Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wadda ta kasance lawyer, da kyar yayi iyakacin kokarinsa har ya samu aka barshi ya taho UK karatu duk da cewa iyayensa basu so hakan ba sunfi son ya zauna tare dasu amma saida ya taho tare da daurin gindin kakar tasa, yayi hakane saboda ita, saboda Khausar, for she now lives in UK tare da auntyn su. But sai me kuma? He realized bayan zuwansa cewa ai she is already dating his cousin kuma, wannan yasa ya daura damarar ganin ko sama da kasa zasu hadu sai ya raba wannan relationship din, wannan ya jawo rigima ba yar kadan ba tsakanin sa da cousin dinsa Ayan and he failed miserably. A karshe Khausar looked into his eyes and said "I will never marry you ko mazan duniya sun kare", and that made him mad, so mad that when his aunty tries to resolve the issue he looked into her eyes and said "go to hell".

Sati biyu kenan da faruwar hakan. Tun daga ranar ya hado kayansa ya dawo wannan hotel din da zama shi kadai. Kuma tun daga ranar babu wanda ya neme shi kaf family dinsu not even his Mami.

But wannan duk ba shine babban problem dinsa ba. Problem dinsa shine satin sa daya da barin gidan auntyn sa parents dinsa sukayi blocking dinsa out of their family bank account. Tun tashinsa da wannan account din suke amfani gaba daya gidan, kowa yana da access da shi sai dai kawai a karshen wata kayi bayanin abinda kayi da kudin daka dauka, yanzu babu. Shi kuma ba aikin yi ba, dan haka blocking dinsa daga family account ya mayar dashi almost koboless. Bashi da komai, hatta kayan abinci bashi dasu kuma kudin siyan abincin nasa has almost run out, zuwa karshen satin nan yasan ko na abinci bashi dashi.

Yasan wannan duk hikimar Mami ce, they want to fish him out ya kawo kansa ya karbi laifinsa, shi kuma yana jin tsoron yadda hukuncin sa zai zama, ba zaiji da dadi a gurin daddyn sa ba. Kuma yasan he have lost Khausar for good. Yayi biyu babu. Abinda yake bukata a yanzu shine karfin gwuiwar facing family dinsa, accepting mistake dinsa da kuma repenting, but to do that yana bukatar courage, yana bukatar wani yayi masa magana at least ko fada ne ayi masa a gaya masa yayi ba dai dai ba.

Bai san mai yasa yarinyar dazu ta fado masa a rai ba, Diyam. Ya kwanta ya rufe ido yana tunano fuskarta, tabbas tana da courage. From her looks, yadda take ware kanta daga cikin mutane zuwa yadda turancinta bai gama nuna ba yasan cewa she is from a poor background, maybe irin yayan talakawan nan ne da gwamnati take dauka take basu scholarship suke tahowa kasashen waje suyi karatu. But she really does have courage, daga yadda tayi magana rannan a class da kuma yadda tayi facing dinsa straight in the eyes ta gaya masa maganganu. Har dare yarinyar tana cikin ransa, amma kuma ya kasa yanke mata hukunci a ransa.

Washegari kamar kullum Diyam ta riga kowa tashi. Tayi wanka tayi alwala tazo ta bude al'qurani tana bita har akayi assalatu sannan ta je dakin Murjanatu ta tashe ta tazo ta tayar da sallah. By seven har ta gama komai, ta dumama sauran tuwon jiya ta zauna tana ci Judith ta fito tayi joining dinta sannan Murjanatu ta fito itama, but sai taki cin tuwon ta hada tea da bread ta sha. Suna yi suna hirar abubuwan da suka shafi karatun su, Murjanatu tana ta mitar takura musu da Diyam take yi suke zuwa school a kafa bayan ga mota an ajiye musu musamman saboda zirga zirgar su.

Suna shiga makaranta Murjanatu tana haki ta kalli Diyam tace "you and yaya na deserve each other. Kafiya ce daku da naci akan abinda kuka sa kanku. At the end kuma ku wahalar da wanda yake tare daku. Ni dai daga yau na daina turturing kaina wallahi, motar zanke shigowa koda ni kadai ce" Diyam ta daga gira daya tace "ba sai ki shiga ba, in kin iya driving din" suka yi dariya tare da Judith, ita kuma Murjanatu ta tura baki tayi gaba tana kunkuni ta barsu tunda ba department dinsu daya ba, suna dan yin gaba kadan suka rabu da Judith itama sannan Diyam ta karasa department dinsu ita kadai.

