Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels Bismillahir Rahmaanir Raheem.

             *DUKAN RUWA...*

FARKO.

Ta yi zugum kanta jingine jikin kujera tana kallon halittun manyan  duwatsun da suke ratsawa a wannan dajin, tafiya suke yi tamkar ba za su kai ba. Wani lokacin idan sun gifta bukkokin jama'ar wani yankin, takan yi murmushi cike da al'ajabin ta yadda mutum ƊAN ADAM ke iya rayuwa a wannan wuri. Tun tana kallon har dai ta zame ta gyara zama gami da lumshe idanu, bacci ke ƙoƙarin ɗaukarta tana yakicewa. Babu abin da ta tsana sama da bacci a hanya, hanyar ma da ko a mafarki ba ta taɓa ganin za ta bi ba,  zuwa Nijeriya daga Nijar.
Ajiyar zuciya ta saki tamkar wacce ta ci gudu, lokaci guda nannauyen tunanin da take ƙoƙarin kaucewa na ƙara yi mata saukar aradu a kwakwalwa. Idanunta ta sauke akan matar dake kusa da ita, baccinta take haiƙan har carbin da ke riƙe a hannunta tana ja, ya faɗi. Sai dai duk da baccin da ta lula, hakan bai sa ta saki yaronta ba, yana rungume a kirjinta ɗam! Kai ka ce wani ne zai ƙwace mata shi. Juya kai tayi ta koma kallon hanya da murmushi ɗauke saman fuskarta. Soyayya da shaƙuwar dake tsakanin ɗa da uwa na daban ne, a kowane yanayi, a kowace rana burin kowace uwa ganin gudan jininta cikin walwala da annashuwa, ba ta fatan wani mugun abu ya same shi. Shakka babu duk wanda ya rayu da uwa ya more.
  Sai kuma kewa ya lulluɓe ta dalilin Dada da ta tuno, watanni biyar kenan da rasuwarta amma jin sa take a rai tamkar jiya-jiya. Kullum mutuwar kakarta kamar sabo ne fil a wurinta, mace mai hakuri da dattako, ta yi namijin kokari wurin ba ta kulawa daidai gwargwado da kuma tarbiyyar islama. Ba ta shaƙu da kowa ba sama da ita sai ko Kawunta ɗan uwan Mamanta, Kawu Umaru. Shi ma ba ta jin za ta manta da irin namijin ƙoƙarin da ya yi a kanta, koda dai dama barewa ba ta yi gudu ba ɗanta ya yi rarrafe, wannan kyawawan ɗabi'un Dada ne suka kwaso. A wannan irin namijin ƙoƙarin ne a yau Kawunta ya tashi haiƙan suka bi wannan doguwar hanyar kawai don ya sada ta da mahaifinta, mutumin da tun da ta buɗi ido ba ta taɓa ganinsa ba. Hatta a waya ba su taɓa koda gaisawa ba.  Duka wannan bai sa ta riƙe mahaifinta a zuciya ba domin kuwa ya samu kyakkyawar shaida a gurin Dada da Kawu. Ko sau ɗaya ba su taɓa kawomata kushensa ba, asalima sun ce yana sonta sosai, kuma acewarsu ya sha zuwa ganinta tana ƙarama, su ɗin ne suka ƙi amincewa ya tafi da ita bisa dalilan da su kaɗai suka bar wa kansu sani. A yau kuma da aka wayi gari babu Dada, Kawunta ya ɗauki ɗamarar cika wasiyyar da Dada ta bari na cewar ya sada ta da Mahaifinta idan har rai ya yi halinsa.

  Ɗan girgizar da motar ta yi sakamakon taka wani ɗan tudu ne ya sa ts ji saukar ruwa a saman leɓɓanta, sai lokacin ta gane kuka take. Kukan kewa da damuwa ne, Dada ta tafi, tafiya ta har abada, ta tafi wajen da ba za ta sake ganinta ba sai ko idan nata ajalin ya iso, ta je ta tarar da ita.
  _"Kar ki taɓa bakin ciki da zuwa wurin Mahaifinki Shatu, mutum ne nagari mai sanyin hali, za ki yi farin ciki da ganinsa. Yana sonki sosai Shatu."_

Kalaman Dada suka faɗomata a rai, ta sauke ajiyar zuciya na samun nutsuwa, lokaci guda ta ciza leɓɓanta na ƙasa tana ƙara murmusawa karo na barkatai. Ya mahaifinta yake? Da wane ido za ta ɗaga ta kalle shi ya kalle ta? Dagaske tana kama da shi ko kuwa dai Kawu ya faɗi ne don ta ji dadi? To an ce yana da wasu yaran, su ma tana kama da su ko aa?

