Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*
_______
*DANDANO🥰*
*1*
Cikin tsananin gajiya da ishirwa nake tafiya burina kawai na isa gida na samu na watsa ruwa a jikina na kwanta na hutawa rayuwata. gabana ne ya fad'i! lokacin dana tuna d'an iskan yaron nan yana gari nasan da wuya ya barni na sha ruwa a gidan Khalid mugun fitinan nan yaro ne wallahi........Daf da zan shiga layin namu motar Alhaji Nura take kokarin fitowa d'auke kaina nayi na bashi hanya domin ya wuce! girgiza kaina nayi ganin yayi parking din motar ya tsaya cikin raina nace"Ai dama na san sai ya tsaya, galashin motar ya sauke muka had'a ido fuskata na saki nace"Alhaji barka da rana." Cikin kulawa yace."Barka dai Sa'ida ya aiki."? Nace" Aiki Alhamdullihi." kokarin wuce wa nake ya dakatar dani da fad'in "Sa'ida ina al'kawarinmu."? Gefan hijab d'ina nasa na goge gumin fuskata nace" Alhaji al'kawari yana nan inaso na ware ranakun da zan fara gudanar da aikin naka."

Yace."Me zai hana ki ware ranaku biyu a cikin sati wato alhamis da juma'a tunda a ranakun yaran basa zuwa isilamiyya in yaso idan sun dawo daga boko misalin biyu ko uku sai ki dinga shiga kina musu lesson d'in."

Shuru nai ina nazarin maganarsa nace"Shikkenan Alhaji zan duba maganarka insha Allahu." Yace."To godiya nake gimbiya duk shawarar da kika yanke sai ki kira waya ta ki sanar dani."


Nace"To shikkenan babu damuwa." Har nayi yunkurin barin gurin ya dakatar dani! cikin k'osawa na tsaya amma ban nuna masa ba, kudi ya miko min kusan dubu biyar.....murmushi nai nace"Kasan ba zan kar'ba Alhaji nagode." da sauri na bar gurin ina mamakin yawan kyautar da yake min duk had'uwar da zamuyi sai ya dauki kudi ya bani bayan uwar hidimar da yake mana a gida........Tun kafin na karasa na hangoshi dogare a bakin kofar gidan namu yana sanye da k'ananun kaya 3qutar da singlet wacce ta matse shi gabad'aya suffarsa ta mazantaka ta bayyana Gabana ya yanke ya fad'i! duk sanda zan ganshi a haka hankalina yakan tashi ni kaina ina mamakin halin da nake shiga wannan dalilin yasa idan yana gida bana sakewa sosai mutukar zai dinga shige da fice a gidan babu sutturar arziki a jikinsa.

Fuska a murtuke na 'karaso...."Malami Bani hanya na wuce." babu wasa nayi maganar.

Hanyar ya sake tarewa yana kallona da 'batacciyar fuska yace."Aunty Sa'ida me ya tsayar dake a gurin wancan mutumin."? wani irin kallo na watsa masa nace"Ina ruwanka da shiga sabgar da bata shafeka ba, dan Allah ni bani guri na wuce na gaji."

Hanya ya matsa min naja tsaki had'e da kokarin ra'bashi na wuce kawai naji ya matseni a jikin kofar fuskokinmu suka hade numfashin mu na had'uwa.


Cikin fad'uwar gaba na tureshi! nayi saurin fad'awa soron ina addua akan Allah yasa wani bai ganmu ba! hannuna ya rike yana marairaice fuska yace."Kina so zuciyata ta buga ko na hanaki kula wancan Alhaji kin raina magana ta ko." Cikin takaici nake kallonsa a fusace! nace"Wallahi Khalid ranka zai 'baci! mutukar baka fita harkata ba shin wai ni sa'arka ce da zaka dinga yi min iskanci."