Tun daga nesa ta gane shi. Yana tsaye kamar kullum da headphone a kunnensa da kuma sigari a hannunsa. Ta duba agogon hannun ta taga it is not 8:00 yet amma har ya fara zuke zuke, maybe ko breakfast baiyi ba. Ta dauke kai ganin cewa bai ganta ba dan kamar yayi zurfi cikin tunani.

Har suka yi nisa da lecture din tana ta saka ran ganin ya shigo amma shiru bai shigo ba, sai da aka fara concluding sannan ya shigo dan haka ko zama bai gama ba malamin ya fita, and she felt sorry for him. Suna nan wani malamin ya sake shiga ya gama ya fita daga nan kuma zasuyi one hour break sai su sake wata shikenan. Ta fita ta nemi coffee shop ta zauna aka kawo mata coffee da cake taci duk da dai ba yunwa take ji ba but she just need to eat something saboda suna da wata two hours lecture din, Madam Sally. Tana zaune ta hango wucewarsa yayi hanyar gate. She wonders ina zaije tunda suna da wata lecture din? Sai kuma ta daga kafada tana mamakin me yasa ta damu da business dinsa.

Har suka tashi a ranar bata kara ganin sa ba. Da daddare suna cin abinci ta bawa su Murjanatu labarin encounter dinta da guy din tace "I am just feeling sorry for him. He obviously is distracted, confused maybe" Murjanatu ta harare ta tace "ni dai babu ruwana. Daga tausayi kuma sai muji wata magana ta daban. Kinsan in yaya yaji wannan maganar zai iya harbo nuclear bomb ya tarwatsa Oxford gaba-daya" Diyam ta daga kafada tace "Allah yasa uranium zai harbo ba nuclear bomb ba. I will talk to whoever I want to talk to" Murjanatu tace "you are not going to give my brother a break are you?" Diyam ta mike tsaye tace "no i am not, har sai yayi abinda nace masa" Murjanatu tayi murmushi tace "maybe baki san shi ba kamar yadda kike tunani" Diyam ta wuce daki da sauri tana jin zafi yana taso wa a zuciyarta.

Da safe basu da lecture da wuri dan haka suka yi baccin su sosai. Sai after ten Diyam ta tashi ta fita parlor ta tarar Judith tana kitchen tana hada musu breakfast. Ta dawo dakin ta ta shiga wanka. Tana fitowa wayar ta tana ringing amma ko kallonta bata yi ba ta dauke kanta ta cigaba da shiryawa amma a zuciyarta tana mamakin yadda yake keeping track din komai nata, yasan sanda take da lectures yasan kuma sanda take free. Wayar tana katsewa taji text ya shigo, ta dauka takaranta, sakon barka da safiya ne mai hade da tsadaddun kalaman da sai da suka huda zuciyarta amma sai kawai ta tabe baki ta ajiye wayar. Ita dashi a ga wanda yafi taurin kai.

Diyam......... writing
[1/3, 10:07 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Four

Tana saka kaya Murjanatu ta shigo dakin, daga ganin fuskarta Diyam tasan akwai problem, ta ajiye skirt din hannunta tana bawa Murjanatu data zauna a kan gado dukkan attention dinta. Ta daga gira daya sama tace "me yace kuma?" Murjanatu tace "he asked me about Judith" Diyam ta hade rai tace "what about her" Murjanatu tace "he asked wai bata kawo mana maza gida? Na gaya masa bata kawo wa but he didn't sound convinced." Ta sunkuyar da kanta kasa tace "am afraid he is going to send her away" Diyam ta dafe kanta tana zagaye dakin da bacin rai a fuskarta sannan tace "tell him nace Judith is my friend, if he wants to get to her he will have to go through me. Ni na kawo ta gidan nan, in yana son ya kore ta sai ya fara kora ta tukunna" Murjanatu ta saka hannayenta biyu ta toshe kunnuwanta tace "ba dani ba, bani Murjanatu ba. Uwata ta daina haihuwa ballantana ta sake haifo ni" Judith ta bude dakin ta leko kanta tace "hey girls, food is ready" sai kuma ta tsaya tana kallon yadda suke kokarin kakaro murmushi.

