Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ji kaunar Abban ya lulluɓeshi, ƙauna dai kwatankwacin irin kaunarsa da Alhajinsa. Sallamar Tasleem din karo na biyu ya katse dukkan tunaninsa. Ganinta ɗauke da tray na kayan sanyi nan da nan ya ɗan ɗaure fuska, shi fa duk ba wannan ne a gabansa ba. Tana ajiyewa ya ga tana kokarin zama ya karya bille ya ce.

  "Where is she?"

Ta dube shi cikin rashin fahimta, ta yi ƙarfin hali ta ce.

"Who?"

Ya dauke kai daga kallonta, ya soma hasaso wani abun, ya gane ita ɗin manufarta daban, tunaninta ya tafi wani wajen. Mafarkinta daban.

"Wacce na zo domin ta, Humaira."

Kirjin Tasleem ya hau bugu, har ji ta yi ganinta ya ɗan dusashe. Miyan bakinta haka ta neme shi ta rasa, dakyar ta tattaro jarumta ta ce.

"Humaira kuma? Dama wajenta ka zo."

Sai a sannan ya dube ta tsakar ido.

"Yes, wurinta na zo. Ko sadda muka haɗu dama haka nace wujenki zan zo?"

Tasleem da har ta soma hawaye ta kasa magana, eh bai furta cewa wajenta zai zo ba, amma wane rainin hankali ne ya sa bai nemi kwatance daga Humaira ba sai a wurinta? Ta kuwa daure fuska tamau, ta rantse daga ita har Humairar sai dai su yi biyu babu. Kowa ya rasa don hana ta ce.

"Toh Humaira ban santa ba, asalima a wurin biki muka haɗu. Na yi zaton gidanmu kake nufin na kwatanta mana. Don haka babu Humaira a gidannan."

"Ko?" Ya furta idanunsa a saman hoton Abba, itama ta kalli hoton. Ranta ya ɓaci ainun, ta san kamannin Humaira muraran da ya gani a fuskar Abba ya sanya shi furta hakan. Ta mike tsaye ta  koma gefen Fadeel  ta zauna. Zuwa yanzu ransa ya kai maƙura wajen ɓaci amma yana tausar zuciyarsa da tunanin bai dace ba, ta ci alfarmar abin sonsa. Ko babu komai tace masa  mahaifinsu guda. Ita kuwa da muryar kuka ta soma magana.

"Wallahi ina sonka. Tun ganin farko da nayi maka zuciyata ta kamu da begenka. Me za ka yi da Humaira? Da me ta fi ni? Na rantse babu abin da za ta nunamin."

Ya runtse idanu, ransa ɓaci yake ya na kokarin danneshi, amma jin ana kushe abar sonsa ya bude idanunsa da suka yi jawur tarr a cikin nata. Sai da ta ji rishin kukan ya tsaya na ɗan lokaci tsabar fargabar kar ya shaƙo ta.

"Ki san kalaman da za ki faɗi a kanta. Idan kuma kina son kanki da mutunci, ki yakice ni a ranki. Ki sani kuma ki kara, Humaira ta fiyemin ire-irenki dubu. Kyau da sura ba su ne a gabana ba. Da ace su ne, na bar da yawansu a inda na fito, ba na sonki, ba kuma na son kowa sai ita ɗin. Idan za ki iya ki shiga ki yimin sallama da ita, idan ba ki iyawa ni zan sa a kira ta."

Da gudu Tasleem ta mike ta yi hanyar fita tana kuka sosai. Fadeel ya mike tsam ya fito farfajiyar gidan inda ya ci karo da Muhsin na wasa da keke. Ƙarasawa ya yi wurinsa ya ɗan durkusa daidai tsawon yaron yana murmushi kamar ba yanzun aka ɓata ransa ba.

"Boy, ya sunanka?"

"Muhsin."

Ya jinjina kai, da alama duka sunayen yan gidan su Humaira masu dadi ne, shi kam dadi yake mishi, ya ji ance Futuha, Tasleem yanzu kuma ga Muhsin.

Ganin yaron na shirin janye keken ya sanya shi saurin riƙe keken.

