Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

goshina. “Saina dawo”. Kaina kawai na jinjina masa dan na kasa kallonsa. A hankali na furta, ”ALLAH ya tsare”. Inajin yana murmushi. Nidai ban kallesanba har ya fice.
Sassanyar ajiyar zuciya na sauke tare zubewa a kujera daɓar na dafe kaina, wlhy abun mamaki yake ban, boss fa! Kai rayuwa bata rabo da abubuwan al'ajabi. Naja kusan mintuna biyar a haka kafin na miƙe naje ɗakinsa dan na gyara. Sosai ɗakin yake ƙamshin turarensa daya fesa yanzun, tsaf na gyarashi na saka fresheners sannan na koma kicin na ɗauraye kwankina da mukaci abinci shima naɗan gyara abinda bai minba.


Koda Jawaad ya fito sai ya iske baƙonsa cikin rumfar bunun dake harabar gidan maigadi ya kawosa, ƙarasawa yay yana faɗin, “Ai bammayi tunanin kai bane Munkaila”. Baƙo mai suna Munkaila daya miƙe domin girmamawa ga Jay yay murmushi, “Nine wlhy Oga barka da fitowa”. “Yauwa sannunka da zuwa” Jay ya faɗa yana zama tare da masa nuni daya zauna shima. Cikin girmamawa Munkaila ya gaishe da Jay kasancewarsa ogansa, file ɗin gabansa ya miƙa masa yana faɗin, “Oga dukkan abinda kake buƙata gashi, harma da abinda bakaceba dukna haɗo maka”. Kai Jay ya jinjina masa da faɗi, “Sannu da ƙoƙari” yana buɗe file ɗin. Da hotuna ya fara cin karo waɗanda sukai masifar ɗaure kansa dan harda Alhaji baba tare da mata biyu wadda ɗaya a ciki takasance kakarsace mahaifiyar su Ummah da shima a hoto ya santa, kallon Munkaila yay kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya maida file ɗin ya rufe.
Munkaila yace, “Oga akwai matsala ne?”. Kai Jay ya girgiza masa, “Babu matsalan komai, yaya maganar wancan aikin?”. “Shima ina gab da kammalawa oga, saboda naga ka matsu da wannan ma shiyyasa na dakata da wancan”. “Shikenan kayi ƙoƙari shima ka haɗamin shi a satin nan, ga wannan ka saka mai nima nayi aljihun nawa yay ƙasa”. Godiya Munkaila yayi sosai sannan suka fito a rumfar. Jay ya shiga mota shikuma ya fice dan mashin ɗinsa na daga waje bai shigo da shiba.
★★★★★
Fitar jawad babu jimawa su Ummie suka isa gidan amarya Bilkisu, Ummie, Zuhrah, Rebecca, Nazifa. Duk da jiya suka rabu da juna tuni suka haukace da ihun murnar ganin juna, suka saka bily tsakkiya da tsokana kala-kala, tun tana musu shiru dai harta koma ramawa itama dan taga shirun nata bazai sa su barta ba.
_________________________
Asibiti yay niyyar fara zuwa saboda Uncle Sulaiman daya tilasta masa yaje, to amma wannan bayanan da Munkaila ya kawo masa yanzun sun ruguza komai, burinsa kawai ya dangane da gidan Alhaji Babba. A waje yay fakin motarsa ya shiga shi kaɗai, Alhaji babba na zaune a falo hannunsa riƙe da Jarida Jay ya shiga da sallama. Ɗagowa yay yana kallonsa fuska ɗauke da murmushi, cikin tsokana yace, “A lallai wannan angon da gaske bahausa ya aura, ashe ba gidan jiya ya komaba”. Jay dake murmushi ya girgiza kai kawai yana zama, “Wannan itace tarbar da zakamin ma na baro matata na taho ganinka da farar safiyar nan”. Alhaji babba yay dariya irin tasu ta manya yana faɗin, “Ja'iri kenan bakifa ya buɗe”. Gaidashi Jay yayi yana murmushin tsokanar da kakan nasa ke masa. Sai da suka kammala gaisuwar da tambayar lafiyar juna da amarya Bilkisu kafin jay ya buɗe file ɗin da Munkaila ya kawo masa, hotunan ciki ya fiddo gaba ɗaya ya miƙama Alhaji Babba shi kuma ya maida hankali ga duba bayanan cikin file ɗin.
