Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

don gani tayi tamkar a mafarki wai wata ƙaramar yarinya na gasawa uwarta maganganu, sai da ta motsa da zummar barin ɗakin sannan ta zabura ta janyo igiyar chazarta. Nan fa ta hau jibgar Humaira amma kamar ba mutum ake duka ba, ta ƙi tafiya ta kuma ƙi ƙwatar kanta. Zuciyarta tafarfasa take yi. Kallon Jannat take kawai tsakar idanu yayinda idanunta suka kaɗa sosai sai ruwan hawaye. Ganin da ta yi Humairar babu ko gezau sai kawai ta hau wanke ta da mari tana zaginta. Ta yi biyu, za ta ƙara ta riƙe hannunta gam, ba ta san ya aka yi ba, ba ta kuma jin za ta iya tunanin mai kyau da marar kyau a lokacin, kawai ta ji yatsun hannunta sun sauka saman fuskar Jannat da mugun ƙarfi ji kake tas!!! Ya yi daidai da faɗowar su Futuha ɗakin waɗanda dawowarsu kenan daga shoprite cike da nishadi. Ganin abinda ya faru ne ya sa Tasleem sakin ihu mai ƙara da ya ja hankalin Abba da Mami dake a sashin Abban, suka nufo da sauri Abba ya ɗan tsaya daga ƙofa yayinda Mami ta kutsa kai ɗakin. Alokacin rufewar idanun Humaira har ya kainta shaƙi wuyan Jannat ta dangana ta da bango, babu sautin kuka sai ruwan hawaye, Jannat ta raina kanta, ta ji ashe ba ta da ƙarfi don ji tayi kamar ba iyaka Humairar ba ce ta shaƙe ta ba.

"Wayyo Allahna! Ku taimaka za ta kashemin yarinya!"

Jin wannan furucin na Anna ya sa Abba danno kai cikin ɗakin. Tsawa ya dakawa Humaira ba ta ko kalleshi ba. Ya kuwa ƙarasa ya ɗauketa da wani marin sannan ya fincike hannunta. Mami kuwa mutuwar tsaye ta yi, ita kadai ta san me take ji a zuciyarta, wannan shi ne lokacin da take gudu, ta juya da sauri ta bar ɗakin. Su Futuha kuwa suka yi kan Antinsu suka rirriƙe suna kuka yayinda Anna ma kukan take har da biyu saboda ganin Abban. Shi kuwa rufe Humaira ya yi da duka sai da ya ga har ba ta motsi kafin ya karasa ga Jannat yana ba ta hakuri, Jannat kamar jira take kawai sai ta fashe da kuka sosai da fadin.

"Wannan wane irin cin mutunci da zarafi ne? Da aurena da darajata da shekaru sa'ar ƙanwar ƙanwata ta shaƙi wuyana? Wannan rayuwar da me ya yi kama? Kiyi hakuri Humaira, watakila laifina ne da na zo gidannan. Na saba ganin girmamawa daga mahaifinki, hatta da marigayiya Anti Fati ba ta taɓa yimin koda kallon banza ba, amma yau ga ɗiyarta nan ta shaƙeni tana ƙoƙarin kai ni lahira. Aikuwa a yau zan bar maki gidanku."

Ta ƙara fashewa da kuka, Abba ya ji kamar ya ƙara rufe Humaira da duka, wannan banzan halin a ina ta ɗaukoshi? Tabbas ba halin mahaifiyarta ba ce.

"Nima yau zan bar gidanka Isuhu, tun zuwan yarinyarnan naga rashin kunya iri-iri da ban taɓa gani a wajen yan uwanta ba. Na yi kokarin janta a jiki da nunamata kauna, sai dai ban sani ba ko tana ji a ranta ni ban kai ta girmamani ba saboda ina zaune ina cin arzikin gidan mahaifinta ba, tunda abin ya kai ga haka in sha Allahu zan tattara na koma can Agadez, kiyi hakuri Humaira, wallahi ni ba muguwa ba ce. Tsakanina da duk abin da ya fito daga jikin Isuhu babu komai sai girmamawa."