"Ɗan shiga ciki ka ce Humaira ta zo, Fadeel ya iso."

Jin haka Muhsin ya amsa da toh, ya juya kan kekensa bayan Fadeel ya saki ya wuce ciki.

***
A can kuwa, Mami da Futuha na zaune sai gani suka yi  Tasleem ta fado falon a guje, tana  zuwa ta zube cinyar Mamin tana kuka.

"Ke lafiya? Meyafaru?" Cewar Mami cikin ɗaga murya gaba daya ta ruɗe. Wannan ya yi sanadin fitowar su Humaira daga ɗaki sai a sannan Tasleem ta ɗago ta dubi Mami.

"Wai ba ki yake so ba, wajen Humaira ya zo."

Jin haka Futuha ta ji zuciyarta dan yi sanyi, ko ba komai Tasleem ba za ta ƙara hura mata hancin ta yi wanda ya fi Ibb ba kuma ta gane ba Ibb ne masoyin Humairar ba. Amma a gefe kuma kishi da tsanar Humaira ne ya kara mamaye ta, mene ne da ita wanda har namiji irin Fadeel zai gani ya maƙale mata, su da suke buzaye ma ta kasa shawo kan Ibb ya kaunace ta sai wata can bafulatanar ruga?

Mami kuwa gaba daya fuskarta ta sauya, kafin ta yi magana dai ga Muhsin a guje da kekensa ya shigo falon, yana cin karo da Humaira ya ce.

"Adda Humaira, ki je inji wani a waje."

"Ka je ka ce ba za ta fito ba! Kada ya kara gigin zuwa gidannan!"

Gaba daya suka dubi fuskar  kowannensu dauke da mamaki idan ka cire Humaira da kalaman ya yi mata dadi ainun, haba ta gaji da naci irin na Fadeel, shi bai san ba ta son komai da ya danganci saurayi ba. Meyasa ya ƙi fahimta? Ai gwara Mamin ta kora mata shi. A bangaren Raihana da Ummita kuwa tunaninsu daban da nata. Akan me Mami za ta ce Fadeel ya tafi? Wato don ba ya sin Tasleem shikenan kowa ma ya rasa? Tasleem da Futuha kuwa dadi ne ya mamaye su, wato dai uwa uwa ce, ta damu da yaranta. A farko sun yi zaton kwata-kwata Mamin ba ta kaunarsu ta fi kaunar ƴan riƙonta musamman ma Humaira. Amma a hukuncin da ta yi abin ya musu dadi, Tasleem ta ji gwara ma kowa ya rasa.

Muhsin kuwa tuni ya fice don cika umarnin Maminsa. Humaira dai ta juya zuwa daki don ci gaba da abin da ya rage na ninkin da take yi, ganin haka Ummita ta bi bayanta, Raihana kuwa da sauri ta bi bayan Muhsin. Futuha na kwala mata kira ta yi mata banza.

***
A can farfajiyar gidan kuwa, Muhsin ne ya karaso har kusa da Fadeel, yana shirin faɗin saƙon Mami da sauri Raihana ta kwala mishi kira.

"Kai Muhsin." Suka juya har Fadeel suka dube ta, ta karaso da sauri ta ce.

"Jeka zan faɗamasa." Ya kuwa tura kekensa ya ci gaba da zagaye a gidan yana waƙe-waƙensa da ake musu a boko. Ta gaida shi ya amsa, zuwa yanzu ya karaya da ganin Humaira.

"Suna na Raihana ƙanwa ce ga Humaira, don Allah ka yi hakuri ba za ka samu ganinta ba a yau sai dai ko watarana idan an ɗan kwana biyu."

Murmushin da bai kai zuci ba ya yi, ta tabbata shi kadai ke kiɗa da rawar sa, wacce ya ke yaƙin don ita ba ta san yana yi ba, ko kuma ya ce ta sani amma ra'ayinsu ya sha bamban.

"Kar ki damu, ba komai. Idan kin shiga ki ce ina gaishe ta, na kuma cika alƙawarin da na daukarwa kaina na zuwa gidansu. Amma hakan ba ya nufin ko a mafarki zan iya fita a rayuwarta. Ina sonta."

