Join Our WhatsApp Group

NAMIJIN GASKE Book 1 Complete Hausa Novel Document by NAMIJIN GASKE Book 1


NAMIJIN GASKE Book 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 9291



NAMIJIN GASKE Book 1

Reading Time: 0 Hours

Added On: 11, Nov 2023

Author: Shuraihu Usman ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08140419490

Book License : Free

Category: Adventure novels

File Size: 53.65 kb

File Type: txt

Views: 632+

Download: 159+

Last download: 2 days ago

Description/Story: NAMIJIN GASKE
Littafi na daya
Complet
Na
Shuraih Usman


Namijin gaske
Part 1A
(c) shuraih Usman
@shuraih 99%
NAMIJIN GASKE
Littafina daya 1
Marubuci:- Shuraih Usman
Typing:- Shuraih Usman
Tel. 08133209890
Part A
.
Doka, banyarda wani yayi copy ko ya sarrafa
wannan labari ta
ko wace hanya batare da izni na ba. Dafatan
za'a kiyaye
Copyright
Shuraih Usman
.
Saurayi ne kyakkyawa ma'aboci kyawun
fuska, wacce duk ya
macen da yai arba da ita sai kware masa.
Babu komai ajikinsa face wata falmara ta
fatan zaki, falmarar
ba'a rufe madannin ta ba, hakan tasa dukkan
ilahirin kirjinsa a
bayyane yake a fili,
Gaba daya kirjinsa waje yake, hakan ce ta
bayyana surar kirar
jikinsa, ko ina ajikinsa a murmurde suke, a
yayin da wasu
guruna suka bayyana bisa tumbinsa kai kace
baya cin abinci ne.
A kasansa kuwa wata gajeriyar wando ce iya
guiwa , ya sanya
,rike yake da gabjejiyar itace a hannunsa .
Yana tafe yana waige waige koda zaici karo
da abinda ya fito
nema, kai da gani kasan wannan kyakkyawan
saurayin farauta
ya fito yi,
.
Yana tafiya yana gunaguni a cikin zuciyarsa
kuwa tunani yake
"wai yayane anya wannan karon da sa'a
kuwa, Ni dana ke fitowa
farauta na kamo manyan namun daji masu
ababen al'ajabi,
Kuma cikin kwanaki biyu rak nake kamosu
sannan na tasamma
gida,amma wannan karon gashi har na
tasamma kwanaki hudu
amma ko tsuntsu banyi arba da shi,
Maganar tasa ta katse a dalilin wani gurnani
daya ji,
Ai koda yaji wannan gurnanin sai ya cika da
farin ciki ainun
bisa ganin wahalarsa tazo karshe,
.
Gurnanin yaci gaba da kusanto shi, ta cikin
wata duhuwar
sarkakiya ne gurnanin ke fitowa.
Nan ya tasamma wannan sarkakiyar, koda ya
rage baifi saura
kadan ya karisa ba, kawai gani yayi wata
murgujejiyar damisa
ta fito daga cikin sarkakiyar ta bayyana a
gabansa,
.
Ya dubi wannan damisar sai ya ganta
lafceciya, sai yayi
murmushi sannan a fili yace da alamu dai
yau zan koma izuwa
gida da karamin nama.
Itako damisar sai dalalar da yawu take bisa
kasa,
Yau kwanakinta kusan goma kenan bata
dandani Nama ba ,
kullum sai ciyayi take ci
Toh yau ga tsuntsu daga sama gasasshe,
.
Mayunwaciyar Damisar tayi ruri sannan ta
fada kan jarumin
saurayin ,
Nan suka zube kasa gaba dayansu
Damisar tana bisansa sai kokarin farke
wuyansa take da
hakoranta, a yayin da shi kuma saurayin ya
rike habarta da
hannunsa, sannan yasa kafa ya taka ta , take
damisar tayi sama
yadda kasan an dauketa da majaujawa , koda
damisar ta fado
