Join Our WhatsApp Group

BAKIN ARTABU Book 1 Complete Hausa Novel Document by BAKIN ARTABU Book 1


BAKIN ARTABU Book 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 8023



BAKIN ARTABU Book 1

Reading Time: 0 Hours

Added On: 06, Jan 2024

Author: Abdulaziz Sani Madakin Gini ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Adventure novels

File Size: 44.53 kb

File Type: txt

Views: 991+

Download: 248+

Last download: 1 day ago

Description/Story: ***★BAKIN ARTABU**cigaban
**JARUMA*YAZILA★***
Littafi Na Daya {1}
Na Abdul Aziz Sani Madakin gini..
TYPE Suleiman zidane kd...
Whatsapp 09064179602
*****
Marubucin ya fara da cewa:
====================================
Lokacin da aka kacame da azabebban yaki tsakanin jaruma dabira da jaruma yazila acikin keji sai suka wanzu suna masu kaiwa juna sara da suka cikin tsananin zafin nama. Juriya da jarumtaka tamkar jikinsu bana jini da tsokabane. Sai da suka shafe sa a uku cur suna wannan gumurzu amma dayansu bai sami nasarar koda lakuyar jikin abokin gwaminsa ba. ' Yan kallo kuwa da sarki raihan hankalinsu ya dugunzuma ainun bisa ganin yadda ako yaushe yakin nasu dabira kekara tsamari. Tashin hankalinsu sarki raihan shi ne. Idan jaruma yazila ta sami nasarar hallaka dabira sunyi asarar sarkin yakinsu wacce babu kamarta aduk fadin mayakan birnin. Lokacin da sa a uku ta cika sai dabira da yazila suka tsaya da yakin suka jada baya suka yi cirko cirko suna haki da kallon juna kamar zakaru saboda gajiya.
A sannan ne dabira ta fara tunanin hanyar dazatabi ta sami nasarar akan yazila amma kuma bisa mamaki sai taji zuciyarta na bugawa da karfi a duk sa adda ta kalli fuskar yazila.
Abu na biyu daya fado mata arai shi ne batun wannan laya dake wuyan yazila anya kuwa wannan laya dake wuyan yazila ba ita ce tasa nakasa samun nasara akantaba ? Yazama wajibi agareni na cire wannan laya daga wuyan yazila tunda dai tace daga hannun musulmi take.
Koda gama aiyana haka acikin zuciyarta sai tayi jifa da takobinta gefe daya ta dubi yazila tace , ” tunda dai munkasa yiwa junanmu illa da makami saimu gwada yar kashi domin mu kawo karshen wannan gabatamu ”.
Koda jin haka sai jaruma yazila ta bushe da dariyar mugunta irinta ma abota shirka sannan ta murkushe fuska kuma itama tayi wurgi da takobin tace. ” Ai dama haka nakeso. Domin ta haka ne kadai zamu iya bambancewa tsakanin aya da tsakuwa ” ™Nasiru Muhammad™
Nan take duk su biyun suka dunkule hannayensu suka gyara tsayawa sannan suka fara zagaya juna. Kwatsam ! Sai suka kacame da azababban fada suka rinka kaiwa juna naushi da bugu. Hannu da kafa.
Babu abinda zai baiwa mutane mamaki face yadda suke bugun jikinsu tamkar suna bugun buhun hatsi. Ma ana ko gezau basayi. Sai dai kaga sun shanye dukan sun maida martani.
Aikuwa kafin an juma sun hadawa junansu jini da majina. Ana cikin haka ne suka jada baya alokacin guda suka bayar da tazarar taku shida shida sannan suka rugo da gudu kowacce ta daka tsalle sama. Suna haduwa sai kowacce ta gabzawa yar uwar mummunan naushi a kumatu tun a saman feshin jini yai fitsar burgu daga cikin yanayi mai kama da suma
Suma.
Al amarin daya sa gaba dayan mutanen dake fadar suka mike tsaye zumbur cikin firgici domin a zatonsu jaruman biyu sunyi ragas babu wanda hankalinsa yatafi na kowa dugunzuma face sarki raihan domin yana mikewa tsaye a dimauce bai san sa adda maya ruga da gudu izuwa bakin kejin dasu jaruma dabira keciba. Al amarin humaira kuwa dama bata fito ba zata iya kallon wannan gumurzu da za ayi ba tsakanin yazila da dabira.
