Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a hannun yarancan da jininsu ya halatta ga Bakandamiya. Kurakuranka zasu goge a dutsen rubuta laifuka bayan ka cika alƙawuranka da jinin babban ɗanka Jariri kamar yanda yake a rubuce a sharuɗan Bakandamiya”.
        “Naji na karɓa yake mai biya mana dukan buƙatunmu”.
      “Hhhhhhhhhhhhhhhhh!!!!!!!!!!!!!!” ta kece da wata mahaukaciyar dariyar da ta saka duk saida muka toshe kunnuwanmu saboda yanda dajin gaba ɗaya yake amsawa bama gidan kawai ba, tanayi tana tsiyaya masa wani abu mai kama da jini a cikin ƙoƙon hannunsa. Da baya baya ya baro gabanta yana wasu surkulle da shi kaɗai yasan abinda yake faɗi, sauran na amsa masa.  
        Mamaki, tsoro, al'ajab da ruɗani duk suka saukarmin lokaci guda ganin Dad a inda tunanina ko tsammani bai taɓa raya minba, saurin ɗaura hannuna nai na rufe bakinna jin kuka na neman kufce min. “D... Da...Daddy!!”. na faɗa cikin rawar murya dana jiki ina mai matsawa jikin boss dake tsaye abinsa yana kallonsu Dad ɗin shi da su Oga Hafiz.
        Cikin matsanancin furgici Dad ya saki ƙoƙon hannunsa da kai dubansa inda yaji muryar da bai zatoba ta ambaci sunansa. Ido huɗu sukai da bilkisu da jikinta ke wani irin matsanancin tsuma.
     A take Dad ya zazzaro idanu waje cikin tsananin firgici da ruɗani, jikinsa sai wata iriyar tsuma ya keyi domin ganin wadda bai taɓa zato ko tsammani ba. duk da glashi ya raba tsakaninsu, bai gaza gane bilkisu da Jawaad ba harma da jin furucinta raɗam a kunnuwansa, dan basu da wani shamaki wajen iya jiyo maganar juna duk da akwai hilashin daya rabasu.
      Bansan sanda wani ƙarfi da zafin nama yazomin cikin jini da jiki ba na bigi gilashin wajen da ƙafa jikina karkarwa saboda wata irin mummunar tsanar sa ce ta saukarmin lokaci guda da ƙyamarsa.
       Sauran abokan shaiɗancin nasa da tuni suma sun mike suna kallonmu a cikin matsanancin firgici na alamun bazata a fuskokinsu suka shiga ƙoƙarin motsawa cikin rawar jiki dan neman kariya.
        Kafin suyi wani yunƙuri su Jabeer sun afko suma tare da su Ummie dake jiran umarni a waje. Zagayesu akai da bindugu, hakan ya tabbatar musu basu da wata dama kuma saina miƙa wuya........
      “Ƙassaaa!!!!” Boss ya faɗa a iya ƙololuwar hasala jijiyoyin jikinsa na sake mimmiƙewa. Durƙushewa sukai bisa gwiwoyinsu suna aza hannayensu bisa kawunansu alamar yin surrender.
      Ban samu dawowa hayyacina ba daga kallon al'ajabi da ruɗanin da nakema Dad sai da Wani irin ihu shaiɗaniyar matarnan da tayi ya shiga dodon kunnena. miƙewa tsaye tai da buga sandar hannunta ƙasa, a take ɗakin ya fara turniƙewa da hayaƙi, sake bugawa tayi, sai jikinta ya fara canja launi harda su Dad ɗin suma. ta ɗaga zata buga na uku nai wani wawan tsale na dire a gabanta na riƙe sandar. Bazan iya fassara muku mawuyacin halin dana shiga ba a wannan lokacin, domin tsafi gaskiyar maishi ne, abinda kawai nake iya jiyowa harmutsewar wajen da ƙarar harbe-harbe ta waje alamar musayar wuta ta ɓarke tsakanin wasu a cikin  jami'anmu da suke a waje da yaransu masu tsaron gidan.......

