Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta, daga baya kuwa Mami ta nemi ɗan sahun da zai dinga kai ta kuma ya ɗauko ta. Watarana kuwa da aka yiwa ɗan sahun rasuwa da kanta ta Mami ta sanya yaron gidan me musu wanki ya raka ta titi ya sanya ta a adaidaita, a dawowa da kanta ta dawo. Tun kuma daga nan ta soma zuwa da kanta ta dawo, a karshe kuma ya kasance koda ɗan sahun bai zo ba ita ke zuwa ta dawo. Ganin ta gane hanya ya sa Mami kawai ta sallami ɗan sahun ake ba ta kuɗin mota.
Komai idan ta koya tana samun ɗan littafin da Ummita ta bata ta rubuce tsaf da hausar ajami. Rubutunta mai ɗan karen kyau da burgewa har ya kasance Ummita ta yi ta santin handwritting din.

A bangaren Islamiyya kuwa, kusan tare suke tafiya da Ummita a aji duk kuwa da cewar a can karatunta ya zarta na su, akwai abubuwa da dama da ta sani na daga litattafan addini wanda na ajin ƴan gaba ne. Hakan ya sa idan ba sa komai ta ke zama malamar Ummita. Su yi ta karatunsu musamman yanzu da ake cikin hutun dogon zango na makarantun boko. Idan ka cire Tasleem da Futuha sai samarin, babu wanda ke zuwa makaranta. Gidan sai yake yiwa Humaira daɗi fiye da a baya.

Ranar wata Asabar da yammaci su na zaune a ɗakinsu, Humaira ke taya Ummita gyaran sif ɗinta, gaba ɗaya sun sauke kayan Ummitan saman gado. Humaira sai tsokanarta take yi akan da tuni yanzu an sanya ranar aurenta da Yusuf, ita kuwa tana kai mata bugu da ninkakkiyar rigarta. Sai kuma ta ja guntun tsaki ta zauna gefe tana murmushi.

"Ke nifa ina da mijin aure a hannu, kawai dai bai taɓa zuwa gidannan ba, ba na so kowa ya sani sai na kammala karatu."

Humaira ta zaro ido da wani irin zumuɗi ta ce.

"Don Allah dagaske? Waye wannan mai sa'ar?"

Ummita ta ɗan harareta sai kuma ta miƙe ta ci gaba da ninkin da take yi.

"Oho, idan ta yi wari kya ji."

Duk irin magiyar Humaira dai ba ta samu Ummita ta furta komai ba, da ta ga hakan ba mai ɓulla bane sai ta sauya ta ce.

"Toh abu ɗaya za ki faɗamin, Allah kuwan daga shi ba zan ƙara tambaya ba. Na san shi, na taɓa ganinsa? Eh ko aa?"

Dariya Ummita ta yi.

"Wai ni za ki yiwa wayo ko me?"

Itama dariyar ta yi.

"Allah ba wayo ba, kawai ina son sani."

Ummita ta ɗan yi shiru, ta sani idan har ta ce mata ta san shi to za ta ƙara damuwa da son ji ita kuwa duk data yarda da Humaira ba ta shirya kowa ya ji yanzu ba. Sai ta girgiza kai.

"A'a toh."

Jin haka Humaira ta taɓe baki.

"Toh shikenan, idan ta yi wari ma ji."

Kafin Ummita ta tanka sai ga Muhsin ya shigo a guje.

"Adda Humaira, ki zo inji Mami za ku gaisa da Yaya Kabeer."

Humaira ta ji kanta ya yi wani dum, wani irin ɓacin rai da bakin ciki na taso mata da ba ta san silarsa ba. Nan da nan ta haɗe fuska tamau kamar ba ita ke dariya yanzu ba.

"Ka ce gatanan zuwa." Ummita ta amsa jin ba ta da niyyar amsawar. Ta sani Humaira ta tsani Kabeer, tun ganin da ya yi mata a gidansu tare da Mami yake bibiyarta. Amma yadda fuskarta ta sauya ita kam ba ta taɓa ganinta cikin wannan yanayin ba.