Zuba min idonsa yayi fuskarsa a had'e yace."Ni ina sonki Aunty Sa'ida kuma kin san Allah baki da miji sai ni da kika raina zaki gane baki da wayo."
Yana gama maganarsa ya fita, na dinga kallon bakin kofar ina mamakin maganarsa, bani da miji sai shi! Lallai Khalid baida hankali da tunani. tsaki naja na shiga gidan raina duk babu dadi.

"Ummatu sannu da aiki." ciki-ciki ta amsa min ban damu da yanda ta amsa maganata ba kawai na shige ciki gidan, Gwaggo kakarmu na samu tana kad'in lagwani! hijab na cire na nemi guri na kwanta ina mayar da numfashi.

Kallona tayi tana cigaba da kad'in ta tace" Yau kin dad'e baki dawo ba Sa'ida anya baki fara yawace yawace ba ni wallahi wannan aikin naki ban yardar dashi ba."


Cikin mamaki na kalleta, tace"Ai da gaskiyata wane irin aiki ne wannan da za'a fita tun karfe takwas ba za'a dawo ba sai karfe uku ko biyu haba jama'a."


Murya na rawa Nace"Gwaggo mai kike nufi dani."? ba tare da wata damuwa ba tace"Abinda nake nufi ai kin san shi."


"Kina nufin ina yawon karuwanci kenan."? da sauri tace." Ooh! ni kada ki daura min jakar tsaba ba haka nake nufi ba." hawaye na zuba nace"To meye na cewa baki yarda da aikina ba wato kema kin fara daukar magana aikaina ko."


Shuru tayi tana cigaba da kad'in ta, komawa nayi na kwanta hawaye wani nabin wani! nace"Wato saboda 'kasa ta rufe fuskar mahaifina shiyasa kike nema ki d'ora min kazafin na zina kamar bake kika haifi ubana ba."


"Kinga Sa'ida kada kisa hawan jinina ya tashi da wannan magana taki ta isheni haka aiki kije kiyi tayi tunda ba zakiyi aure ba sharrin zina da bin maza dole jama'ar gari suyi miki."


Da sauri na mike Nace"Gwaggo na gaji zan tattara kayana na koma gurin mahaifiyata tunda keda kika haifi ubana kin kasa yi min uziri a rayuwa ta ni ba ni zan dauki kaina nakai gidan aure ba sai ranar da Allah ya nufa to tunda kun kasa fahimta zan bar muku gidanku." Saukowa nayi na fara hada kayana,


Kayan kad'in ta ajiye a gefe tace"Ke Sa'ida bana son shashanci da rashin tunani babu inda zakije kinji na fada miki maganar aure kuma ba zan fasa yi miki ba har sai kin tsayar da miji zanja bakina nai shuru to kaji."

Jakar kayana na dauka na kama hanyar fita, sai ta fashe da kuka da fad'in" Au! takani zakiyi ki wuce to bari Babanku Iro ya shigo zan fada masa rashin mutuncin da kike min." Saboda nasan banyi abinda take zargina dashi ba yasa ko sauraranta banyi ba na fita daga dakin da kayana a hannu, haba jamaa na gaji da masifar Gwaggo.

Turus! nayi ganin Baba Iro a tsaye suna magana da matarsa! ya kalleni yana kokarin yayi magana! Gwaggo ta fito daga daki tana kuka da fyatar majina da sauri ya karaso gurin yana fadin"Gwaggo lafiya kukan me kike."? Ta 'kara rurucewa da kuka da fadin"Gatanan saboda nai mata maganar aure shine ta hada kayanta wai gurin uwarta zata koma shine har tana sa kafarta tana taka ni ta wuce."
Da sauri na kalleta ina mamakin sharrin ta gwaggo tsohuwa mai sharrin tsiya.

