aka saka masa rana watanni takwas masu zuwa za'ayi duk a tare, sannan kuma ya fara ginin gidan sa a hankali. Gidan da yake da yakinin zai zamanto tushen sabuwar rayuwa a gurin sa.

****************************

A lissafin Sadauki so yayi in sun bar Nigeria su fara tafiya Canada suyi kwana biyu tukunna, amma Diyam ta tubure masa ita bata son zuwa, ya gane abinda yasa bata so, ita kunya take ji ake ganin ta da ciki. Yayi dariya "to wai ke banda abinki, ni fa banga abin kunya anan ba, kowa ma fa yana yi" ta juya masa baya tana kallon Subay'a a cikin swimming pool tace "kuma kawai sai in je gidan inyi ta yawo da ciki suna kallona?" yace "baiwar Allah, idan baki je da ciki ba in kika haihu dai ai dole zasu ganki da dan ko? Ko shima cewa zaki yi ba ke kika haifa ba?" Tace "ai kuwa in naje gidan da baby to har in bar garin ba zan dauke shi ba" ya rike baki "to waye zaiyi feeding dinsa?" Tace "sai ya sha madara" ya kwanta akan camp bed din da yake zaune akai ya rufe ido yace "you are impossible Diyam, ke fulatancin kamar a kanki ya kare" ya sake cewa "kiyi addu'a to, kar a saka bikin su fanna kafin ki haihu, sai muga yadda zakiyi da cikin a gurin biki" tayi saurin cewa "Allah ya kiyaye, insha Allah sai na haihu". Sai ta jawo kujerar da take kai kusa dashi tayi tagumi tana kallon sa, ya bude ido yana kallon ta yace "what?" A hankali tace "I want to kiss you, kuma Subay'a tana kallon mu" yace "ohh, a wannan bangaren kam kin ajiye fulatancin ko?" Sai kuma ta rufe ido tana dariya.

Addu'ar Diyam dai bata karbu ba, dan suna komawa makaranta aka saka ranar bikin su Sa'adatu kuma wata biyu kadai aka saka, meaning cikin Diyam yana da wata takwas kenan za'ayi bikin. A dole Diyam ta taho Maiduguri lokacin bikin da katoton cikinta, Sadauki yana ta yi mata dariya amma sai ta maze da shiga harkokin bikinta sosai ta rike role dinta na matsayin babbar yaya. Da ita akayi shawarar komai, da ita aka sayi komai, wani abun ma in ana nema sai Mama tace azo wajen Diyam.

Su Inna da Mama da Asma'u ma duk sunzo gurin bikin sun kuma Kawo wa amaren gift sosai har sai da Maman su Murjanatu tace "kayan nan anya basu yi yawa ba Amina?"

Aka daura aure aka kai amare gidajen su. Sa'adatu ta auri Aminu an kaita Abuja. Falmata kuma Saifullahi mutumin Kano amma mazaunin Canada dan haka can zasu koma, Fanna kuma ta auri cousin dinta Al-mustapha zasu zauna anan Maiduguri amma zata zauna a gurin su Diyam ta karasa karatun ta.

Bayan su Diyam sun koma England sai hankalinsu kuma ya koma kan haihuwa, Sadauki yana ta rawar kai, duk zuwa asibiti tare suke yi idan kuwa yaga namiji ne zai duba ta sai ya ja abarsa su bar asibitin. Twins ne kamar yadda Sadauki yake ta addu'a. Diyam tayi tunani sai taga cewa ba zata iya tuno yadda haihuwa take ba tunda bata yi labor a haihuwar Subay'a ba, haihuwar twins kuwa ba zata iya tuna yadda abin ya kasance ba dan haka sai ta shiga maternity classes, anan ta fahimci komai ta kuma yi browsing wasu abubuwan ta sake fahimta.

Abinda take tsoro guda daya shine shigar Sadauki gurinta in tana labor, tasan kuma za'a bashi option din shiga kuma tasan zai shiga din. Sannan tasan in dai ya shiga sai ya hargitsa daga ita har me karbar haihuwar kuma in yaga wahalar da ake sha a gurin haihuwa sai sunyi rigima kafin ya barta ta samu wani cikin. Ta kuma san yadda yake son yaya, dan haka ta yanke shawarar yi masa dabara yadda ba zata haihu a gabansa ba saboda ta haifa masa yaya as many as yadda Allah ya basu.

Ranar data fara jin alamar labor da daddare sai taki nunawa Sadauki, da safe kuma sai tayi pretending as if bacci take yi har ya gama shiryawa a hankali dan kar ya tashe ta, ya zo yayi mata kiss ya fita. Sai bayan fitarsa sannan ta tashi ta dauko jakar tafiya asibitin ta wadda already ta riga ta shirya ta ta kuma yi driving kanta zuwa asibitin. Sai da taje suka aunata suka kuma tabbatar mata da cewa haihuwa zata yi sannan suka bata daki suka kuma nemi su kira mijinta amma ta hana su tace sai ta haihu tukuna.