"Ke lafiya? Daga ance maki Kabeer ya zo?"

Tsaki ta ja ta miƙe a fusace cike da wata iriyar tsiwar da ita kanta Ummita ba ta san ta da ita ba ta ce.

"Aikin banza da wofi, na tsani naci da takura wallahi. Mutum sai shegen naci, itama Mami ta biyemishi har da wani aikowa a yi kirana." Ta kara jan tsaki. Maganarta na karshe kan kunnen Raihana da ta shigo ɗakin tana danna waya, baki buɗe take kallonta.

"Ke, Mami za ki yiwa rashin kunya? Har da tsaki?"

Ko kallonta ba ta yi ba ta juya ta ci gaba da ninkin kayan da alama ba ta da ko niyyar tashi balle ta je. Ummita ta kalli Raihana itama ta dube ta, a fusace Raihana ta karaso ta fisge rigar dake hannun Humaira ta yi jifa da shi. Humaira ta mike a zuciye ta ce.

"Malama na fada! Nace na fada! Kabeer din banza da wofi! Ba zan je ba din akwai abin da za ki iya yi? Ko waye ya tilasta ni shiga lamarinsa sai na gasa mishi maganganun da zai yi dana sani!"

Raihana gaba daya ta tsorata, kamar dai Humaira kamar ba ita ba. Kawai sai ta gifta ta fice daga ɗakin ba tare da ta tanka ba don dama Raihana akwai tsoro. Ummita ta mike ta kama hannun Humaira a sanyaye.

"Humaira, lafiyarki kuwa? Me ya yi zafi?"

Ba ta ce komai ba kawai ta zare hannunta a cikin na Ummita, zama ta yi ta yi shiru sai huci ga gumi na tsastsafo mata. A haka Mami ta shigo dakin, Raihana duk ta ba ta labarin abin da ya faru, kallon Humaira take yi a nutse, sai kuma ta karasa ta zauna gefenta. A hankali ta dafe hannunta. Humaira ta kalleta, kawai sai ga mamakinsu ta fashe da kuka.

"Mami don Allah kiyi hakuri, wallahi na tsane shi, ki ganinsa bana son yi. Kiyi hakuri don Allah ki janye batun zuwa mu gaisa da shi."

Wani irin kuka ne da sheshsheƙa tamkar wacce ake kokarin raba ta da numfashinta. Mami da Ummita wacce duk ta firgice suka dubi juna sai kuma ta rungumo Humaira.

"Kar ki damu, ya tafi ya bar gidan ma. Kuma na yi maki alƙawari Kabeer ba zai ƙara takura maki ba. Kin ji ko?"

Sai a sannan ta gyaɗa kai ta bar kukan, lokaci guda kuma ta fara dawowa hayyacinta. Ita dai Ummita ikon Allah ta zubawa ido tana kallo. Abin dai kamar a wasan kwaikwayo.

06

Dare ne misalin karfe ɗaya da mintoci, ɗakin ya yi shiru ban da munsharin Tasleem ba abin da kan addabesu kullum ba abin da ke motsi. Humaira wacce abu biyu suka hana ta sukunin bacci, ta zubawa tagar ɗakin ido tana kallon farin wata da ya hasko har cikin ɗakin nasu. Garin babu zafi sai iska dake kaɗawa kaɗan kaɗan hakan yasa rashin wutar bai hana mutanen gidan sukuni ba. Ta ja guntun tsaki ta miƙe zaune gami da runtse idanunta.

_'Humaira ba ki kyautata kalamai ga Mami ba. An sani maganar Kabeer kika tsana, sai dai yanayin da kika yiwa Mami magana kamar wata Humairar aka chanja ba ke ba. Idan kin yiwa Raihana wannan dama abokiyar yinki ce, amma ga Mami, kin yi kuskure.'_

Ta tuno kalaman Ummita, wannan na daga cikin abin da ya damu zuciyarta, Mami fa, matar da ta ke ba ta kulawa da zuciya ɗaya. Ta maye mata gurbin Dada da Mamarta wacce ba ta buɗi ido ta gani ba. Ta kuma zame mata abokiyar hira a lokuta da dama idan tana zaune ita kaɗai a gidan. Hakan za ta dinga ba ta labarin Nijar itama ta ba ta na ainahin garin iyayenta wato Agadez su yi ta nishaɗi.

