Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Ali aka buƙaci ya kawo, shi a take ya bada na Mamansa da ƙanwarsa, da ɗansa na biyu, sai dai kuma nace bai isa ya bada na ƴar uwataba (Mom), wannan dalilin yasa ƙungiya tai masa lamuni akace ya bada na wata matar idan yanada ita, kokuma ya ƙara aure, sai kuma jinin ƴarsa babba mace shima. Hankalinsa ya tashi dan yana tsananin son Shahudah, a lokacinma batafi shekara huɗu da wata bakwai da haihuwaba, yayta roƙo da neman alfarma akan zai canja da wani. Da farko Bokanya bata amince ba, sai bayan kusan kwana biyu dayin hakan ta bashi umarni akan ya auri Rahmah, hakan shine kawai zai kawo sake rufuwar asirinmu, sannan idan Shahudah ta girma yay ƙoƙarin haɗata aure da Jawaad, nanma zamuci moriyar hakan, indai ya aikata haka ƴarsa zata tsira da matarsa, idan Rahmah da ta haihu sai ya bada duk abinda ta haifa madadin Shahudah. Da wannan shawara da umarni yay amfani, na shige masa gaba ya samu auren Rahma ta wajen mahaifinta, dan lokacin Mama Maryam ta rasu. Tabbas badan baƙin asirin da mukaima Rahma ba bazata taba yarda ta auri Ali ba, duk da kuwa abinda ya faru kusan shekara bakwai a lokacin, amma  bata da wani zaɓi, dan ta ko'ina mun gama ƙulleta.
     Kafin auren Rahma da Ali ya tattara su Humaira ya bar ƙasar dasu, wannan duk yana cikin dabarun karta tada hankalintane akan za'ai mata kishiya, shi kuma Ali yana matuƙar sonta bayason tashin hankalinta. Sai da ya maidasu da kusan wata biyar sannan akai bikin, lokacin Bilkisu ta gudu daga gida saboda asirin da muka kuma tafka mata aka kai gidan Alhaji Kokino, burinmu haukanta ya nisan tata da gida har abada koda ƙasar waje ne ma taje. Badan Ali nason Rahma ya aura ba. bayan bikinsa da Rahmah itama ya ɗauketa daga ƙasar ya maidata Ghana da zama duk a cikin shirinmu, sai dai kuma acan ɗin saita gamu da wata ƙawa data tsaya tsayin daka wajen taimakonta da addu'oi ganin kamar batama cikin hayyacinta a rayuwar aurenta da Ali. ba komai yaja hakanba sai ganin yanda Ali ke gallaza mata, bata taɓa yunƙurin barinsa ba ko faɗama ƴan uwanta, sai dai tai kukanta ta share hawaye. gashi tana zuwa ta samu ciki kuma. Ganin matarnan zata buɗe mana aiki ya sake ɗakkota ya maido ta nan ƙasar, inda mukai zaman dakon haihuwarta....” Kuka ya sarƙe Uncle Nasir ya kasa cigaba, sai Dad da shima ke kukanne ya cigaba da faɗin,

__________________
ZAFAFA 2021
_______________

             Masoya naku taurarinfa sun sake dawowa da sabon salo a 2021.

       Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
  
          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO

TEAM#ZAFAFABIYAR🔥

________________

            “Tabbas na zalinci Rahama, dan a zamana da ita bata taɓa jin daɗiba koda na awa ɗaya, daga hantara sai ƙyara da gallazawa a tsakanina da ita. Bantaɓa bata ƴanci na matar aure ba. Abincima nakan batane tamkar wata dabbar da nake turka, kullum cikin roƙona take daban haƙuri amma ban taɓa saurarentaba, tunda cikinta ya cika watanni bakwai ta fahimci manufata a kansa sai hankalinta ya sake tashi, zuciyarta ta bushe, ta daina kuka akan dukkan gallazawar da nake mata, ta maida hankalinta wajen addu'oi akan ALLAH yakare mata cikinta, ƴan uwanta duk wanda yazo wajenta ko ƴan uwana roƙonta shine su tayata addu'a ta haihu lafiya. Daga randa na fahimci haka saina hana kowa shigowa gidan har ƴan uwana, na saka maigadin da babu wanda yake bari ya shiga saida izini na. Hakan ya ƙara saka Rahma a ƙunci da damuwa, nikam ko'a jikina ban taɓa jin tausayintaba, burina kawai ta haihu na samu cikar burina. A wannan halin cikinta ya cika watanni tara da wasu kwanaki, haihuwa kawai muke saurare, bana yarda nai tafiya mai nisa dan karta haihu bana nan, dama gashi na hana kowa shigowa gidan, na kuma ƙulle bakunansu da asiri har mahaifinta da ƴan uwanta. A wani dare ta farka da naƙuda, babu ko tausayi nazo kanta na tsaya, duk taimakon data buƙata naƙi yimata shi, haka taita wahala har wayewar gari bata haihunba, tunanin kar abinda zata haifamin ya mutu nayi asara ya sani shiryawa na nufi wajen bokanya ni da Nasiru, ko zamu samo wani taimakon da zamu bata ta haihu. Lokacin da muka dawo sai muka isketa ta haihu, sai dai babu ɗan sai ita kaɗai. Hankalinmu ya tashi, muka shiga mata tambaya sai tahau dariya da faɗin, “UBANGIJI baya zalinci ga kowa sai dai bawa ya zalunci kansa, jinin jinina yafi ƙarfinku azzalumai, ALLAH ya cire ƙwai a cikin ƙaya sai dai ku mutu, a yau kuma ALLAH ya tunatar dani duk abinda kuka binne akan yah Abdull, babu shakka kuma saina tona muku asiri, sai duniya tasan kuɗin su wanen........”
       Wani wawan mari na ɗauke fuskarta da shi tare da buga kanta a bango har saida ta suma, kafin na shureta da ƙafa ta farfaɗo, a hakanma bakinta bai mutuba, gaya mana duk maganar da tazo bakinta takeyi, hakanne ya harzuƙamu muka kwasheta zuwa wajen bokanya. A can ɗinma bakinta bai mutunba, ta dinga faɗa mana jininta shine jini mafi tashin hankali da zamu salwantar, “Daga wannan ranar bazaku sake samun kwanciyar hankaliba azzalumai, insha ALLAHU wataran sai Ƙaddara ta haɗa Jini da jini sun addabi jininku, Jawaad da ɗiyar dana haifa da izinin UBANGIJIN al'arshi sune zasu zamewa rayuwarku barazana da tashin hankali tun anan duniya, kuma in ALLAH ya yarda sune sanadin tonuwar asirinku a duniya, waɗanan kwayayen guda biyu sai sun kunna wuta bisa kanku ku ƙayoyi kun ƙone ƙurmus kafin kuje ga UBANGIJI shima yay muku nasa hukuncin. Sai kun tuna wannan ranar da wannan furucin da izinin ALLAH. Daga yanzu ku zauna zaman saurare da cikar lokacin da ƘWAI zai fita a cikin ƘAYA ta inda bakuyi zato ko tsammani ba. Domin biyune zasu ɗau fansa tare da ɗunbin al'ummah”.
      Wannan shine furucin Rahma na ƙarshe a garemu, muka aikata mata mummunan aiki tamkar yanda mukaima duk wanda muka salwantar. Duk da kuwa maganganunta sun shigemu, kuma tabbas sunyi tasiri a zukatanmu. Iya bincike bokanya tayi ko zata samo inda abinda Rahama ta haifa yake amma hakan ya gagara, abindama take gani jaririyar ta mutu, tun zukatanmu na rawa akan hakan har muka cire abin a ranmu muka cigaba da harkokin gabanmu, ciki harda aƙidar fyaɗe wa ƙananan yara domin amsar budurcinsu kawai kamar yanda bokanya ta sharɗanta mana. Rayuwa ta shuɗa, duniya ta samu a garemu, dan kuwa dukiya ta zauna ga kowanmu, duk abinda bokanya ta sharɗanta mana bi mukeyi, musamman ma ni da bana tsallake komai duk dan gudun kar bokanya tace na bada jinin mamana (Shahudah), haka kawai ALLAH ya jarabceni da matsanancin sonta fiye da suran ƴaƴana. gashi kuma bokanya tace min akwai nasarata tattare da ita, dama ƙungiya baki ɗaya, amma hakan bazai tabbata ba sai anyi aurensu da Jawaad. Da wannan damar mukai amfani wajen jan Jawaad jikinmu, duk da ita Humaira dai batasan ai nahin manufar ba, hankalinmu bai kwantaba har saida akai aurensu, sai dai kuma baiyi nisaba komai ya lalace, a lokacin mu kaɗai mukasan a irin tashin hankalin da muka tsinta kanmu, duk da daga baya bokanya tace mubarsu zatai wani aiki a kansu, amma a aura masa wata matar cikin ƴaƴan family ɗinsu, hakanma zai taimaka mana, sai dai sam Jawaad yaƙi hakan, mun buga ta kowanne fanni babu nasara, tun daga wannan lokacin komai na ƙungiyarmu ya ringa samun tangarɗa da ruɗani, ciki harda shigowar wani maharbi rayuwarmu, sai dai daga baya shi munyi maganinsa ta hanyar salwantar da rayuwar duka iyalansa dashi kansa. Ƙwatsam muna a wannan ruɗanin kuma sai ga Bilkisu ta shigo rayuwata a bazata, inda naci karo da ita a gidan ƴar uwata. Banyi sakaciba na ɗakkota, a washe gari kuma nakai sunanta ga bokanya kamar yanda mukeyi akan budurwar da duk muke buƙatar budurcinta, sai dai kuma Bilkisu sai tazo da banbanci ga sauran, dan bokanya tamin alƙawarin inhar na mallaki budurcin Bilkisu na cika dukkan sharuɗan ƙungiya, dukiyata zata sake haɓaka, zan kuma samu nutsuwa akan komaina. Tamin alƙawura da dama game da yarinyar, sai dai kuma komai bai yuwuba, dan yarinyar tana tattare da wasu sirruka da muka gaza ganewa har zuwa yau, ta zama sanadin rushewar abubuwa masu yawa a garemu ciki harda aurenta da Jawaad, tashin hankalin da muka fahimci yana tunkaromu a dalilinta yasa muka sadaukar da jininta ita da Jawaad.........”
     
