Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

doguwa ce ƴar kanti ta sa mai kama jiki.

"Kallon me kike yimin kamar wata mayya? Kar ki ji ance wai wani ke ƴar Abbanmu ce ki yi ƙoƙarin haɗa kanmu da ke, wallahi kar ki kuskura don bakin rijiya ba wajen wasan yaro ba ne, atoh. Gwara ma Abban ya zo a yi meeting ɗin a bambance tsakanin aya da tsakuwa."

Duka wannan bayanin daga bakin Raihana su ke fitowa, Humaira ta sauke idanunta a hankali zuciyarta na zafi, dagasken dai ba ta samu karɓuwar kenan ba, zuciyarta na da ƙarfin jure abu idan har wanda ya fi ta a shekaru ne ya aikata gareta, amma ba ta jin za ta iya ɗaukar wannan rainin wayon.

"Futuha mene ne haka wai? Meyasa kullum burinku ku tozarta mutum?"

Maganar Ummita ya sanya Humaira ɗago kai, ashe wai akwatinta wacce aka kira Futuha ta nufa ta buɗe. Ita dai wacce ke faman  waya tun ɗazun.

Ai kuwa kamar an mintsile ta haka ta miƙe tsaye a zafafe, ta ƙarasa daidai sadda Futuha ta ɗaga akwatin da niyyar doka shi da ƙas, da wani irin zafin nama ta ture ta, daga ita har akwatin suka faɗi, akwatin ya faɗa saman  gado, ita kuwa ta yi rashe-rashe a ƙasan gadon bayan ƙugunta ya bugi katakon. Ai kuwa  ta kurma ihu, Raihana da ɗaya budurwar da  Ummita ta ambata da Tasleem suka yo kai Humaira gadan-gadan, Ummita ta tare su. Ita kuwa Humaira  ko a jikinta ta nufi akwatin ta shiga harhaɗa kayan da suka zube tana maidawa lokaci ɗaya hawayen da ta fi zaton na ɓacin rai ne, su na kwaranya. Ya yi daidai da faɗowar Maminsu ɗakin wanda hakan  bai wuce sanadiyyar ihun Futuha da ya mamaye ilahirin ɗakin ba. Jin muryarta da ta yi sai da gabanta ya faɗi, ta rasa dalilin da yasa take jin haka a kanta. Ta shiga ambaton sunan Allah a ƙasan ranta.

  "Lafiya? Me nake gani haka kamar waɗanda aka ƙwato daga bakin kura? Ke Ummita sake ta, kyale su na ga gudun ruwansu. Au, don ku nuna mata rashin tarbiyyarku ba komai ba ne ba ko? Har kun soma yada halin?"

Tana maganar ne fuskarta a murtuke tana bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya, ita dai Humaira sam ba ta tofa ba sai ci gaba da tsince kayanta da tayi tana harhaɗawa tana mayarwa ciki. Ba ta san ma'anar juya harshe zuwa wani can daban da ba ta sani ba, ta dai ji Mamin a cikin yare ta yi musu magana wanda ba ta fahimci koda harafi guda a ciki ba, sai gani kawai ta yi duka sun fice daga ɗakin idan ka cire Ummita da ta durkusa tana taya ta haɗi da ƙara ba ta haƙuri. Tana niyyar amsawa Ummita ta ji  an shafa kanta, ta runtse idanu ba tare da ta  ɗago kai ba don tasan Mami ce.

"Ki yi hakuri kin ji Humaira, su Tasleem su na da irin wannan halayyar na son yiwa baƙo shaƙiyanci. Kinga yau ki ka zo kuma kafin su karɓe ki za'a ɗan kwana biyu, a hankali idan sun gane ke ɗin ɗaya ce a cikinsu komai zai wuce kin ji ko? Ki ɗauke ni madadin Uwa, don mahaifiyarki mun yi zaman mutunci da nutunta juna da ita. Kema kuma nasan muddin dai kyawawan ɗabi'unta kika kwaso, ba za mu samu kowace iriyar matsala ba. Ina fatan haka?"