Abu na biyu da ya tsaya mata a rai bai wuce na mamaki da tunanin abin da ta yi ɗin ba. Eh ta san ba ta son Kabeer, ta tsani ma ganinsa, amma tsanar har ta yi yawan da za ta kasa ɓoyewa har haka? Ita kam abin ya sha mata kai.

Tana nan zaune dai ganin ɓatawa kanta lokaci da tunani take yi da b zai magance mata komai ba sai kawai ta maida kai filo a hankali bacci ya sure ra. Duka wannan zaman da ta yi har zuwa kwanciyarta akan idanun Raihana wacce munsharin Tasleem ya hana ta sukunin bacci. Tsoron yarinyar ya ƙaru a zuciyarta, ta kasa kwakkwarar motsi ga fitsari cike fal a mararta amma ina, ga ni take ai tana miƙewa Humaira za ta tashi ta shaƙe ta don ta gama ba zuciyarta cewar iskokai ne da Humairar. A wannan daren dai bacci ɓarawo ne ya sace Raihana.

***
Ta kammala shirinta tsaf kamar koyaushe za ta wuce wurin koyon girki, ta fito falon. Ummita na zaune tare da su Muhsin a falon, Raihana kuwa na gefe ɗaya ta hakimce tana abin da ta saba, latse-latsen waya. Ganin Humaira yasa ta kalle ta sau ɗaya ba ta ƙara ba don ita ba ta so ma su haɗa ido, har ga Allah tun can tana tsoron mai aljanu. Tana kuma shakkar yi musu rashin kunya tun wataran tana jss 2 da wata abokiyar karatunta ta shaƙe ta akan ta zauna a kujerarta ta kuma yi magana amma ta ƙi tashi. Da ta fusata ta shaƙo wuyanta sai da malaminsu ya kwace ta. Abba har makarantar ya je, iyayen yarinyar suka ba da hakuri aka kuma sauya musu aji. Tun daga nan ta ke tsoron duk abin da zai danganta ta da mai iskokai. Ko kusa da su ba ta raɓa.

"Har kin fito kenan?" Ummita ta tambaya tana kallonta fuska a sake. Itama murmushin ta yi.

"Na fito, ina Mami?"

"Tana sashinta." Daga nan ta nufi sashin Mamin, a falo ta iske ta tana waya tana dariya, ganinta yasa ta yi sallama da ɗaya ɓangaren ta ajiye waya. Cike da walwala ta ce.

"Ƴar Mami har an fito?"

Kunya ta kamata, ita kunyar Mamin take ji wallahi, ta karasa ta durkusanta gaida ta.

"To, wata sabuwar gaisuwa ce nan ban da wacce muka yi ɗazu?"

Mamin ta faɗi cikin wasa da dariya, Humaira dake sunne kai ta ɗan murmusa, ita ta manta ma sun gaisa ɗin. Mamin ta ƙara magana.

"Au, ashe gidan Laila za ki ko? Bari ma na ba ki saƙonta ki tafi da shi." Mamin daga haka ta miƙe ta nufi ɗaki, can ta fito ɗauke da leda wacce Humairar ba ta san ma ko mene ba ta karɓa. Ta ba ta kuɗin mota tana fadin.

"Abbanki ya riga ya fita na mance ban karɓar maki na motar ba, ki je kawai idan ya dawo sai na karɓa."

Ta gyaɗa kai ta sa hannu ta karɓa da godiya, ganin ta ƙi motsawa balle ta tashi ya sa Mamin tattaro nutsuwarta gareta.

"Lafiya Humaira? Akwai magana a bakinki ko?"

Gyaɗa kai ta ƙara yi a karo na biyu, cikin nutsuwa kuma ta soma magana.


"Mami dama akan abin da ya faru jiya ne, ina neman gafara."

Murmushi Mamin ta yi ta girgiza mata kai.