A bayan lecture hall dinsu ta hango Sadiq. Shi kadai kamar kullum, da sigari a hannunsa kamar kullum, tayi saurin dauke kanta ganin yana kokarin juyowa. Amma sai ta tsaya a kofar hall din bata shiga ba tana so taga yau zai shiga ko yauma zamansa zaiyi a waje. Sai da aka kusan fara lecture din sannan ya taho, a gabanta a jefar da sigarin hannunsa ya saka kafa a murje ta, zai wuce Diyam tace " you know smokers tend to die young ko?" Ya kalleta for some seconds, ya busa mata hayakin bakinsa yace cikin husky voice "says who? I can't believe malama kamar ki ta yarda da wannan saying din. Kin manta kaddara? Ina islamiyyar taki ta tafi?" Ta sa hannu ta kade hayakin daya huro mata tace "maybe ni da kai munyi understanding kaddara differently. Tell me why do we pray? Why do we struggle? Me yasa muke neman duniya kuma muke neman lahira in dai har an riga an rubuta komai, me yasa ba zamu kwanciyar mu ba mu jira abinda aka rubuta mana yazo ya same mu. Yes kaddara rubuyacciya ce, major abubuwan da zasu faru a rayuwar mu a rubuce suke but what is in between depend on choices din da muke making. Wannan shine fahimtata. Yes, kamar yadda ka fada shekarun da aka rubuta maka ba zasu chanza ba amma how you are going to spend them depend on you, ko dai kayi spending dinsu healthy and happy in ka daina shan sigari ko kuma kayi spending dinsu with lung cancer in ka cigaba da smoking" ya kalle ta daga sama har kasa yace "go to hell, both you and your preaching" ya shige class din ya barta a tsaye. Taji zafin maganar sa amma sai ta hadiye ta bishi a baya.

Suna shiga class din wani guy ya kalli Sadiq yace "the Nigerian guy. Why do you skip madam Sally's class yesterday, don't you want to depend your country anymore?" Sadiq yayi banza dashi ya shige ya samu guri ya zauna. Sannan yan ajin suka juyo gabaki daya suka zubawa Diyam ido, ta yi gyaran murya tace cikin harshen turanci "abinda na fada rannan gaskiya ne, gaskiya ne based on sani na. Shima kuma musa min din da yayi gaskiya ne based on sanin sa. We may have come from the same country but we live in different worlds. Muna zama cikin different mutane, muna kallon rayuwa from different perspectives. My being right doesn't makes him wrong. You as potential lawyers should know that" duk yan ajin suka kada mata kai cike da gamsuwa sannan ta wuce ta shige seat din karshe ta zauna.

Madam na shigowa ta fara tambayar Diyam "will you like to continue with that day's argument?" Diyam ta girgiza kai tace "no ma'am, it's okay" ta juya gurin Sadiq tace "what about you, are you satisfied as well?" ya gyada kai yace "am okay ma'am. We now understand each other" sai ya juya a hankali ya kalli Diyam, itama ta dago kai suka hada ido and she smiled at him, a take ya fahimci cewa she have the brightest smile he have ever seen.

Bayan sun gama dukkan lectures dinsu, ta fito tana tsaye tana jiran Murjanatu sai gashi ya taho, ya tsaya dan nesa da ita kadan yace "waiting for a friend?" Ta daga murya tace "yeah" sai kuma taga ya zo zai wuce ta, tace "my name is Haleema. Haleema Usman Kollere. But people call me Diyam" ya gyada kai yace "I am Sadiq, Sadiq Abubakar Sadiq. Most people call me Bassam. You can call me that as well".