Jin bayanan Mamin sai ta tsinci zuciyarta da yin sanyi, ta ji lokaci guda kaso saba'in na fargabarta akan Mami ya ragu, wannan furuci nata na madadin Uwa, ba ta jin za ta iya kwatanta daɗin da ya sanya ta. Kai ta gyaɗa alamar toh,  Mamin ta maida dubanta ga Ummita.

"Sai ku hanzarta ku fito ta ci abinci daga nan zuwa bayan sallar isha'i, Abbanku na neman mu duka."

"Toh Mami." Faɗin Ummita cike da girmamawa. Daga haka ta fice ta bar mu. Ummita ta kalli Humaira da murmushi saman fuskarta.

"Sai fa kin yi hakuri sosai Humaira, da gaskiyar Mami, dama ya lafiyar giwa balle an jefe ta da kashi. Su Tasleem ba su da kirki, har gwara su Yassar a kansu, don su ba su kunyar ido, za su yi maka abin da suka so. Ki yi hakuri don Allah. Nima haka nake fama da su, don ma dai babu yadda suka iya da ni ne, Mamin na taka musu burki sosai a kaina."

Jin haka ta ji ta sosamata inda yake mata ƙaiƙaiyi. Aikuwa ta kasa shiru sai da ta furzar.

"Yauwa nikam Ummita, amma ba Mami ce ta haifeki ba ko?"

Ummita ta yi dariya.

"Kin gan ni ƴar baƙa ko?"

Sai kuma ta gyaɗa kai ta ɗan sauya fuska alamar damuwa.

"Ba Mami ce ta haife ni ba kuma ba Abba ne mahaifina ba. Mahaifina ƙanin Abba ne, mahaifiyata kuwa ƴar asalin garin Bichi ce, gaba ɗaya sun rasu ne a sanadiyyar gobara. Ni kaɗai ce rai da aka fitar a gidanmu ko kwarzane tun ina da shekaru biyar a duniya, amma daga su har ƙannena jarirai ƴan biyu duka sun rasu. Tun daga wannan lokacin ne, na soma rayuwa a hannun Kakarmu sai daga baya ne Abba ya maido ni gidansa ya damƙa amanata ga Mami. Matar da ta riƙe ni har zuwa yau ba tare da ta nuna bambanci tsakanina da nata yaran ba, kusan ince a zamanin dai samun irin Mami abu ne mai wahala. Ga kirki da son mutane, ke ba don dai kar nayi hauka ba zan iya ce maki Mami ta fi nunamin ƙauna da so fiye da nata yaran domin hatta da ragamar kula da ɗakinta da na Anna ni ta damƙawa. Ke daidai da shawara wani lokacin da ni take yi. Sai ta ture shawarar nata yaran ta ɗauki nawa."

Jinjina kai Humaira ta yi, eh lallai kam Mami ta yi abin a yaba mata, a zamanin nan kafin a samu mai fifita ɗan wani akan nashi abu ne mai matuƙar wahala.

"Wace ce Anna?"

Humaira ta watsa mata tambayar.  Ta miƙe ta shiga rufe akwatin a lokaci guda tana ba ta amsa.
  
  "Anna kakar su Tasleem, wacce ta haifi Mami. Ai anan gidan take rayuwa, a baya ma har da ƙanwar Mami da ba ta yi aure ba muka zauna. Amma yanzu Allah ya taimaka tayi aure tana zaune a can Misra da mijinta, ke kam ai Allah ya taimake ki ba za ki rayu inuwa ɗaya da ita ba. Don ta fi su Tasleem zafi da tsangwama, ke ta dai tsani duk wanda ba jininsu ba. Hatta da dangin Abba ba ta kaunar gani a gidannan, sai kuma Allah ya sa su ɗin ma ba su fiye zuwa ba."

Humaira ta buɗe baki za ta yi magana kenan sai ga wani ƙaramin yaro cikin yara ƙananu uku da ta gani ɗazun ya shigo a guje. Masha Allah yaron kyakkyawa duk kuwa da cewar bai ɗau hasken Mamin sosai ba, ya fi yin kalar Abba, amma kuma hakan ma sai ya ƙara mishi wani kyan na daban.