Dakyar Abba yake magana saboda ɓacin rai ga nauyin Anna da ya dinga ji, wai yau diyar cikinsa ce ke ci wa tsohuwar mutunci ta hanyar dukan ɗiyarta a gabanta.

"Ki yi hakuri don Allah Anna, wannan gidana ne ba na Humaira ba. Mallakina ne, kamar yanda uwata mahaifiya da ace tana raye take da iko kai karfi a kaina da gidannan, haka nake ganinki don haka ina roƙonki kiyi hakuri ki janye ƙudurinki. In sha Allahu daga yau irin haka ko da wasa ba zai ƙara afkuwa ba. Ni zan ɗau mataki kwakkwara a kanta."

Ya ƙarashe yana duban Humaira da sai lokacin take sheshsheƙar kuka, itama shi take kallo, ta sunkuyar da kai.

"Don ubanki ba za ki buɗi baki ki ba su hakuri ba?!"

Ya faɗi a tsawace, hakan ya yiwa ran su Tasleem dadi, yau dai ga wacce suke ganin ta fi su a wurin Abba tana ɗanɗanar kudarta. Abin ya zo musu a daidai. Ita kuwa mikewa ta yi dakyar ta durkusa sosai, hakuri ta shiga ba su har Jannat din. Dakyar suka ce ya wuce saboda ganin idanun Abba.

"Muje." Ba musu ta mike jikinta duk ya yi tsami ta bi bayan Abban zuwa falonsa yanda ya buƙata.

***
Fadeel da murmushi ya ɗagawa yayartasu hannu alamar jinjina. Yayar Ibb, Anti Ruƙayya wacce ke aure a Kano, sun saba sosai da Fadeel din tun kafin ma ta yi aure. Ibb ya dube shi.

"Wai ni ban gane ba, toh idan odar ta sauka wa zai karɓa?"

Fadeel ya yi murmushi karo na biyu.

"Nan gidan Antinmu za'a kawo mana, ni kuma sai na zo na karɓi rabona."

Hajiya Ruƙayya ta yi dariya.

"Amma dai wannan ina zaton ita ce zaɓin ƙanin nawa ko?"

Ya kasa magana sai shafar sumar kai, Ibb ya taɓe baki.

"Ita ce dai yake yiwa son mutuwa ba ta san da zamansa ba."

Fadeel ya harareshi shi kam dauke kai ya yi ya cigaba da ba Ruƙayya labarin komai. Sosai ta ji ya ba ta tausayi.

"Allah Sarki, yanzu kai zaman jiranta za ka yi kuma?"

"Um." Shi ne kawai abin da yace yana hararar Ibb da ya kasa rufamasa asiri. Ibb shima ya rama sannan ya ce.

"Ai wai haka yake nufi, nidai ban san irin wannan abu ba, ace mutum ya kasa hakura da son wanda ba ka gabansa? Kinsan Allah, mutumin nan akwai mata da yawa da suke kawo mishi hari, na ce ya runtse ido ya zaɓa ya darje amma ina. Wai ya hakura da auren har sai Humaira ta yi koda ba shi ta aura ba sannan zai yi nashi."

Rukayya ta yi salati.

"Fadeel kana cikin hayyacinka kuwa? Wannan wane irin so ne?"

Nan da nan fuskarsa ta sauya.

"Nawa son da haka ya zo. A sanya ni a addu'a kawai Anti."

Ta ɗan yi jim tana kallonsa. Sai kuma ta numfasa.

"Shikenan, Allah ya zaɓa abinda ya fi alheri. Zan so naga wannan yarinyar da ta sace zuciyarka har haka."

Ba musu ya fiddo waya ya buɗe hotunan Humaira wanda hatta a saman screen dinsa ita ce ya miƙa mata. Ta kalla sosai ta ce.

"Babu ƙarya Humaira kam ta haɗu. Daga kuma yanayin fuskarta ka san za ta yi haƙuri."

Yabon da ta yi sai ya karawa Fadeel farin ciki, a duniya ya tsani wanda zai kushe abar sonsa. Ganin har Ruƙayya ta yaba sai hankalinsa ya kwanta. Sun jima suna hirar lamarin Humaira kafin a karshe su yi sallama bayan Fadeel ya ce mata zai dawo idan an kawo odar snacks ya karɓa.