Daga nan ya juya ya fice. Raihana ta zuba masa idanu har ya fita daga gate din gidan, tausayi sosai ya ba ta, Humaira dai tana neman cutar da kanta. Samun masoyin gaske irin Fadeel abu ne mai matuƙar wahala. Ta ji haushin Humaira a zuciyarta kamar ta je ta rufe ta da duka. Gwuiwa a sake haka ta juya ta koma ciki.

***
Tun faruwar wannan lamarin Fadeel ya shiga damuwa ainun, yana da tabbacin shi yake so ba a sonsa, ya kuma shirya rungumar wannan jarrabawar ya yaƙe shi. A gefe ga mahaifansu da suka soma matsawa akan su fito da matan aure shi da Ibb. Satinsa guda bai kira ta ba balle ya aika mata saƙo, jarrabawa ya yi domin ya ga ko zai iya yakice ta a rai bisa shawarar Ibb amma sai ya ji kamar yanzun ne ma ya soma kaunarta. Ba kuma ya jin zai iya haƙura da ita. Ya miƙe daga saman gadon da yake kwance wanda tashinsa kenan daga bacci mai cike da mafarkan Humaira, kamar daga sama ya ji ana kwankwasa ƙofar falon, agogon dake maƙale a bangon ɗakin ya kalla, ƙarfe goma har ta gota. Ya ɗan ja ƙaramin tsaki, ya tuna yau suka yi da Alhaji zai soma zuwa kamfaninsa ya kama aiki, jin ƙarar kwankwasar yake har cikin kansa dake radadin ciwo, iya sati ɗaya zuciyarsa ta jigatu da rashin ji ko ganin Humaira, ta ina zai soma fidda ta daga rayuwarsa? Wannan abu ne da ba zai yiwu ba sam. A hankali ya miƙe daga shi sai vest da dogon wando ya fito falon.

"Waye?"

"Ni ce Yaya Fadeel, abin kari na kawomaka."

Guntun tsaki ya ja jin muryar Murja. Ƙofar kawai ya bude ya juya ba tare da ya ko kalle ta ba ya ce.

"Ki ajiye ki fice. Na gode."

Ta ji ciwon hakan amma da ta tuno da batun Malam na cewa idan har ya ci abinda ta girka da laƙanin da ya ba ta to fa ba makawa hankalinsa zai karkato gare ta. Ya yi mata gargadi akan lallai ta tabbata ya ci, idan kuwa bai ci ba to fa haka za ta kara narka uban kudade a yi mata wani sabon aikin. Don haka sai ta zauna a falon ta ƙi bin umarninsa, shi kuwa wanka ya shiga bayan sun yi waya da Alhaji ya buɗe mishi wuta akan rashin zuwansa ofis da wuri, hakuri ya dinga  a shi ya ce yana tafe. Suka yi sallama. Koda ya fito wankan a gaggauce ya shirya cikin kananun kaya, dark green din tshirt sai wandon jeans. Ya ɗaura agogo a tsintsiyar hannunsa, ya gyara sumar kansa. Fitowarsa falon ya ga mutum zaune, nan da nan ya tamke fuska, ita kuwa Murja da rawar jiki ta ce.

"Barka da safiya, bari na haɗa maka shayin."

Ba tare da ya kalle ta ba ya ce.

"No ki bar shi nayi latti, Alhaji na jirana. Ki je da su kawai."

Murja cikinta ya bada sautin kululu, ita dai ta shiga uku, wannan rashin sa'a har ina? Yanzu shikenan ta yi asarar dubu tamanin? Ita kuwa wa za ta je ya ba ta wasu kudaden a ƙara maimaicin aiki?

"Ba kya ji ne?"

Wannan karon ya yi maganar yana ji kamar ya ɗauke ta da mari hagu da dama, abu ɗaya da ya sa yake raga mata bai wuce na tunanin shi ɗin ma fa haka yake fama da soyayyar wata ba ta sonsa.