Duka waɗannan tambayoyi ne da ta hargitsa lissafin kwakwalwarta da su alhalin babu mai ba ta amsa. Haka dai ta yi ta saƙe-saƙenta har suka fita gaba ɗaya daga Nijar suka nufi bodar Nijeriya.
Nan ɗin ma bayan kammala cike-cike da duba kayyakinsu, suka gangara cikin Nijeriya, ta baza ido tana kallon yanda cikin iko da hukuncin Allah, shuke-shukensu ya sha bamban da na ƙasar da ta fito.

***

"KATSINA" Ta karanta sunan a hankali, sannan ta dinga bin garin da kallo tana ƙarewa bambance-bambancen garin da nasu. Tunaninta ya katse sa'ilin da direba ya  tsaya a gefen hanya domin ba su damar gabatar da sallar la'asar. Mazan duk suka riga su sauka, su ma suka sauko. Kawu ya dube ta.

"Ki bi su ku yi sallah kar ki je ko'ina kin ji ko?"
Ta gyada kai ta amsa da toh, tana rungume da ƴar ƙaramar jakarta ta hannu haka ta dinga bin matan su uku har zuwa wani ɗan wuri da aka katange, suka samu gefe guda da ba mutane, masu jin fitsari suka yi sannan suka ɗaura alwala. Bayan sun idar suka dawo motar, nan kuma kowa ya hau zuge jaka ya na siyan abin motsa baki. Tana nan zaune cikin motar Kawu ya kawo mata ruwa da lemu sai nama a leda, kaɗan ta ci bayan ta yiwa ƴan motar bismillah, sauran ta naɗe ya ajiye a gefe, lemun dai ta sha sosai.

Daga nan suka ƙara miƙa hanya har dai cikin hukuncin Allah suka ƙaraso cikin garin KANO.

Ta nanata sunan a kan harshenta jin wata Mata ta ambata, ta maimaita har sau uku, lallai idan ba ta mance ba shi ne sunan da Dada ke yawan ambata idan ta tambaye ta sunan garin Mahaifinta.  Nan da nan zuciyarta ta yi fari ƙal, ta kasa rufe bakinta, wannan karon murmushi take tun daga ƙasan zuciyarta har saman leɓɓanta don har siririn wushiryarta na bayyana. Sai da suka ƙarasa tasha suka sauka, daga nan ne kuma Kawunta ya ɗauki akwatin kayanta suka fito bakin titi. Suna hawa taji ya ce unguwar Gadon Ƙaya, daga nan direban ya hau tafiya ita kuwa tana ta kallon hanya har suka sauka. Sun yi ƴar tafiya a ƙafa sannan ta ga ya tsaya daidai bakin wani ɗan shago ya yiwa mai shagon sallama. Koda suka gaisa ya ce.

"Don Allah gidan Alhaji Isuhu Maiagogo nake tambaya."

Mai shagon ya gyada kai ya ɗan fito sarari ya hau yi musu kwatance da hannu. Ya yi godiya suka nufi inda ya ce.

Koda suka karasa wajen wani ƙaton gini ta ga ya tsaya cak a gaban ginin, ta bi ginin da kallo ta ji gabanta ya yanke ya faɗi lokaci guda, ba kuma don tasan dalili ba. Ta kasa kwakkwaran motsi har Kawunta ya taka zuwa ga kofar gidan yana tambayar wani dattijo ko nan ne gidan, amma ita kam ba ta dauke kai daga kallon ginin ba, gwuiwoyinta suka yi wani irin saki, ganin yanayin da ta shiga har zufa na tsastsafomata a goshi yasa ta dinga maimaita kalmar innalillahi.

"Shatu ke!"

Kiran da Kawu ya kwalamata ne ya maido ta hayyacinta, a hankali ta soma takawa har ta ƙarasa gefensa, ba ta kuma san dalili ba ya ji ta sa hannu ta riƙo nashi yatsun gam!
Hakan da tayi ya sanya shi dubanta, itama shi din take kallo, ya yi dariya.