"Kar ki damu, ni nasan ba laifinki ba ne. Hakan ya sa na yi maki uzuri. Ki cire komai a ranki kedai ki tattara nutsuwarki ki cigaba da maida hankali ga darussanki. Laila na ta yabon kwazonki don haka ki ƙara dagewa, na maki alƙawarin Kabeer ba zai ƙara shiga sabgarki ba, kin ji ko?"

Sai a sannan ta sauke ajiyar zuciya ta samun nutsuwa, ta amsa da toh daga nan suka yi sallama ta mike ta fita, Mamin ta bita da kallo tana murmushi.

***
Tuƙi ɗan sahun ke yi cike da nutsuwa, sosai tuƙin ke mata daɗi yayin da iskar dake kaɗawa a garin ke ƙara jefa ta cikin walwala. Damuwar da ta kwana da shi a ƙarƙashin ranta, tas ya wanke ya koma annashuwa. Don haka murmushi take yi ma ba tare da sanin tana yinsa ba. Ba zato ta ji ta yi wani irin hantsilawa sai ga ta a bayan ɗan sahun nan hannayenta rungume a kan wuyansa kai kace wacce aka goyo. Shi kuwa ɗan sahun kansa ya ƙumu da jikin gilashin da karfi har sai da gilashin ya tsage, saura kaɗan adaidaitar ta wuntsila amma Allah ya taƙaita faruwar hakan, sai ya koma baya da ƙarfi har tayoyin na bugun ƙasa da ƙarfi, wannan ya sa ta koma mazauninta, lokaci guda ta saki ƴar guntuwar ƙara sakamakon cikinta da ya bugu da ƙarfen jikin mazaunin direban yake mata zafi dalilin buguwar da ta ƙara yi dalilin komawa baya. Ta runtse idanu daidai sadda ta ji salatin jama'a a kansu. Gaba ɗaya ma ta kasa buɗe idanunta tana dafe da cikinta, ta yi shiru kawai don hayaniyar ma ba burge ta take ba.

"Sannu ƴanmata, sauko."

Ta tsinkayi ɗaya daga cikin jama'ar wurin na fadi, wasu kuwa na hayaniya su na fadin ai laifin mai motar ne. Can kuma ta ji an ce.

"Alhaji kai ne da laifi, kai ka bugi motarsu garin cin burki a kurarren lokaci."

Ta buɗe idanunta a hankali jin wani daddaɗan kamshi a gefe, a hankali ta sa hannu ta ɗauki jakarta da ta tarwatse a ƙasa, duk tarkacenta sun zubo. Wani matashi ya shiga tattara mata ita kuwa tana son ta fito a adaidaitar kamar yanda ɗan sahun ya fita ya zauna gefen kwalta, amma ina tururuwar mazan dake wurin ya sa ko motsin kirki ta kasa. Da murya irin ta manyan mutane ya amsa.

"Baba, ba abin zafi ba ne. Na sani ni keda laifi, ina mai ba da hakuri garesu. Zan kuma yi kokarin gyara ɓarnar da nayi. Ku yi hakuri don Allah."

Humaira ta juya ta kai duba ga mai maganar, daidai lokacin da shima ya ɗan rankwafo don ya yi mata sannu da kuma neman alfarma akan ta sauko su je asibiti. Kalma ɗaya ta kasa fita a bakinsa da ya yi nauyi. Ƙafafunsa suka soma ƙoƙarin kayar da shi. Zai iya rantsuwa ba kaffara son budurwar yarinyarnan yake da idan da ace Uwargidansa ta yi haihuwar wuri to fa ya ci ya yi haihuwar fari da ita. A ɓangaren Humaira kallon da ta bishi da shi bai wuce na son ganin marar hankalin da bai iya tuƙi akan ƙa'ida ba har yake shirin kai ta barzahu. Babban mutum wanda ba gigin kuruciya tattare da shi, ya sha manyan kayansa har da babbar riga da hula. Kana ganinsa dai ka ga wanda ya ba arba'in baya. Ganin yadda ya ƙuramata idanu sai nan da nan ranta ya yi masifar ɓaci, ta ja tsaki wanda ya ba Alhajin nan mamaki, ba ta jira komai ba ta sauko daga adaidaita sahun ta ɗaya ɓangaren mutane na mata sannu. Matashin da ya tattara mata kayan ta yiwa godiya ta karɓi jakarta, ba ta so dubawa ba amma da yake ya matsa sai kawai ta duba, komai nata yana nan cif ba abin da ya ɓata. Dakyar take tafiya dalilin gefen cikin da har sannan ke mata ɗan zugi.