Ganin yanayinsa sai ta maida kayan kwandon ta dauka ta fice har da kwallarta. Fadeel yana so ya kashe ta, yanzun ma ji take kamar ta faɗa wannan faɗaɗɗan kirjin nasa ya yi mata rumfa da hannuwansa, sai dai kash! Wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa. Amma kuma komai nisan jifa ƙasa zai faɗo kuma sannu sannu ba ta hana zuwa, ta na ji a jikinta watarana haƙanta zai cimma ruwa.

***
Abba ne zaune fuskarsa cike da walwala, babu jimawa iyayen Hamza suka tafi bayan sun nemawa ɗansu auren Tasleem kuma ba musu ya amince ya ba su. Tasleem da kanta ta kira Hamza ta ce ya turo saboda bakin cikin abinda Fadeel ya yi mata, ga faɗan da suka yi da Futuha me  yi mata dariyar ta rasa shi, ita kuma don ta nunawa Futuha tana da mai sonta dagaske ba irin ita me bin Ibb ba ya sonta ba yasa ta kiran Hamza ta ce matukar dagaske yake toh ya turo a nema mishi aurenta a kwana uku, idan kuwa ya wuce haka to kaunar da yake mata a baki ne. Dama kuma shi abin da yake jira kenan, don haka sai kawai ya ba da kai bori ya hau.

Mami ta shigo itama fuskarta dauke da walwala ta zauna gefen Abba. Kafin ma ta ce wani abu ya riga ta.

"Maryama yau ina cike da farin ciki, ba ni da burin da ya wuce naga na aurar da yarannan mata lafiya kowaccensu ta tare a ɗakinta. Ina tsoron sharrin wannan zamani. Ita ma Futuha zan mata magana, ta fito da miji na haɗa aurensu baki ɗaya zai fi min. Karatun can su je su ƙarasa a ɗakin mazajensu, naji da kannensu masu tasowa."

Mami ta jinjina kai,

"Hakane Abban yara, in sha Allahu itama zamu yi magana da ita naji ko tana da tsayayye. Na san dai wani yaro da ta kwallafa rai a kansa amma shi bai san tana yi ba."

Abba ya ɗan yamutse fuska.

"Ai kinji irin shirmen yaran yanzu masu biyewa soyayya, ban da shiririta ke ba manema kika rasa ba, mutane nawa ne suka tare ni akan suna sonki amma ki nacewa wanda ba ya so? Allah ya kyauta, lallai ki ce mata nace ta nutsu ta fiddo miji a haɗa aurensu da ƴar uwarta. Kina ji dai iyayen shi Hamza sun ce nan da wata shida suke so a yi komai a ƙare."

"Shikenan, zan mata magana." Mami ta amsa a sanyaye, fatanta Allah yasa Futuha ta cire ran da ta kwallafa akan Ibb ta kama wani.

***
  Futuha na zaune tana danne-dannenta a waya kamar koyaushe, bidiyo mai zafi ta ɗora tana bin waƙa, ta ci ado a bidiyon har ta gaji, ta yi ɗaurin ture ka ga tsiya da dankwalinta na leshi, karanta comments kawai take tana jin dadi tana zabga murmushi, wasu kuwa zagi ne da addu'ar nema ma ta shiriya. Irin wannan sai dai ta ja tsaki ta wuce. Ta ci gaba da kallon bidiyoyin jama'a nan ta ci karo da wani bidiyo da ya ɗaga hankalinta wacce wata Sa'a Ƴar snow ta yi a kanta, zagi ne na cin mutunci da sharri, wai Baby Futuha ta tiktok karuwa ce kuma tana da hotunanta da shaidu akan hakan. Tashin hankalin har da hotonta daga ƙasa gefen bidiyon. Ba ta san sadda ta kwalla ƙara ba a ɗakin bar ya farkar da Humaira me baccin sha biyu. Su biyu ne dama kaɗai a ɗakin, ita Humaira ma ba ta san Futuhar ta shigo ba domin gaba daya sun fita makaranta, kenan ta dawo ita. Kuka sosai Futuha ke yi hannunta har yana kakkarwa. Humaira ta ji hankalinta ya tashi, duk kuwa da cewar ba sa shiri ta miƙe ta ƙarasa gareta.