“Sa'adatu! kuma?”. Alhaji babba ya faɗa da alamun bazata. Kallonsa Jay yayi amma baice komaiba. Alhaji babba yace, “Jawaad kana nufin matarka nada alaƙa da wannan ta hoton?”. Zama Jawaad ya gyara sosai yana maida dukkan hankalinsa ga kakan nasa, “Baba abinda bincike ya nuna min kenan, sai dai nima kaina a kulle yake musamman da ganin hotonka a tsakkiyar mata biyu bayan mata ɗaya nasan kanada ita kafin Mama Maryam”. Shiru Alhaji babba yay na wasu mintuna kafin ya sauke ajiyar zuciya, yace, “minene sunan mahaifin nata?”. “Adam makaho” Jay ya bashi amsa a taƙaice. Nanma shiru Alhaji babba yay na wani ɗan lokaci yanata faman jinjina kai da murmushi a fuskarsa kafin yace, “Abin akwai ɗaure kai da ban al'ajabi”. Jawaad yace, “Miyasa zai ɗaure maka kai bayan na fahimci kasan wani abu”. Murmushi Alhaji babba yayi mai ciwo da sake maida hankalinsa ga hotunan guda biyar, ɗaya shine da mata biyu a jiki sai jaririn yaro da alamu suka nuna ranar sunansa aka ɗauki hoton ma ƙila, ɗaya kuma matane da miji matar gurguwa sai mijin da alamu suka nuna makaho ne, sai hoto na uku jaririyace nannaɗe cikin farin showal da gani kaga sabuwar haihuwa, hoto na huɗu, mata da minjin nan ne da jaririyar, na ƙarshema dai mata da mijinne sai bilkisu a tsakkiyarsu da bazata wuce shekaru goma sha biyarba. Ya ajiye hotunan yana kallon Jawaad da ƙyau. “Akwai abinda ku baku saniba Jawaad, mahaifiyarka cema kawai zata iya sanin wani abu itama ba duka ba dan a labari ta sani. Ba Amina da Maryam kawai na taɓa aureba, na taɓa auren wata matar mai suna Sa'adatu. Kafin aurena da Amina Sa'adatu itace yarinyar da naso aura dan itace muke soyayya amma iyayena suka ƙi, bakomai ne ya sakasu ƙinba sai kasancewar Sa'adatu batajin magana, duk da yarinyace da bata wuce shekaru goma sha biyarba a lokacin mutane kan jefeta da kalmar ƙarancin tarbiyya, Sa'adatu ta tashi a gidansu bata da uwa a hannun kakarta ta tashi, hakan yasa ta tashi sangartacciya da batajin ƙwaɓa, a dalilin ɗan karatun da aka sakata na boko wanda a wancan lokacin iyakamu maza kawai keyinsa yasa idanunta buɗewa dan ita kaɗaice mace a cikinmu, Sa'adatu ji take tafi kowa a ƴammatan yankinmu dama gata ƴar gata kuma babanta shine maigari, ALLAH ya jarabceni da sonta fiye da yanda kake tunani har takai naima iyayena maganar aurenta. Amma sai mahaiyata tace sam batasan wannan zanceba tama rigada tamin mata Amina, na ɗaga hankalina matuƙa a lokacin amma dole na haƙura muka rabu da Sa'a ina kuka tanayi. Hakan ya zafi kakarta har tayi alwashin sai nayi nadamar yaudarar jikarta da nayi. Babu wanda ya ɗauki alwashinta wani abu aka ɗauramin aure da Amina ta tare. Banason Amina amma ita tana sona kuma mace ce mai haƙuri da kawaici, a zamanmu tasha wahala kafin na ɗan fara fuskantarta, aurenmu da Amina yakai shekara shida amma bata taɓa ko ɓariba, a wancan lokacin dan mace takai shekara goma ma bata haihuba babu mai damuwa da hakan balle ya zama abin magana shiyyasa nima ban taɓa damuwaba. Zuwa lokacin Sa'a itama tayi aure amma ba a wannan garin namu ba, wani ɗan uwanta mai kuɗi aka aura mata, sai dai kuma hankalinta