"Sannu baiwar Allah, kiyi hakuri ba da gayya hakan ta faru ba. Direbana ne ya ɗauki waya bisa umarnina ba kuma mu ankara ba hakan ta kasance. Akwai inda ke maki ciwo sai a karasa asibiti."

Ya karashe yana kai idanunsa kan gefen cikinta da take ta faman dafewa. Ganin haka sai ta saki cikin don ba ta kaunar taimakonsa saboda irin kallon da yake jifanta da shi, kwatankwacin irin kallon Kabeer. Fuskarta a daure tamau ta amsa.

"Na ce maku babu abin da ke damuna, lafiyata kalau. Nagode da taimakon."
Daga haka ta karasa tana cije lebba ta yiwa ɗan sahun sannu kafin ta kai hannunta dake rawa don har lokacin ba ta dawo daidai daga razanin da ta shiga na hatsarin ba ta fiddo kudi za ta ba ɗan sahun na hakkinsa dake wurinta amma ta kara tsintar muryar Alhajin nan wannan karon muryarsa har ƴar rawa take yi, kirjinsa kuwa bugu yake da karfi tsabar son da ya shiga zuciyarsa farat ɗaya na yarinyar.

"Ki bar shi zan biya. A wane unguwa kike sai mu sauke ki?"

Jama'ar duk idanunsu a kansu, wadanda suka lura da yanayin mutumin ba su ga laifinsa ba don Humaira ta haɗu iyakar haɗuwa, sai dai a ganin wasunsu, girma ne zai fadi muddin ya bari ta gasa mishi magana. Aikuwa masu wannan tunanin ba su kai ga furtawa ba suka tsinkayi muryarya cike da tsiwa tana magana tana kara zaro manyan idanunta masha Allah.

"Baba ina mutunta furfurarka hakan yasa nake gargadinka akan ka fita a hanyata wallahi tun ban gasamaka wacce za ta hanaka bacci ba. Haba! Wannan ai shiga sharo ba shanu ne, ka kusan kaimu lahira na maka uzuri yanzu kuma me ya shafeka da kudin da zan bayar? Da kai ke biyamin kudin motar? Ina ruwanka da ni?" Daga haka ta ja dogon tsaki ta miƙawa ɗan sahun dubun gaba daya na motarta zuwa da komawa ba tare da ta jira chanji ba, daga haka ta juya daidai sadda wannan matashin ya kara miƙo mata ledar da shaf ta mance da batunsa, saƙon Mami zuwa ga Anti Laila. Sai lokacin ta ga ashe ma leshi ne sai atamfa. Godiya ta yiwa matashin a fusace ta bar wurin tana huci, ga cikinta inda ta ɗan bugu bai bar raɗaɗi ba. Kunya da tarin bakin ciki suka lulluɓe Alhajin, bai taɓa zaton yarinyar ba ta da kunya ba da tuni ya ɓoye zalamarsa a kanta.

"Sai hakuri Alhaji, yaran yanzu ba su da kunya."

Ya basar da zancen yana maida duba ga Ɗan sahun nan da ba da umarnin ya tashi su karasa asibiti ko kuwa dai ya sallame shi yanzun a nan, ɗan sahun ya aminta da hakan, nan take ya ba shi kuɗaɗe masu ɗan kauri gami da ƙara ba shi hakuri. Daga haka ya juya zuwa motarsa har lokacin bai daina jin kunya da ɓacin rai ba su sake shi ba. Ya kuma ƙudurta a ransa idan har haka yaran zamani su ke, to ya yi Allah wadai da ire irenta, ba kuma ya jin zai kara kallonta da sunan wata da ya taɓa gani har ya ji kaunarta cikin ransa.