       Jawaad yay azamar nufar inda Bilkisu da matar nan ke riƙe da sandarnan, jikin bilkisu wani irin rawa yake da karkarwa ga zufa, amma dan taurin zuciya taƙi yarda ta sakar matar sandar.  ta gama fuskantar buga sandar nan da take sonyi zai iya zama kuskure ko halaka a garesu wajen baki ɗaya, kokuma wani siddabarun nasu zasuyi don son ƙuɓuta.
       Cikin tsawa Baba ƙaura ya dakatar da Jay da ya kai hannu domin bama bilkisu taimakon. “Karka taɓata, barta da ita!!”. Ya faɗa a kausashe yana nufosu, Hankalin Jay a tashe ya juyo yana kallon Baba ƙaura da girgiza kai, “Bazan iyaba bab....” kafin ya gama rufe baki baba ƙaura ya riƙo hannunsa, hakan yayi dai-dai da hankaɗa bilkisu baya da matar tayi, ta ɗaga sandar zata buga a ƙirjin bilkisun.

     Da sauri nai wani irin juyi sandar ta caki ƙasa, nasa ƙafa na taɗo tata ƙafar itama, baya tai, na bigi sandar da ƙafa itama tai sama na cafe cikin hannuna daga kwancen da nake.

         Wani irin mummunar amsa kuwwa ce ta karaɗe jejin lokaci guda, hakan ne ya saka ruɗani gasu Jay kowa ya shiga ƙoƙarin toshe kunnensa banda baba ƙaura da yasa ƙafa ya hankaɗa tukunyar kaskon wutar nan dake ci har yanzu ya kife a kujerar da matarnan take zaune ɗazun. Tamkar an tsaida ihun sai dajin yay cak lokaci guda kuma. Waige-waige su Jabeer suka fara dan su Dad gaba ɗaya basu a wajen sai matar kawai dake a kwance ƙasa inda bilkisu ta zubar da ita, saboda take mata ƙafa da Baba ƙaura yayi.
       Hankalinsu duk tashi yayi suka shiga leƙe-leƙen lungu da saƙo na cikin gidan hankulansu a tashe, sai dai abin mamaki babu ko ɗaya a cikinsu sai mutane da aka ringa zaƙulowa a cikin ɗakunan cikin hardasu Alhaji Babba da ke a cikin mawuyacin hali.
      Baba ƙaura ya cire jikkarsa ta fatar damisa ya ajiye ƙasa, da hannunsa ɗaya ya buɗeta ya ɗakko wani wani irin kibiya ta ƙarfe sai sheƙi take da walwali ya shaƙo wuyan matarnan ya miƙar da ita tsaye, watsa mata wani mugun kallo yay yana huci, a take ta ƙwalla kururuwa jikinta na rawa. “Barde kaga zan dawo dasu kaimin rai karka kassarani mai babban suna, na tuba nabika”. “Bana buƙatar tubanki shaiɗaniya, ai dama na faɗa miki nine ajalinki kokin manta na tuna mikii!!!!”. “Cikin rawar jiki take girgiza masa kanta, ya fincike manyan layun dake a wuyanta ya watsar ƙasa, a take ta zube a wajen tana fashewa da kuka. Cikin ƙwarewa da sararafa hannunsa guda ɗaya da dungulmin ɗayan ya ɗana kibiyar nan ta ƙarfe a kanta. Da sauri ta buga ƙasa da hannunta har sau uku sai gasu Dad dake can gefe rufe da wani jan ƙyalle sun bayyana.
       ‘Innalillahi wa'ina ilaihirraji'un yau muna ganin tsantsar tashin hankali da shaiɗanci, da a labaran tatsuniyoyi da fina-finai kawai muke jinsu. Koda ake cewa akwai matsafa a duniya da yankunanmu ban taɓa yardaba, a nawa zaton labarine kawai na ƴan shafawa labari shuni, ashe gaskene, ashe zan gani da idanuna, ashema harda jinina a cikinsu wanda na ɗauka uwa uba ma. Hawaye nake masu zafi da ƙunar zuciya, kaina juyamin yake gaba ɗaya dama duniyar kanta, tun ina fahimtar abinda ke faruwa har jina da ganina suka ɓace ɓat daga duniyar mutane, daga haka ban sake sanin abinda ke faruwaba kuma.