__________________
ZAFAFA 2021
_______________

             Masoya naku taurarinfa sun sake dawowa da sabon salo a 2021.

       Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
  
          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO

TEAM#ZAFAFABIYAR🔥

________________
    
       “Babban sirrin dake tattare da ita shine amincewar UBANGIJI game da furicin mahaifiyarta game daku”.
          Wata murya ta bada amsa ga Dad a bazata. Gaba ɗaya falon suka juya suna kallon mai maganar cike da mamaki da al'ajabi. A bazata Bilkisu ta miƙe zaram tana share hawayenta, jikinta na wani irin tsuma da rawa tace, “Inna! Baba! Firdausi da gaske kune? Kodai gizon da kuka saba yiminne?”.
    Fuskar Baba cike da murmushi yace, “Mune ƴata ba gizo muke miki ba, mune tsaye a gabanki bayan rabuwar ƙaddara ta tsahon shekaru, na godema UBANGIJI daya sake haɗamu Bilkisu, na godema ALLAH daya kawoni wannan ranar dazan sauke nauyin da ɗan uwana abokina ya ɗauramin tsahon shekaru”.
     Da gudu Bilkisu ta nufesu ta rungume Inna da firdausi tana mai fashewa da matsanancin kuka, suma kuka suka sanya harda Baba. Mai martaba ne yay gyaran muryar da ta sakasu yin tsuru lokaci guda, cikin nutsuwa yace, “Su wanene ku? Mi kuma ya kawoku nan?”. Kafin a cikinsu wani ya samu damar bada amsa Jabeer dake bayansu tsaye yace, “Ranka ya daɗe suna tare da magana mai muhimmanci, tun da sassafe suke a gidan Jay suna jira dan suga matarsa, duk korar da maigadi yaymusu basu tafiba. Kasan yanayin da ake ciki, shinefa drivern sa ya kirani ya sanarmin, da naje bayanin da sukaiminne yasa na gamsu na kawosu nan”.
    Umarnin ƙarasawa ciki aka basu, sai da suka zauna da mika gaisuwa Bilkisu na maƙale da inna sannan takawa ya bama baba damar yin bayani akan abinda ke tafe da su. Baba ya sauke nannauyan numfashi yana mai duban Bilkisu da Inna ke sharema hawaye, sai kuma ya duƙar da kansa ƙasa ya fara magana da rawar murya. “Sunana Abdullahi, babban amini ga malam Adamu makaho. Abotarmu ta farane tun lokacin daya kama haya a gidan da nake, tun muna iya gaisawa da mutunci sama-sama tsakanin iyalanmu har muka zama aminai, matanmu ma haka. Kamar yanda na daɗe ban samu haihuwa ba Adamu ma hakane, cikin hikimar ALLAH sai ga ciki a jikin matanmu kusan lokaci guda ni da shi. Matata itace ta fara haihuwar ɗiya mace, ga tanan (ya nuna Firdausi) dan dama ta riga matar Adamu samun ciki da kusan watanni biyu zuwa uku. Kamar yanda al'adarmu take matata ta tafi wankan jego ƙauye, bayan tafiyarta da kusan wata ɗaya matar Adamu ta wayi gari da naƙuda, hankalinmu ya tashi dan ba watan haihuwarta bane, a haka muka ɗauketa zuwa asibiti, ƴan kuɗin sana'arsa ya ƙundume ya miƙa akai mata duk abinda ya dace, sai dai daga ƙarshe likita yace sai an mata aiki, dan ɗan dake cikinta ya ruɓe, ma'ana yadai mutu ma, barinsa itama zai zamarwa tata rayuwar barazana. Hakan ba ƙaramin tada mana hankali ya sake yi ba, gashi ƴan kuɗaɗen hannunmu sun ƙare, kuma suna