Baba Iro murmushi yayi inda sabo ya saba raba fad'a tsakanin mahaifiyar tasa da 'Yar d'an uwansa Yace."Haba Sa'ida in da sabo ai yaci ace kin saba da halin Gwaggo me yasa ba zakiyi hakuri ba yanzu da kika had'a kayanki ina kike nufin zuwa." Gwaggo da sauri tace" Zataje can gurin Uwarta ne." Cikin k'unci nace" Baba Iro wai kamar gwaggo itace take min k'azafi to meye amfanin zamana da ita."

"Aa ni kada kiyi min sharri Sa'ida daka fada miki gaskiya sai kice nayi miki sharri." Baba Iro yace."Gwaggo maganar ta 'kare haka." Tace."To kace mata kada ta tafi dan taurin kaine da ita."

Baba Iro yasa hannu yana kokarin kar'bar jakar hannuna, nace"Baba dan Allah ka kyaleni na tafi wallahi na gaji da rashin hakurin gwaggo ka gafarce ni idan maganata ta 'bata maka rai."

Yana 'kokarin magana ya shigo gidan hannunsa ri'ke da leda indomee yaje ya siyo, babu walwala a fuskarsa yace."Me yake faruwa ne naga duk kunyi cirko-cirko a tsaye."

Da sauri gwaggo tace"Yawwa d'a nagari ka ganta nan wai barin gida zatayi saboda nai mata maganar aure." wani irin kallo yayi min kafin ya kalli jakar kayana dake hannun mahaifinsa, cikin yanayin takunsa ya karaso inda muke jakar kayan ya kar'ba hannun mahaifin nasa ba tare da yace wani abu ba ya shige dakin Gwaggo da jakar gwaggo bayansa tabi tana surutai!

Baba Iro ya kalleni a nutse yace."Sa'ida kiyi hakuri kinji ko gwaggo tun kafin ta tsufa take da rikici ki fahimci halinta sai ki zauna lafiya kada wani sa'bani ya sake shiga tsakaninki da ita kice zaki bar gida nan shine tushenki, sannan kuma inaso ki bawa Alhaji Nura dama ya turo da maganar aure kamar yanda ya nuna alama.

Nace"Kawu babu wata maganar aure data ta'ba shiga tsakanina da Alhaji Nura kawai muna gaisawar mutunci dashi ne." Cike da mamaki yace."Sa'ida babu maganar aure data ta'ba shiga tsakanin ki da Alhaji Nura amma yake mana hidima a gida." murmushin takaici nayi nace."Wallahi Kawu babu maganar aure a tsakanina dashi." girgiza kansa ya shigayi yana mamakin maganar, yace."Shikkenan to tunda kince haka dukkaninmu zamu cigaba dayi miki addua akan Allah ya baki miji nagari." a cikin zuciyata na amsa da ameen. gurin ya bari nima a sanyaye na d'aga labulan dakin Gwaggo na shiga, abinda naji suna tattaunawa yasa gabana fad'uwa....


*Masoya ayi min sharing A gruops👏🏻*



*IDAN KINA BUKATA KARANTA LITTAFIN NAN #400 NE NORMAL VIP GRUOP #600 ZA'A TURA KUDIN TA WANNAN ACCOUNT DIN.....0542382124....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURO SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*
*2*
"Haba 'Da nagari ai idan da gaske kake wallahi ni zan baka goyon baya kaga sai ayi towo na maina dama hausawa na cewa gida bai koshi ba ai ba za'a kaiwa dawa ba insha Allahu Sa'ida matarka c.....Shigowa ta dakin ya hanata k'arasa maganar gabad'aya ita dashi suka bini da kallo, ni kam jiri ne naji yana nema ya kayar dani a gurin dan tsaf na fahimci akan abinda suke tattaunawa Khalid yayi masifar raina ni da har yake iya bud'ar baki ya furta min kalmar so ina a matsayin yayarsa wacce ta girme masa nesa ba kusa ba na rasa wane irin tsaurin ido ne da yaron a matsayina da tsayin shekaruna sai nake ganin bai cancanta ya iya kallon tsabar idona yazo min da wata banzar maganarsa ba, Khalid da wayo na da shekaruna yayi girman jikin da yake tunk'aho dashi kuruciyarsa kaf a gaban idona yayi ta amma yau wai an wayi gari ni yake tare wa hanya yana cewa yana sona.