bisa kasa sai tayi wata irin kara sakamakon
jin zafin takun da
saurayin yamata .
.
Saurayin ya mike tsaye sannan yayi wata irin
tsayuwa irin na
Mazan kwarai,
.
Damisar na ganin haka sai ta kara dumfaro
shi da nufin tai tsalle
ta diram mai a wuya,
Koda tai tsallen da nufin ta fada akan
wuyansa sai kyakkyawar
saurayin ya sanya hannunsa guda . Ya rike
mata makoshi, sai
gashi murgujejiya kuma lafceciyar damisar
na wutsil wutsil a
hannunsa kai kace, masunci ne ya kama kifi.
.
Take saurayin ya daga damisar sama sannan
yai jifa da ita ,
koda yai jifa da ita sai taje ta gwaru da wani
babban bishiya ,
take bishiyan ya fadi rikica,
Wannan damisar ko shurawa batai ba,
Kyakkyawan saurayin yazo gaban gawar
damisar , ya tsugunna
da nufin ya sabata a kafadarsa yayi gida,
.
Ba zato babu tsammani kawai sai ya fara jin
Dirdir gowan wasu
abubuwa a bayansa,
Koda ya juya don yaga mene wannan.
Anan ne yayi arba da su,
Wasu gabza gabzan Arnan daji ne,
Su wayannan arnan dajin suna sanyene
warki na fatun
mesa,dukkanninsu kamanninsu da fasalin
surar jikinsu dayane ,
Lafta lafta ne ma'abota tarin damatsa babu
kaya a jikinsu face
wannan warkin na fatan mesa,
.
Daya daga cikinsu yazo gab da wannan
kyakkyawan saurayin
yace " yakai wannan kyakkyawan saurayin
kayi sani cewa ka
aikata babban kuskure a garemu wanda
hukuncinka shine kisa
mafi muni"
.
Cikin gadara saurayin ya dubi arnan dajin
nan wayanda
adadinsu yakai dari yace
"Ku sani ni bansan mai na aikata a gareku ba
da har zaku yanke
wannan hukuncin akaina "
.
Shugaban arnan dajin ya daka masa tsawa
sannan yai nuni da
dan yatsansa izuwa ga gawar damisar nan
yace "shi wannan
damisar daka hallaka , shine mafi kusanci ga
abin bautarmu,
duk wata bukata da muke da ita ga abin
bautarmu muddin muka
kama kafa da wannan damisar toh take abin
bautarmu yake biya
mana buka tunmu.
.
Kasani yakai wannan gafallallen saurayi, ako
wacce rana mun
kasance muna farauto ma wannan damisar
mutun daya don tayi
kalaci da shi,
Haka muka kasance muna yi har tsawon
wasu shekaru,
Kwatsam sai gashi an wayi gari mun fita
nemo wa damisar abin
kalacinta, har muka debi tsawon lokaci bamu
dawo ba,
Hakan yasa yunwa ya addebeta ta fito neman
wanda tsautsayi
ya kasa dashi, sai gashi ka kashe mana ita,
Abisa wannan mummunan zunubin daka
aikata mana ne
shugabanmu Boka Abulzulmu ya turo mu
damu yimaka kisa irin
ta wulakanci ,
Don haka ina umartarka daka bani kanka
cikin maslaha nai
maka kisan sauki, "
Koda jin haka sai kyakkyawan sauyarin ya
tuntsire da dariya,
sai da yayi mai isarsa sannan yace "Ashe ma
mugun iri na rage
A doron kasa kunga yanzu babu wata rai
dazata kara salwanta a
dalilin wannan Damisar"
Yana rufe bakinsa sai shugaban arnan dajin
yayi kukan kura
sannan nufo kan saurayin, hannunsa rike da
sharbebiyar takobi,
Koda yazo daf da saurayin sai ya kai mai sara
da nufin ya cisge
mai kai, cikin zafin nama saurayin ya sunkuya
saran tabi iska,
.
Kafin shugaban arnan dajin ya sake kaimai
wani saran . Sai