buƙatar kuɗi kafin su mata aiki. Adamu ya barni a asibiti ya hau acaɓa ya kaisa can anguwarsu gidan iyayensa dana sani, dukda dai ya sanarmin mahaifiyarsa aka haifa a gidan (Alokacin Adamu na gani da ido ɗaya fa) sai dai kuma bai wuce awa biyuba sai gashi ya dawo rai a ɓace alamar bai samo komaiba. A gabana ya labartama Asiya komai, dukda halin ciwo da take ciki saita kwantar masa da hankali, tace yaje wajen yayanta Alhaji Ali (Dad) tasan zai taimaka musu. Baiyi musubu ya jani muka tafi tare, gidane katafaren gaske mai ƙyau da gate, a lokacinma duk gidan da kaga gate to lallai maishi ya tara, munta ƙwanƙwasawa amma ba'a buɗe mana ba, Adamu ya tura ƙofar cikin haushi sai gata ta buɗe a bazata, sai da muka lalleƙa babu kowa sannan muka shige cikin gidan batare da tunanin komaiba. Munta sallama a ƙofa nanma dai bamuji motsin kowaba, sai wani irin nishi da gurnanin kuka. Babu tunanin komai Adamu ya nema cusa kansa, na riƙesa ina girgiza masa kai akan karya aikata haka, tunda ba gidanmu baneba, kuma akwai mace a ciki. Hankalinsa dake a tashe na halin da asiya ke a ciki yasa bai saurareniba, ya fisge hanunsa ya shige ciki babu ko sallama. Duk da a tsorace nake banida zaɓin daya wuce bin bayansa nima. Sanda muka shigo cikin falon sai mukaji kukan ya yawaita, gashi ana kukan ne da addu'ar fatan neman ɗauki daga ALLAH, Adamu ya kalleni na kallesa, sai kuma duk muka kalli ƙofar da muke jiyo kukan. Kukan jinjiri ya sakamu dawowa a hayyacinmu batare da mun shiryaba, Adamu ya matsa jikin ƙofar da sauri yana magana. Daga ciki aka amsa da faɗin “ko wanene ya shigo dan ALLAH” kamar bazai shigaba sai kuma ya afka kansa tsaye, duk kiransa da nake famanyi bai saurareniba. Haka nabisa na leƙa sai dai ban shigaba, daga ƙofa na hango mace durƙushe tana naɗe jariri dake cikin jinin hauhuwa a zane, ita kanta inda take durƙushen duk jinine. Adamu na tsaye hankalinsa a tashe yana kallonta. Ɗagowa tai ta miƙa masa jinjirar jikinta na rawa, sai kuma tai cak tana kallonsa, kallo irin na kamar na sanka kokuma ina nasanka? Da rawar baki tace, “Mai kama da Baba!”.  Sai kuma ta girgiza kai da sauri tana hawaye. “Wannan ba lokacin tunanin hakan baneba, bawan ALLAH koma miya kawoka gidannan nasan UBANGIJI ne ya aikomin kai danka taimaki wannan baiwa da batasan komai ba sai iskar duniya data shaƙa a yanzun. Dan ALLAH ka ɗauketa, ka nisantata da gidannan, itaɗin ɗiyatace, mijina ke neman kasheta saboda matsafine, kaimin alfarmar saka mata suna BILKEESU, karka taɓa faɗa mata bakai ka haifetaba dan girman ALLAH har sai takai shekaru ashirin a duniya, ka binciki ɗan gidan tsohon shugaban ƙasa daya rasu, JAWAAD ABDUL-AZIZ ka haɗata dashi, ka sanar masa suɗin ƴan uwan junane, ɗiyar Rahama ƙanwar mahaifiyarsa Bilkisu ce. Suyi ƙoƙari su haɗa hannu wajen binciken mai gidannan da duk abokan da yake mu'amula dasu, babu isashen lokacin dazan maka bayani aka kaina da abinda ya faru, amma nasan komin daren daɗewa lokaci zai fiddo komai