Tayi murmushin ta mai kyau tace "nice to meet you Bassam" ya danyi dariya yana jujjuya kai yace "You have a beautiful smile, very beautiful. Ban san me yasa ba kya yawan yinsa ba. Ta daga gira daya sama tace "if it is beautiful than it is precious kenan. Abu mai tsada kuma kasan ba'a ko ina ake ajjiye shi ba" ya sake dariya, his eyes twinkling, amma bai ce komai ba, tace "and you. Ban dauka ka iya dariya ba" ya gyara fuskarsa yace "believe me, I do laugh alot. Yanzu ne dai I am in kind of not laughing situation. But na miki alkawari in na fita daga ciki we will laugh more" daga haka ya juya da sauri ya bar gurin.

Yana tafiya Murjanatu tana karasowa. Tana kallon bayansa tace "who is that guy? Amma ya hadu fa" Diyam tayi murmushi bata ce komai ba, Murjanatu ta sake cewa "ko shine rannan kuke maganar sa da Judith?" Suka jera suna tafiya da Diyam tace "yeah shine" Murjanatu ta bata rai tace "then it is official, gaskiya ina taya yayana kishi. Lallai ma Diyam din nan" ta turo baki, Diyam tace "oh ashe baku hadu ba daga ke har yayan naki tunda insecurity yana damunku. Ashe kujerar taku bata kafu ba, ai hausawa sunce fargaba asarar namiji" Murjanatu ta harari bayan Bassam da har yanzu suna iya hango shi tace "ohh dama wancan namiji ne? Ai na dauka macece ta aske kanta ta saka wando. Ai wannan yana ganin yayana zai narke a gurin dan tsoro. Wannan daga ganin sa rainon madara da cerelac ne, yayana kuwa tuwon biski yaci da kunu dan haka ba sa'an sa bane wallahi" Diyam da take ta dariya tace "naga alama kam. Tuwon biskin ne yasa kansa yayi tauri da yawa" ta fada tana lakucewa Murjanatu hanci, Murjanatu tace "ouch, sai kin nane min hancin kinsa na rasa mashinshini?" suka yi dariya baki daya, sannan Murjanatu ta fara rokon Diyam akan ta fita dasu yawo yau da yamma "Please, Please Diyam, this routine is killing me slowly, ai ance taba kida taba karatu ko?" Diyam tace "sai jibi weekend sai muje muyi siyayyar abubuwan da bamu dasu a gida"

Washegari Friday, Diyam tana zaune a seat dinta tana rubutu taji ance "hi Diyam" ta dago tana kallonsa bata ce komai ba, sai kuma ya shafa kansa yace "Assalamu alaikum" tace "ameen wa alaikas salam Bassam" ya kalli seat din kusa da ita yace "can I?" Ta gyada kai ba tare data dago ba. Ya zauna ya fito da book dinsa pretending to be reading amma ita tasan ba karatun yake ba. Can ya ajiye littafin yayi tagumi yana kallonta yace "can I ask you something?" Ba tare da ta kalleshi ba tace "sure" yana taping hannunsa akan desk yace "me yasa ake ce miki Diyam? It means water right? Me yasa ake ce miki water?" Ta daina rubutun ta na kallonsa tace "maybe I am as important as water is to some people" yayi dariya yace "your boyfriend maybe" tayi murmushi kawai. A lokacin lecturer din su ya shigo, ya gyara zamansa yace "boring, boring, boring" ta sake murmushi kawai tana wandering me yake yi a makarantar in bashi da interest a karatun.

Diyam............... writing
[1/4, 10:30 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ Diyam ❤️

By

Maman Maama

Episode five

Yana tashi da safe kamar kullum abinda ya fara yi shine duba wayarsa, hopping to see ko dan text message ne ko da kuwa daga brother dinsa ne amma kamar kullum nothing, ya runtse idonsa ya bude, haushin su yake ji gabaki dayansu, wato suna nufin zasu iya cire shi daga rayuwarsu ko? Suna nufin zasu iya shafe babinsa su manta dashi, wato suna nufin koma me zai same shi basu da problem ko?

Ya sake duba account balance dinsa yaga kudin ciki ko ticket ba zai siya masa ba in ma yace gidan zai koma. Jin dadinsa daya ya biya kudin hotel room dinsa in advance tun kafin suyi blocking dinsa daga family account. Ya jima yana tunanin abinyi sannan yayi scrolling through contact dinsa ya nemo number din brother n sa ya tura masa text message. Ya duba wallet dinsa ya ga cash din daya rage masa, yayi tsaki tare da komawa ya kwanta a ransa yace "makarantar ma ba za'a je din ba". Ya jima a kwance sannan kuma ya mike da sauri ya shiga toilet, ya yanke shawarar abinda zaiyi. Idan ba zasu turo masa kudi ba to shi zai nemi kudi da kansa.