***
Jannat ce tsaye tana kallon hanyar waje, har lokacin zafafan hawaye take fitarwa na baƙin cikin abinda Humaira ta aikata gareta. Fuskarta ya yi jazur, ta juyo ta kalli Anna wacce ta yi shiru tana kallonta, a duniya Anna ba ta son damuwar yaranta.

"Anna, na yi alƙawari sai na ga bayan Humaira da duk abin da take taƙama da shi. Ta yimin cin fuskar da ban taɓa tsammata ba, ni zan nunamata iyakarta koda kuwa zan yi yawo tsirara."

A firgice Anna ke duban ɗiyarta, ta san halin kayanta, muddin ta furta abu, komai nisan lokacin da za a ɗauka sai ta aiwatar. Wani lokacin ma, sai ta tabbatar da shafewar abin a kwakwalwarka kwatsam sai dai ka ga sakamako a aikace. Don haka ta sani ko mene Jannat za ta aikata ba ƙarami ba ne duba da yanda ta saki fuska lokaci guda har da dariya. A karshe ma hatta da abincin da Humairar ta kawo sai da ta ɗiba ta yi zaman ci tana santi. Ita dai Annar ba ta ce mata komai ba, ta fi kowa sanin baƙar zuciya irin na ɗiyarta.

*LITTAFIN NAN NA KUƊI NE. SIYA AKAN NAIRA ₦400 KI KARANTA BA TARE DA SHIGA HAKKI BA. KAR KI MANTA BAYAN NAN AKWAI CAN, ALLAH YA SA MU DACE AMEEN.*


*5407827015*
*FCMB*
*Farida Abdullahi*

09034973645



Gidan Alhaji Yusuf wanda aka fi sani da Maiagogo sun wayi gari ranar alhamis da shirye-shiryen bikin yaransa biyu, Futuhatul-Khair Yusuf da kuma Tasleem Yusuf wanda kwanaki uku kawai ya rage a fara. An samu sauye-sauye da dama, na farin cikin ya fi kowanne yawa ga Humaira da duk ma wanda ke tare da ita. A wannan watannin ta samu alheri mai yawa daga sana'arta. Babbar customer dinta ita ce Hajiya Rukayya wacce ta hanyarta kaɗai ma ta samu oda na biki da party har ya zamana tana gwada na abinci bayan snacks sai dai gaba ɗaya sau biyu ta gwada abincin taro ba laifi kuma masu shi sun yaba hakanan Hajiya Rukayya ta ji dadi da ba ta ba su kunya ba. Duk abin nan ba su taɓa ganin juna da ita ba sai dai waya. Mami ta sa an buga leda da stickers mai tambarin DEELSHA'S DELICACIES. Suna na musamman da Raihana da Ummita suka ba Humaira a sadda Mamin ta ce ta yi tunanin sunan da za'a sanya a ledar. Sunan ya yiwa Humaira daɗi ko kadan kuma ba ta tambayesu ma'anarsa ba. Mamin ma ta ji dadin sunan, ganin kalmar turancin ya sa ta tambayar wacce ta sa, nan Humaira ta sanar da ita su Ummita ne. Daga haka ba ta kara cewa komai a kai ba.

  A yau da ya rage kwanaki uku bikin yan matan Mamin, gidan nasu ya soma karɓar baƙi ƴan uwan Mami daga Agadez sai ko ƙawayen Futuha waɗanda suka zo daga nesa kasancewarta mai jama'a fiye da Tasleem. Yan uwan Abba kuwa ba wanda ya zo gidan da zummar kwana. Mubarak shima ya zo gari, sai kuwa Anti Jannat. Ya kasance a wannan lokacin gidan ba ya rabo da jama'a, Mami ta sa Ladidi kawo mataimaka a aiki har su uku saboda yanayin cikar gidan da zummar bayan biki za ta sallame su.
  Anko har kala biyar aka fitar, na ƙawaye daban wanda zasu sanya ranar kamu da na daurin aure da yini sai ko na ranar dinnerparty. Na manya su ma kala biyu, na fita kamu sai na ranar daurin aure.