Kwanciya nayi ba tare dana cire hijabin jikina ba kawai na dinga binsu da kallo ina jin tsantsar takaici a cikin zuciyata ni kam ko zan rasa miji a gidan duniya banga abin aure a jikin wannan mara mutuncin yaron ba........Tun sanda na kwanta a gadon yake min wani d'an iskan kallo irin na manufarci a hasale! nace"Wallahi idan baka daina yi min wannan d'an iskan kallon ba sai ranka ya 'baci shashashan yaro mara kunyar banza da wofi."

'Bata fuskarsa yayi dan har sai da fatar saman goshinsa ta tattare haka yake tun yana yaro idan ransa ya 'baci sai goshinsa ya tattare ya watsa min kallon banza had'e da girgiza kansa.......Yana kokarin yin magana ta rigashi da fadin" Ke Sa'ida meye kuma na kiransa shashasha ina laifin wanda zai tallafe ki ni wallahi naji dadin maganar da yazo min da ita duk girmanki da shekarunki ba zaki gagareshi ba dan mace komai girmanta bata fin karfin namiji."

Tsaki! naja ba tare da nace komai ba na juya musu baya....'Kawataccen sajan fuskarsa ya shafa idonsa 'kur! a mazaunanta da yake bala'in 'kwa-'kwa! duk da da hijabi a jikinta hakan bai hanashi ganin tudunsu ba, ya dinga jin wata lafiyayyar sha'awa na taso masa, a sanyaye ya kalli Kakar tasu yace."Gwaggo ga indomee na nan ki dafa min zanje na dawo." da sauri tace"To d'a nagari bari na kunna risho ai ina da kalanzir a ciki." Fita yayi daga dakin yana shafa sumar kansa.

Sama-sama nake jin surutan ta kafin bacci mai nauyi yayi gaba dani......Can cikin baccin naji maganarsa sama-sama! "Haba gwaggo kefe ba'a abin arziki dake yanzu dan Allah haka ake dafa Indomee duba kin zabga mata ruwa sai iyo take a ciki kawai kinsa nai asarar kudina." Zaune na mike nai saurin cire hijabin jikina jin yanda ya jike da gumi! ina kallonsa yasa hannu yana sosa kansa idonsa kur! a kirjina. girgiza kaina kawai nayi na fara yunk'urin mikewa......Tace."Sa'ida duba dan Allah wai duk wannan gwanintar da nayi masa ban birgeshi ba cewa yake banyi daidai ba."

Tukunyar indomee din na kalla da sauri na dauke kaina jin dariya na nema ta sub'ce min indomee guda uku amma ta cika tukunya da ruwa indomeen tayi tsululu duk ta narke a ciki.........Yace." gwaggo bafa zanyi asarar kudina ba ki cinye wannan indomee ki bani dari ukuna ba." da sauri tace ." Wallahi baka isa ba ba zanci kayan atini ba hakan nan zaka daure kaci idan kuma ba hakaba Sa'ida ta baka wata indomee tunda tana da ita in yaso sai ka kaiwa babarka ta dafa maka tunda ni ban iya ba."

Ta'be bakinsa yayi yace."Sai dai na kwana da yunwa akan na kar'bi abunta ni ba shashashan namiji bane kamar yanda take kira na nafi karfin ta ciyar dani sai dai ni na ciyar da ita."