           Cikin zafin nama Ada ta tare Bilkisu da juwa ta ɗiba, a tsorace take kiran sunanta tana girgizata ganin batama numfashi gaba ɗaya. Aliyu ne yayo kansu yana tambayar lafiya, dan Jay tunda aka fiddo su Alhaji Babba yabar nan zuwa garesu.
       Ba Bilkisu ce kaɗai ta sumaba, Zuhrah tun cin karo da idanunta sukai da Abbanta ta sume, hakama Ummie ganin yayan mahaifinta tuni ta suma, sai cikin mutanen da aka iske a wajen da yawansu basa cikin hayyacinsu harda su Alhaji babba da basu wuci awanni da kawosu wajenba, dama ga tsufa kuma. Wasu daga cikin yaran su Dad an harbesu, harma da waɗanda aka kashe.
        Jejin ya hargitse sosai, bakajin komai sai ƙarar helicopters na sojoji dake shigowa cikin jejin saboda wayoyi da su Sir Ahmad suketa faman yi da amsawa. Dandanan sojoji da masu bada taimakon gaggawa harma da ƴan jarida dake cikin jami'an tsaron da su Qaseem duk suma suka iso. Cikin ƙanƙanin lokaci jejin ya sake harmutsewa da motsin mutane dana ababen hawa.
       Su Dad na durƙushe cikin ƙasƙanci daga su sai jajayen ƙyallayen kawunansu dana ƙugu da sukaɗan rufe jikinsu kaɗan, sai da jami'an tsaron da suka iso suka sauka sannan bisa alfarmar da General ya buƙata aka basu mayafai suka rufa, amma da Jawaad yace a haka za a fita jejin dasu har cikin gari domin sauran al'umma su gansu.

          Dajin fa kamar wasa sai gashi ya tara jama'a masu yawa kama daga manya-manyan jami'an tsaro, zuwa shugabannin ƴan siyasa da ƴan jaridu, dan babu abinda ke kai kawo sai helicopters da ƙananun jirage na yaƙi. Mutanen dake a cikin gari kansu sun fahimci ƙasar babu lafiya yau, dan kai kawon da helicopters keyi kawai ya isa amsa. yayinda kuma ƴan Jaridu suka fara nuna komai ta gidajen tv'n su live. Duk ta yanda manyan ƙasar sukaso kar hakan ta kasance basuci nasaraba, dan kuwa ƴan jarida sunada ƙarfin iko da ƴancinsu suma, balle kuma akan wannan al'amari mai tsananin saka ruɗani da al'ajabi ga duk mai sauraro bama kallo kawai ba.
       An shiga kwasar su bilkisu da suke a halin suma aka fara barin jejin dasu domin miƙasu ga likitoci su samu taimakon gaggawa, sai waɗanda suka sami harbi da gawawwaki da mutanen da aka samu an kawo harma da gawarwakin mutane da aka iske a wani ɗaki cikin freezer irin wadda ake saka gawarwaki a asibiti, dan gidan suna amfani da babban janareto dake basu wuta 24hours, duk wani abun more rayuwa kuma akwaisa a gidan hatta da ruwa.
        Su Jay ne keta kai kawo haɗa rahotanni har aka kammala kwashe mutane da gawarwaki da wasu kayan sirrika da ke a cikin gidan tas, basu baro jejinba sai bayan sallar la'asar, zuwa lokacin labari ya gama karaɗe lungu da saƙo na ƙasar harma da ƙasashen ƙetare, to abinka da manyan mutane da ake ganin mutuncinsu acikin manyan riguna da kuɗi suka saya musu.
      