na kaina dan haka shekararta uku ta kashe auren ta fito da yarinyarta guda safara'u, a lokacinfa na tsaya kai da fata saina auri Sa'a dan sonta na nan daram a raina. Zakasha mamaki idan nace maka Amina itace taita kai kawo ga iyayena har mahaifiyata ta amince na auri Sa'a. A farkon shigowar Sa'a gidana ta kwantar da kanta tanama Amina biyayya kamar gaske, amma tunda muka wayi gari ta samu ciki sai abubuwa suka fara canja salo, raini da wulaƙanci babu wanda take ragewa bataima Amina shi ba a bayan idona, amma a gabana babu abinda ya sauya na ladabin da take mata da. Sam ban fahimci zaman kisan mummuƙen da akeyi a gidana ba dan Amina ko a fuska bata taɓa nunaminba har ALLAH ya sauki Sa'a lafiya ta haifi ɗa namiji wanda yaci sunan kakana Adamu. Bayan haihuwar Adamu ne na fara fuskantar akwai matsala a zaman nasu, dan wataran na shigo a bazata na iske Sa'a nama Amina gorin haihuwa. Ranar nayi tamkar bansan Sa'a ba saboda biji-biji nai mata tare da dogon gargaɗi na saki ɗaya. Kamar Sa'a ta nutsu bayan wani lokaci saita dawo da halinta na rashin arziƙi har ƙawaye take kawowa suna haɗuwa cin zarafin Amina. Cikin amincin ALLAH Sa'a bata yaye Adamu ba saiga Amina da ciki. Munyi murna sosai fiye da zato, ganin Amina itama ta samu cikin da ake mata gori sai Sa'a ta sake sabon salon iskanci, Amina dai bata kulata dan ta bama banza ajiyartane. Cikin ikon ALLAH itama cikinta yakai haihuwa ta haifi mace wadda taci suna Bilkisu (mamanka kenan) dariya Sa'a taitayi alokacin da faɗin ai dai itace a sama tunda namiji gareta, Amina dai bata kulatan, bata yaye Bilkisu ba sai ga wani ciki, Sa'a kuma shiru, hankalin Sa'a ya kuma tashi ainun da wannan ciki na Amina harta sake haihuwa bata barta ta hutaba, a wannan haihuwarma dai mace ta samu itace Wasila (Ummah babba). dukda Sa'a ta nuna bata damuba tunda Amina mace ta sake haihuwa saita kasa daurewa, tashiga ƙananun magana Amina tai mata asiri haihuwarta ta tsaya, tun ina tsawatarwa har al'amari yafi ƙarfina na saki Sa'a saki biyu ya zama uku dan al'amarinta ya isheni. Wannan saki yama dangina daɗi yama nata zafi dan dangina dama babu mai sonta sai ƙalilan a cikinsu. Nayi ƙoƙarin na amshi Adamu amma kakar Sa'a tace ban isaba, duk hanyar data dace nabi suka hanani ɗana, acewarsu kishiya bazata riƙe musu yaroba wataran ta kashesa. Rabuwarmu da Sa'a da shekara guda Amina ta sake haihuwar mace dai again, wadda taci sunan Rahamah (ɗiyar Alhaji babba wadda ta rasu) haihuwar Rahama babu jimawa kakar Sa'a ta rasu, alokacinne na shirya amshe yarona dan banaso ya tashi da kalar tarbiyyar gidansu, sai dai a randa naje nai magana da mahaifinta washe gari aka nema Sa'a aka rasa ta gudu da Adamu. Neman duniya anyi babu wanda yaga Sa'a, munɗauki tsahon lokaci muna nemanta amma babu Sa'a babu labarinta. Har kuma ALLAH yayma Amina rasuwa ta barni da ƴaƴa huɗu duk mata ban sakejin ko labarin Sa'a ba balle yarona, kullum yana a raina, dan harda Maryam mun taɓa yin labarinsa”.
Ajiyar zuciya Jawaad ya sauke yana mai jinjina al'amarin a ransa, yace, “to Amma baba miya nisantaka da danginta harmu bamu taɓa saninsu ba ballema shi labarin Uncle ɗin? Tunda gashi dai alamu sun nuna shi Uncle ɗin ya dawo gida har yay aurema kenan ya haifi Miemaa”.