Humaira, Raihana da Ummita daban aka fitar musu da na sisters wanda zasu saka na yini sai kuma na dinnerparty da Mami ta yiwa su Futuha jan ido ta karɓar musu katinsu ta riƙe a wajenta don a farko sun nuna su ko kusa ba su kaunar su halarci dinner din.

   Amare sun sha gyara ba na wasa ba daga mai gyaran jiki na musamman da Mami ta samar musu suke sintirin zuwa. Hajiya Lubna ita da kanta ta ɗauki nauyin gyara su, gyara irin na mata. Ta kashe kuɗaɗe masu kauri kuwa wanda hakan ya burge aminiyarta kwarai ta yaba.  Ba ma ita ɗaya ba, ƙawayen Mami da dama manyan mata masu kudi sun ba da gudunmuwa mai yawa na kudi, kanta ya fasu sosai ta kuna ga fa'idar mu'amala da masu hannu da shuni.
Su Raihana sun karɓi dinkunansu a hannu, sun yo ƙunshi da kitso abinsu sun fito fes.
   A na washegari kamu ne su na zaune suna hira a daki tare da wasu yan uwan su Raihana sa'anninsu da suka zo daga Nijar, Tasleem ta shigo. Fatarta har wani ɗaukar ido yake, ba ta da ƙiba irin na Futuha ita nata jikin daidai misali ne, duban Humaira ta yi fuska ba fara'a.

"Ke Humaira, ke da Ummita ku zo na aike ku."

Humaira ta ji ciwon ke din da tayi kiranta da shi, ita kuwa Ummita ko a jikinta ta miƙe tana murmushi. Hakanan halittarta yake, tana da yawan murmushi, abinda zai sanya hawayenta zuba kuwa, toh fa ba ƙaramin abu ba ne kamar dai akan Humaira ko kuwa wani abun daban. Kamar ba za ta miƙe ba sai kuma ta yi tunanin ba komai ta yi tunda dai aure ma za su yi su bar gidan sai ziyara don haka ta taushi zuciyarta ta miƙe itama. Saƙo ta ba su a leda na ankon Dinner su je su kai can asibitin Malam wajen ƙawayenta kuma abokan karatunta da suka samu dakyar don har ta ƙare. Ta miƙawa Ummita dubu su yi kuɗin mota sai kuma lambar wayar ɗaya daga ciki, Sadiya, sun gane ta, takan rako Tasleem din gida wasu lokutan don ta dauki wani abun ko kuma ta zo takanas ziyara.
   Bayan sun fito waje Humaira ta dubi sararin samaniya yanda garin ya haɗu da hadari ana cida, lokacin uku da mintoci, ta ja guntun tsakin takaici.
 
"Kinsan Allah, sa'ar da ta ci kawai na ganin wannan shi ne aike kusan na karshe da za ta yi mana kafin ta bar gidannan shiyasa kawai zan je, amma ban da haka wannan ke ɗin da ta ce wallahi da babu inda zan je matukar ba Mami ce ta sa baki ba."

Ummita dake kokarin cusa ƙaramar lema a jaka ta ɗago tana murmushi.

"Humaira ko rigima, rabu da ita lokaci ne ai wataran sai labari fa. Yanzu kalli, ina Anti Jannat? Ba ta yi aure ba sai dai ta zo kawai ziyara ta tafi? Toh su din ma hakan ce za ta kasance, mu ma watarana sai ki ga mun yi namu auren mun tafi mun bar gidan. Sai a dade ma kafin a ganmu."

Tsaki Humaira ta ƙara ja.

"Ke dai Ummita kina son aure na lura, magana kaɗan za a yi da ke sai kin yi zancensa."

Da mamaki Ummitan ta kalleta kafin ta amsa.

"Aure ai abin so ne saboda sunnar ma'aiki (s.a.w) ne. Ke din ma ba sunnar kika tsana ba, mazan ne. Ban kuma san laifi kwakkwara da suka yi gareki ba."

Taɓe baki Humaira ta yi daidai lokacin da suka fito babban titi.