Lokacin da gari ya waye taji gaba dayan gidan sarautar tayi tsit tamkar babu mai rai acikinsa sai ta gane cewa lallai kowa na can fada ana kallon wannan fada daza ayi. Dama tun a daren jiya tsakanin yarta dabira da tsohuwar abokiyar gabarta tazila wanda tazo musu a siffar tsoho kasim. Bayan humaira ta gama dan kintse kintsenta saita mike tsam ta fito daga cikin turakarta ta kamaa tafiya acikin harabar gidan sarauta inda ta rinka arba da dai daikun dakaru masu tsaro da bayi masu kai kawokai tsaye humaira tawuce izuwa dakin da aka sayki bako ™Nasiru Muhammad™kasim duk inda ta wuce sai aka ga dakaru da bayi suna rissinawa suna gaisheta har ta isa kofar dakin da zuwa ta iske kofar dakin a bude batayi mamaki ganin hakan ba saboda dama tasan yanzu ankama yazila an tafi da ita.
Duk da cewa humaira taga fuskar jaruma yazila ajiya da daddare amma har ayanzu zuciyarta na wasi wasi akan anya kuwa yazila yarta ce?
Zuciyar humaira na bugawa da karfi ta kunna kai izuwa cikin dakin ai kuwa tana shiga tayi arba da jakar guzurin yazila wacce ke rataye ajikin bango. Kawai sai ta dauko jakar ta sauketa akas ta bude.
Nan take idanunta suka yi arba da wadansu surutu wadanda dabira tanada irin su sak. Sannan kuma taga rigar da aka sawa yazila a ranar da aka haifeta wacce dabira ma tanada irinta.
Koda ganin wadnnan tufafi sai humaira ta dubesu ta rungumeshi a kirjinta sannan ta fashe da matsanancin kuka domin a yanzu ta tabbata da cewa lallai yazila yarta ce kuma yar uwar dabira. Tana cikin wani hali ne ta tuno da cewa yanzu haka fa yazila da dabira na can fada suna yaki kuma za su iya kashe junansu.
A firgice humaira ta mike tsaye ta juya da baya a guje ta rungume da wannan tufafi ta nufi filin fada. * * *
Lokacin da yazila da dabira suka baje akas cikin mawuyacin hali. Sarki raihan ya rugo da gudu izuwa bakin kejin yana isowa sai yai turjiya bisa ganin abin daya faru.
Bawani abu bane yafaru ba face tashin yazila da dabira atare lokaci guda kamar wadanda suka farfado daga dogon suma.
A tare yazila da dabira suka mike tsaye. Kowacce ta sake dunkule hannayenta kuma suka goge jinin dake yoyo abakinsu. Kawai sai yazila ta kurawa hular karfen dake kan dabira idanu. Itakuma ta kurawa layar wuyanta ido take suka sake rugowa da gudu batare da sunyi ™Nasiru Muhammad™ yunkuri daka tsalle samaba.
Cikin bakin zafin nama dabira ta kaiwa layar yazila cafka tayi saar damketa kuwa itama yazila saitayi sa'ar damkar hular karfen dabira
. Alokaci guda kowacce ta cire abinda ta damka. Wato yazila tasami nasarar cire hular karfen dake kan dabira. Sai ga kyakkyawar fuskarta ta baiyana a fili dogon gashin kanta mai haske da kyalkyali ya zuba har kasan kwankwasonta.
Dabira kuwa sai tasami nasarar cire layar dake wuyan yazila tayi wurgi da ita. Atare duk su biyun suka naushi juna da kafa a kirji kowacce tayi baya taga taga kamar zasu fadi kasa. Amma sai suka cije.
Adai dai wannan lokaci ne sarki raihan da sauran gaba dayan jama'ar dake fadar suka kame kamar gumaka saboda tsananin mamaki bisa ganin yadda kamannin yazila da dabira suka zo iri daya sak tamkar an tsaga kara yazila da dabira suka kurawa juna idanu kowacce jikinta na tsuma cikin mamaki.
Bisa mamaki kuma sai kowacce ta sunkuya ta dauki takobi suka ruga ga juna suna ihu irin na manyan sadaukai domin su sake kaurewa da sabon yaki. Lokaci guda suka sake tsayawa suka waigo baya sakamakon jiyo muryar humaira wacce ta taho da gudu tana daka musu tsawa bisa umarnin su dakata da wannan yaki. Ai kuwa sai suka kame suka kura mata ido. Da isowar humaira sai tayi sauri ta bude kofar kejin dasu yazila ke ciki ta kamo yazila da dabira ta rungumesu atare ta fashe da matsanancin kuka
Gaba dayan jama ar dake wajen sai suka rude da kabbara ™Nasiru Muhammad™