“Kasan na faɗa maka dama akwai damuwa tun hanani aurenta da akai a farko, sannan koda mukai aure danginta sunajin zafin mahaifiyata dani kaina, badanma sunso Sa'a ta dawo ta aureni ba, bayan guduwarta kuma sai abubuwa suka sake ƙwaɓewa suka ɗaura laifin akan Amina ce tai mata kurciya tabar gari saboda ita ƴaƴanta matane Adamu kuma namijine, dalilin wannan sheɗancin nasu nema yasa nayo nesa dasu na dawo nan dan lokacin garin bai haɗe ya zama babba ba gaba ɗaya kamar yanzun, ahankali abubuwa sukaita canjawa dangi makusanta sunata ƙarewa, shiyyasa kusancin namu ya sake taɓarɓarewa ma baki ɗaya tunda wanda za'aiyi dominsa babu shi tare dasu”.
Kai kawai Jawaad ke iya jinjinawa amma ya kasa magana, Alhaji babba ya katse shirun nasu da faɗin, “Duk da na daɗe banga Adamu ba tun yana yaro amma ƴarsa sai ta ɗakko kamanin Rahamah sosai musamman tana yarinya fiye da nasa kamannin, dan ni randa na farama ganinta a asibiti kamannin Rahamah na gani tattare da ita bana Adamu kawai ba, hikimar UBANGIJI kenan mai tsara yanda yaso a lokacin da yaso, Jawaad yanzu kenan Adamu baya raye?”. Cikin damuwa Jay ya jinjinama Alhaji babba kai, “Ta faɗamin mahaifinta ya rasu bayan rasuwar mamanta kusan shekara bakwai kenan ana cikin na takwas, kuma a yanda bayanai suka nunama kenan anan ɗin ya rasu, to amma abinda yama ɗauremin kai sufa danginsa ma suna nuna tamkar bashi da wata alaƙa da ɗiyar tasane fa, wannanne dalilin daya raunana zumincinsu ya dawo gefe yana rayuwarsa shi da matarsa kawai da yarinyar, kuma ko bayan rasuwarsa abinda yasa sukai watsi da ita kenan sai dai batasaniba ita”.
“Jawaad ban gane basu da alaƙa ba, duk wanda ya kalli matarka aiko yaga jinin Adamu ai”. “Gaskiya ne Baba, a hoton dai kam daka gani kasan jinsa ce, nima inason zuwa da kaina garesu naji miyasa suke nisantashi da abinda alamomi suka nuna nasa ne?”. “Bakai kaɗai zakajeba Jawaad, tare zamuje ai, dan nima ina buƙatar amsoshi da yawa a garesun”. Sun daɗe suna tattaunawa akan batun kafin jay yayma Alhaji babb sallama ya tafi asibiti.
★★★★★★
Tunda ya shiga asibitin sukai masa caa da idanu, shiko ya fuske abinsa fuska a ɗaure ya gaidasu da tambayar jikin Shahudah, kafin ya shiga ya dubata tana barci har yanzun, dan data farka suke sake mata wata allurar barcin tunda taƙi kwantar da hankalinta ta saurari kowa, ta dage sai an kira mata Jay.
fitowa yay daga ɗakin ya dawo wajensu da nufin yimusu sallama ya kama gabansa, amma sai mama Atika ta dubesa cikin gadara fuska babu wasa tace, “Mun gama magana da ƙannen ubanka yau bayan sallar azhar za'a maida aurenka da Sabira, kuma gobe idan ALLAH ya kaimu zata tare koda ba'a sallameta daga asibitin ba”.
Wani lallausan murmushi Jay ya saki da ya bama kowa al'ajab da mamaki, dan ba murmushin sukai tunanin gani daga garesa ba. Ya kalli mama Atika da ƙyau yana tura hannayensa cikin aljihun wandon shaddarsa da gyara tsaiwa yace, “Shi kuma mijinta yaya zakuyi dashi”. Yay maganar da maida kallonsa ga ƙofar shigowa.
Gaba ɗaya suka maida kallonsu ga ƙofar inda ɗan-fir'auna ke tsaye akan ƙafafunsa ya warke sarai sai tabbunan raunikan da yaji waɗanda basu gama bajewa da ƙyauba.............✍
(Kana basu pepe da ginger ɗan bilkisu da Abdul-Aziz mijin bilkisu🤣😂🚴🏼)