"Mu bar wannan magana, nikam ba kya ganin lamarin Anti Jannat da ɗaure kai?"

Ummita ta yi shiru cikin nazari, tabbas da daure kai, tun bayan sadda ta zo hutun sallah lamarin nan ya afkuwa tsakaninta da ita, ba ta kara dawowa gidan ba sai yanzu. Wannan dawowar kuwa, daidai da kallon Humaira ba ta yi balle har ta jefe ta da kallon banza. Ta lura ko tana wuri Humaira ta shiga, mikewa take ta bar wurin. Haka dai tana ta kaucewa abinda zai haɗa su a inuwa guda.Har Humaira ta tarar musu abin hawa suka shiga ba ta amsa mata tambayarta ba sai da ta ƙara nanatawa kafin ta sauke ajiyar zuciya ta ɗan yi murmushi.
  
   "Na lura sosai, amma ni abin da tunanina ya ban ko dai ta sauya ne tana gudun wani abu ya ƙara haɗaku ki maimaita abin da kika yi. Kin san fa ba zai yiwu ace ta mance ba."

Dariya  ta yi.

"Ikon Allah, toh ni ai na mance. Kawai dai sauyin ne ya ɗan bani mamaki. Babu kyara babu hantara, babu kirana da bare da ta saba yi ba komai. Sai na ke ganin kamar da walakin goro a miya."

"Ki yi mata kyakkyawan zato, Allah yasa sanadin abin da ya kasance ta yiwa kanta faɗa. Ni kaina idan kin lura ai ta rage ɗoramin aiki tunda wannan zuwan ta sa an nemo mata yarinya mai kula da yara. Kawai dai mun saba da yaranta ba yanda za a yi ta iya raba wannan kaunar."

Humaira ta kalle ta, zuciyar Ummita mai kyau ne, da Allah ya tashi, sai ya yi haɗa ta da mutumin kirki irinta wato Malam Sahabi. Mutum mai hakuri da kunya kamar wani mace. Amma abin mamaki duk kunyarsa idan suka ga saƙonnin soyayyar da yake turowa Ummita sai mamaki ya kusan kashe su ita da Raihana. Har rantsuwa suke kusan yi su ce ba shi ba ne waninsa ne.

Ummita ta harareta.

"Kallon fa?"

Murmushi Humaira ta yi mai kyau da ya fiddo wushiryarta.

"Kawai kina bani mamaki da kike kokarin kare wadannan mutanen da ba su taɓa kaunarmu ba koyaushe."

"Uzurin kenan Humaira. Aure fa zasu yi su bar mu yanzu. Mu ma kuma..."

"Toh naji ya ishe ni hakanan Malama matar Sahabi."

Ummita ta sa dariyar jin abinda ya fito bakinta, ita din ma taya ta ta yi. Har suka isa ƙofar asibitin su na hira abinsu ana iska kaɗan kaɗan mai daɗi.

  
   Ibb ne tsaye tare da masoyiyarsa Dr Salma, yayinda Fadeel ke zaune cikin mota yana jira su yi sallama. Mahaifiyarta ce kwamce a asibitin inda anan take aiki, suka zo dubiya ta yo musu rakiya har gaban mota. Bayan sallama da Fadeel ya koma mota yayinda suke hirarsu da Ibb tamkar kada su rabu, shi kuwa Fadeel kansa ya kwantar jikin kujera yana ɗan kallonsu yana murmushi. Shakka babu sun dace dari bisa dari. Dogaye ne su duka biyun don zasu kusan yin kai ɗaya, Dakta Salma baƙa ce, kwayoyin idanunta da haƙora ne kawai idan ta bude masu haske a fuskarta. Tana da kyau, ba ta da jiki sosai amma ba za ka kirata da siririya ba. Tana da diri masha Allah, sanya take da doguwar riga sai coat na likitoci da ta sanya saman kayan, sai kuwa mayafi ƙarami da ta yi rolling kanta da shi. Hannunta cikin aljihun rigar, gaba daya hankalinsu ba ya kan Fadeel da ya lula duniyar tunani da jin inama ace shi da Humaira ke wannan hirar ta nishaɗi. Allah kaɗai yasan yanda zai ji a lokacin. Ya soma gajiya, hakurinsa ya soma kai wa karshe amma yana dannewa gudun ɓacin ranta. Ya horu da rashin ganinta ido da ido ba hoto ba, ya sha zuwa ya tsaya a nesa kaɗan da gidansu ko zai ga wulkawarta sai dai ko mai kama da ita Allah bai taɓa ba shi ikon gani ba. Tabbas Raihana na kokari gurin aikamasa hotunanta wasu lokutan ma ba ta san ana ɗaukarta ba. Hatta da karamin video sadda take aikin snacks sai da ta ɗauka ta aikamasa. Yakan ji inama yana da iko da ita, inama matarsa ce yana kusa ya riƙo ƙugunta ya sanya ta a jikinsa ya bayyana mata irin yanda soyayyarta ke cin zuciyarsa sai dai kuma babu hali. Azabar da bidiyon ke sanya shi ciki ne ya sanya shi dakatar da Raihana daga turo bidiyo face hotuna.