dan sharri baya ɓoyuwa a duniya. Ka ɗauki wancan akwatin akwai kuɗi da kayanta a ciki na baka halak malak, dan ALLAH ka bata tarbiyya irin ta addini, karka bar rayuwarta ta tarwatse da ruɗanin duniya, ka faɗa mata ina tsananin ƙaunarta fiye da komai dana mallaka a duniyarnan. Kai maza ka fita, suna gab da dawowa, idan suka iskoka zasu halaka ka da ita da ni baki ɗaya, ni kuma bana fatan hakan”. Ta ƙare maganar da wani irin kuka mai cin rai da zuciya. Motsin buɗe gate da mukaji ya sakamu fita da gudu, kafin mukai ƙofa mukaji ana shirin buɗewa, wani ɗaki muka shige da gudu muka ɓuya muna leƙen masu shigowar ta taga, a gaban idanmu Wannan (Uncle Nasir) da wannan (Dad) suka shiga ɗakin da matarnan take, duk maganganun da sukai ita dasu muna saurarensu, har lokacin da suka fita da ita daga gidan. Da ga ni har Adamu kuka muke rurus, sai dai bamu da wani ƙarfin ikon sakawa ko hanawa, sannan muna son cika mata alƙawarin fita da ƴarta daga gidan cikin aminci. Sai da muka tabbatar motarsu ta fice a gidan sannan muka fito muma muka fice da gudu, cikin amincin ALLAH mai gadin gidan yanzunma bai ganmuba ya shige cikin ɗakinsa kamar ɗazun da muka shigo yana ciki.
     Da kuɗin da matarnan ta bama Adamu akaima Asiya aiki, aka cire ɗanta mara rai, bayan an kamala mata aiki aka kaita ɗakin hutu. Adamu yakai jaririya da ya roƙa wata nos ta gyara ya kwantar kusa da Asiya. Bayan ta farfaɗo cikin dare bai ɓoye mata komai game da bilkisu ba, ita kuma saita amsa da daraja ta rungume tana kuka, dan koba komai ai ɗiyar ɗan uwantane. Abinda kawai Adamu ya ɓoye ga Asiya shine ɗan uwanta matsafine, bai faɗa mata wannanba, ya kuma roƙeni na ɓoye wannan sirrin dan ALLAH har sai lokacin da jaririya Bilkisu takai mizanin shekarun da mahaifiyarta ta roƙa kafin mu bayyana komai ga kowa. Na masa alƙawari da karɓar amanarsa, na rufe wannan zance a raina tamkar yanda shima ya rufesa ga kowa nasa suka cigaba da rainon bilkisu, har ALLAH yasa takai shekarun girma, sai dai kafin lokacin da Adamu ya cika alƙawarin sanar mata ita wacece ALLAH yay masa rasuwa sakamakon bigesa da mota tayi, itama kuma Asiya ALLAH yay mata rasuwa kafin shi. Musan ƴan uwan Adamu bazasu ɗauki Bilkisu ba, dan sun saka wasiwasi a ransu game da ita tun tana jinjira. Na ɗauki Bilkisu na cigaba da kulawa da ita kamar yanda Adamu yayta roƙona gab da numfashinsa zaibar jikinsa. Sai dai kuma na gaza cika alƙawarin lokacin da taƙadin yaron mai gidanmu ya shigo rayuwar gidan............” ya ƙarashe labarinsa da zaman Jazuga a gidansu, har faruwar komai na abinda bilkisu tai musu, da maidasu ƙauyensu da Alhaji Lado yayi, tare da gargaɗi da baza abokan Jazuga a ƙauyen suyi gadinsu. Doguwar jiyyar Firdausi da sukasha wadda tai kamar bazata rayuba har tsahon shekara kusan guda kafin ta warke ayi bikinta da ɗan uwanta, gashi a yanzu sunada yara uku, Musa (Fharhan), Abbas, sai bilkisu da firdausi taima bily takwara saboda ƙauna da soyayya haɗe da ɗunbin bege a gareta.