__________________________

            
              Su Ummah basu farga da rashin su Jawaad a gidanba sai da su Nabeelah sukai kusan mintuna talatin da baro kitchen. Cikin ƙaguwa Umm-Anum ta kalli ƙannen nata cikin hausarta da bata fita da ƙyau yanzun tana faɗin, “Mariya wai ina ɗanku ya shige da matarsa ne? Nifa na ƙagu naga ubana, gara yazo ya kaimu ala bashshi sai su ɗakko su Abbun Anuwar ɗin daga can idan sun iso”. Murmushi Ummah babba tayi, ta kalli Nabeelah da suke kallon hotuna a wayarta da Anum. “K Nabeelah kiramin yayanku”. Cikin ƴar ruɗewa Nabeelah tace, “N...n.....na'am Ummah mi kika ce?”. “Ƙaniyarki nace dan gidanku” ta faɗa tana mata daƙƙuwa. “Kai Ummah ALLAH nifa banji bane ba”. “ALLAH ya shiryeki to, canai kije ki kiramin yayanku”. Jimmm tai na tunanin abinda zata faɗa, sai kuma dai ta miƙe ta fita, a babban falo ta tsaya tanata kaikawo, tarasa wacce amsa zata koma ta bama Ummah ne, tsoro faɗar gaskiya take kodan gargaɗin da Jay yay mata akan hakan”. Anuwar da ya shigo falon ya lallaɓo ta bayanta yaja jelar gashinta. A firgice ta juya zata ƙwalla ƙara na tsorata yay azamar rufe mata baki yana kallon sashen Bilkisu cikin ɗan zaro idanu. Sai da ya tabbatar ta nutsu sannan ya saketa yana sauke ajiyar zuciya da murmushi kan fuskarsa, “beauty ke matsoraciya ce gaskiya”. Cike da shagwaɓar data saba ta tura masa baki, “Yoni tsoro naji ALLAH, nazata Yayanmu ne”. Murmushi Anuwar yayi dake sake bayyana kamaninsa da Jawaad sosai yana ƙara narkar da idanunsa a kanta, “Kiyi haƙuri tam, halan laifi kikaima Yayan kike tsoron ku haɗu?”. “A'a ba laifi namasa ba, sai dai Ummah nason tajamin nayi masa yanzu”. ta ɗan wawwaiga kamar mai tsoron Jay ɗin ya ganta sannan ta juyo ga Anuwar da shima ke tayata waigen, ƙasa tai da murya cikin raɗa ta faɗa masa gargaɗin Jawaad. Sosai abin yaso bashi dariya, shifa tun a bikin su Jay ya fahimci Nabeelah akwai wautan autanci tattare da ita, “To ai kin kuma faɗamin yanzu, kenan bakiji gargaɗin nashi ba?”. Idanu ta waro waje sosai tana ɗaura hannunta biyu aka zata fashe da kuka”. “Kinga wasa nake miki” Anuwar ya faɗa da sauri ganin zata saka masa kuka. “To faɗamin mi zan cema su Ummah?”. Kafin ya bata amsa Aunty Batool ta shigo, ganin ta wucesu tana kuka sukai saurin bin bayanta.

      Hankalin su Umm-Anum a matuƙar tashe suka tari Batool, kowa tambaya yake jeho mata akan miya sameta?. Yanda duk suka rikice sai suka bata matuƙar tausayi, bata ɓoye musu komaiba ta labarta musu halin da ake ciki har zuwan su Jawaad da tafiyarsu office akan case ɗin.
        Faɗuwar Umm-Anum kawai sukaji batare da kowa yaga sanda tai yunƙurin faɗuwarba, hankalinsu a take ya sake tashi, basu wani tsaya maida yanda akayiba suka kwasheta zuwa asibiti, dole Batool ce tai driving ɗin, dan Anuwar baisan hanyaba.
      Anum da Nabeelah nata kuka su Ummah na rarrashinsu. Saboda ta samu kulawar gaggawa sai Batool ta nufi asibitin Dr Tayyeb da su, ai ko babu ɓata lokaci aka karɓesu da bama Umm-Anum taimako akan lokaci..........