  Ya ja dogon numfashi ya furzar gami da kallon gefe guda yana mai kauda kai daga kan lovebirds. Hango wata ya yi kamar Humaira, ya ɗan yi tsai da idanu don so ya tantance abinda yake gani, sai kuma ya kauda kai. Ya fi tunanin gizo Humaira ta soma yi mishi, sai kuma ya kara kallo. Wannan karon ita ce tabbas, tana sanye da doguwar riga na material mai mayafi Jajaye. Yanayin kalar da garin ya yi, sai ya ba wa hasken fuskarta damar sheƙi musamman da ya kasance tana cikin annashuwa da kwanciyar hankali da alama babu wani abu dake damunta. Sai hira suke da abokiyar tafiyarta wadda ya gane ta, Ummita ce. Ya ganta a hoto don ba hoton Humaira kaɗai ba, hatta da ƴan gidan sai da Raihana ta turamishi hotunansu da kuma bayanin alaƙarsu. Har ya kama murfin mota zai fito ya tuna alƙawarin shekara da ya ɗaukar mata kawai ya fasa ya cigaba da kallonta. Dab da motar suka tsaya suna kalle-kalle kasancewar gilasanta tinted ya sa basu ganshi ba, shi kuwa Ibb shalelan Juliet, bai ma gansu ba ya lula wata duniyar sai buɗe haƙora yake yi kamar gonar auduga.

Humaira ta ɗan yamutse fuska tana gyara gyalenta da iska ke kaɗawa.

"Nikam asibitin nan juyar da kai gareshi, don Allah ƙara kiranta ki ce bamu gane wajen da ta ce ba kinga garin yana kara haɗewa."

Itama Ummita duk ta damu ganin hadari ta fiddo waya ta dannawa Sadiya. Nan ta ce su tsaya inda suke ta gansu.

Suka ja kuwa suka tsaya, Humaira ta zubawa mutanen dake ta shawagi a wurin idanu tana godiya ga Allah a ranta idan ta ga an wuce da marasa lafiya dayake suna daidai Emergency. Ba su wani jima ba sai ga Sadiyar ta iso, bayan sun gaisa ta karɓa ta yi musu godiya suka juya suka kama hanyar fita.

Fadeel kamar wanda aka tsikarawa allura haka ya zabura ya fito daga motar ya dubi Ibb.

"Malam ka zo mu tafi ba ka ganin yanda garin ke haɗewa wai?"

Suka dubeshi, Dakta Salma ta yi murmushi.

"We are sorry Amininmu. Bari na kyale shi haka. Nagode sosai ku gaida gida."

Bai ko kalleta ba ya amsa da toh don shi gaba daya hankalinsa na ga su Humaira yana fatan Allah ya sa su amince su sauke su a gida. Ibb ganin an soma yayyafi ya yi mata sallama ya shiga motar ya tayar.

"Please and please ka yi sauri kada su hau abin hawa, so nake ko yaya ka yimin kokari ta amince mu kai su gida."

Ya tayar da motar ya soma tafiya sannan ya dubi Fadeel cikin rashin fahimta ya ce.

"Wa kenan kake magana a kai?"

