Join Our WhatsApp Group

RIJIYA GABA DUBU Book 6 Complete Hausa Novel Document by RIJIYA GABA DUBU Book 6


RIJIYA GABA DUBU Book 6

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 10907



RIJIYA GABA DUBU Book 6

Reading Time: 0 Hours

Added On: 13, Feb 2024

Author: Abdulaziz Sani Madakin Gini ,

Ebook Compiler : Al'amin Ahmed Misau

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Adventure novels

File Size: 58.56 kb

File Type: txt

Views: 704+

Download: 228+

Last download: 1 day ago

Description/Story: RIJIYA GABA DUBU
Littafi Na Shida (6)
Part A.
Na Abdulaziz Sani M Gini
AA Misau ke Magana

Labari Ya Isowa Shagala Cewa
Marubucin Yaci gaba da cewa.....

Badakaren ya kawo
gwauron numfadhi ya ajiye sannan yace ai
muna rabuwa da kai na taho iZuwa nan
dakina domin na yi shiri na tafi izuwa
cikin gari don cika umarninka. Na juya
baya ina sa tufafina sai na ji an turo
kofar dakin nan an shigo. Katin na
waigo naga mai shigowa sai ji nayi an
gabza mini naushi a kan kunnena na
hagu. Daga nan ban san abin da ya faru
ba sai farkawa nayi na ganni a kwance
da rub da ciki kuma a daure.
Kafin badakare ya gama rufe
bakinsa tuni Zamaru ya nike tsaye ya
ruga waje da gudu. Wannan shi ne abin
da ya faru a cikin gidani sarautar sarki
Taryan bayan dare ya raba a ranar da
jaruni imhal ya lashe gasar lambun
jarumta a zagaye na hudu,
Al'amarin jarumi Imhal kuwa sa
da ya shafe kwana biyu a kwance yana
cikin natsananciyar rashin lafiya da
jinya ba tare da ya ma san wanda ke
kansa ba.
A tsawon wadannan kwanaki babu
mai shiga cikin dakin da aka ajiyeshi
face sarki Taryan da likitansa. Ita kanta
gimbiya Shumaira babu yadda bata yi ba
akan sarki Taryan ya amince mata ta
shiga taje ta ga lafiyar Imhal amma ya ki.
Babban abin da ya dada dugunzuna
hankalinta shi ne gaba daya ta daina
ganin Muzaira a tsawon kwanakin biyu
bare ta toketa ta shigar da ita inda aka
6oye jarumi Imhal kuma bata san dalilin
bacewar Muzaira ba.
A wannan dare na biyu ne kafin
daren ya raba jarumi Imhal ya dawo
cikin haiyacinsa har ya bude idanunsa.
Yana bude idanun nasa ya yi arba da
sarkí Taryan da likitansa zaune a
gabansa kawai sai ya yunkura ya mike
Zaune, yana shirin mikewa tsaye kenan
sarki Taryan ya ce, kada kayi
Kwakkwaran motsi domin dinkin da na
yiwa raunikan jikinka zai iya farkewa kuma
kaga raunikan basu gama
warkewa ba.
Ko da jin
wannan batu sai kwallar
takaici ta zubowa jarumi Imhal ya du
ikitan sannan ya dubi sarki Taryan ya
ce, na gaji da wannan gasa haka kuma
na gaji da irin bakar wahalar da nake sha
don baka lallai gobe da safe nake son na
yi wasan karshe da sarki Gurzalu domi
na kawo karshen komai, ko ni ko shi
Ina son na sami'yancin kaina haka na
gaji da ganin jinina na zuba.
Ko da gama fadin haka sai jarumi
Imhal ya yunkura cikin zafin nama va
hankade sarki Taryan da likitansa daga
gabansa suka zube kasa sannan
takarkare ya kwarara uban ihu wanda ya
sannan ya
Cika gidan sarautar gaba daya da amsa
kuwa. Hatta sarki Gurzalu dake tsaye a
Can cikin turakarsa sai da zucivarsa ta
buga da karfi sakamakon jiyo wannan
sautin ihu domin ya gane muryar mai
ihun ba ta wani bace face ta jarumi
Imhal. nan take ya cika da tsananin
mamaki bisa yadda akayi jarumi Imhal