***
A ɓangaren Humaira dakyar ta karasa gidan Anti Laila, ita sai da suka yi nisa ma ta tuno ba ta da chanjin da za ta sallami mai adaidaitan don haka ta ce ya jira ta kawo mishi. Wajen Anti Laila ta karɓa bayan ta mata bayanin hatsarin da suka yi, nan kowa ya hau ta da sannu. Anti Laila da kanta ta kira Mami ta shaida mata, hankali tashe ko mintuna talatin ba a yi ba sai ga Mamin da direban Abba. Daukarta ta yi suka nufi asibiti, koda likita ya duba ta ya tabbatar kawai buguwa ce. Magunguna ya ba ta sannan suka wuce gida. Maganin ta sha bayan ta ci abinci ta kwanta.

Abba har ɗakinsu ya shigo ya duba ta, ganin da sauki bacci ma take ya sanya shi fita.

Sai da ta yi kwanaki uku ba ta leƙa ko farfajiyar gidan ba a rana ta hudu ta koma zuwa koyon girke-girke abin ta.

***
Rayuwar ta ci gaba da tafiya yau dadi gobe babu, rashin dadin a wajen Humaira bai wuce na yadda su Tasleem ke kara nuna mata kiyayya a fili ba. Har ta kai da an wayi gari watarana sun yi mata sharrin sata, domin an tashi Mami tana neman kudin har dubi ashirin da ta ajiye ƙasan filo, gaba daya ran Mami a ɓace yake, sannan ma ita Humaira ba ta nan kuma ita ce ta gyara ɗakin kafin ta fice gidan Laila. Ganin an duba ko'ina sai Futuha da su Yassar suka ba da shawarar a duba ɗakunansu. Mami a farko ta ƙi, sai da Ladidi ta ce ya kamata a duba ko'ina tunda dai nema ake kuma abin da yasa Ladidin faɗin haka ganin su na neman ɗorawa yarinyar kirki Humaira ita kuwa tana da yaƙinin idan har Humaira ce ba za a sami ko sisi na wani a kayanta ba. Tasleem da ta dage tunda Humaira ce ta yi gyaran ɗakin a soma duba kayanta ya sa Ummita cike da kwarin gwuiwar sanin wace ce Humaira ta shiga fiddo kayan Humairar daga sif dinta. Sai dai tun kan ta yi nisa Futuha ta zura hannu ta jawo wata doguwar riga.

"Kambu! Dama yarinyar nan ita ta ɗaukarmin wannan rigar? Tasleem ku dubi rigar da nake tunanin ta ɓata a wajen wanki?"

Mami ta kalle su, ta yi shiru da mamaki. Can kuma sai ga ɗan kunne da sarƙa sun faɗo. Raihana ta zaro ido tana ɗauka.

"Innalillahi, ku ga sarƙata da nake nema kwanaki? Ashe ita ta ɗauka?"

Kai kamar wasa jikin Ummita na sanyi da wannan sharrin, ba ta yi aune ba ta kai hannu kan takardun kuɗi, tsabar razanar da ta yi ya sa ta fiddowa da sauri. Ladidi ce ta karɓa tana salati ta ƙirga, aikuwa dubu ashirin cif ne wanda Mami ke cigiya, Ummita kawai sai ta fashe da kuka tana faɗin.

"Wallahi Mami wannan sharri ne, Humaira ba ɓarauniya ba ce. Ko kwandalar mutum ta gani idan tana aiki ajiyesu take a wurin da ta gan su."

Mami dai ba ta iya magana ba domin kanta ya ƙulle, a sanyaye ta sa hannu ta karɓi kuɗin ta fice a ɗakin tana ji su Yassar na yiwa Ummita masifa wai sai ta faɗi wa ke mata sharrin amma ba ta ko iya tankawa ba. Ita kanta ta sani sata ba ya daga halayyar Humaira don ta sha ajiye kuɗin da suka fi waɗannan kauri ba ta taɓa su ba, amma ta sani mutum ka iya sauyawa. Bare ma a irin gidan nan na Alhaji Isuhu da ba a facaka da kuɗi.