"Adda Ummi ku zo inji Mami."
Ya kai ƙarshe yana nuna su duka biyum da yatsa, alamun dai mu biyun ake nema. Sai ma ya ba Humaira dariya. Suka miƙe a tare zuwa falon. Ko ɗaya ba abokan faɗan nata a ciki, bada ɗayansu ba sa nan sai Mami da yaran, sai kuwa ɗaya a cikin matasan nan na ɗazu kwance saman doguwar kujera ya toshe kunnuwa da earpiece.

Suka ƙarasa ga Mamin, ta zauna a gefe a ƙasa. Duk yadda Mamin ta so ta hau kujerar ta ƙi, haka dole ta rabu da ita. Ummita ta kawomata abincin amma gaba ɗaya ta kasa sakewa balle ta ci, ƙarshe dole dai ɗakin suka yi da abincin bisa umarnin Mami. Nan din ma dai kaɗan ta ci ta ce ta ƙoshi. Hankalinta kuma ya koma ga Kawu da Abba, ba ta gaji da ganin Abba ba, ba ta kuma gaji da jin muryarsa ba. So take ta samu damar da za su yi doguwar hira da shi, tasan dai ba yau ba domin dare ya yi.

Suna nan da Ummita tana ƙara ba ta labari akan zuri'arsu har lokacin sallar isha'i ya yi, koda suka idar kai tsaye falon Abba suka nufa sakamakon kiran da ya yi musu. Nan suka tarar shima Kawu har ya ci abinci ya yi wanka, hirarsu kawai suke yi da Abba wanda shima ya sha doguwar jallabiya ruwan madara. Har Humaira ta zauna kallonta yake da murmushi saman fuskarsa kafin ya maida duba ga Kawu ya girgiza kai.

"Allahu Mai Halitta." Kawun shima murmusawar ya yi, ita kam sai ta yi kasa da kai. Zamansu ba jimawa sai ga Mami ta shigo ta lulluɓe jikinta da ƙaton mayafi. Sai da ta zauna ne ta dubi Kawu.

"Umar, kwana da  yawa. Idan babu Fatima  a gidan shikenan kuma sai zumunci ya yanke? Dama kun raba ni da ɗiyata, toh dama ƙarshen alewa ƙasa, ka ga yau dai ungulu ta komo gidanta na tsamiya."

Kawu ya yi ƴar dariya.

"Hajiya Maryam kenan, idan dai kin yarda kin amince da komai lokaci ne, ba za ki ga laifinmu ba. Sai dai kamar yadda kika ce, na yi kuskure kuma na ji kunya da ban tashi zuwa ba sai bayan babu Adda Fatima, Allah ya gafartamusu. Ina kuma neman afuwa."

Gaba daya suka amsa da amin.  Abba ya yi gyaran murya ya dubi Mami.

"Ina yaran nan suka shiga ne wai?"

"Su na can wurin Anna, na rasa me suke yi alhalin na sanar da su. Bar..."

Ba ta ƙarasa ba sai ga su sun faɗo ɗakin kamar daga sama, babu ɗaya cikinsu da ya yi tunanin yin sallama. Yaron ɗazu ne da ya je kiranmu ya shigo a guje ya rungume kafaɗun Abba, wani da ya fi shi tasawa yana biye da shi a gujen. Sai kuwa su Tasleem da samarin nan uku.

"Kai Muhsin, me ya yi maka ne?"

Wanda aka kira Muhsin ya turo baki ya nunawa Abba bindigar ruwa da aka raba gida biyu.

"Ba shi ne ya karyamin bindiga ba. Allah kuwa sai ya biya ni."

Abba ya ja hannun karamin mai suna Waleed ya maido shi gabansa.

"Haba Autan Mami, ya haka? Ba shi hakuri toh."

Da dariya irin na yarinta ya furta kalmar sorry. Abba ya maida idanunsa ga su Tasleem waɗanda suka yi ɗare-ɗare saman kujera ba su ko gaisar da Kawu ba. Fuska ya ɗan ɗaure.