ya
Sami lafiyar da har zai iya yin
Wannsn uban ihu a vanzu
Saboda ihun da jarumi Imhal ke yi
sai dinkin raunikan jikinsa suka rinka
farkewa amma kuma sai gashi raunikan
sun warke babu inda jini ya tsattsafo.
Al'amarin da ya yi matukar baivwa
sarki Taryan da ikitansa mamaki kenan
Imhal ya ci gaba da kwarara ihu
yana zarya. a cikin dakin tankar
mahaukacin tsohon rikakken zalki
wanda ya fusata ainun a cikin daji.
Sai da sarki Taryan ya taso da
sauri ya kama jarumi Imhal da karfin
tsiya ya zaunar da shi kasa sannan ya
shiga rarrashinsa yana bashi baki amma
Imhal bai nutsu ba sai da sarki
Taryan ya amince da batun cewar
gaba da gasar kambun jarumta gobe da
safe.
A cikin wannan dare kuwa aka
yada labarin ci gaba da gasar kamnbun
jarumta gobe da safe.
Ai kuwa nan da nan labari ya bazu
a ko ina birni da kauye, mutane suka
rinka cewa lallai jarumi Imhal ba mutum
ba ne, aljani ne shi don babu yadda za a
yi ace mutum ya warke daga iin
mugayen raunikan da ke jikinsa guda
shida.
Al'amarin gimbiya Lamrita kuwa
tun daga lokacin da ta sami nasara
kufcewa daga hanun su sarkin yalki acan
birnin Kisra ta fada cikin daji. bata
saurara ba da gudu akan doki don gudun
kada su sarkin yaki su biyo bayanta su
cimmata saboda ta san cewa sarkin yawa
yafi sarkin karfi. idan suka yi mata
rubdugu zasu iya cafketa su je su jefataa
cikin kurkukun da ba za ta iya guduwa
ba.
Lamrita bata yada zango ba sai da
ta ga dokinta ya gaji likis kuma itama ta
gajin kuma yunwa da kishirwa sun fara
galabaitar da ita sannan ta tsaya a bakin
wata korama ta sauko daga kan dokin
suka kama shan wannan ruwa ita da
dokin nata.
Da yake tana tsoron kada cikinta
ya kulle sakamakon yunwar da take ji
sai ta sha ruwan dan kadan.
Ita dai wannan korama tana da
zurfi amma bata da fadi sosai kuma
mahada ce ta ruwan wani katon kogi da
ke can gaba a cikin daji.
Kash rashin sani yafi dare duhu.a
she dai dai wurin da gimbiya Lamrita ta
tsuguna tana shan ruwa akwai wata
murtukekiyar macijiya mai kauri da
tsawon gaske wacce ta yi lambo a
AA Misau ke Magana
Karkashin ruwan, kawai jira take Allah
ya kawvo wata dabbar mai tsautsayi
shan ruwa ta yi kalaci da ita saboda
tana cikin matsananciyar yunwa. Ko do
Lamrita ta gama shan ruwa ta mike zata
kama dokinta su bar wajen sai kawai taji
an fincikota izuwa cikin ruwan da Karfin
tsiya, kafin tayi wani yunkuri macijiyar
ta fara kanannade kafafunta ta kasa
zuwa kugunta ne ta sa hannayenta ta
tokare macijiyar.
Nan fa suka kama kokowa suna
nutsewa izuwa kasan ruwan Suna
dagowa sama Suna ta birgima,
Sakamakon nutsewar da suke yi izuwa
kasan ruwan sai Lamrita ta fara
galabaita saboda daukewar numfashinta,
gashi dai suna ta fafatawa ita macijiyar
ta kasa karasa kanannadeta ita kuma ta
kasa samun damar zare wuka ko
takobinta ta cutar da ita.
A daidai wannan lokaci hankalin
gimbiya Lamrita ya dugunzuma ainun
domin karfinta ya fara karewa ta san
cewa da zarar macijiyar ta karasa
kanannadeta zata karya gaba dayan
kasasuwan jikinta ta hadiye ta.
Nan take Lamrita ta cire kai ga
samun tsira ta saddakar da cewa lokacin
mutuwarta ya yi.
Kwatsam sai ga wani matafiyi bisa
wani dogon rakumi sanye da fararen
tufafi ya zo giftawa. Matafiyin ya rufe
fuskarsa, idnaunsa ne kadai ake gani.