kyakkyawan saurayin yayi wuf cikin zafin
nama ya kirba ma
shugaban arnan dajin dundu a baya,
Nan take shugaban arnan dajin ya kwalla
kara sannan yayi taga
taga tamkar zai fadi amma sai ya tirje, take
ya furzar da jini
daga bakinsa.
Saurayin baiyi kasa a guiwa ba ya kama kan
shugaban arnan
dajin ya murde, karan karyewan kashi ta
bayyana, duk wata
gaba ta daina motsi ajikin shugaban arnan
dajin,
.
Kyakkyawan saurayin yai jifa da gawar izuwa
ga sansanin da
arnan dajin ke tsaitsaiye,
.
Wasu arnan daji biyu suka cafe gawan amma
sabida karfin jifan
da saurayin yayi da gawan sai da suka zube
kasa gaba dayansu.
.
Koda arnan dajin suka ga abinda saurayin ya
aikata ga
shugabansu sai dukkaninsu suka yi kururuwa
sannan suka zare
makamansu, nan suka rugo da gudu da nufin
su isa wajen da
saurayin yake su gididdibashi gida gida.
Shi ko saurayin koda yaga sun nufoshi sai
yayi murmushi
sannnan ya gyara tsayuwansa.
Koda arnan dajin suka kariso wajenda
saurayin yake sai sukai
mai rubdugu.
Shi ko saurayin koda yaga haka sai ya sanya
dukkan karfinsa ya
tarwatsasu, hohoho!!
Da mutum yana wajen yanaganin yanda
mutun daya ya gagari
daruruwan mutane lallai daya tabbatar da
cewa wannan
kyakkyawan saurayin ya cika NAMIJIN GASKE
mai tarwatsa
maza.
.
Arnan dajin sai kai masa sara da suka suke ,
shi ko ya wanzu
yana mai zullewa da gociya,
Babu abin da zaibaka mamaki da saurayin
face ganin ko
makami babu a hannunsa.
A duk lokacin daya samu arnen daji ya kirba
mai naushi ko
dundu. Nan take zakaga mutun ya fadi
wanwar akasa ko
shurawa bazai yiba
.
Sai da aka dauki tsawon lokaci ana wannan
fafatawan inda
saurayin yai ta ragargazar arnan dajin ,
Har ya samu nasarar karkashesu gaba daya.
Sannan ya dauki gawan damisar ya azata
bisa kafadansa, yayi
tafiyarsa
.
Tafiya yake har ya kawo bakin wata bukka ,
sannan yayarda
gawar damisar a kasa,
.
Ya nufi wani turki ya zauna ,
Zamansa keda wuya sai waya kyakkyawan
mace ta fito daga
cikin wannan bukkan
.
Wannan matar zata kai shekaru hamsin da
doriya amma in
kaganta kace yar shekara talatin da wani
abune.
Matar ta dubi saurayin tace dashi
"MUHAISIN sai yau kadawo"
Jarumin saurayin da aka kira da muhaisin ya
dubi wannan matar
yace
"Ummi na kenan kisani dadewar danayi ta
samo asaline daga
rashin samun dabbar danake nema"
.
Wannan matar sunan ta hamasiya sun
kasance suna rayuwa
acikin wannan kungurmin dajin shekara da
shekaru ita da danta
muhaisin
Tun muhaisin bai mallaki hankalin kansa ba
Ya taso ya tsinci kansa acikin wannan daji,
Tun baifi shekaru tara a duniya ba
mahaifiyanshi hamasiya take
ganin ababen al'ajabi a tattare da shi.
Don alokacin baifi shekara tara a duniya ba
amma sai taga ya
fita da nufin zai je farauta, in ya fita kuwa
baya da wowa sai
bayan kwanaki biyu
.
Nan zai dawo da manyan namun daji
wayanda ko rikakken
mafarauci ma sai yayi da gaske kafin ya kama
irinsu
.
Tun hamasiya tana al'ajabi har tazo ta daina
,bangaren jarumta
kuwa duk yawan abokan gaba tarwatsasu