Yana gama shiryawa ya tafi wani sabon mall da aka bude nan kusa da hotel ɗin sa, tunda sabon guri ne yasan suna bukatar ma'aikata dan haka yaje ya nemi aikin salesman, bai sha wahala ba saboda yadda suka ganshi fes fes dashi dan gayu suka bashi aikin, zasu ke biyansa daily kuma pay din babu laifi, at least ya samu kudin abinci kafin komai ya warware masa.

A bangaren Diyam kuwa yau Saturday tun da suka tashi suke aikin sanitation din gidan kamar yadda suka saba yi duk sati. Sai da suka share ko'ina suka goge sannan ta shiga toilet tayi wanka ta fito ta tsaya gaban mirror tana kallon reflection dinta. She have come a long way. Last year kamar yanzu in aka ce mata zata zo inda take a yanzu she won't believe it, her life have been so fast, so dramatic and so challenging kuma she have succeeded all those challenges har ta kawo inda take a yanzu. Ta dauki mai tana shafawa a hankali tana noticing irin laushi da santsin da fatar ta take kara yi kullum, tabbas weather din London ta karbe ta.

Sai kuma taji tana kewar gida, ta gama shiryawa ta fita parlor ta zauna jiran su gama su fito su tafi shopping kamar yadda suka shirya. Anan ta dauko wayarta tana noticing time sannan ta kira Inna. Bugu daya ta dauka daga dukkan alamu tayi missing dinta itama. Ta gaishe ta, Inna tana ta tambayarta lafiyar ta data Murjanatu, sannan Diyam tace "ya naji ki shiru? Ina rigimammiyar taki ne?" Inna tace "babanta yazo ya dauke ta sun fita" Diyam ta lumshe idonta ta bude tace "ya zo garin kenan?" Inna tace "eh dazu da safe yazo, shine ya dauketa suka fita wai za'a siya mata keke, ko me zatayi da keke tana mace? Yace min ai zuwa nan da wani satin zai samu yazo ya ganku" Diyam ta kawar da maganar ta hanyar cewa "sun shirya kenan, shi da yar tasa" Inna tace "ina fa? Ta dai bishi da kyar. Daga gani ba da son ranta ba dan dai babu yadda zatayi" Diyam ta kwantar da kanta a jikin kujera tana jin duk tension din data bari a Nijeriya yana dawo mata. A hankali tace "ki gaishe ta inta dawo, a gaishe min da Asma'u" suka yi sallama lokacin da Judith da Murjanatu suka fito kusan a tare.

Duk su ukun suka tafi shopping din a tare, Diyam tana driving, Judith a side dinta Murjanatu kuma a baya. Annashuwa suke ji suna ta wake waken su da dararrakinsu. Murjanatu ce tace su je sabon mall din da wata kawarta tagaya mata an bude, nan take suka karbi address din suka saka a GPS ya kaisu har kofar mall din. Suka fito suka yi locking motar suka shiga suna yaba kyau da haduwar gurin. Suna shiga suka ji ance "welcome, what do you want to buy today" suka juya gaba dayansu a tare, idon Diyam ya sauka a kan Bassam da yake kallonsu da murmushi a fuskarsa, for the first time ta ganshi babu cigarette amma headphone din yana nan sai dai ya sauko dashi wuyansa, three-quarters wando da farar riga mai tambarin mall din wadanda suka kama shi suka fitar da ainahin cikar zatin sa. Cikakkiyar sumar kansa a taje a gyare tas. He looks so handsome and matured. Nan take murmushin nasa ya bace, ita kuma ta fara yi tace "Bassam?" Ya shafa kansa ya juya baya yace "damn it" Diyam tayi dariya tana zagayo wa gabansa tace "wow. This is no nice of you Bassam. Mutum mai dogaro da kansa ba sai ya jira an yi masa ba, ka burge ni sosai. And you look good" ta fada tana kallonsa daga sama har kasa. Ya kalle ta shima yace "you don't look bad yourself" tace "thanks" sannan ta gabatar dashi a gurin su Murjanatu wadda tunda ta ganshi ta gane shi ta kuma bata rai take ta zabga masa harara. Amma ba karya, ita kanta tasan kyakykyawa ne.