Ko da ya ga abin da ke faruwa sai
ya dako tsalle sama daga kan rakumin,
tun kan ya fado kan macijiyar ya zaro
wata sharbebiyar wuka kawai sai ya
sokawa macijiyar wuka a idonta guda
Take idon ya fashe, macijiyar ta yi wani
uban ruri saboda tsananin zafi da zogin
da taji a sa'adda iini ya kama shatatowa
kasa, ba ta san sa'adda ta saki Lamrita
ba saboda dimaucewa, ai kuwa sai ta
koma kan wannan bakon matafiyi shima
ta fara kanannadeshi amma sai ya yi wuf
ya kama jelarta da hannu guda kuma ya
wuyanta da daya hannun ya
warware nadewar da tayi masa a hankali
da karfin tsiya.
Nan take kwanjin hannayensa suka
kumburo har hannun rigarsa ya yayyage
saboda tsabar karfin damtse nasa. Tuni a
wannan lokaci gimbiya Lamrita ta fito
daga cikin koramar da kyar tana jan ciki
saboda tsananin galabaitar da tayi.
tana numfarfashi
Ko da ta ga irin tsananin karfin
wannan matafiyi da ya kawo mata dauki
sai ta ci gaba da kura masa idanu tana
kallon gumurzun da yakeyi da wannan
katuwar macijiya a cikin ruwa. Tun da
gimbiya Lamrita ta zo duniya bata taba
ganin mutum mai kirar sadaukai ba da
tsananin karfi kamarsa domin duk
girman macijiyar sai ga ta hannunsa ta
kasa kufcewa.
Ana cikin wannan artabu ne taga
jarumjin ya daga macijiyar sama ya tabe
hannayensa yana mai kwala kabbara.
Nan take ya tsinke macijiyar ta dare gida
biyu ya yi jifa da gawarta a cikin ruwan.
Saboda tsananin mamaki
gimbiya Lamrita ta sandare kamar
gunki, baki a bude, idanu a kafe ta kura
masa idanu ko kiftawa ba ta yi har ya
fito daga cikin koramar ya zo daf da ita
ya tsuguna sannan ya kwaye rawanin da
ya rufe fuskarsa da shi suka yi arba da
juna yana mai yi mata murmushi.
sai
Ko da gimbiya Lamrita ta ga irin
tsananin kyawun fuskar saurayin sai ta
sake dimaucewa har yayi mata kwarjini
ainun ta kasa ci gaba da kallonsa ta dan
sunkui da kanta kas, a sannan ne ya
dubeta ya ce, ina fatan dai babu wani
rauni a jikinki?
Ko da jin wannan tambaya sai
gimbiya Lamrita ta mike tsaye ta duba
ko ina a jikinta ta tabbatar da cewar
babu wani rauni sannan ta dubi saurayin
ta ce, ina godiya a gareka mara adadi
bisa ceton rayuwata da ka yi daga
sharrin wannan katuwar macijiya.
Sunana gimbiya Lamrita 'ya ga sarki
Gurzalu na birnin Kisra kuma ina kan
hanyata ne ta zuwa bimin Misra don
hallarar gasar kambun jarumta, wanene
kai, daga ina ka fito kuma ina ka dosa
yanzu?
Sa'adda kyakkyawan saurayin ya
ji wannan tambaya sai ya cika da
mamaki amma sai ya dubi gimbiya
Lamrita cikin murmushi ya ce, ni sunana
Salman bin Usman kuma na fito daga
wata kasa da ake kira Madinatul Ansar
dake kudancin nahiyarku. Babu inda na
nufa face birnin Misra inda ake wannan
gasa ta kambun jarumta domin nima n
AA Misau Ke Magana
shiga gasar amnma da wata manufa. Na
dade ina jin labarin wannan gasa da
yanayinta irin yadda ake fafatawa da
manyan jarumai na duniya ana yi musu
kisan gilla. Lallai idanuna sun kagu da
su ga yadda ake wannan bakin gumurzu.
Yake yar sarki ki yi sani cewa
kafin anzo nan na sauka a cikin birninku
na Kisra har na kwana biyu kuma na
sami labarin cewa mahaifinki sarki
Gurzalu shi ne zakaran wannan gasa ta
kambun jarumta kuma yanzu haka yana
can birnin Misra yana yin gasar. Menene