  "Anti Futuha lafiya?"

Ba ta ko kalleta ba ta wuce da sauri ta yi hanyar fita. Humaira dai na kallon ikon Allah. Toh me ya yi zafi haka? Ta watsar da batunta gami da buga hamma.

Futuha kai tsaye falo ta nufa, babu kowa, cikinta ya ɗuri ruwa, yanzu wa za ta faɗawa wannan abu? Muddin Mami ta ji ranta zai ɓaci don dama ba da son ranta Futuhar ke ɗora bidiyo a Tiktok ba. Anna kuwa, ba lallai shawararta ya yi wani tasiri ba. Don haka kawai sai ta yi ɗakin samarin yayyunta. Kwankwasawa take iya karfinta, babu kowa sai Dawud dake baccin rana. Ya taso a firgice, har zai soma masifa amman ganin yanayinta sai ya fasa.

"Meyafaru?" Ya tambaya a ruɗe. Ta bude wayar da tuni ta shige lock, miƙamasa ta yi. Ya kalla tun farko har karshe, ya dafe kai yana mai runtse idanu.

"Kinga irinta ko! Kin ga abinda nake faɗamaki. Na faɗamaki matan nan na Tiktok muddin suka ga kina musu shiga hanci da kudundune zasu sanyoki a gaba. Ballantana ma ganin kin kama hanyar shahara. Sa'a ƴar snow! Yarinyar ba ta da mutunci ko kadan, matar da ke ikrari a fili ita karuwa ce kuma ba ta ga ranar da za ta rabu da karuwanci ba sannan ta shirya tone-tonen yan barikin tiktok."

Futuha ta jinjina kai har sannan tana sheshsheka, ta san da wannan, haka ɗin ne ma ya sanya ta shiga ruɗu da tashin hankali, waɗanda za su yarda da zancen sun fi waɗanda ba za su ɗauka ba yawa. Ko ba komai jita-jita ya fi saurin yaɗuwa koda kuwa akan ƙarya ne.

"Ya zan yi Dawud? Na shiga ruɗani, me zan ce jama'a su yarda sharri ne aka yimin?"

Dawud ya yi shiru, shima dai kansa ya yi masifar ƙullewa. Ya rasa me zai ce, daga  kuma irin yanda ake zuba ruwan comment na zagi da ma  masu rubuta ai za ta aikata lamarin ya samu karɓuwa kenan.

Kafin su ce komai sai ga wayar Aina'u ya shigo, Dawud ya ɗaga.

"Ke Futuha! Kinga wani  ɗan iskan bidiyo da Snow ta yi a kanki? Wallahi na shiga rudani, mene gaskiyar abin da ta ce game da ke?"

Hankalinta ya kara tashi.

"Aina'u ke ce mafi kusa da ni a ƙawayena, yanzu kin yarda da abin da aka ce a kaina? Idan kika yarda waye ba zai ƙi yarda ba? Wallahi Allah karya take yimin, ni Futuha ban taɓa zina ba a rayuwata. Ke kanki kin sani."

"To ai kuwa wallahi kinji na rantse sai kin yi dagaske za ki wanke kanki a idanun duniya musamman ƴan Tiktok, yanzu na faɗamaki a whatsapp na ci karo da bidiyon an turo group dinmu na makaranta."

Zaro ido Futuha ta yi, ji take komai tamkar a mafarki, ta kasa amsawa. Ga Aina'u a layi tana faman hello hello, ga kuma sunan Babban Yaya (Wato Mubarak) yana yawo a saman screen din, shaidar kiransa ya shigo. Dawud zai katse na Aina'u ya ɗaga  cikin sauri Futuha ta warce wayar ta kasheta gaba ɗaya. Cikinta ya murɗa ba ta tsaya ba shi amsa ba ta ruga ɗakinsu. Ta tsallake Mami wacce fitowarta kenan daga bangaren Anna su na tattaunawa akan auren Tasleem da wadanda ya dace su gayyata cikin yan uwansu na Agadez. Mami ta bi ta da kallon mamaki da tunanin ko lafiya, wayarta ta yi ƙara, ganin Mubarak yasa ta ɗaga.