"Ba ku iya gaisuwa ba ne?"

Jin furucin Abban ya sa suja gaida Kawu ciki-ciki, ba tare da jin komai ba  ya amsa har da nema musu albarkar Allah. Babu wanda ya amsa da amin a cikinsu. Mami ta kalle su ta yi musu alamar su sauko ƙasa su zauna, ba a son ransu ba dole suka zaune a ƙasan kafet kamar dai yadda Humaira da Ummita suka yi. Sai dai Abba ya buɗe taron nasu da addu'a sannan ya gabatar da Humaira a wajensa. Ya kuma gargaɗe su da kar su kuskura ya ji wani zance na daban koda nuna bambanci ne. A karshe ya sa kowannensu ya gabatarwa da Humaira sunansa. Su tara ne cif, Mubarak ne babban ɗan Abban, shi kuwa yana ƙasar Ghana yana karatu, sai Dawud, Yassar, Ƙasim, Futuha, Tasleem, Raihana, Muhsin da autansu Usman da ya ci sunan baban Mami suke kiransa Waleed.

"Humaira toh, yanzu dai ba wanda ba ki sani a ƴan uwanki ba ko? Sai babban yayanku shi kam sai ranar da ya samu hutu idan ya dawo sai ku gaisa. Ko kuma ma ina iya haɗa ku a waya wataran."

Jin abinda ya fadi ya sa ta murmushi, ta gyaɗa kai tare da furta toh. Daga haka Abba ya sallame su baki ɗaya suka tashi.

A wannan daren dai ba ta samu damar hira da Abbanta ba, ta koma ɗakin da ba ta kauna dalilin yadda suka kaya da masu ɗakin. Mami ta sa aka yi mata shimfiɗar katifa a ƙasa kafin nata gadon da sif ya iso, acewarta. Hakanan ta kwanta, mutanen ba su ƙara tanka mata ba musamman ma Futuha da ta sha ƙasa har lokacin ƙugunta na ciwo. Sun dai sha jinin jikinsu, sun kuma fahimci Humairar ba kanwar lasa ce ba itama.

***
Washegari tun da asuba ta ga ƴanmatan ba su koma bacci ba, ita daman baccin safe ba ya daga cikin ɗabi'unta, a can ƙauyensu daga sun tashi to sannan za'a hau ɗora ruwan wanka da kuma abin kari, wannan dalilin yasa ta kwanta kawai tana kalle-kalle da saƙe-saƙen zuci. Tana kallo suka yi wanka har Ummita, kowannensu ya hau shiri. Ummita da Raihana cikin shigar uniform na makaranta, ita kuwa Tasleem shigar fararen kaya ta yi na ma'aikatan asibiti riga da wando da ɗan ƙaramin hijab. Sun mata kyau kwarai, gogar kuwa, wato Futuha, kayan gida ne jikinta, riga doguwa ta atamfa da ya ɗame ta ɗam ya fiddo da surarta.

"Wai ke Futuha ni ban gane ba, ina mamakin yadda kike rawar ƙafa da jiki duk sadda aka ce kuna da English, ko uban me yasa oho." Faɗin Tasleem kenan sa'ilin da take ɗora agogo a tsintsiyar hannunta. Kafin Futuha ta yi magana, Raihana dake fesa turare a jikin uniform dinta wanda iri ɗaya ne da na Ummita, kalar fari da ruwan makuna dinkin riga da wando sai ɗan hijab da ya rufe kirji kaɗan, dariya ta yi ta amsa wa Tasleem.

"Wai ke ba ki da labarin IBB Gusau? Tab, ai kusan kaf matan department dinsu sonsa suke ban ciremaki matan aure ba, toh itama har da ita a ciki, ba ki ganin kwalliyar ta daban ce."

Futuha ta jefowa Raihana murfin man shafawa, Raihana ta kauce tana dariya.

"Af, akwai ƙarya cikin maganata ne? Ke fa naji kuna hirar da wannan ƙawartaki me wuya kamar mariƙin lema, ni me ma sunanta? Yauwa Khalisat, kina wani koɗa shi kina cewa nan duniya shi kike so."