______________________
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.



ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[1/2, 11:31 AM] HASNA✍🏻: Billyn Abdul:
Page 41

.................A firgice Mama Atika, Dad, Mom, Uncle Nasir, Uncle Uwaisu, Aamilah, Salman duk suka miƙe baki hangame. Uncle Sulaiman da Uncle Sadiq da basusan komaiba illa cewar ɗan fir'auna ya mutu suka bisu da kallo dansu basusan ɗan fir'aunan ba a zahiri har yanzun. Cikin tsananin firgici da suɓutar baki Mama Atika tace, “Nasiru ba kunce sheɗanin nan ya mutu ba wai?”. Rasa mai bata amsa akai a cikinsu.
          Ƙyalƙyalewa da dariya ɗan-fir'auna yay irin ta asalin tsagerun nan da suka gama gawurta a fitsara, ya nuna Mama Atika yana tsuke fuskar tamkar ba shine ya gama dariyar ba, “Ke dai tsohuwarnan anyi ƴar buƙulu, to idanma na mutu ban kwashi garaba ashe kanwa na kawo duniya, koda yake ashefa shirya kasheni akai ko? To anyi tabanza dan shegen taurin raine dani zanyi dogon zamani fiye da naki, a nunamin inda matata take malamai”. Jikin Aamilah na rawa tace, “Brother ga shi nan”. Harara ya zabga mata, “K dan tsohuwarki waye Brother ɗin? Yayah zaki ringa cemin dan gyatuminki hausa zakimin, kujimin faratun banza mai suffar yahudawan farkon ƙarni”. “Kayi haƙuri dan ALLAH yaya bazan sakeba” tai magana tana komawa bayan Jay da yay kunnen uwar shegu dasu kamar baisan wainar da ake toyawaba ta maƙale, Jay wayama yake latsawa abinsa hankali kwance kamar baya wajen. Dariya ɗan-fir'auna ya sake kecewa da ita yana faɗin, “Kaji bayani, da kikace ke tsagerace? Hegiya nifa bar ganinki ƙanwar matata billahillazi jinake kamarfa nai miki eyane dan zaki bada kala a garin maji daɗi. Amma kinci arziƙin musulunci ba'a wannan haɗin. Oga bara na shige daga ciki duk da fa inajin nauyinka fuska kawai zanyi aradun ALLAH na siɗaɗa”. Yay maganar da wani ɗora hannu ɗaya kan ɗaya irin salon nan na gaisuwar gayu ga na gaba dasu. (ALLAH ya daidaita sahunka akan lokaci habibullah😂🤣)
      Jawaad da baiko ɗagoba ya jinjina masa kai kawai yana cigaba da aikin latsa wayarsa. Sai da ɗan fir'auna ya shige ɗakin da Shahudah ke kwance sannan Jay ya ɗago yana kallon Dad da yay sagade kamar wani gunkin hanya yana kallon ƙofar, firgigit ya dawo hayyacinsa saboda bugo ƙofar da ɗan-fir'auna yayi da masifar ƙarfi.
           Inda Jay yake ya nufa da sauri-sauri yana baza babbar riga, Muryarsa da zafi ya furta, “Inason muyi magana”. Kallonsa kawai Jay yayi baice komaiba, sai dai fuskarsa shima a haɗen take, da ya kai maƙurar da ayanzu zai ɗauki matakin da bai ɗaukaba ada akan kowa. Guntun Murmushi yay da miƙewa yana ɗan kallonsu Uncle Nasir da suka zubo musu idanu. Rai a ɓace Dady yace, “Jawaad!!....” saurin ɗaga masa hannu Jay yayi batare daya kallesa ba. “Karkai saurin harzuƙa, muje waje muyi maganar”. Ɗauke kai Dady yayi kamar bazai sake tankawa ba sai kuma miya tuna oho ya nufi ƙofar fita yana jiyo kukan Momy dake sukar masa zuciya. Tashi Jay yay shima ya fice baiko kalli inda ƴan gidan nasu sukeba balle ya nuna yaji ihun kukan Momy dana Mama Atika.
             A can gefe inda babu mutane ya hango Dad nata kai kawo ransa a ƙololuwar ɓace, Jay yay ɗan murmushi ya ƙarisa. Kallonsa Dad yay ya ɗauke kansa, “Jawaad!! Tun muna ƴar kunyar juna ka saka wannan ɗan iskan yaron ya sakarmin yarinya ta”. Murmushi Jay yayi da tura hannunsa ɗaya aljihu ɗaya kuma ya shafi kumatunsa da gashin saje ke kwance kaɗan saboda yana askewa, “Miyasa kukai tunanin kashesa ne zai baku mafita domin farin cikin ƴarku?. Irin wannan raɗaɗin da kakeji a yanzun, ita kuka shiryama taji mafiyisa Dad, Miye dalilinku na janta jikinku bayan baƙwa buƙatar ta raɓu jininku?........”     
          Dady ya kallesa da ɓacin rai sosai ya katsesa da faɗin, “Ya ina maka magana akan Mamana kanamin wata banzar magana taka mara tushe?”. Haɗe fuska Jawaad yayi da tura ɗayan hannunsa aljihu cikin ƙoƙarin danne nasa fushin yace, “Banason mu bama juna wahala, dan inhar muka kai ga haka komaima zan bankaɗo babu ruwana, dan haka mu tsaya iya haka ɗin kamar zaifi sauƙi. Batun Hudah na riga na gama da wannan matsalar yanzu tsakanin kune ku da sirikinku. Lokaci yayi da zaku nuna gajiyawar da baƙwaso a gareta na bakomai zaku iya bata ba, ALLAH shike bada komai ga wanda yaso a lokacin da yaso ba mutum ma