yake, kuma shi baya
fada da makami don ko dabbobi ma wuyanzu
yake murdewa.
Tun da yake a rayuwarsa bai taba yin yaki ko
fada da makami
ba da zallan karfin damtse yake yakan ayari
guda na yan fashi,
da kuma gungun yan harin sumame.
Haryanzu da kwai wasu yanfashi dake
tarkonsa
Su yan fashin sun riga da sunsan yafi
karfinsu shi yasa da sun
hadu sai kaga yan fashin sun ruga a guje .
Ace warsu wai lokacin haduwarsu baiyiba
tukun idan lokaci
yayi su da kansu zasu nemeshi,
.
Alokacin da muhaisin ya mallaki hankalin
kansa sai ya fara
tambayar hamasiya mahaifinshi
Hamasiya takance da shi mahaifinsa ya rasu.
.
Alokacin da hamasiya tazo gaban muhaisin
don taga alamun
gajiya ajikinsa sai taga gefen damtsensa na
zubar da jini , nan
da nan hankalinta ya tashi ta yagi wani kyalle
dake rataye bisa
wannan turkin , sannan ta kama hannun
muhaisin tana daure
mai wannan raunin
.
Nan ta tambayeshi meya ji mai wannan
rauni,
Bai boye mata komai ba , ya labarta mata
artabonsa da arnan
daji
.
Koda hamasiya ta saurari labarinsa sai nan
da nan kwalla ya
cika mata idanu, koda muhaisin ya lura da
yanayin da
mahaifiyarsa ta shiga sai ya ce" yake ummina
shin ina dalilin
zubar da hawayenkinnan , "
Hamasiya tayi sauri ta share kwallan tace"
yakai dana kayisani
bako maine ya sanya ni zubda hawaye ba
face tuno da
mahaifinka da nayi, Lallai ka gaji mahaifinka
dana."
.
Muhaisin najin haka sai ya durkusa bisa
guiwowinsa yace" Na
rokeki ummina daki sanar dani labarin
mahaifina da kuma
dalilin dayasa muke rayuwa a cikin wannan
kungurmin dajin"
.
Koda jin wannan tambayan sai Hamasiya ta
mike tsaye sannan
ta nufi wannan bukkar koda tazo gab da
bukkan sai ta tsaya ta
dafa bukkan da hannu daya sannan ta juyo ta
dubi muhaisin
tace " yakai dana hakika yau kayi mani
babban tambaya ,
hakika bawai banason sanar dakai labarin
mahaifinka bane sai
dai, bana son tuna baya, bana son tuna
babban masoyina abin
kauna na" koda tazo nan a zancenta sai wasu
kwalla na bakin
ciki suka gangaro bisa kuncinta.
.
Muhaisin ya kariso wajenda take sannan
yace
"Ya ummina hakika kece kadai nake gani
nakejin farin ciki a
cikin zuciyana, bana son ganin zubowan
kwallanki, bana son
jin labarin muddin hakan zai tsaida zuban
kwallanki"
.
Hamasiya najin haka sai ta tausaya ma
muhaisin ainun ta sanya
hannu ta tallafo habarsa tace
"Yakai dana kasani Mahaifinka Gawurtaaccen
Sarki ne Adali
mai jinkan talakawa,
Mahaifinka shike mulkin birnin Tehran .
Kamanninka dana mahaifinka sak babu
banbamci, Sunansa
Sarki HINZUR IBN HUMAS"
.
Namijin gaske 1
Part 1B
(c)shuraih usman
@shuraih 99%
NAMIJIN GASKE
Littafina daya 1
Marubuci:- Shuraih Usman
Typing:- Shuraih Usman
Tel. 08133209890
Part B
.
Doka, banyarda wani yayi copy ko ya sarrafa wannan labari ta
ko wace hanya batare da izni na ba. Dafatan za'a kiyaye
Copyright
Shuraih Usman
.
Kimanin shekaru ashirin da suka gabata a birnin tehran , birnin
tehran babban birnine wanda mutanen cikinsa yawancin
sana'arsu itace Noman kayan Abinci iri iri,