Cikin yanayin rashin fahinta dabira ta janye jikinta daga cikin na humaira ta dubeta tace. ” Yake ummina yanzu kina nufin kice yazila ce yar uwatace da nadade ina son na gani ? ” Humaira ta gyada kai tace. ” Kwarai kuma ga cikkakkiyar shaida ”. Nan take humaira ta tunawa dabira wannan riga ta tarihi tace, "kin shaida wannan riga kuwa ? Irin taki ce da kike ta ajiyarta.
Ki gafarceni yake 'yata hakiki na boye miki wani babban sirri na dangane da asalinki da kuma tarihin tawa rayuwar. "
Koda humaira ta zo nan azancenta sai hawaye ya zubowa dabira ta dubi yazila tace, "ke kuwa me yasa kika boye kamanninki agareni ? Yanzu ashe ke jini nace amma ban saniba, yanzu inda da tsautsayi da shikenan sai dayammu ya kashe daya".
Yayinda yazila taji wannan batu sai itama zuciyarta ta karaya, hawaye ya zubo mata. Kawai sai ta bude hannayenta biyu tana mai fuskantar Dabira.
Nan take Dabira ta fada kan kirjinta suka rungume juna kuma suka fashe da kuka a lokaci guda suna dada kankame junansu.
A wannan lokaci gaba dayan jama'ar dake fadar suka cika da tsananin mamaki bisa ganin yadda Jaruma Dabira ta rungume babbar abokiyar gabarta.
Bayan dabira da yazila sun dan jima a rungume da juna kuma fadar tayi tsit kamar babu mai rai acikinta, sai yazila ta janye jikinta daga jikin Dabira ta dubeta cikin murmushi tace, "yake 'yar uwata kiyi sani cewa tun daga ranar da nazo garin nan naku naga irin yanayin rayuwarku naga ya banbanta da irin tamu ainun akan adalci,karamci da zaman lafiya, sai naji nakamu da sha'awar wannan addini naku Ina son yanzu take ki shigar dani wannan addininaku. Ina son yanzu take kishigar dani cikin addinin".
Koda jin haka sai Dabira ta cika da tsananin farin ciki batare da bata lokaci ba Dabira ta biyawa yazila kalmar shahada ta maimaita.
Koda sauran jama'a suka ji YaZILA tayi kalmar SHAHADA, sai suka rude da kabbara. Shi kansa sarki Raihan bai san sa'adda yakama murmushi ba saboda farin ciki.
Nan take sarki RAIHAN maya shiga cikin kejin ya kamo hannun DABIRA da YAZILA yajasu suka tafi izuwa cikin gidan sarauta, HUMAIRA nabiye dasu.
A sannanne fadar ta watse kowa ya kama gabansa kai tsaye sarki raihan, humaira, yazila da dabira suka wuce har izuwa turakar sarki raihan suka zauna.
Zamansu keda wuya sai wadansu likitoci mata guda biyu suka hau duba Yazila da Dabira suka samusu magani a fuskokinsu inda jini yafito. ™Nasiru Muhammad™
Bayan sun kammala aikinsu na likitoci sun fita sai Sarki Raihan ya dubi Yazila da Dabira cikin murmushi yace, "ya ku wadannan zaratan jarumai kusani yau ni da mahaifiyarku muna cikin matukar farin ciki bisa ganin yadda allah ya hadaku har kuka gane juna.
Tabbas shigowar yazila izuwa cikin addinin allah cigaba ne babba a garemu. Yanzu dai kafin na yiwa yazila bayanin halin da muke ciki ke humaira sai ki basu tarihin rayuwarki da yadda yazila da Dabira suka rabu tun suna jarirai, har izuwa lokacin da kika gudo izuwa nan kofar birninmu tare da mijinki aka kashe shi a gaban idanunki".
Batare da bata lokaciba Humaira ta kwashe dukkan labarinta ta zaiyane wasu yazila.
Ai kuwa tana gama bayar da labarin, Yazila da Dabira suka fashe da matsanaicin kuka saboda bakin ciki kuma suka harzuka ainun.
Cikin tsananin fusata Yazila ta mike tsaye ta dubi Dabira tace , "yake 'yar uwata kizo mu tafi izuwa birnin kisra yanzu domin mu dauki fansa akan sarkin kisra da sarkin yakinsa. "
Koda jin wannan batu sai dabira ta kama kafadun yazila tace, "yake 'yar uwata kiyi sani cewa zuwa da shiri yafi zuwa da wuri.
Ina tabbatar miki da cewa ahalin yanzu wadannan abokan gabar tamu ba a zaune suke ba, harma sunyi gagarumin shirin yaki sun taho nan garin domin su baje wannan birnin namu. Labari ya riskemu....."
Kafin dabira ta gama fadin abinda ke bakinta sai sarki Raihan ya tari numfashinta yace, "yake Dabira ai wannan jawabi bana bane, nawane".
Dabira tayi murmushi tace, "ka gafarceni yakai abbana hakika na wuce gona da iri".