i barci, mai mutuwa, mai mantuwa ba. Koda yake, wannan bashi bane matsalata. Minene Ya kai Qaseem China kuma?!”.
         “Kai Jawaad!! Tsagerancin naka da su Alhaji Nasiru ke faɗa har yazo kaina nima kenan? Minene matsalarka ko alaƙarka kuma da barin Qaseem ƙasar nan?, Qaseem fa ɗanane, babu kuma wanda ya isa ya sakani koya hanani a kansa, itama bilkisun ba tsoro yasa na bar maka itaba dan inada ikon hanaka auren nata tunda ɗiyar ƴar uwa tace, a hannuna kuma ka ganta. Niba sa'an yinka bane, ka kama kanka kajiki”. Ya ƙare maganar da fara tafiya zai bar wajen.
         Jay dake binsa da kallo yay murmushi, “Tabbas kanada iko da ita fiyema da hakan, kuma har gobe ita kallon uba take maka dan ta baka dukkan yarda kai da ahalinka, babu wani laifinku da take kallo laifi sai dai kuskure. Haka take komai nata irin na masu ƙyaƙyƙyawar zuciya ne, tana ƙyautatama kowa zato musamman wanda ya nuna tausayinta saboda a irin rayuwar data tsinci kanta ciki, Dady ka daina tunanin har yanzu al'amarin a rufe yake, na tanadi hanyoyi masu yawa dazan bankaɗo komai harda na Qaseem da kukai ƙoƙarin rufewa dan ina bibiyarsa kuka turasa China”.
            Juyowa Dad yay daga tsayuwar da yay tun fara maganar Jay. Idanu suka zubama juna na kusan mintuna biyu kafin Dady yay wani murmushi yana girgiza kansa. Batare da yace komaiba ya juya ya tafi.
        Da kallo kawai Jay ya bisa har ya shige, ya lumshe idanu da furzar da huci mai zafi daga bakinsa, batare da yay ƙoƙarin sake komawa cikiba ya nufi motarsa ya bar asibitin