dalilin da ya sa baki bishi kun tafi tare
ba izuwa birnin na Misra, kuma ta yaya
kina matsayin 'yar sarki guda za ki
shigo cikin wannan daji mai hadarin
gaske ke kadai?
Ko da jin wannan tambaya sai
kunya ta kama gimbiya Lamrita ta
dabarbarce ta kama in ina, shi kuwa
jarumi Salman sai ya tari numfashinsa
ya ce, bana son karya a rayuwata kuma
bana tafiya tare da makaryaci. Kawai ki
fito fili ki gaya mini gaskiyar
tambayoyin da na yi miki, idan kuma
kin san cewa ba za ki iya gaya mini
gaskiyarki ba to ki yi shiru da bakinki
ina ganin cewa zai fi alheri a garem
ubaki daya.
Ko da gama fadin hakan sai jarumi
Salman ya mike tsaye ya je inda
rakuminsa ke tsaye ya dauko wata jaka
tasa ta guzuri gami da battar shan ruwa
ya dawo wajen Lamrita ya baje jakar
guzurin ya fiddoa gasasshen namna
tsuntsu nannade a cikin wani ganye ya
ajiye a gaban Lamnrita ya yagi cinyar
tsuntsun guda daya sannan ya dubeta ya
ce, ki cinye wannan naman duka don
naga akwai alamun matsananciyar
yunwa a tare da ke. Dan wannan da na
yaga ya isheni.
Yana gama fadin hakan sai ya
koma can inda rakumin nasa yake ya
shimfida buzu a kasa ya zauna a kansa
yana mai juya mata baya ya cinye dan
guntun naman dake hannunsa sannan ya
mike tsaye ya fuskanci alkibla ya kama
sallar nafila.
Al'amarin Lamrita kuwa ko da
jarumi Salmanu ya ajiye wannan
gasasshen tsuntsu a gabanta sai ta cika
da murna, Nan take ta kama Cin nanan
har sai da ta ci ta koshi ta taune kashin
duka sannan ta dauki battar ruwan shan
nasa ta kwankwada har sai da taji tayi
Byatsa.
Tana ajiye battar ruwan ne ta
hango jarumi Salman yana sallar nafila,
a sannan ne ta gane cewar lallai shi
ma'abocin addinin musulunci ne addinin
da yake da tsananin bakin jini a
nahiyarsu gaba daya.
Nan dai ta ci gaba da kallonsa tana
mamakin irin yanayin aikin bautar da
yake yi har sai da ya kammala ya shafa
addu'a sannan ya juyo ya dubeta ya ce,
ina neman alfarma a wajenki guda daya.
Ina son ki nema nini damar shiga
wannan gasa ta kambun jarumta idan
mun isa birnin Misra.
Ko da jin wannan tabaya sai
mamaki ya kama gimbiya Lamrita ta
dubeshi ta ce, tabbas kai bako ne baka
san dokokin wannan gasa ba. To ka sani
cewa yanzu saura zagaye daya kacal a yi
gumurzun karshe na wannan gasa a
wannan shekara, babu mamaki ma a yi
fafatawar ta karshe a cikin wannan sati
da muke ciki. ldan har kana son ka
fafata da jarumin da ya lashe gasar dole
ne ka fara kafsawa da wadansu manyan
jaruman guda hudu kuma sai ka biya
dinare dubu dari biyu da hamsin sannan
za a yarda ka kafsa da jaruman dake rike
da kambun gasar.
Sa'adda jarumi Salman ya ji
wannan jawabi na bimbiya Lamrita sai
ya yi murmushi ya ce idan da mutum
dari zan kafsa kafin na hadu da mai
kambun jarumta babu matsala kuma
batun kudin ba matsala ta ba ce ko
dinare miliyan daya ake bukata zan
biya.
Ko da jin wannan batu sai gimbiya
Lamrita ta karewa jarumi Salmanu kallo
daga sama har Raş cikin raini domin
bata ga alamar yana da ko dinare dubu
ba bare miliyan daya.
Ko da jarumi Salnanu ya fahimci
cewar kallon rauni take yi masa sai ya
dauko wata katuwar jakar fata a kan
rakuminsa ya ajiye a gaban Lamrita ya
budeta sai ga dinare cike fal. Take
gimbiya Lamrita ta dimauce ta kidime
saboda mamakin ganin wannan dukiya