A fusace Futuha ta nufo ta, Raihana ta sunkuci jakar makarantarta da waya a gefen gado ta fice daga dakin da sauri tana dariya. Itama Tasleem dariyar ta yi.

Ummita kam dama ta fice daga dakin tun da ta zura uniform, dakin su Muhsin ta wuce don yi musu shirin makaranta.

Humaira lumshe idanunta ta yi tana ji suna faman hira tsakanin Tasleem da Futuha inda Futuha ke kara jaddada dagasken dai tana son Ibb Gusau.

"Ke malamin fa ƙarshe ne wallahi, ya haɗu ba zan nuna masa komai ba. Nidai fatana Allah yasa ya karɓi tayina ya aure ni. Wallahi zan jure dukkan wulakanci muddin zai yarda ya so ni. Yau in sha Allahu sai na nemo lambar wayarsa."

"Lallai, kina ruwa kusa da breaker." Cewar Tasleem.

Fuska dauke da damuwa Futuha ta amsa.

"Ai na yi nisa ma cikin ruwan Tasleem, ki dai yi fatan kar Allah ya jarabceki irin yadda ya jarabtan."

Tasleem cike da mamaki ta ce.

"To tsaya, don iskanci kwanakin nan da wa kike waya kike kashe murya kina furta kalaman so?"

Yamutsa fuska Futuha ta yi.

"Mujahid ne, wallahi akan dole nake kula shi, shi ke fa taya ni da attendance da ma test. Kinga kuwa dole ce ta haifar da shiga lamarinsa. Ɗan taya ni na ci jarrabawa ne."

Suka sheƙe da dariya. Ba jimawa suka fice zuwa falo.

Ita Tasleem nursing take karanta duk ta fi su kwakwalwa da basira, tana da kokari sosai shiyasa wasu lokutan take samun alfarma daga Abba koda zai yi hukunci ba ya tsaurara mata, yayinda ita kuwa Futuha ke karantar Mass Com, ba laifi tana da kokari sai dai matsalar tun zuwan wani matashin malaminsu makarantar ta susuce ta zama shiritacciya. Wannan yasa lokaci guda ta kwaso C.O a zango na biyu a aji na biyu a makaranta, hakan ba ƙaramin ɓata ran Abba ya yi ba. Shi mutum ne da ya tsani asarar kwandalarsa a abinda ba zai kawo mishi ribar komai ba sai asara, hakanan mutum ne mai son abin hannunsa sosai, dakyar Mami ta shawo kansa ya aminta da tura Mubarak karatu, ya kuma ce daga kansa ya rufe, sauran kowanennsu sai dai ya yi a jami'o'in Kasarnan.

Dawud na ajin karshe a jami'a inda yake karantar Accounting, Yassar wanda tare suke tafiya da Dawud din adalilin maimaicin aji da Dawud ya yi a sakandire, shi kam Bussiness ya ke karanta, su biyun tare suke da Futuha a jami'ar Bayero. Sai Ƙasim dake karantar fannin Kasuwancin shima dai inda yake aji na uku a jami'ar Maitama Sule Kano.

Wannan kenan.

Humaira jin ɗakin ya yi shiru ta buɗe idanunta, ajiyar zuciya ta saki tana mai jinjina wannan rayuwa ta Futuha, shakka babu ta ɗorawa kanta wahala, koda dai faɗan da ba ruwanka, daɗin kallo gareshi. Mikewa ta yi ta nufi banɗakin bayan ta ɗauki zanin wankanta da brush. Sai da ta wanke jikinta tsaf kafin ta fito ta soma shiri cikin doguwar rigarta ƴar kanti ruwan madara, tana daga cikin suturun da Kawunta ke siyamata. A dai fannin sutura daidai gwargwado itama tana da su, sai dai ace ba wasu masu tsada ba ne, ba kuma masu kyawun gaske ba ne idan an haɗa da na su Tasleem da ta gansu a jikinsu a kwana ɗayan nan. Tana cikin kwashe shimfiɗarta sai ga Ummita ta shigo da sauri, ganinta ta saki fuska sosai.