Shi ya zagaya dasu zuwa gurin duk abinda suke son siya, in sun je kuma zaiyi musu bayanin different brands na abinda zasu siya da kuma banbancinsu. A haka suka yi ta lodar kaya kamar Allah ya aiko su, kayan abinci kayan kwalliya kayan sawa, kayan ciye ciye da kayan shiririta, har sai da Bassam da kansa ya tsorata da siyayyar tasu yana gudun kar su je biya kudin su ya gaza suzo suji kunya kuma shi gashi bashi da kudin da zai biya musu amma dai sai yayi shiru. Amma suna zuwa gurin biya sai yaga ta basu credit card, ya dauke numfashin sa yana jiran yaji ance insufficient fund amma sai yaga an ciri kudin an miko mata card dinta. Nan aka loda musu kayan a manyan ledoji aka bawa labourers su kai musu mota, shi kuma ya bisu da niyyar ya tare musu cab amma sai yaga sun doshi wata lafiyayyar mota sun bude an saka musu kayan a ciki. Ya tsaya yana mamaki, a car? Student? In UK? Who is she? She definitely is not on scholarship kamar yadda ya dauka daga farko. Ya zagaya side dinta ya dafa windown yace "so, this is your car?" Tayi dariya tace "not mine, ara nayi from a friend of mine" tana jin Murjanatu tayi gyaran murya amma bata kula ta ba. Tace "to naga gurin aikin ka, zanke kawo maka ziyara" ya daga kafada yace "it is just a temporary part time job, kafin inyi clearing some situation" ta gyada kai tace "the not laughing situation?" Yayi dariya yace "yeah, one and the same" tace "da fatan ba zai ke hana ka zuwa school ba kamar yadda ya hana ka zuwa ranar Friday" ya kalle ta cikin ido yace "I will come, ko dan in ganki ma" tayi saurin fitar da idonta daga cikin nasa tace "see you on Monday then" suna jan motar daga gurin Murjanatu tace "you really are playing with fire" babu wanda ya bata amsa a cikin su. Daga nan basu koma gida ba sai suka shiga gari yawo, shiga can fita can suna ta bin GPS, suka tsaya wani restaurant suka ci abinci, suka je gidan wata kawar Murjanatu suka yi sallah, basu suka dawo gida ba sai yamma likis.

Da dare Diyam na kwance a kan gadon ta, jikinta likis saboda gajiyar zirga-zirga da sukayi tayi duk da cewa a mota suke. Ita kanta taji dadin fitar duk da dai bata nuna wa Murjanatu a fuska ba, she maintained her serious face. Ta tashi ta dauki ledar sweets da biscuits din da ta siyo da yawa kamar wata yarinya, ta jera su a bedside drawers dinta sannan ta dauko ledar m and m's ta kwanta ta na jefa wa a baki tana duba lecture note dinta.

Wayarta dake gefenta ce tayi kara, tana dubawa taga alert na kudin daya haura wadanda ta kashe musu, ko bata tambaya ba tasan daga inda kudin suka taho. Ta danyi tsaki ta ajiye wayar dai dai shigowar wani text message din. Ta sake dauka ta karanta kamar haka:

For the shopping you went to. Hope baki sha wahala da yawa ba. Kuma da fatan baki siyo sweets da yawa ba dan na sanki kamar shazumamu.
Your Love.
[1/5, 9:23 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: ❤️ DIYAM ❤️

By

Maman Maama

Episode Six: The Lucky Ones

Ta kalli jakar alawar kusa da ita ta sake karanta text din sai kawai tayi murmushi, sai kuma ta bata rai ta mike da sauri ta tafi dakin Murjanatu. Ta tarar da ita tana arranging kayan kwalliyar data siyo tace "ke kika gaya masa munje shopping?" Ba

Please Login or Register in order to submit comment