Fadeel da idanunsa ke kan su Humaira wadanda suka kara ɗaga ƙafa ganin ruwa ya soma sauka bai ce komai ba face nuni da ya yi mishi da hannu. Sam bai ga fuskokinsu ba sai baya, kafin ya yi magana Fadeel ya sake tarar numfashinsa.

"Humaira ce."

"Ohh." Abin da kawai Ibb ya ce kenan.

Yana zuwa daidai saitin inda suke ya tsaya har yana tare musu hanya, Humaira dake saitin wurin ta kalli motar ranta a ɓace don a ganinta ko waye yana sane ya sha gabansu. Ta bude baki da zummar magana Ibb ya sauke gilashi suka kalli juna. A gaggauce ta gaishe shi, itama Ummita haka, ta gane shi saboda tana ganin hotunansa a wayar Raihana, shi ne dai wanda y taimaki Raihanar.

"Gida ku ka nufa ne? Ku shiga na sauke ku don yanzu idan ku ka shiga napep jiƙewa zaku yi."

Ruwan sosai ya ƙara ƙarfi, Humaira ta buɗe baki za ta ja musu Ummita ta dafe hannun da sauri ta amsa.

"Toh mungode." Ta kalli Humaira, a hankali kuma a gaggauce ta ce.

"Muje Humaira, yanzu ba lokacin jan musu ba ne, wallahi nidai ina mura kin sani, ruwannan ya dake ni kuma lafkewa zan yi da bikin nan."

Jin haka Humaira ta amince suka shiga, ita ta soma shigewa sai Ummita. Motar sanyi sakamakon Ac dake aiki. Sai a lokacin ta lura da wanda ke zaune a gefen Ibb din, ji ta yi kirjinta ya buga dam, ta rasa dalilin bugawar kamar yanda ta kasa dauke idanu a kansa. Shi ɗinma ita yake kallo babu ƙakƙautawa har bai iya ya amsa gaisuwar Ummita ba. A bangaren Humaira ji ta yi idan ta cigaba da kallonsa ranta zai iya fita saboda wani irin zafi da take ji a kirjinta ga kanta dake faman sarawa don haka da sauri ta kauda kai ta matsa ta maƙure a kujerar bayansa tana jingina da kofar motar. A hankali Ibb ya dan bubbuga kafaɗar Fadeel, firgigit ya dawo hayyacinsa ya gyara zama, gilashinsa ya zaro a aljihu ya rufe kwayoyin idanun da so da tsananin kauna ga kewa suka haɗu suka galabaitar. Dakyar Humaira ta iya gaida Ibb sannan ta gaida Fadeel din ba tare da ambaton suna ba. Shi ma amsawa ya yi can ƙasa.

Ibb ke tambayar Ummita abin da ya kawo su asibiti.

"Kuna da marar lafiya ne?"

"Aa, aiko mu dai Anti Tasleem ta yi. Ita ɗin ɗaliba ce a nan. Nursing take karantawa ne."

Dan jinjina kai Ibb ya yi.

"Ok, na fahimta."

Jin motar ta ɗauki shiru sai rediyo dake aiki sai ko ruwa da ke jiƙa gilasan motar yana sauka a guje saboda karfin da ya yi. Ummita ta dubi Humaira.

"Wai, da tuni yanzu fa mun jiƙe."

"Uhm." Shi ne amsar da ta ba ta. Fadeel kuwa lumshe idanun ya yi ya ji sautin Uhm din har tsakar kansa, gaba ɗaya sai da ya ji tsikar jikinsa ya tashi. Kamar kuma haɗin baki sai ga gidan rediyon sun saki waƙar Breaker mai taken Kalmar So. Humaira sam hankalinta ba ya jikinta, ji take kamar ta buɗe motar ta dira a cikinta. Gaba daya koina a jikin rawa yake, Ac ke kaɗawa a motar amma ita zufa take. Ta tuna da ambaton Allah ba shiri ta shiga ambata a ƙasan ranta a hankali ta soma dawowa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

5 Comments On DUKAN RUWA
avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

hhh

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
north

1 year ago

Reply

hhhhh

Please Login or Register in order to submit comment