__________________________

                A ɓangaren su Mom kuwa sun gama yanke hukuncin sake ƙulla auren Jawaad da Shahudah batare da neman yardarsa ba, dan haka babu wani ɓata lokaci mama Atika ta saka aka tattara mata su Uncle Sulaiman, sai dai kuma babu Uncle Nasir, acewar matarsa yayi tafiya tun daren jiya.
        Mom ta kira wayar Dad shima a kashe, hakan bai dameta ba, dan tasan shima burinsa kenan ai, dan haka sukace Uncle Uwaisu ya wakilci Dad ɗin, Uncle Sulaiman kuma Jawaad.
        Duk yanda Uncle Sulaiman yaso fahimtar dasu kuskuren yin hakan sam Mama Atika taƙi fahimta, saima rufesa da tayi da masifa tamkar zata cinyesa ɗanye. Haƙuri ya bata, a take aka tattara samarin gidan da maƙwafta kasancewar weekend ne aka sake ƙulla auren Jawaad Abdul-Aziz yusif da Sabeera Aliyu Fillo akan sadaki naira dubu ɗari da Uncle Sulaiman ya biya.
         Zo kuga farin ciki wajen Shahudah amarya dasu Mom da Mama Atika, dan a wannan karon sun ɗauki alwashin babu abinda zai dakatar dasu daga cika burinsu akan abinda suka jima sunama ƙwaɗayi. Ana cikin wannan murnarne ɗiyar Uncle Sulaiman tazo sashen mama Atika da gudu tana kuka da faɗa musu cewar suzo mama Badiyya na wani abu mara daɗin gani.
     Gaba ɗayansu suka kwasa Uncle Sulaiman har gudu yake da tuntuɓe dan mahaifiya tafi gaban wasa. Sosai hankalinsu ya tashi, murnar ɗaurin auren da sukeyi ta gushe tabar fuskokinsu baki ɗaya. Cikin gaggawa aka ɗauki Mama Badiyya zuwa asibiti, kasancewar kowa yasan matsalolin asibiticinmu na gwamnati sai Mom ta bada shawarar a nufi asibitin Dr Tayyeb zatafi samun kulawar gaggawa. Da wannan shawarar sukai amfani suka nufi can, sauranma suka shiga motoci suka dafa musu baya.
        Da gaggawa aka amsheta, itama sauran likitoci suka rufu kanta dan Dr Tayyeb yana wajen Umm-Anum a lokacin, sai da yaga numfashinta ya dawo jikinta, ma'ana ta farfaɗo sannan ya saka mata ruwa ya fito dan amsa kiran da Mom keta masa a waya. Sai a lokacinne shi yakejin cewar mama Badiyya suka kawo, bai tsaya bama su Ummah gamsashshiyar amsar da suke buƙatar jiba ya basu haƙuri akan su jirashi ya nufi ɗakin da aka kai Mama Badiyya..............✍

Hummmm koya zata kaya a asibiti kuma tsakanin waɗan nan familys guda biyu? Ga tashin hankalin dake faruwa daga su Jawaad wanda duk ya shafi waɗanan ahali, kumuje zuwa dan jin yanda zata kaya masoya, dan aski yazo gaban goshi insha ALLAHU, kuma da gaske bily ta DAWO GARE KU🤗😍😍😘.

ALLAH Ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[2/12, 7:51 PM] Wasila: *_ƘWAI CIKIN ƘAYA!!_*


*_Bilyn Abdull ce🤗_*


_ASSALAMU ALAIKUM MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR... 🙋🏿‍♀️🙋🏿‍♀️INA KUKE NE? 🔊🔊KU MARMATSO, DOMIN ZAMAN JIRA YA KARE, HAZIKAN MARUBUTAN NAN DA SUKA HADA HAZAKA DA KAIFIN TUNANI SUN SAKE ZAGE DAMTSE SUN ZO MU DA WASU SABBIN SALON RUBUTUN SU, WADANDA ZASUWA’AZANTAR, SU NISHADANTAR, KANA SY DILMIYA KU A KOGIN KAUNA, BASU TSAYA ANAN BA SALON RUBUTUN SU YA SAKE ZUWA DA SABBIN TSARE TSARE NA DARUSSA DABAN DABAN, DA KUMA HANYOYIN GYARIN JIKI DA WAJE._

_KADA KU MANTA MARUBUTAN ZAFAFAN DAI SUNE WADANDA SUKA YO MUKU HAR KASHI BIYU A SHEKARAR 2020 DATA GABATA,: WUTSIYAR RAKUMI DA GUDU DA WAIWAYE NA BILYN ABDULL. 2-DAURIN BOYE DA ALKAWARIN ALLAH NA SAFIYYAH HUGUMA.3-BURI DAYA DA QAUNAR MU NA MAMUH GEE-4- SAUYIN KADDARA DA DAURIN GORO NA HAFSAT RANO. SAI 5-KAI MIN HALACCI DA IGIYAR ZATO NA MISS XOXO.._

_A WANNAN SABUWAR SHEKARAR TA 2021 MA HAZIKAN MARUBUTAN SUN SAKE DAWOWA DA WASU SABBIN DA’DADAN LITTATTAFAN NASU:_

_1_

_* SAFIYYAH HUGUMA* MARUBUCIYAR KUNDIN KADDARA DA ABADAN TAZO MUKU DA SABON LITTAFIN TA MAI SUNA: *(SIRADIN RAYUWA)💜*_

_2_

_*HAFSAT RANO* MARUBUCIYAR GUGUWAR SO DA RUHI DAYA, TA ZO DA SALON NATA LITTAFIN MAI SUNA: *(ABINDA KE CIKIN ZUCIYA..*)💘_