Ta sha wahala ba kadan ba, Sadauki ya sha kira kamar sunan sa zai kare ta kuma yi nadamar kin gaya masa dan da yana kusa ko ganin sa in tayi zata ji dadi. A haka har Allah ya sauke ta lafiya ta haifi namiji first, sai data huta sannan labor ya sake dawowa ta haifi mace. Ana miko mata su taga fuskar babansu amma fatarta, sai dai namijin bai kai macen haske ba.

Sai da aka gama garata aka kuma gyara babies din ta kuma danyi bacci kadan ta huta sannan tace su kira shi. 30 minutes after kiran nasa sai gashi ya shigo asibitin hakan yasa Diyam ta tabbatar da cewa yayi breaking every traffic rule a hanya saboda sanin nisan asibitin daga office dinsa.

A rikice ya bude kofar dakin da aka nuna masa ya shiga. A tsaye ya ganta a gaban window ta juya masa baya. T-shirt dinsa ce a jikinta, wadda ta kawo mata har zuwa rabin cinyarta, gashin kanta a barbaje wani ya sauka a bayanta wasu akan kafadun ta wasu kuma sun zubo kan kirjinta. "Diyam" ya fada cikin sarkewar murya. Ta juyo tana kallonsa, hannunta rike da jariri tana rocking a hankali, fuskarta da faffadan murmushi. Ya karaso cikin sassarfa ya jawo ta jikinsa ya rungume ta yace "don't you ever do that to me again" ta kwantar da kanta akan kirjinsa tace "am sorry my Lion. Bana son in tayar maka da hankali ne" yace "kinsan tashin hankali da naji kuwa? Kinsan da yadda nazo asibitin nan kuwa? I tot karya suke yi min da suka ce lafiyar ki kalau, I tot ba zaki iya haihuwa ba tare da ni ba" tace "I missed you sosai, nayi ta kiran sunanka" ya danyi dariya yana dago fuskarta da hannun sa daya, taji kunya ta mayar da fuskar kasa.

Ta zaunar dashi akan kujerar da take dakin ta mika masa babyn hannunta, ya dan leka cikin diaper dinsa fuskarsa kamar zata yage dan murmushi. Ta dauko dayar da take bacci a kan gadon su ta mika masa itama. Ya rike su hannu bibbiyu inya kalli wannan sai ya juya ya kalli wannan ya kasa tantance wanne yafi kyau a cikin su. Yayi musu addu'a. Tana tsaye a gabansu tana kallon su sai ta fara buga kafa cikin shagwaba, ya dago kai yana kallon ta cikin alamar tambaya sai tace "ni a ina zan zauna, sun tare min gurin zama na" ya daga babies din da sauri yace "zo ki zauna akan cinya" ta tafi ta zauna tana karbar daya, ta rike ta da hannun ta daya dayan hannun kuma ta zagayo wuyansa dashi. Sun jima a haka suna kallon kyautar da Allah yayi musu sannan yace "Baffa ne da Ummah. Baki ga yadda suke ta kokarin rike hannun juna ba?" Diyam tayi dariya tace "babu ruwana sai na gaya wa Inna" yayi murmushi yace "so kike ta biyo ni da muciya?" Sukayi dariya a tare. Sai ta kwantar da kanta a wuyansa shi kuma yayi kissing forehead dinta tare da sauke ajjiyar zuciya. A hankali yace

"ALHAMDULILLAH"

Godiya ta tabbata ga Allah da ya bani ikon kammala wannan littafi lafiya. Allah ya kara salati ga fiyayyen halitta (SAW) Allah kuma yasa muna da rabon ganin sa baki daya.

Godiya ga fans dina wanda na sani da wanda ban sani ba a duk inda suke, alkhairi ya kai muku har dakunan ku, ina sonku sosai da sosai, idan babu ku to kuwa tabbas babu ni.

#MyWattpadpeople, thank you for all the votes, the comments and the encouragement.

#MamanMaamaNovels na Facebook ina godiya da soyayyar da kuke nuna min a duk books dina, ina ji daku sosai mazan ku da matan ku.

#MamanMaamaNovels groups 1,2,3,4,5 na WhatsApp, ina ji daku tamkar nama daya a miya. Allahu ya bar kauna.

The ladies at #Shatuuskingdom, #zaurenBiebeeIsa, #KDM soldiers, #ZeenatNovel, #SameenaAliyuNovels, da sauran groups din da nake ciki da wadanda ma bana ciki, ina godiya kwarai da gaske. Allahu ya bar zumunci.

Zaku sake ji na da wani labarin, amma banan kusa ba, maybe sai 1-1-2021 maybe kuma kafin nan. In kuma babu rabo to Allah ya hada fuskokin mu a aljannatul Firdaus. Allahumma ameen.

Please pray for me a duk sanda labarin mutuwa ta ya riske ku.

ILYSM.
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Please Login or Register in order to submit comment