Ni kaina AA Misau saida naa dimauce har na kasa cigaba da wannan rubutun kuma na dakata anan

Saikuma wani lokaciRIJIYA GABA DUBU
Littafi Na Shida (6)
Part B.
Na Abdulaziz Sani M Gini
Typing By
AA Misau ke Magana

(Rashin Sakin Litattafan da muke kawo muku akan lokaci daga gareku ne domin muddin zaku dinga nuna kuna so a cigaba ta hanyar LIKES & COMMENTS bamuki kullum mu kawo muku cigaban ba)

Labari Ya Isowa Shagala Cewa
Marubucin Yaci gaba da cewa....

tsananin mamakin wannan dukiya
mai yawan gaske a hannun mutum daya
mugayen
kuma matafiyi mai ratsa
dazuzuka haka.
Nan fa ta fara aiyanawa a ranta
cewar anya kuwa wannan saurayin ba
dan sarki bane ko wani mashahurin
attahiri? Amsar da ta kasa baiwa kanta
kenan.
Ko da jarumi Salmanu ya ga
gimbiya Lamrita ta tsaya tana tunani sai
ya katse mata tunanin ya ce, ai sai ki
tashi mu hanzarta zuwa birnin Misra don
ka da a yi wannan fafatawa ta karshe ba
ma nan.
Lamrita ta yi ajiyar zuciya ta ce, na
yarda zan taimaka maka ka shiga
wannan gasa amma bisa sharadi biyu.
Sharadi na farko shi ne dole ne ka zama
kamar yarona, ma'ana za mu shiga cikin
birnin Misra kana matsayin sabon
jarumina wanda na kawo na shigar da
shi gasar kuma ina matsayin bakon
attajiri daga wata nahiyar, kaga kenan
babu abin da zaka yi sai bisa umarnina.
Ko da įin wannan batu sai mamaki
ya kama jarumi Salmanu ya ce yanzu
kina nufin kice za ki boye siffarki ta 'ya
mace kenan ki yi shigar mata, sannan
kuma ni na zauna a matsayin bawanki
• alhalin na fiki ma arziki?
Ko da jin wannan tambaya sai
gimbiya Lamrinta ta yi murmushi ta ce
kwarai kuwa abin da nake nufi kenan
kuma in dai baka bi wannan umarni
nawa ba ina tabbatar maka da cewar ba
zaka taba samun damnar shiga wannan
gasa ba.
Sa'adda Lamita ta z0 nan
jawabinta sai hankalin jarumi Salmanu
ya dugunzuma ya dubeta cikin matukar
damuwa ya ce haramun ne a addinina
mace ta yi shiga irin ta maza ko kuma
namiji ya yi shigar mata.
Kafin ya gama rufe bakinsa sai ta
ce, ai ana iya hakuri da wata dolen bisa
lalura, kuma a kowane addini akwai
lalura.
Ko da jin haka sai jikin jarumi
Salmanu ya yi sanyi ya yi shinu yana
tunani da nazari daga can sai ya numfasa
ya ce, shi kenan na yarda da duk
sharadin da kika zo mini da shi.
Cikin tsananin farin ciki gimbiya
Lamrita ta mike tsaye ta kimtsa kayanta
ta hau dokinta shima jarumi Salmanu sai
ya hau kan rakuminsa, har ya yunkura
zai wuce gaba sai ta sha gabansa ta ce,
saboda me zaka wuce kan gaba alhlain
ni ce na san banya fiye da kai?
Salmanu ya yi murmushi ya ce, ai
dole ne na wuce kan gaba ke ki tsaya a
baya saboda haka dokar addinina ta ce,
in ya so idan na kauce hanyar sai ki
saitani.
Lamirat ta jinjina kai ta ce, shi
kenan amma ka sani cewa dole ne ka
Boye addininka idan mun shiga birnin
Misra, in ba haka ba kuwa duk shirinka
sai ya wargaje.
Salmanu ya sake yin shiru yayi
dan guntun tunani da nazari sannan ya
saki rakuminsa ya yi gaba itama Lamrita
sai ta sakarwa dokinta linzami ta bishi a
baya dá sauri suka nausa cikin daji.
A can...


Read / Download RIJIYA GABA DUBU Book 6

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album