"Mami, kina sane da abin da yarinyar can ta aikata ko?"

Cikin rashin fahimta da tsananin ruɗewa ta ce.

"Wa kake nufi? Meyafaru wai?"

Nan ya ba ta labarin ire-iren raye-raye da Futuha ke ɗorawa a Tiktok, ya kuma cewa Mamin ta duba whatsapp zai aikomata da wani bidiyo ta gani. Hannayen Mami har rawa suke yi, ta hau online bayan ta kunna data, saƙonni suka shiga faɗowa har na Hajiya Lubna wacce itama bidiyo ta aikomata. Sam hankalinta ya yi gaba akan saƙon Mubarak, ta buɗe ta soma kallon irin ruwan rashin mutuncin da wata wai Sa'a ƴar Snow ta saukewa Futuha, ga hoton Futuhar nan daga ƙasa. Mami tuni hawaye sun wanke fuskarta, ban da innalillahi ba abinda take furtawa, ya yi daidai da shigowar Dawud falon, ganin yanayin Mamin sai ya tabbatar abin da yake gudu ya afku, wato dai Mubarak ya sanar da Mamin komai. Ya kuma san halinsa, maganar ba iyakar Mami za ta tsaya ba, sai ya dangana da Abbansu.

Ganin tsayuwa na neman gagarar Mamin sai ta zauna a hannun kujera mafi kusa da inda take tsaye. Dawud ya karasa da sauri.

"Mami, yi a hankali."

Ta girgiza kai, ina batun hankali anan bayan ɗiyarta ta jawomusu abin kunya abin kuma magana. Kamar kuma wacce aka tsikara ta mike da sauri ta nufi hanyar dakin su Futuha sam hankalinta ba ya tare da ita. Ganin haka Dawud ya mara mata baya, fadi yake "Mami wallahi sharrin ƴan Tiktok ta hadu da shi, ke kin sani diyarki ba za ta aikata maki abin kunya ba. Don Allah Mami ki saurare ni, nasan wace wannan Sa'ar, ba ta da mutunci na ƙarshe."

Inaa! Ba ta san ma yana yi ba, shigarta ɗakin ya yi daidai da fitowar Futuha daga banɗaki, har a lokacin sheshsheƙa kawai ta ke yi. Humaira tuni ta tashi tana zaune gefen gado ta yi shiru, ita dai ta san babu lafiya. Ba ta taɓa ganin Futuha na irin wannan kukan ba kamar na wacce aka yiwa mutuwa. Shigowar Mamin ya sa ta maida hankali gareta, ba ta yi wata-wata ba ta hau dukan Futuha tana kuka tana fadin.

"Shegiya marar tarbiyya! Wato ke ga yar iska ashe raye-rayen da na nunamaki bana so shi ne kika cigaba da yi har ya jawomaki kalmar karuwa?!"

Mami bugu take ita kuwa Futuha tana ihun kuka. Humaira da Dawud hakuri kawai suke ba Mami, su kansu hankalinsu ba a nutse ba. Babu kamar ita Humairar da ba ta san hawa da sauka ba. Mami don kanta ta ture Futuha ta juya, har za ta fice ta dawo ta nuna ta da yatsa.

"Na ba ki mintuna uku ki gaggauta goge account dinki kaf na social media da kike raye-rayen banza, wallahi kika bar ko guda daya ban yafemaki ba. Shashasha kawai!"

Tana kai wa nan ta fice daga dakin har tana bangazar Dawud. Jikin Humaira a sanyaye ta kalli Dawud, kamar jira yake kuwa ya watsa mata banzan kallo.

"Algunguma, ficemin daga daki za mu yi magana da yar uwata."