Shima sarki Raihan sai yayi murmushi sannan ya dubi yazila yace, "yake 'yar uwar Dabira kiyi sani cewa a halin yanzu a ko yaushe abokan gaba zasu iya baiyana a kofar birninmu kuma labari ya riskemu cewa sun zo da mayaka masu tsananin yawa da ya wuce misali domin har gudummawar mayaka suka samu daga sauran kasashen makwabtaka.
Tabbas yanzu bamu da wani zabi wanda yafi mufita mutari abokan gabar nan tun gabannin su iso".
Koda sarki raihan yazo nan azancensa sai yazila ta dubi Dabira tace, "yake 'yar uwata kisani cewa nice sarkin yakin birninmu kamar yadda kike sarkin yakin nan birnin, saboda haka nasan dukkan sirrin mayakanmu da irin yanayin yakinsa, lallai zan bayar da gagarumar gudummawa a wannan yaki daza ayi kuma na tabbatar da cewa ba karamar barna zan yiwa su sarki Daksur ba.
Babban burina shine, na kashe sarkin yaki da sarki Daksur da hannuna".
Koda jin haka sai Dabira tayi murmushi tace, "ni kaina burina kenan domin dole ne mu dauki fansa akansu bisa bakin cikin da suka jefa mahaifiyarmu a ciki.
Ya ke 'yar uwata tunda dai yanzu allah yasa kin karbi addinin musulunci na san cewa zuciyarki zata sake kekashewa ga barin tsoro kuma zaki sami kwarin gwuiwa fiye da da can, saboda haka ina ganin idan muka hada karfi da karfe ni dake a wannan yaki zamu iya samun nasara akan abokan gaba ".
Kafin yazila ta budi baki tace wani abu sai sarki Raihan ya tari numfashin Dabira yace, "ba haka bane yake 'yata,ke dai kawai munemi taimakon allah, amma ai karfinmu ko dabarar mu baza su sa musami nasara ba akan makiya ba domin na tabbatar da cewa suma baza su fito ba kai tsaye sai da kyakykyawan shiri irin wanda basu taba yin kamar saba.
Yanzu abin da nake so dake yake Dabira ki tafi tare da 'yan uwarki yazila ki tara dukkan mayakan kasar nan ku fara shirye shiryen dabaru na yaki wanda yakamata kuyi, nima yanzu zan je na tara dukkan 'yan majalisata domin mutattauna akan wannan yaki, amma dai kusani nine wanda zan jagoranci wannan yaki inyaso kubiyu kurufa min baya idan allah yasa narayu abayan wannan yaki ™Nasiru Muhammad™ kuma nasami nasara za a daura aurena da mahaifiyarku domin mun daidaita junanmu".
Sa'adda sarki raihan yazo nan a jawabinsa sai yazila da dabira suka kamu da tsananin farin ciki basu san sa'adda suka rungume sarki ba a tare lokaci guda suka sumbaci goshinsa.
Batare da bata lokaci ba Yazila da Dabira suka fice daga cikin dakin da sauri suka nufi wani bangare daban na gidan sarauta inda suka iske wani barde a tsaye cikin shigar yaki.
Dabira ta dubi Barden tace, "ma za ka busa kahon tara mayaka domin yanzu nake son mu shirya yadda zamu bullowa wannan yaki". Koda jin haka sai barden yacika Umarni.
Ai kuwa nan take dakaru suka dinga tuttudowa daga wajen gidan sarauta suna rugawa izuwa filin fada suna taruwa da jeruwa a sahu-sahu.
Wannan shine abin yafaru abirnin misra bayan jaruma yazila taga mahaifiyarta da 'yar uwarta Dabira kuma ta karbi addinin musulunci.
*** ***
A can birnin kisra, bayan sarkin yaki da sarki Daksur sun yi bincike a cikin halwar tsafi sun ga duk abinda ya faru ga jaruma yazila wadda ta bijire musu kuma tazama babbar abokiyar gabarsu sai hankalinsu ya duguntsuma ainun domin sun tabbatar da cewa aikin dake gabansu ba kadan bane.
Bisa wannan dalili ne sarki daksur yasa aka shiga sauran kasashen kafirai dake makwabtaka don neman gudummawar Dakarun yaki. Duk sarkin da wasikar ta iskeshi sai yaba da hadin kai ya aiko da dakarun masu yawa da makamai da kuma isasshen guzuri.
A yamma da birnin kisra akwai wata babbar kasa mai suna tashwar.
Birnin tashwar na karkashin mulkin wani sadaukin saurayi...


Read / Download BAKIN ARTABU Book 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album