_3_

_* MAMUH GEE* MARUBUCIYAR TARAYYAH DA EZNAH, TAZO DA SABON ZUWA MAI SUNA: *(MIN QALB)❤️.*_

_4_

_*MISS XOXO* MARUBUCIYAR NAUFAL DA SAIFUL-ISLAM, TA YUNKURO DA WANI MAI SUNA: *(KIBIYAR AJALI)*💜_

_5_

_SAI MARUBUCIYA *BILLYN ABDUL* WADDA TAYO MUKU KWAI CIKIN KAYA, DA CIKI DA GASKIYA TA YINKURO DA WANI MAI TAKEN: *(YANKAN BAYA)*💝_

_RIGIJI GABJI DUKKAN WADANNAN LAGWADAR DADADAN LITTAFAN BIYAR ZASU ZO MUKU NE INSHA ALLAHU AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA;_

Duka BIYAR 5 zaku samesu akan garabasar naira 700 kacal,

Guda hudu 4 Kuma 500,

Guda uku 3 Kuma 450,

Guda biyu 2 Kuma 400,

Guda daya akan 300.

Ma'ana
Each one is 300
2 is 400
3 is 450
4 is 500
5 is 700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*+234 903 234 5899*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

*09033181070*

Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO

TEAM#ZAFAFABIYAR🔥




Page 59

..................Motoci na alfarma aka aika daga masarauta domin tarbo su Abbu a airport kamar yanda aka aika tarbar su Umm-Anum, sai dai su masarauta aka wuce dasu, inda acan ɗinma suka sami tarba ta musamman da mutuntawa ga mai martaba sarki Sameer Saifudden da iyalansa, harma da ƴan majalissar sarki baki ɗaya. A yanda masarautar take yau ko ba'a faɗa makaba kasan anyi manyan baƙi a cikinta, waɗanda suka isa suka bunƙasa. An baje musu abinci na alfarma na ƙasarmu masu daɗi da daɗaɗa zuciya.

         Tun kafin tafiya ɗakko su Abbu Gimbiya Munaya tasa Amaturrahman ta nema Number Jawaad, amma taƙi shiga sam, ta kira ta Bilkisu kuma ba'a ɗagaba. Hakan ya bata mamaki matuƙa, dan tasan dai ai su Jay ɗin sunsan da zuwansu Abbu, a yanda suka tsara al'amarin kuma daga tarbo su Abbu a airport zasu wuce masarauta ne harsu Umm-Anum ɗin, bayan su Abbu sunci abinci sun huta sai su ɗunguma baki ɗayansu gidan Alhaji Babba, daga can idan dare bai rufaba zasu ƙarasa family house ɗin su Jay. To amma gashi har lokaci ya shige babu Jawaad ɗin babu dalilinsa.
         
          Basu ji halin da ƙasar take ciki ba sai sai kusan isowar su Abbu da awa ɗaya da rabi sannan takawa ya samu kiran waya daga gwamna akan ya buɗe television yaga tashin hankalin da a yanzu shima aka faɗa masa game da manyan mutane da ake ganin mutuncinsu a ƙasar, babban abinda ya razana gwamna kuwa harda wasu a abokansa masu manyan muƙamai kuma a gwamnatin tasa.
             Al'ajabi daya kume sarki lokacin daya buɗe tv kasa ƙwaƙwaran motsi yayi, dan shima ɗin ai akwai waɗanda suke matuƙar gaisawar zuminci a cikinsu sosai..........