"Tsoro gidan ya ba ki ne? To ki shirya yaƙar tsoron nan don nan ne gidan zamanki daga yau in sha Allahu."

Dattijon ya taya shi darawa kaɗan duk da bai fahimci komai ba. Amma ta lura da yadda yake ta kallonta har ya kasa hakuri ya tanka.

"Amma dai wannan ƴar uwar Alhaji ce ko?" Kawuna ya yi dariya ya amsa da eh kawai. Ita dai ba ta ce musu uffan ba sai sadda kai ƙasa da ta yi, ta na ji Dattijon nan na kara zuzuta kamanninta da Alhajin wanda shi ya sanya shi tankawa.  Suna nan dai  tsaye sai ga wani ɗan matashin yaro ya fito, ashe wai Dattijon ne ya aika shi gidan don a shaida wa Maigidan zuwansu.

"Ya ce maza ku shigo ciki. Muje na raka ku."

Daga haka  suka shiga ciki. Madadin faɗuwar gabanta ya ragu, sai ma ƙara hauhawa da ya yi, ta ci gaba da maimaita innalillahi har ƙarshe, sai ta ji gaba daya ta bar rawar ƙafar son haɗuwa da Babanta Isuhu.

   Koda suka ƙarasa cikin ƙaton falo, wani irin sanyi da ƙamshi mai dadi ne ya daki hancinta. Ta gefen ido take bin wurin da kallo tana so tayi ido huɗu da Babanta, sai dai kuma duk irin girma da daular da ke shimfiɗe a falon wanda ya ƙara ƙawatashi, babu rai ko ɗaya mai numfashi face su ukun da suka shiga.
Wuri ya nuna masu saman kujera suka zauna, ita kuwa ƙasa ta zauna gefen Kawu don ba'a ba ta tarbiyyar zama saman kujera alhalin manya na zaune ba. Matashin ya kara juyowa fuskarsa a sake.
  "Ku jira Yallaɓai nasan ba zai jima ba zai fito." Kawu ya amsa daga nan ya fice ya bar su a nan. Sun samu mintoci goma da sakanni, don gaba daya hankalinta yana kan ƙaton agogon da ta zauna saitinsa, kafin ta ƙarasa ƙirgenta suka tsinkayi sallama. Lokaci guda suka kai duba ga gefen da muryar ta ɓullo, baki da ido ta saki tana kallon mutumin yayinda shi kuma idanunsa ke kan Kawu, kallon mamaki da tsantsar farin ciki yake binsa da shi.

A gefenta kuwa halittar fuskarsa take ƙarewa kallo. Eh, tabbas suna kama, fuskarsa doguwa kuma siririya irin nata, yana da dogon hanci masha Allah, sai kuwa bakinsa daidai. Idanunsa manya kamar naya hatta da cikar halittar girarsa da gashin kai, duk kuwa da cewa shi nasa gashin ya yi fari fat na manyanta amma kamanninsu da shi sun fito fes har tsawon. Ba ta ƙara gani ba sai da ya saki dariyar farin ciki, anan kuma baki hangame ta ce. "Kai!" Ta furta a fili ba tare da ta shirya ba. Gaba daya suka juyo su na dubanta. Ta kama bakinta da sauri gami da ƙara sunkuyar da kai, mutumin ya matso ya durƙusa a gabanta, zuciyarsa ta yi wani irin nauyi, abubuwa da dama suka shuɗe a tsawon shekarun baya suka dawo mishi sabo fil. Ita kuwa kunya ce ta kama ta, bata ma gaida shi ba, ta gaishe shi a hankali don a zaton ta ma bai ji ba, amma ga mamakinta ya amsa.

"Barka da zuwa Mamana. Ki saki jikinki nan gidanku ne, gidan Abbanki, ba ki da inda ya fi nan kinji ko?"

Da ya fadi haka wai sai ta kalli Kawu, hakan da tayi ya ba su dariya. Kawu ya gyaɗamata kai.

"Idan eh kike so nace ko aa, toh eh Shatu, gidan mahaifinki kenan. Abin tunƙahonki."