Kamar ta ce mishi ai Abba ya hana su shigowa dakin sai dai ta hadiye ta fice sum-sum zuwa falon da babu kowa ta zauna jugum. Yau ba ta je gidan Anti Laila ba sakamakon rasuwar da aka yiwa Anti Lailar a can dangin mijinta. Tana nan zaune ta ji muryar Abba a bangarensa yana tashi har zuwa cikin falon, faɗa yake kamar zai ari baki. Mamaki ya kama ta, Abban bai fita kasuwa ba ko kuwa dawowa ya yi? Yanzun tare suke tafiya da su Yassar har Dawud wanda shi yau din bai jw ba sanadin ciwon kai da ya addabe shi Abban ya ce ya zauna, ya ce musu sam ba ya son zaman banza.

Humaira ta mike tsaye kirjinta na bugawa da sauri. Ta dai tsinkayi Abban na cewa "Cire ta zan yi daga makarantar! Itama ta fiddo miji na aura mata ko kuma na aurar da ita ga koma wane ne don wallahi ni dai Isuhu ba za ta yi sanadin zubewar mutuncina ba a garinnan!'

Gaba daya jikin Humaira ya hau rawa, ko ba a faɗa ba ta sani akan Futuha ake tashin hankalin nan. To me ta aikata mai muni har haka da maganar ta yi zafi? Tana nan tsaye Yassar ya shigo falon bai ko kalle ta ba ya yi hanyar dakinsu, shi ma Dawud na ciki. Ba ta motsa ba kuma sai ga yan makaranta sun dawo. Hankalinta ya dan kwanta ganin Raihana da Ummita. Ta karasa da sauri.

"Ku gidannan fa ba lafiya. Kin sani ne?"

Ta jefawa Raihana tambaya ganin yanda hawaye suka wanke fuskarta. Jikinta ya kara yin la'asar. Raihanar ce ta ba ta labarin abin da aka yiwa Futuhar, dafe kai Humaira ta yi gami da ambaton sunan Allah.

"Tirƙashi!" Abin da kawai ta ce a baki kenan. Dama tun sadda Futuha ta soma yayin ɗora bidiyo Tiktok ta so ace ta mata magana amma ta sani ba za ta ji komai ba. Watakila ma ta kira ta da mai hassada kamar yanda ta kira Tasleem sadda ta yi yunƙurin hana ta ɗorawa. To na kusa ma an mishi wannan ikrarin ina kuma ga ita da suke mata kallon bare a cikinsu?

Yinin ranar dai gidan ya kasance babu dadi, Abba ya yiwa Futuha kaca-kaca ya kuma rantse ya dakatar da karatunta har sai idan ta samu miji ta yi aure. Ya ba ta lokaci kankani akan ta fitar da daya cikin masoyanta a haɗa bikin da na yar uwarta. Idan kuwa ta ƙi shi da kansa zai nema mata abokin rayuwa.

Tasleem haka ita ma ta dawo daga asibiti ta iske wannan abin wanda tuni tana da labarin komai. Futuha ranar kamar an aikomata saƙon mutuwa haka ta wuni babu ci babu sha, Mami ta ce a kyale ta. Ganin ba ta da mafita ya sanya ta komawa ɓangaren Anna inda anan ne ta samu sassauci domin Anna goyamata baya ta yi, ta ce Mamin su yi mata uzurin kuruciya. Ta dai lallaɓa ta kwantar mata da hankali.

***
A sati biyun da Abba ya ɗibarwa Futuha don ta fiddo mijin aure, a wannan satin kafin su cika gaba daya ta rame ta zama mai wani irin sanyi, yan uwan Abba babu wanda ya goyi bayanta balle ya lallaɓa mata shi. Ganin haka Mami ta tashi takanas ta je ga aminiyarta Hajiya Lubna ko za ta amince Khalil ɗanta ya auri Futuha
su rufawa junansu asiri. Amma ina, Hajiya Lubna ta nunamata ita gogaggiyar yar boko ce ta biyo mata ta kissa ta nunamata ta amince, amma bayan kwana biyu ta kira ta tace Baban Khalil ya ce shi kam ya riga ya gama magana da abokinsa akan ƴarsa da yake son Khalil
DOWNLOAD
DOWNLOAD

5 Comments On DUKAN RUWA
avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

hhh

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
north

1 year ago

Reply

hhhhh

Please Login or Register in order to submit comment