       Jin wannan labari daga bakin Baba ya saka falon sake ruɗewa da koke-koke, Bilkisu kuwa data gigice tamkar wadda ciwon hauka ya sama lokaci guda ta miƙe zaram tana nuna Dad jikinta na wani bala'in karkarwa. “Baba kana nufin shine Mahaifina?”.

      “Tabbas Bilkisu shine mahaifinki?”. Ai ganin Bilkisu kawai akai ƙasa wanwar ta sume. Dad kuma ya fashe da wani irin gigitaccen kuka da ƙwalla ƙara, ya shiga buga kansa jikin bango yana ihu maiban tashin hankali da faɗin “Tabbas Rahmah maganar ki ta zama gaskiya, Alaƙar ƙaddarar jiji dake cikin jini ta tabbata.....”. Ƙoƙarin riƙesa ƴansanda sukeyi, yayinda can kuma aka rufu kan Bilkisu ciki harda Jawaad daya ƙwace daga riƙon da Alhaji Babba yay masa.

         Bayyana muku tashin hankalin da waɗanan mutane ke a ciki a wannan lokaci zaici tsahon lokaci bamu gamaba, komai ya sake hargitsewa da ruɗewa, dole ƴan-sandan dake a waje suka shigo cikin gidan tare da dogarawan sarki wanda shi yama rasa abin faɗa tsabar mamaki, a da gani yake babu wata ruɗaɗɗiyar rayuwa irin tasa, sai a yau yaga wadda tafi tasa muni da tashin hankali.
            Da ƙyar aka iya fita dasu Dad daga gidan, suna kuka da roƙon a yafe musu amma babu wanda ya sauraresu, sai ma tsinuwa da sukesha daga bakin kowa harda ƴaƴansu kansu da matansu. An shiga ƙoƙarin yayyafama waɗanda suka suma ruwa harda Shahudah da Bilkisu, da Mama Atika. Wadda itakam da alama ma dai faɗuwar da tayi tazo da sakamakon paralysis, dan ta gaza motsa komai nata sai ido takebin mutane da shi kawai tana kuka.
______________