Kasuwar garin nacine a duk mako. Kuma daga wasu garuruwan
sukan ziyarci wannan kasuwa a duk makon da zaici,
.
Al'umman birnin tehran ma'abota son zaman lafiya ne, A yayin
da adalin sarkinsu hinzur bin humas, ya tsaya tsayin daka wajen
yada zaman lafiya a duk sassan birnin
.
Sarki hinzur babban sadaulkine wanda duk ilahirin nahiyar
babu sadauki kamarsa.
Ya kasance yana da wani dan uwa mai Suna Humaiz bin Humas
.
Shi Humaiz yan uba suke da hinzur wannnan tasa ya kullaci
hinzur sosai a cikin zuciyarsa,
Wacce har takai ta komo So yake yaga bayan sarki hinzur
sannan ya kwaci mulkinsa. Duk da kuwa alokacin matsayin
wazirin tehran yake.
Duk wani bakin ciki da hassada gami da kyashi da yake wa
sarki hinzur bai taba Nuna wa a gabansa ba, hasalima irin
biyayya da so da kauna da yake nuna wa hinzur kai kace tamkar
da gaskece amma na ciki na ciki
.
Waziri humaiz yasan bazai iya tarar sarki hinzur gaba da gaba
ba, don kuwa linzami tafi karfin bakin kaza.
Hakan tasa yaje ya samu wasu yanfashi a wajen gari cikin wani
kungurmin daji , nan take ya zayyane masu bukatarsa na son su
taimakeshi su hada karfi da karfe, don su kawar da sarki hinzur
a ban kasa.
.
Shugaban yan fashin mai suna kallabu ya dubi waziri humaiz
bayan sun gama sauraron bayaninsa yace da shi ,
"Yakai wazirin birnin tehran hakika kazo mana da abinda muka
dade muna jira tsawon wasu watanni, lallai kasani wannan
taimako daka nema daga wajenmu tamkar mune muka nemi
taimako daga gareka"
Waziri najin haka sai ya cika da tsananin mamaki sannan ya
dubi kallabu yace "shin kai kuwa wannan shugaba ta yanfashi
meye dalilin ka na fadin hakan"
Nan take Kallabu ya bushe da dariya saida yayi mai isarsa
sannan ya dubi
Waziri humaiz yace da shi "yakai humaiz kai sani cewa mun
dade muna son ganin bayan sarki hinzur bisa takura mana da
yayi, lallai zamu taimakeke ba tareda mun karbi ko kwandalarka
ba, Abin dana ke jimana shakka iyace ta yaya zamu ratsa har
mu shiga gidan sarki hinzur .
Humaiz najin wannan tambayar sai yayi murmushi sannan
yace" indai maganan shiga gidan sarkine toh lallai ina tabbatar
maku shan ruwa ma ya fishi sauki a wajena, domin kuwa akwai
wani hadimina da zansa ya jagoranceku har zuwa turakar sarki"
."
Koda yamma tayi sai shugaban yanfashi da yaransa kimanin su
dari biyar, sukayi shiri irin ta fatake sannan suka tasamma
birnin tehran
.
Koda suka iso bakin kofan birnin tehran sai masu tsaron kofa
suka tsaida su,
Wani badakare wanda da alamu shine babba acikin dakaru masu
tsaron kofan garin ya kusanto gaban wayannan yanfashi
wayanda suka yi shirin fatake ya tambayesu
"Yaku wayannan ayari su waye ku , sannan Me ke tafe da ku
izuwa wannan kasa tamu mai tarin daraja"
.
Koda jin haka sai kallabu wanda yabadda kamanninsa ta hanyar
nade wata katuwar rawani a kansa ya dubi wannan dakare yace
"Yakai wannan mai tsaron kofan kasani mu fatakene sannan
bada niyyar komai muka iso wannan birnin ba face don
kasuwanci"