Ta yi murmushi tana kara duban wanda ya kira kansa da Abbanta, sai nan da nan kwalla ta cikamata idanu. Wannan fargabar ta kau, so da kaunar suka dawo daga hutun da suka je, ta rungume hannunsa ta saki kuka sosai. Abubuwa da dama take tunawa, tabbas ta yi kewarsa a rayuwa. Koda ace ba ta rasa ci, sha da sutura ba daidai da kwana ɗaya a rayuwa, to ta rasa wannan kusancin na ɗa da mahaifi, shi din na dabanne. Ko ma dai tace ta rasa soyayyar iyaye gaba ɗaya.

"Kiyi hakuri Mamana, ba zan ƙara yin nesa da ke ba, wancan ma ƙaddara ne, amma wannan karon in sha Allahu ni da kaina zan miƙa ki ɗakin mijinki. Allah ya ji ƙan Mahaifiyarki da Hajiya Dada."

Suka amsa da amin. Nan kuma ya shiga jan ta da hira kadan har ta sake, waya ya zaro a aljihu ya danna kira, sunan wata ya ambata, Ummita, ya ce ta zo yanzu. Daga haka ya  juya ga Kawu suka yi ta hira yana ba shi labarin rashin lafiyar Dada har zuwa rasuwarta. Suna nan zaune ita kam ta kasa ɗquke ido akan Abban, suka tsinkayi sallamar wata ƴar budurwa da ba ta wuce sa'arta ba. Baƙa ce, irin baƙin da hutu ya ratsa, riga da wando ne a jikinta sai dai ba su ɗame ta ba, ta saka hijabi iyaka kafaɗarta. Ta gaida Kawu sannan ta maida hankali ga Abba.

"Yauwa Ummita, kama hannun ƴar uwarki ku je a ba ta abinci ta ci ta yi wanka. Ki kuma faɗawa Maminki ina da baƙo a shirya masa abinci kafin mu yi sallah. A kawo ruwan sha."
Ummita ta amsa da toh tana kallonta fuskarta a sake ta ce.  

   "Lah Abba wallahi kuna kama sosai."

Duk sai ta ba su dariya, Abba ya dubi Aisha Humaira kafin ya maida duba gareta.

  "Itama ƴata ce, ita ce mai sunan Umma."

"Abba ita ce wacce ka ce tana Nijar ko?" Wannan karon da wani irin zumuɗi ta yi tambayar. Ya amsa mata da eh. Ta kuwa karaso da sauri ba tare da nuna kyankyamin komai ba ta rungumeta tana fadin. "Welcome Sister." Ba ta gane me ta ce ba amma itama ta rungumeta tana mai jin kaunarta har can ƙasan ruhinta.
  Ummita kenan, tana daga cikin mutane masu girma da matsayi sosai a rayuwar Humaira, har abada Humaira ba za ta cire ta a tarihin rayuwarta ba, ta karɓe ta a yadda take, ƴar kauyen Maine. Ƙamshi take a yayinda ita kuwa ba ta ma sani ba, ƙarnin kifin da ta ci a mota take yi ko kuma naman da ta ci ne. Kai ko ma mene ne, ta sani Ummita ba ta irin wannan ƙarnin, ƙamshi ne a jikinta, amma ba ta duba komai ba ta rungumeta. Ta tabbata tana daga cikin masoyanta na haƙiƙa. Ta kama hannunta ɗayan hannun kuma ta ɗauki akwatin kayanta wanda duk ya ci gidansu, akwati ne irin na da da aka yi yayinsa, Dada ta ce nata akwatin tun na auren Mamanta ne.
  Suka nufi wata ƴar siririyar hanya suka fito wurin wani ƙaramin hanya nan ma gefensa duk shuke shuke. Wurin ya burge Aisha Humaira sosai, a daidai ƙofar shiga wajen ma, shukoki ne sun kewaye jikin ƙofar da bango sun ba da zane mai kyau. Ummita ta ci gaba da tafiya har suka nufi wani ɓangaren, baranda ne sai kuwa wata ƙofa, suka shiga Ummita ta shiga kwala ihun kira.
"Mami! Mami!! Fito ki gani!"

Ihun da take tana kira ya sa sauran mutanen dakin suka fito. Maza da mata wadanda sun ɗan girme ta sai ko yara.

"Wai Ummita me ke damunki haka? Tun ɗazu bakinki ya ƙi..."