           A ciki kuwa tunda ɗan fir'auna ya shiga da maida ƙofar ya rufe babu wanda ya sake jin ɗuriyarsa balle sanin mi yayi a ciki har saida Dad ya koma ciki da kusan mintuna biyar sannan ya fito yana wani ɗan iskan washe baki kamar gonar audiga. tsayuwa yay ya gama kallesu a ɗage sannan ya wuce batare da yacema kowa komaiba, sai wani rangaji yake irin na tsageru tamkar wani bishiyar giginya.
       Babu wanda ya iya cewa uffan dan har ransu tsoronsa sukeji, sai da ya kai ƙofa sai kuma ya juyi da sauri, “Af kunga nayi mantuwa zan wuce, Surukina inafa da magana da kai a ina zamu haɗu mu tattauna ta?”. Kafin Dad yay magana Uncle Sulaiman yace, “Haba yarona, hakan duk bai kamataba kaji, koba k.......” Da sauri ɗan-fir'auna ya katse Uncle Sulaiman cikin ɗaga masa hannu da faɗin, “Nifa ka ganninan duk tsagerancina ina girmama masu mutunci, kai Uncle ɗin Ogane mai daraja babba, dan ALLAH na roƙeka ka zama ɗan kallo, dan ko takalmin Oga bazan so na takaba balle kai Uncle ɗinsa”. Uncle Sulaiman ya jinjina kansa kawai batare daya ƙarasa abinda ya faroba, sai dai a ransa yana mamaki. Juyawa ɗan fir'auna yay yana faɗin, “Duk da ni mutumne mai kunya da baya son yawan shiga gidan surukai Zanzo gida na sameka surukina”.
       Kallo kawai suka iya binsa dashi harya fice tamkar wasu wawaye babu wanda ya iya sake tanka masa.  

___________________________

                  Ɓangaren su Bilkisu kam sunsha firarsu cike da nishaɗi kasancewar sun daɗe basu sami damar irin wannan haɗuwar ba, abincin da driver ya kawo daga gidan Ummah babba suka ci, dan Nabeelah ƙin biyosa tayi dan tazata Jawaad na gidan. Sai dai batasanma yana tafe zuwa gidan nasu ba, dan bayan sallar azhar can ya nufa. Tana falo zaune tana kumburin fushin Ummah tace taje tai kitso yay sallama. Ai da wani shegen gudu ta kwasa sai ɗakinta ta garƙame ƙofa. Hakan datai ya saka kowa fahimtar laifi tai masa.
      Zama yay suka gaisa da Ummah tare da musu godiyar hidima da gajiyar taro, Aunty Batool ma ta gaidashi da tambayarsa bilkisu. Anan yaci abincin rana suka ɗan tattauna da Ummah akan abinda ke faruwa, kuka rurus Ummah keyi na farin ciki da al'ajabi, kai ita kanta tana mamakin irin yanda takejin Bilkisu har cikin jinin jikinta da ɓargo, san nan tana hango abubuwa da yawa dake mata kamanceceniya da jininta tattare da Bilkisun amma tarasa wacece?, wato jini ya wuce gaban wasa duk inda yake. Tace, “Jawaad bazan iya haƙuri ba gobe idan ALLAH ya kaimu zaka ganni a gidanku”. Murmushi Jay yayi, “To ai Ummah itama bata saniba, bamason ta san komai yanzun har sai mun bincika sauran

abinda ke faruwar tukunna, dan kinga al'amarin yazo da ruɗani a ciki”. Shiru Ummah tai na wasu sakanni, cikin sauke ajiyar zuciya tace, “Hakane kuma Jawaad, rashin faɗa matan yanzu yanada amfani, dan ko ƴan gidanku karmu bari su sani yanzun sai mun gama sanin komai mu kanmu”. Jay yace, “Insha ALLAHU Ummah bazasu sani ba”.
       Baibar gidan Ummah ba sai kusan ƙarfe uku na rana. Daga nan gida Ummah ƙarama yaje itama, itakam harma tafi Ummah Babba shiga ruɗani, saboda ita mutumce mai ƙarancin juriya akan farin ciki ko ɓacin rai, duk wanda ta tsinci kanta a ciki saika ganesa tattare da ita. itama dai ya jima anan suna tattaunawa, dan saida akai sallar la'asar sannan ya baro gidan.
           Gida ya nufa dan a gajiye yake ga barci yanaji sosai cikin idanunsa. Dai-dai traffic light ta tsayar dashi idonsa ya hango masa ɓaleru cikin mota, wanda ke a bayan motar ya kalla ya ɗauke kansa, sai kuma yay saurin sake kallon motar. Abinda ya faɗo masa a raine

1 Comments On KWAI CIKIN KAYA
avatar
zainab-nasir

1 year ago

Reply

Muna jin ddin yanda kuke ilimantar damu

Please Login or Register in order to submit comment