          Komai fa ya sake rikicewa, gari ya ɗauki magana da ba'asan tayaya ta fita daga gidan Alhaji babba ba, sai daga baya aka fahimci camera aka saka jikin su Dad da ba'asan wanene ya sakaba, ta naɗe komai daya faru a gidan Alhaji babba, lokacin da aka maidasu office kuma a take aka fidda komai ta kafafen yaɗa labarai.
        Lokacin da takawa ya baro gidan Alhaji babba zuwa inda ake jiransa zasuyi meeting da ƙyar suka kai saboda hargitsewar da garin yayi, matasa ta ko'ina sun fara fitowa zanga-zanga da makamai akan sufa sai an basu su Dad sun kashe. Kamar wasafa saiga zanga-zanga ta fara faɗaɗa, dan harda ƴammata da zawarawa a cewarsu suma sunabin kadin haƙƙin ƴan uwansu dasu Dad suka lalatama rayuwa ta hanyar fyaɗe. Idan ba'a basu su Uncle Nasir ba zasu bankama station ɗin da aka ajiyesu wuta.
        Sai kuma rukunin magidanta da tasu zanga-zangar ta ɗauki manufa akan kisan tsohon shugabanƙasa Abdul-aziz Yousif Tafida, a cewarsu sumafa sai sunbi kadin jinin adalin shugabansu. Tofa jama'a sun fusata ainun, kowane titi ka zagaya mutane ke tittiɗowa zuwa station ɗinsu Jawaad da aka ajiye su Alhaji Kokino, tun jami'an tsaro na ƙoƙarin kwantar da tarzomar dake nemans harfa al'amarin ya nema gagararsu sai da aka kawo wasu jami'an tsaron kala-kala. Amma duk da haka al'amarin ya gagara. daga ƙarshema sai suka zagaye hall ɗin dasu Takawa sukai zaman meeting, acewarsu su fito su bada damar a fiddo musu dasu Kokino kokuma su haɗa dasu. Dan bazasu taɓa yarda sai ankai su Dad Kotu ba, su duk duniya basuga alƙalin da zai iya yima su Dad shari'a ba sam. Gara kawai su kashesu a haɗu a kotun UBANGIJI kawai.

★★★★★★★

         Har dare gari yaƙi lafiya, tamkarma ƙara ƴan zanga-zangar akeyi. Jawaad na gida tare da ƴan uwansa dake cike da ruɗani da tashin hankali wannan al'amari har yanzu kira ya samesa daga office.  Duk yanda yaso ƙin fitar Alhaji babba sai da ya takurashi, acewarsa babufa yanda zasuyi, wannan al'amarin su barma ALLAH kawai shine zaiyi maganin waɗannan mutanen bawai ƙarfinsuba ko dabararsu. Haka ya fita jikinsa duk babu wani daɗi, ya sumbaci goshin bilkisu daketa barci yana haɗiye hawayen da suka cika masa ido, tausayin kansu yakeji daga shi har ita, musamman ma ita da nata al'amarin yazo a yanda basuyi zato ko tsammaniba, kenan Shahudah da Bilkisu ubansu ɗaya fa kenan? Bilkisu jininsa ce, jini mafi kusanci da muhimmanci a garesu, jinin wadda take da daraja a garesa, wadda ta yarda ta rasa ranta da farin cikinta a dalilin salwantar da mahaifinsa.
         Bai iya jan motarba sai Hafiz ne yazo har gida ya ɗaukesa, shi kansa halin da yaga garin yake ciki ba ƙaramin sake tada masa da hankali al'amarin yayiba, dare harya rufa amma mutane basu da niyya komawa gidajensu. Da ƙyar motarsu ta samu hanyar shiga station ɗinsu.
              Sun sami su Sir Ahmad cikin tsananin tashin hankali da damuwa, sune sukaimasa bayanin yanda akai komai ya fita har jama'a sukayo wannan gangamin na farautar rayukan su Dad. Ajiyar zuciya kawai Jawaad keta saukewa, tausayin su Qaseem da sauran iyalan waɗanan mutane kawai yakeji, dan haka ya bada shawarar a fita dasu Dad ta ɓarauniyar hanya abar station ɗin dasu zuwa cikin prison dasu ko hakan zaisa a samu sassaucin da hankulan mutane. 
       Da wannan shawara ta Jawaad akai amfani, sannan D.G da kansa

1 Comments On KWAI CIKIN KAYA
avatar
zainab-nasir

1 year ago

Reply

Muna jin ddin yanda kuke ilimantar damu

Please Login or Register in order to submit comment