"Au Humaira ashe kin tashi, kinga mu ma makaranta za mu wuce. Mami tace idan kin kammala ga abin kari can an rufemaki a kicin, idan ma ba ki gani ba ki tambayi Ladidi mai aikin Mami tana falon tana gyara."

Duka wannan zancen tana yi ne lokaci guda da sauri tana bincike dirowarta, littafi ta zaro ta dauki jakar makarantarta sai safarta a hannu da takalmi ta kama hanyar fita.

"Toh, sai kun dawo."

Faɗin Humaira, Ummita ta amsa ba tare da ta tsaya ba sakamakon hon din mota da ake faman dannawa. Ganin haka yasa Humaira ƙarasawa jikin windon wanda ake iya hango farfajiyar gidan, ganinsu tayi gaba ɗaya a motar sai Tasleem dake tsaye a waje rike da ƙugu, Ummita na karasawa ta hau ta da masifar wai tana ɓata musu lokaci.

"Allah ya baku hakuri."

Ta ji Ummitan ta fadi sannan ta shige motar da sauri, tsaki Tasleem ta ja ta bita da harara sannan itama ta faɗa ciki, direban ya ja suka fice. Ajiyar Zuciya Humaira ta saki ta bar jikin windon, mamaki fal a ranta na ɗabi'un ƴan matan. Ta lura ba su san wani abu wai shi kara da mutunci ba, haka dai ta ture zancensu ta hau gyaran ɗakin. Abin ban haushi a saman gadon Futuha daidai da ɗan kamfenta da ta cire anan ta bar shi a ajiye, aikuwa haka ta tsallake gadon, ba ta yi karambanin gyara musu gadajensu ba, da ace dai Ummita ba ta gyara nata ba to tabbas wannan kam za ta gyara mata, ita din mutum ce mai mutunta DAN ADAM.

Fita waje ta yi, falon babu kowa hakan yasa ta nufi hanyar kicin da ta nakalceshi tun jiya da Ummita ta tattara kwanukan abinci ta nufi ciki. Anan ta iske wata mata da ba za ta girmi Mami ba tsaye tana goge gas nan ta fahimci ita ce Ladidi. Ta gaisheta a ladabce, matar ta amsa fuska a sake.

"Baƙuwarmu Humaira ko? Sannunki da zuwa, ga abin karinki can."

Ta fadi tana nuna mata wani tireda aka ɗora filet da kofi sai kayan shayi da flask a kai. Humaira ta murmusa.

"Nagode, amma zan sharo dakin sannan na ci."

"Ai da kin bar shi, idan na kammala da nan sai na share."

Girgiza kai Humaira ta yi.

"Babu komai kar ki damu zan yi ai ba wani girma ne da dakin ba."

Ladidi ta amsa da toh gami da yi mata sannu. Tsintsiyar ta nunamata da makwashin shara, ta dauka ta nufi dakin. Sai da ta kammala tas kafin ta koma ta wanke hannu ta dauki abin karin ta koma daki don ba ta jin za ta iya ci a falon. Bayan ta kammala ne ta fito da niyyar maida kayan kicin suka yi karo da Ladidi.

"Yauwa, ki je inji Alhaji wai za ku yi sallama da Kawunki zai wuce."

Ladidi ta karɓi kayan hannunta ita kuwa jin haka jikinta ya yi sanyi, ta koma dakin ta dauki karamin mayafinta ta yafa a kai. Falon Abban ta nufa, Kawun ne kadai a ciki ya yi shiri tsaf na tafiya, sallamarta ya sanya shi dubanta.





 
  

03

Ta durƙusa ta gaida shi, ya amsa sannan ya ce.

"Toh Shatu, ni zan koma. Ina fatan zaman nan zai maki dadi fiye da rayuwar da kika yi a Maine. Ina kuma roƙonki da ki zauna da kowa lafiya, kamar yadda suka karɓeki da hannu bibbiyu, kema ina son ki rike su haka. Gidan mahaifinki ne, nan ɗin dai shi ne gatanki, ba ki da sama da nan. Sannan don Allah ki zama mai hakuri, na sanki sarai muddin aka taɓo ki ba  kya kai zuciyarki nesa. Abu na gaba, kar ki sake ki bada kofar da za'a ga wallenmu, a ga kamar mun gaza a wurin ba ki kyakkyawan tarbiyya a iyaka zaman da kika yi hannunmu. Sannan addu'a, ki yawaita addu'a da ibada in sha Allah sun ishe ki."