Aisha Humaira ta lura haɗa idanun da suka yi ne ya sa sauran kalaman bakin matar suka maƙale. Kallonta take kamar a razane, ita kuwa kallonta take tana so ta ga ta inda suka yi kama da Ummita don ko kaɗan ba su yi kama ba. Ummita baƙa ce, wannan kuwa ta tsaye a gabanta da alama ma buzuwa ce. Gashinta a tufke a baya, ta kai duba ga wasu a cikin yaran, su ma farare ne ƙal, kyawawa da su.

"Wace ce wannan?"
Ɗaya daga cikin ƴanmatan ta tambaya tana bin Aisha Humaira da kallon tara saura. Ummita ta yi dariya ta jawota ta rungumo kafaɗarta.

"Mami, mai sunan Umma ce ta zo daga Nijar, Aisha Humaira. Abba ya ce shikenan ta dawo nan da zama cikinmu."

Wacce aka kira da Mami, ta tamke fuska babu ko ɗigon annuri, suka kalli juna a kar na biyu. Kallon da ya da ya sa Aisha Humaira ta ji hantar cikinta ta kaɗa, dariyar matasan ne ya sa ta maida idanu kansu.
  
"Wai! Ni da yagwalgwal, amma wannan ma a Nijar ɗin a can ƙauyen kike ko?"

Ɗaya a cikin matasan ya furta yana dubanta, idanunta nan da nan suka cicciko da kwalla.

"Kai Yassar, bana son haka. Sannu da zuwa Humaira, maza Ummita kai ta ɗakinku ta yi wanka lokacin sallah ya gabato."

Da sauri na kalli matarnan, na sha mamaki ganin kamar ba ita ba, ta saki fuska sosai tana murmushi har haƙorin makkanta ana gani. Har Ummita ta faɗi saƙon Abba, Humaira ba ta iya tankawa ba hakanan ba ta iya ɗauke idanu daga kanta ba, itama jefi-jefi tana magana da Ummita tana kallonta ta kuma rasa dalili. Har Humaira ta bi bayan Ummita zuwa ɗaki ba ta daina waigenta ba, kuma itama Mami ta ƙi matsawa balle ta dauke ido a kanta.
   Ita kam Humaira jikinta ya ba ta kamar akwai wani abu.

®️Rufaida Umar.

   02

A hankali ta bi kowace kusurwa a ɗakin da ido, gado ne kananu har hudu kowanne a nashi wurin, a gefen kowane gado akwai sif na kaya kamar dai ɗakunan makarantun kwana, babban daki ne mai yalwa wanda har akwai gurbin da ire-iren gadon uku za su samu matsuguni. Daga can gefe jikin taga kuwa, ƙaton madubi ne a saman dirowar gaban cike da kayayyakin kyalkyali na adon fuska da mayuka. Dakin tsaf-tsaf babu ƙazanta, ɗakin ƴanmata kenan. Ummita ta ɗaga akwatin tana shirin ajiyewa saman ɗaya daga cikin gadajen nan, baki bude tana kallon Humaira da niyyar magana, aka daka mata wani uban tsawa daga baya.
Muka juyo, wannan dai budurwar ce ta ɗazu mai ƙibar ciki. Ta zo da sauri ta janye akwatin ta yi wurgi da shi gefe. Idanu cike da masifa ta soma magana.

  "Wallahi kar ki kara  gangancin ajiyemin jakar wannan korar yunwar a gadona, don gulma da kinibibi idan abin naki dagaske ne meyasa ba za ki ajiye a naki gadon ba. Aikin banza kawai, uwar shishshigi. Haka za ki ƙare."

Tana kai wa nan ta  fice daga ɗakin tana mita,  Ummita ta kalli Humaira gami da jifanta da murmushin yaƙe.

"Ki yi haƙuri."

Ta gyaɗa mata kai tana maida mata martanin murmushin sai dai can ƙasan ranta, tana maimaita kalmar da ta ambata "Korar Yunwa". Ta fahimci manufarta tsaf, ta kuma gane ko wace ce ba ta samu karɓuwa a wajenta ba. Koda dai, ba ma ita kaɗai ba, ta lura da irin kallon da Mami ta watsamata. Ko ya zamantakewarta a wannan sabuwar duniyar za ya kasance?

"Hey, tunanin me kike? Amm..nidai bari kawai na kiraki da Humaira, kinga babu damar ce maki Aisha kai tsaye saboda sunan Umman Abbanmu kika ci ko? Hakan ya yi?"