Shugaban masu tsaron kofan yace
"Wacce irin haja kuka dauko"
Kallabu yai nuni da hannunsa ga bayansa wasu rakumane a
kalla sunkai hamsin dauke da manyan sundukai a bayansu,
Sarkin kofa ya iso gaban rakumi daya sannan ya bude sunduki
daya daga cikin sundukannan ,
Babu komai aciki face kayan masarufi kama daga dangin zinare
har zuwa kan su murjani da yakutu.
Nan take shugaban masu tsaron kofa ya bada umarni da a bude
musu kofa su wuce
.
Koda suka shigo birnin tehran basu zame ko ina ba sai cikin
kasuwan garin , inda suna isa suka tarar da wani hadimin waziri
humaiz .
Wannan hadimi yai masu jagora izuwa wata babban gida ta sirri
wacce ta kasance mallakin waziri humaiz ne.
**** *****
Can cikin talaitainin dare kuwa dukkan wayannan yan fashin
sunyi mugun shirin yaki. Kai kace yakin duniya zasuje
Gama kimtsawarsu keda wuya sai hadimin waziri humaiz daya
jagoranci su kallabu izuwa wannan gida ta sirri ya shigo garesu
.
Sunan hadimin KAMSAS kuma shine amintaccen hadimin
waziri humaiz
Kamsas ba karamin hatsabibi ba ne don kuwa duk cikin
hadiman waziri babu wanda yake matukar ji dashi tamkar
kamsas
.
Nan kamsas ya dubi kallabu yace " ya shugabana Muna iya
tafiya yanzu"
.
Ta bayan gari suka bi gudun kar wani yaji takun sawaye ya
yawaita ya farka daga barci.
Ba a dadeba suka fara hango kofan gidan sarki, masu gadi na
nan sai zagaye suke ta ko ina
Koda kallabu yaga haka sai ya dubi kamsas
"Shin ta ya ya kake ganin zamu ratsa wayannan da karu masu
tsananin yawa wayanda na tabbata ko munyi nasarar gamawa da
toh sai nayi asarar dakaru masu yawan gaske .daga karshe kuma
in muka shiga gidan sarki ragowan sauran dakarunsa su
karisamu.
Kamsas na jin haka sai yayi murmushi sannan yace "ya
shugabana kai dai ka tsaya zakaga ta yadda zamu samu nasarar
shiga gidan kuma batare da mun raunata badakare ko guda daya
ba"
.
Kamsas na gama fadin haka sai ya rike hannun shugaban
yafashi kallabu sannan yace mai yai ma yaransa umarni da
kowa ya rike hannun juna,
Cikin dan kankanin lokaci sai gaba daya yan fashinnan suka
rirrike hannuwan yan uwansu.
Nan take kamsas ya fara fadin wasu kalmomi daga cikin yaren
girkawa,
Take sai wata guguwa bayyana , koda bayyanar guguwar saita
nufosu tana zuwa wajenda suke sai ta suresu tai sama da su
****** *****
Marubuci:- Shuraih Usman
Hakkin mallaka (m) Shuraih Usman
Company:- Shuraih 99%
(c) shuraih Usman 2017
Typing:- shuraih 99%
Namijin gaske 1
Part 1C
(c)Shuraih Usman
@shuraih 99%
NAMIJIN GASKE
Littafina daya 1
Marubuci:- Shuraih Usman
Typing:- Shuraih Usman
Tel. 08133209890
Part C
.
A cikin farfajiyar gidan sarki hinzur dakaru sai kai kawo suke
duk da yake cikin darene amma farfajiyar gidan a haskake take
yadda ko Allurace ta fadi sai anganta,
.
Ba zato ba tsammani sai gani akayi wata iriyar guguwa ta
bayyana
Gaba daya dakarun gidan suka mai da hankalinsu...


Read / Download NAMIJIN GASKE Book 1

START READING

OR

DOWNLOAD TXT NOW
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album