Humaira wacce tuni fuskarta ta yi jage-jage da ruwan hawaye ta sa hannu ta share su. Gani take yi tamkar shikenan fa za ta yi nesa da asalin garin da aka haifeta, shi kenan ganin Kawu da Tanti Hafsatu matarsa  zai yi wuya a gareta.

"Nagode Kawu, in sha Allahu zan kiyaye abin da ka ce. Amma ai Abba zai dinga bari na naje maku wataran ko?"

"Me zai hana na bar ki Mamana?"

Jin maganarsa gaba daya suka dub shi, sam ba su san ya shigo falon ba balle kuma tsayuwar da ya yi a bakin  ƙofar da za ta sada shi da sashinsa na ainahi.  Ya karaso da murmushi saman fuskarsa ya zauna, ta gaishe shi, ya amsa.

"Ban maki alƙawarin nan kusa ba, amma da yardar Allah duk sadda na tashi aurar da ke, zan kai ki har Maine ki kwana biyu. Nidai fatana yanzu shi ne  ki saki jikinki ki zauna da mu bisa kauna. Kin ji ko?"

Ta gyaɗa kai tana murmushi mai dauke da kunya jin wai Abbanta ya ambaci aure. Ita duka nawa ma take yanzun a shekarunta goma sha huɗu? Koda dai, akwai sa'anninta su Murja, Fatsima da ma sauransu wadanda duka an aurar da su a can. Tashi tsaye da Kawun ya yi ne ya maido ta hayyacinta. Ta mike itama, Kawu suka yi sallama da Abba. Daidai nan Mami ta shigo da sallama, tana sanye da dogon hijabi har ƙasa, gaida Kawu ta yi sannan ta yi mishi sallama. Sai a sannan Humaira ta gaishe ta.

Humaira ta takawa Kawu har wurin motar Abba inda direban Abban zai kai shi tasha. Tana hawaye haka ta tsaya har Kawun ya shiga motar, hannu ya ɗago mata itama haka har suka fice daga gidan. Ji ta yi zuciyarta ta yi wani irin tsinkewa, haka kurum ta ji wani irin tausayin kanta ya kama ta. Kanta Abba ya dafa da muryar rarrashi ya ce.

"Haba Mamana, kukan fa? Ya isa haka, ba fa rabuwa ku ka yi kenan ba, in sha Allahu zumuncin ba zai yanke a nan ba matukar akwai rai da lafiya,  ki kwantar da hankalinki nan ma gidanku ne."

Ta gyada kai, daga haka suka shige gidan.

Mami dake tsaye a windon falon tana kallonsa, itama juyawa ta yi ta koma ɗakin Abban hawaye a saman fuskarta wanda ita kaɗai ta bar wa kanta sanin ma'anarsu.

A falon Abban suka zauna yana fadin.

"Bari dai nayi hira da ɗiyata kafin na fita aiki ko?"

Ta yi murmushi har sannan yatsunta na saman fuska tana goge ruwan hawaye.

"Ba ni labari toh, meyasa ba ki shiga makarantar boko a can ba? Kawunki dai ya cemin kina zuwa islamiyya har kin yi sauka, na kuma ji dadin hakan."

Ta gyara zama ta amsa a nutse.

"Dada ce ta ce ba zan je ba saboda koda na fara ba lallai na ƙarasa ba. Ta ce kuma faransanci ne."

Abba ya yi shiru, ya gane sarai manufar Dada, wato dai ta san cewa ko ba jima ko ba dade ranar nan za ta zo
DOWNLOAD
DOWNLOAD

5 Comments On DUKAN RUWA
avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

hhh

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
north

1 year ago

Reply

hhhhh

Please Login or Register in order to submit comment