Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

su Ummitan zuwa yanda aka kaya sadda aka je kwato su.

Mami kuwa ta ƙara jifan Anti Maijidda da murmushin cin nasara sannan ta juya ta bar falon zuciyarta fari ƙal yayinda ta bar Anti Maijidda da ɗumbin takaici da cizon yatsa. Ta sani addu'a babu abin da ba ya magani, za kuma ta dage da kai kukanta ga Allah, watarana halin Mami zai bayyana ƙarara a idon duniya.

***
Anti Amarya ta dubi Alhaji bayan gama nuna masa jita-jitar da ake yaɗawa akan su Humaira ta ce.

"Yanzu Alhaji wannan magana ko ƙarya ne a yanda sunan gidannan ya ɓaci fisabilillahi sai ka aminta da auren Fadeel da Humaira?"

Nan da nan Alhaji ya ɗaure fuska ya ajiye wayar.

"Me kike son ki cemin? Sai na tauyewa ɗana farin cikinsa akan ƙaryar da maƙaryata suke yamuɗiɗi da shi?"

Ta tari numfashinsa.

"Saboda farin cikin ɗanka mu kuma za ka zubar da namu ƙimar gidan a idon duniya? Ka san wannan ɓacin sunan kuwa ba iyaka Nijeriya ya zagaye ba? Allah kaɗai ya san inda lamarin ya tsaya. Alhaji ya kamata ka buɗe idanunka sarai ka dubi lamarin da idanun basira, ni ban taɓa ƙin Humaira ba saboda ban ga abin ƙi tattare da ita ba kamar yanda babu wani aibu da ta taɓa yi gareni ba. Amma ana magana ne na haɗa zuri'a, idan ya kasance sai bayan mai afkuwa ya afku maganar duniya ta tabbata gaskiya sai ka sa hannu a kumatu ka ce za ka yi tagumi da nadama?"

Shiru Alhaji ya yi, maganganun Anti Amarya suka shiga tasiri a zuciyarsa. Dagaske yanzu idan har zancen duniya ya tabbata shikenan ya haɗa iri da ɓata gari?

Anti Amarya ganin ya yi shiru sai ta yi ɗan murmushin mugunta, ko babu komai dai alamu sun nuna kwalliya za ta biya kuɗin sabulu, alƙawari ne ta ɗaukarwa kanta yanda Fadeel bai auri Murja ba ya yi sanadin barinta gidan, toh shima har abada sai ta raba shi da Humaira. Sai ta ga iya gudun ruwansa.

"Shikenan Antin yara, zan dai duba zancen. Mu yi addu'a mu kuma jira mu ga ta inda gaskiya za ta yi halinta."

Ta sauke ajiyar zuciya ganin ta yi nasara.

"Hakane, Allah ya bayyana gaskiyar."

Ya amsa da amin.

Ɓangaren Fadeel kuwa har tsawon kwanaki uku da al'amarin ya fasu yake cikin wani irin tashin hankali da baƙin ciki. Soyayyar da yake yiwa Humaira ta yi ƙarfin da ko daidai da ƙiftawar idanu ba ya zarginta da fasiƙanci balle kuma ya aminta da jita-jitar da ake yaɗawa. Wannan ya sanya a ɓangarensa shima ya sanya aka soma bincike akan al'amarin don a gano bakin zarensa. Ga bikin babban amininsa nan da kwanaki uku amma hakanan damuwar yanayinnan ya gusar da murnar bikin a zuciyarsa. Ta yaya mutanen da aka ceto su cikin wani hali na maye da kuma muguwar rama da baƙi ace yawon duniya suka shiga? Har abada ba zai yarda da wannan ba. Da taimakon wani abokinsu na makaranta wanda yake babban ma'aikacin sirri na SS, bincikensu ya dinga zurfi. Ibb dai ya zuba idanu kawai yana ƙara mamakin wannan irin zazzafar kaunar ta Fadeel akan Humaira. Har shakka yake yi kada bayan aure ya zame mata mijin tace saboda shi kam abin ma ya shallake tunaninsa.

***
Tasleem tsaye tana safa da marwa a ƙuryar ɗakinta daga ita sai vest wacce ta ɗage mata saboda girman da cikinta ya yi sai ko ƙaramin short, waya ne a kunnenta, burinta kawai Antinta ta ɗaga domin ta ƙagu ta ji labari. Har sai da ta kusan katsewa sannan Jannat ta ɗaga muryarta a sake. Ko gaisawa ba su yi ba ta gangara inda yake ci mata tuwo a ƙwarya.

"Anti, ina ta neman wayarki a kashe na ƙagu naji daga bakinki. Kin ji labarin da ke yawo a media akan su Humaira ko? Anti hala aikinki ne?"

Wata dariya Jannat ta yi daga ɓangarenta tun ma kafin ta ce komai Tasleem ta samu amsar tambayarta, sai kuma ta magantu.

"Ni ce nan my daughter, ai ban fanshi marin da munafukar ƙanwarki ta yimin ba. Idan sunansu ya ɓaci a idanun duniya wa kike tunanin zai aminta da auren ɗaya a cikinsu? Ko a zatonki wancan sakaran Fadeel ɗin zai ƙara kallonta? Tasleem ki kwantar da hankalinki, yanzu na san na gama ɗaukar fansa akan Humaira don uwarta. Ita kuwa Ummita kinga cikin dake jikinta ya taimaka wurin da jama'a za su yi saurin aminta. Ke tun sadda al'amarin ya faru nake bibiyar kalaman jama'a ina dariya. Huumm muje zuwa."

Tasleem ta yi murmushi sosai.

"Na ji dadin rabuwar Fadeel da Humaira, na sani ko ya nace akan sonta zai wahala iyayen da suka san mutuncin kansu su yarda ɗansu ya aure ta. Amma Anti naji fa wai Abba zai sa ayi binciken wanda ya fara yaɗawa don a gano gaskiyar magana. Bakya tunanin idan aka kama shi asiri ba zai tonu ba?"

Tsaki Jannat ta ja.

"Nawa aka yi irin haka Tasleem, kin taɓa ganin waɗanda aka yi nasarar cafkewa?"

"A'a."

"Toh ki sa ranki a inuwa tawan, babu abin da za su iya. Yanzu ai na kira Abbannaku na jajanta masa har da kukan shegantaka, shi kuwa sai faman godiya da ban hakuri yake."

Suka yi dariya Tasleem har tana riƙe cikinta da ya ɗan motsa saboda dariya.

"Ina yinki sosai Antina."

"Nima haka yar uwa. Maminki ce dai ta matsamin da tambayoyi tun ranar farko shiyasa nake ta kashe waya, wai ita ga mai wayo, bugar cikina take yi don ta gane ko ni ce na sanya a yi amma na nunamata ban san komai ba sai ma da ta faɗamin. Kema ina jan kunnenki koda wasa kar ki kuskura kiyi maganar da kowa."

Tasleem ta amsa cikin jin dadi da walwala.

"Kar ki samu damuwa Anti. Ba ki da matsala da ni."

Daga haka suka yi sallama zuƙatansu cike fal da annashuwar ƙuntatawa bayin Allah.

***
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels

DOWNLOAD
DOWNLOAD

5 Comments On DUKAN RUWA
avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

hhh

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
north

1 year ago

Reply

hhhhh

Please Login or Register in order to submit comment