Gwaggo sakin baki tai tana kallonsa sai kuma tayi dariya da Fadin"Khalid jarumi a gida da wajan ya'ki ka burgeni kwarai da gaske yanzu dai kayi hakuri akan 'barnar da nayi maka." Girgiza kansa yayi yace."Bafa zan hakura ba bari ma ki gani." da sauri ya fara lalaben inda take ajiye Pose d'inta....
Da sauri ta ri'ke gefan rigarsa "Aa Khalid kada ka daukar min kudi wallahi zanyi maka rashin mutunci idan ka daukar kwabo a cikin jakata.....Fita nai daga dakin na barsu suna bugawa dama inda sabo sun saba idan 'yan abin arzikin na kusa suyi ta mutunci idan kuma 'yan tsiyar na kusa suyi ta bugawa, Gwaggo san kudin tsiya ne da ita duk neman da take ba zata ci a cikinta ba sai tai ta tara kudin tana 'boyewa a cewarta sai auran Sa'ida ya tashi sai tayi mata kayan daki da kudin......Pose din ya bude yaga kudi dan'kam 'yan dubu dubu duk sunfi yawa, yace." Lallai tsohuwar nan kudi ne dake duba dan Allah Jakarki kamar ta matar alhaji."

Tana kokarin fizge jakar tace"Khalid wannan kudin da kagani ba nawa bane kada ka dauki ko kwabo a ciki." Murmushi yayi yace."Haba gwaggo ina ganin kudi ki hanani kin san Allah sai na dauka." dubu daya ya zara yasa a aljihunsa ya mika mata jakarta, aikuwa ta dinga yi masa mita tana surutai dariya yayi ya kama hanyar fita daga dakin da fadin"Ki cinye indomee da kika dafa ni kuma anjima zanje tevur din mai shayi." Tace."Kaji dai dashi saboda kai zan sanjawa jakata guri haka kawai ba zaka zo kana daukar min kudi ba."

Ni dai Ina alwala ina dariya a cikin raina gwaggo san kudi Khalid son kudi koda yake dole Khalid yaso kudi tunda dan makaranta ne yanzu haka yana daf da kammala karatunsa a jami'ar Bayero dake jahar kano yana zuwa gida duk bayan wata guda yayi hutu na kwana biyu ya koma makarana..

'Dakin na shiga na sameta tana ta surutai uffan bance mata ba dan har yanxu haushinta nake ji akan irin abubuwan da take min, na gyara dadduma a nutse na fara kokarin tayar da sallah, tace"Sa'ida dan Allah ungo wannan jakar tawa ki 'boye min Khalid ya gane inda nake ajiyeta nasan kuma shikkenan kafin ya tafi sai ya tatike ni."

Ba tare dana kalleta ba nace"Ki ajiyeta nan na idar da sallah." tace"To 'yar albarka, tukunyar indomeen da sauke daga kan risho tana fad'in "Waye zai ci wannan ai ko almajiri ba zan bawa ba zubar dashi zanyi dan ni banga abinso a wannan abincin ba.....har na idar da sallah gwaggo bata fasa surutai ba nace" Yau me aka girka a gidan.''

Ta'be bakinta tayi 'kasa-'kasa tace"Kin san halin matar gidan da jarabar son d'anwake shi tayi masifaffiyar mata kawai na haifi d'ana amma tafi ni iko dashi dama nasan Rabi tana bin malamai akan Ibrahim."

Cikin mamaki na kalleta halin gwaggo sai ita surukar ta ma bata kyale ba kullum cikin zaginta take amma ba tayi a gaban idonta sai a bayan idonta dan itama Ummatu bata daukar raini mara mutuncin kanta ce nace"Gwaggo dan Allah ki daina wannan halin ki zauna lafiya da kowa yanzu meye amfanin zagin Ummatu har kina cewa tana asiri."

Baki ta rike tana kallon hanya tace."Ke! Sa'ida maganar ta isa haka kada ki d'aga murya taji amma ni tuntuni Uwale ta tabbatar min da cewa Ummatu ba'a zaune take ba tana yawace-yawacan malamai wai shin bakya ganin ko kara ta ajiye babanku baya iya tsallakawa gashi muma ta daure mana baki dik abinda tayi a gidan shine daidai sannan kice nai mata sharri."