Humaira ba ta dawo gidan ba sai yammaci bayan la'asar, da murnarta ta tura kyauren gate ta shigo bayan ta gaida Baba dattijo dake zaune a benci yana siyan rogo a wurin ƴar tallah. Farin cikin bai wuce na yadda suka yi snacks har biyu a yau ba, samosa da springroll kuma cikin ikon Allah ta yi ya yi kyau a ido ya kuma yi daɗi a baki har a foilpaper ta nannaɗe ta kawo don Mami ta ci ta ji. Muryar Ƙasim ta tsinta a kanta.

"Ɓarauniya ta dawo."

Kallonsa ta yi gabanta ya faɗi, a duk irin wulakanci da jefa-jefan mugayen sunaye da suke mata, babu wani cinikinsu a ya taɓa kiranta da ɓarauniya wannan ya sa ta ji wani irin sanyi har ta kasa mayar masa da martani yadda ta saba idan ya jefe ta da marar dadi. Ya ɗan ɗaga gira.

"Oh, bakin ta kanwa ya yi la'asar kenan saboda kin sani kin sata shiyasa. Dama ustazancin ashe na ƙarya ne, toh yau asirinki ya tonu. Ɗan adam butulu."

Ta dafa kirji idanunta da suka cicciko da kwalla tun soma maganarsa ta kafa mishi.

"Yaya Ƙasim sata fa ka ce? Ni na yi satar?"

Ya harareta ya wuce kawai ba tare da ya ce komai ba. Ta bishi da kallo har ya shige gidan, itama a hankali ta soma taka ƙafafuwanta da suka yi mata nauyi saboda mutuwar da jikinta ya yi ta yi cikin gidan kirjinta na harbawa.

***

Ma sha Allah, Alhamdulillah. Sai kuma bayan sallah in sha Allah. Allah ya karbi ibadunmu, a sanya ni a addu'a ina bararta don Allah. 🤲🤲 Fatan alheri.

07

Tasleem, Dawud, Yassar da Futuha ne zaune cikin falon sai dai ba ta sha mamakin ƙin amsa sallamarta da suka yi ba, dama ya lafiyar giwa ballantana kuma an jefe ta da kashi? Su na ganinta Tasleem ta miƙe ta yi kerere gabanta hannuwa a ƙugu ta ce.

"Ɓarauniyar banza da wofi, kin dawo kina wani sum-sum kamar munafuka. Koda dai dama munafukar ce, Mamin da ta daukake ki tana maki kallon kamar wata waliyya ai gashinan kin watsa mata ƙasa a ido. Ke ni ba wannan ba ma, earpiece dina da na jima ina nema idan kinsan ke ce ɓarauniyarsa wallahi tun wuri ki fiddomin abina. Atoh, bari ma Abba ya shigo gidan, ko Mami ba ta faɗamasa ba sai mun faɗa."

Humaira wacce ta kasa tsaida hawayenta, kallon Tasleem din kawai take har ta kai aya, lebbanta na rawa amma ko harafi guda ta kasa fitarwa tsabar baƙin ciki. Wannan wace irin baƙar rana ce a wajenta haka da za a wayi gari da yi mata ƙazafin sata? Ta kasa motsawa, haka Futuha ma ta taso da nata kalar rashin mutuncin, su Yassar na taya ta. Ba ta iya cewa uffan ba sai kukan da ta ke rusawa kamar ranta zai fice. Tsawar da ta ji an daka musu ya sa ta kallon hanya, ruwan hawaye ya sa ganinta komawa dishi-dishi, sai a hankali bayan ta ɗan runtse idanu sun ɗan zuba ne sannan ta lura ashe Mami ce. Ƙarasowa ta yi fuskarta a ɗaure, sai
DOWNLOAD
DOWNLOAD

5 Comments On DUKAN RUWA
avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

hhh

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
north

1 year ago

Reply

hhhhh

Please Login or Register in order to submit comment