Humaira ta gyaɗa kai karo na biyu tana mai sakin fuska, ta lura Ummita akwai kirki.  Bandaki ta nuna mata, ita kuwa ta yi  godiya, har za ta shige ta dakatar da ita.

"Yauwa Humaira ga wannan zanin ki yi amfani da shi ki goge jiki."

Ta sa hannu ta karɓa, zani ne a wanke a goge. Ummita har ta kama hanyar fita sai kuma ta dawo ta shiga bandakin gami da ba ta umarnin ta bi bayanta. Su na shiga ta kunna mata famfo gami da faɗin amfanin kowannensu. Ta fiddo mata sabon sabulun wanka daga cikin wata ƴar kwaba dake a gefe jikin bangon, sai kuma ta tambayeta ko ta taho da soso, Humaira ta amsa da eh. Hatta da ƙofar banɗakin sai da Ummita ta nuna mata yadda za ta ƙulle kuma ta buɗe, daga haka suka fito, nan ma sai da ta ajiye mata dardumar sallah saitin gabas sannan ta fice ita kuma ta ciro  sosonta a akwti ta koma banɗakin ta rufe.

Wanka ta yi gaba ɗaya ta ɗauro alwalar Magriba, koda ta fito wannan budurwar ta ɗazu tana zaune gefen gadonta tana waya, suna haɗa ido ta bita da harara ba shiri Humaira ta kauda kai. Idanunta ya kai ga akwatin kayanta, ƙarasawa ta yi ta buɗe sai dai gaba ɗaya ba'a nutse take ba sakamakon idanun wannan budurwar a kanta suke duk kuwa da wayar da take amsawa. Turanci zallah take zubawa har wani shagwaɓa take yi tana dukan gadon, kalmar I Lobiyun da ta ce yasa Humaira ta fahimci koma dai wane ne toh masoyinta ne. Ba ta ko ƙara kallonta ba gudun ganin abin da zai sosa zuciya, ta fiddo doguwar rigarta ta yadi ta warware ta zura. A gurguje ta ciro hijabinta, ta linke kayan da na cire na ajiye daga saman akwatin. Ba ta jima da tada salla ba sauran ƴanmatan nan biyu suka shigo suka cika ɗakin da hayaniya, rabin hirar tasu da harshen turanci suke yi. Koda ta idar ba ta iya nutsuwar jan addu'a mai tsawo ba, ta yi istigfari da hailala da salati ta shafa. Zama ta cigaba da yi anan ba tare da ta miƙe ba gudun ma kar ta yi wani abin ya jazamata baƙar magana. Hankalinta yana ga Abbanta wanda take da tambayoyi birjik da za ta yi mishi a kwakwalwarta. Eh yana sonta yana ƙaunarta, amma meyasa bai ƙara waiwayarta ba, meyasa ba ta taɓa ganinsa ba? Meyasa kuma koda a waya bai kira domin su gaisa ba? Dukkan wannan rashin kulawar nasa da ba ta samu ba, ace yana kaunarta ya kuma damu da itq? Ita kam tana son sanin amsar da zai fito daga bakinsa.

"Ke Indo."

Ta ɗaga kai ta dube su kawa, suka kwashe da dariya.

"Kai Raihana ba ki da kirki wallahi, au ba ma za ki kirata Humairar ba sai Indo ko?"

Wacce aka kira da Raihana ta yamutse fuska.

"Aa, ina ce sunan Umma gareta, tunda kaka ce ai ko Indon ma da na ce ta gode min. Ku ni ba wannan ba, wallahi mu tashi mu yi magana fa tun kan a ƙaƙaba mana ita a ɗakinnan. Ni wallahi  tsoro ma take ban. Mu faɗawa Granny ta yiwa Abba magana don Mami ba za ta goyi bayanmu ba."

Humaira ta kalle ta dakyau, doguwa ce kamar dai Abba, don ta fi Maminsu tsawo, Mamin ba ta da tsawo sai jiki kuma  gajeriya ce. Fara ce tas itama kalar buzayen, gashinta da ya sha kalba ya sauka har gadon bayanta, riga
DOWNLOAD
DOWNLOAD

5 Comments On DUKAN RUWA
avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

hhh

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
daiy drop

1 year ago

Reply

sss

avatar
north

1 year ago

Reply

hhhhh

Please Login or Register in order to submit comment