_________________
ASIBITI
____________

                  Hankalin su Mom a tashe suna jiran fitowar Dr Tayyeb daga ɗakin da aka saka Mama Badiyya kira ya shigo wayarta daga mai aikinsu. Kamar bazata ɗagaba sai kuma mita tuna oho mata ta ɗaga wayar.
         A matuƙar ruɗe Talatuwa dake kuka ta zayyane mata abinda ya faru game da zuwan wasu mutane da sukace su ƴan sandane har gida suka tafi da kuku da maigadi.
    A tsawace Mom tace, “What!! K bansan shirme da hauka kinji, ubanmi suda suke gida kullum zasu aikatama ƴan sanda harsuzo gida su kamasu?”. cikin kuka talatuwa tace, “Wlhy hajiya da gaske nakeyi, yawwa gama wannan da kikacemin shine babban yaronku nan yazo gidan”. Da mamaki Mom tace, “Waye? Kina nufin Qaseem?”.
       “E...e...eh shi hajiya, wanda hotonsa ke a falo sanye da baƙaƙen kaya tare da Alhaji”. Jikin Momy har rawa yake wajen ambaton, “Da gaske Qaseem, yaushe suka barshi ya fito to? Kinga bashi wayar muyi magana nima gani nan zuwa gidan yanzun nan”. “T..t...to hajiya, bara nakai masa”. Talatuwa ta faɗa tana ɗan gudu wajen bin bayan Qaseem dako kallon inda take baiyiba ya haye sama ɗakin Dad direct. Yana kama handle ɗin ƙofar tana ƙarasawa garesa, da rawar jikin tsoro ta miƙa masa wayar tana faɗin, “Alhaji ƙarami sannu da zuwa, gashi inji hajiya zakuyi magana”. Wani mummunan kallo daya kaɗa hanjin cikinta ya zuba mata, cikin daka tsawa yace, “Ɓacemin da gani kona halakaki wlhy”. Zabura Talatuwa tayi da gudu tabar saman, yayinda Momy kuma taji komai ta cikin wayar, ita kanta tsawar Qaseem sai da ta sakata cire wayar daga kunnenta ma.

        Bata iya cewa sauran ƴan uwanta komaiba ta nufi hanyar fita daga asibitin da hanzari, duk faman tambayarta lafiya? da sukeyi bata juyoba balle ta amsa musu harta fice. Da kanta taja motar tabar asibitin zuwa gida.
       Akan hanyar momy na nufar gida ta fahimci garin babu lafiya, dan kuwa babu abinda take gamo da shi a tituna sai matsanancin holdup. Mafi yawancin inda traffic light suke an haɗa cinkoso a wajen sosai, ga jirage masu saukar angulu da keta yawo na kaikawo a sararin samaniya, wasu ma daf da mutane suke. Ratse ta ringayi ta cikin anguwanni tamkar yanda wasu motocin taga sunayi. Da ƙyar ta samu kanta a anguwarsu, tai fakin motar a ƙofar gida batare data kasheba saboda wani bahagon ruɗani da ta sake karo da shi kuma, ƙofar gate ɗinsu a buɗe take, ga jami'an tsaro sun zagaye gidan, cikin sake shiga ruɗani ta afka cikin gidan da sassarfa tamkar zaga kifa, ananma wasu jami'an tsaron ta sake cin karo dasu a cikin gidan, talatuwa na durƙushe gefe tana kuka ita da mai bayin fulawa.
         “Kai lafiya?”. Mom ta faɗa hajijiya na neman ƙwasarta zuwa ƙasa. Wani cikin ƴan sandanne ya bata amsa da faɗin, “Hajjaju wannan gidan yana a hannun hukumane a yanzun, akwai bincike da za'azo ayi a cikinsa daga yanzu zuwa kowanne irin lokaci”. Cikin tsawa da hucin ɓacin rai, “Mom tace kuɗin ubanwa muka sata to? Muba ƴan siyasaba ba ma'aikatan gwamnati ba, amma za'a turo mana jami'an tsaron binciken almun dahana da dukiyar ƙasa?”.
        “A'a hajiya, mu ba jami'an tsaron almun dahana bane ba, jami'an tsarone na farin kaya, da kuma amincewar Sir Qaseem Ali muke anan  bisa Umarnin Sir Jawaad Abdul-aziz Yusuf”. “Qaseem! Da Jawaad kuma?”. “Hakane hajjaju” ya sake bata amsa kansa tsaye.
       Wata ashariya da momy ta manta tama iyata ta kwaso ta dire bisa ƙasa tanayin wurgi da jikkar hannunta, ta shaƙo wuyan police ɗin tana huci, a take sauran suka zagayeta da bindiga. Murmushi Munkaila yayi yana ɗaga musu hannu alamar su barta, ya kalleta fuska babu wasa zaiyi magana ta tare numfashinsa. “Kai shashasha kasan mi kake faɗa kuwa? Ina Jawaad da Qaseem ɗin suke?”. Ɗan murmushi yay mata yana zame hannunta a wuyansa ya gyara rigarsa, “Sir Qaseem yanzu ya fita,

1 Comments On KWAI CIKIN KAYA
avatar
zainab-nasir

1 year ago

Reply

Muna jin ddin yanda kuke ilimantar damu

Please Login or Register in order to submit comment