Nace"Gwaggo ki rabu da Uwale munafuka ce wallahi tana so ta had'a ki rigima da surukar ki ita kuma ta zauna lafiya da tata idan ba hakaba meye na cewa Ummatu na bin malam......bakina ta rufe tana zazzare ido irin na rashin gaskiya tace."Haba Sa'ida nace dake ki daina kiran sunanta kada taji haba jama'a yarinya ba'a sirri da ita mtssw maganar a barta haka."

Murmushi kawai nayi na mike tsaye ina ninke dadduma, ta mika min pose din nata da fad'in "Kar'bi ki adana min kada ya shigo ya sake daukar min kudi." karba nayi na bude gurin da nake ajiye tufafina nasa key na kulle..........Da yake idan mun dauki albashi duk abinda nake bukata naci da sha dana d'aurawa ina siyan abina na ajiye duk ranar da akayi abinda bana ra'ayi sai nayi girkina naci na koshi, fita nayi tsakar gida na dauko doya a kicin na zauna tsakar gidan ina feraye wa.

Fitowa tayi daga dakin da buta a hannunta Gwaggo duk rintsi bata bari yara suyi mata wasa da butar alwalarta kullum butar ta cike take da ruwa Macace mai tsafta da kula da ibadah dama dan adam tara yake bai cika goma ba, ganin ina feraye doya yasa ta washe baki da fad'in "A lallai kice yau dadi zamu ci a gidan." Murmushi nai ina kallonta gwaggo akwai kwadayi amma bata yarda ta fitar da kudinta ta siyi abinda take so ba.

Nace"Eh lallai doya da kwai zan soya nayi miyar alayyahu saboda haka ke zaki bayar da kudin 'kwai dan banda kudi." shuru tayi tana kallona dariya ta kusa ta su'bce min.

Tace." Inji dai guda biyu zai isa." Nace"Haba gwaggo a wannan uwar doyar za'a sa 'kwai biyu guda biyar zaki siya." tace"Haba Sa'ida 'kwai biyar nawa kenan."? kai tsaye nace"Dari uku da hamsin." shuru tayi tana nazari kafin ta girgiza kanta tace"Bari dai nai sallah muyi maganar haba Jama'a yanda rayuwa nan tayi wahala kice 'kwai biyar ina laifi biyu ko uku."

Bin ta nayi da kallo ina k'unshe dariya gwaggo kenan mai kwad'ayin tsiya.......Hayaniyarsu naji yo daga waje kafin nayi wani yun'kuri sun shigo gidan su uku, babu walwala na daga kaina ina kallonsu su biyu suna sanye da kayan 'kwallo (ball) mayar da kaina kasa nayi na cigaba da abinda nake naji yace."Salim ku jira ni nasa kayana na fito." Suka ce okey kayi sauri dan Allah." cikin zuciyata nace "Aikin kenan." " Aunty Sa'ida barka da Yamma." a nutse nace" Barka Salim ya kuke." ya d'an sosa kansa yana mirmushi yace "Lafiya aunty muna fatan kina lafiya." " Lafiya Kalau nake." shuru gurin yay na minti biyu na dago kaina kawai sai naga sun zuba min ido! cikin 'bacin rai nace"Salim kaima ka fara zama mara kunya ko."? da sauri yace."Aunty mai ya faru."? girgiza kaina nayi nace"Kuje waje gashinan fitowa daga yau kada ku sake shigowa gidan nan tunda duk kun zama baligai."

Wannan magana da tayi a kunnasa ya karaso gurin yana mata kallon daya saba "Akan me zaki hanasu shigowa gida abokaina ne na 'kuruciya kin sansu kin san iyayensu kuma iyakacinsu nan bakin 'kofa ko wani yayi miki abinda bai kamata ba."

Nace"Khalid na hanasu shigowa gidan nan saboda bai kamata ba su tsaya a waje ka fito ka samesu." Girgiza kansa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment