Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

we should fight saboda Allah ba wai saboda wani ɗaukaka ba, most of us here na tunanin idan munyi yaƙi kuma muka koma gida lafiya then zamu tadda babban muƙami na jiran mu, da yawan mu sabida kuɗi muke fitowa yaƙi ba sabida Allah ba, how on earth then muke tunanin samun nasara, never consider cewar sun fimu makaman yaƙi or sunfi mu yawa ba zamu iya kawo ƙarshen su ba, most of us abin dake durƙusar damu kenan, am not a citizen of this country but a shirye nake da kare rayukan mutane da dukiyoyin su tare da taimakon Allah, if i can leave my country zuwa nan ƙasar taku and fight da zuciya ɗaya then ku mai zai hana ku yin fiye da hakan, ƴan uwan ku ake kashewa, ƴaƴan ku ake kashewa, iyayen ku, ƙannen ku, abokan ku duk su ake kashewa, yaran da basuji ba basu gani ba, talakawan da basu da haƙƙin kowa akan su su ake kashewa akan laifin da wasu gur'batattun manƴan ƙasa suke aikatawa, we all need to wake up, ba zamu cigaba da zuba ido muna gani ana kashe innocent souls yayin da muke da ƙarfin dakatar da hakan ba, we all need to fight dan samun kwanciyar hankali, we need to put an end to those criminals muddin muna son kwanciyar hankali, ya zama dole ne mu cire son kai da son zuciya a zuƙatan mu, we can't watch our people die anymore, enough is enough we all need to wake up, we are called soldiers and we are all known as heroes of all time, FEAR is the only thing downgrading us right now, we have to fight our fear and face those bandits and show them that we are heroes and that heroes never get scared, we all need to work together as a team, we should fight with our heart ba dan wani abu ba, we should fight for GOD sake, only then we can achieve our goals and only then our children and younger ones will love to be like us oneday."



Duk miƙewa sukayi tare da fara tafawa iya ƙarfin su cike da jindaɗin yadda ya sake ƙarfafa musu guiwa, sosai sukejin zasu iya gamawa da ƴan ta'addan cikin kwana ɗaya, yakamata ace suma sun zuciya yanzu sun ɗau fansar ran wadanda aka kashe sannan zasu cire tsoron komai su sanƴa Allah a ransu sannan su yarda da cewa shine zai taimake su ya kuma kare su da dukkanin kariyar sa, ta haka ne kaɗai zasu ci galaba akan wadannan ƴan ta'addah da basa ƙarewa.



Hannu ya ɗaga musu nan duk suka tsagaita da yin tafin kowanne na komawa mazaunin sa.



Omar dafe kujerar dake gaban sa yayi tare da ɗago idanun sa ya shiga bin kowannen su da kallo, kafin daga bisani yace "There is one more thing da nakeson faɗa."



Duk shiru sukayi suna saurarar abinda yake shirin faɗa, nan ya ɗago yace "Duk wani wanda ya san yana da alaƙa da wannan ƴan ta'addan should step out" ya faɗa cikin muguwar tsarewar da ya daɗe baiyi ta ba.



Duk kallon juna kowannen su ya shiga yi.



"Or else, i will point them out, and when i do so, nothing will stop me from killing the hypocrite."



Tuni wasu suka fara zazzare idanu a cikin su, nan Omar ya sake cewa "I saw you making calls, and i saw you with one of the bandits, let me repeat myself for the last time, that person should not let me point him out or else he die" ya faɗa yana fito da ƴar ƙaramar bindiga a bayan aljihun shi.



Kan kace kwabo tuni har wasu biyu sun miƙe tare suna zazzare idanu cike da rashin gaskiya.



Murmushin gefen baki Omar ya saki, kafin ya shiga bin su da kallo inda duk marasa gaskiyan suka fara miƙewa dan kuwa duk a tsarge suke though basu san wanene ya gani a cikin su ba, sai dai jin yace idan ya fitar da koma wanene zai harbi mutum har lahira ya sanƴa su fara bayyana kansu.



Murmushi Omar yayi ganin duk sun mimmiƙe, dan kuwa bai ta’ba kama wani da ɗan ta'addah a cikin su ba, sai dai ya san da cewa dole akwai masu fitar musu da sirri shiyasa ƴan ta'addan ke saurin gano inda suke suna fito musu suna kashe su.



"Seize them" ya faɗa nan wasu daga cikin sojojin suka mimmiƙe tare da kama su wanda aƙalla zasu kai su shida akayi gaba dasu.



Duk shiru sauran sukayi tare da zubawa Omar da kansa ke sunkuye idanu, sosai yakejin idanun sa na zafi kansa na wani irin sarawa sakamakon rashin bacci, ga kuma surutun da yayi, cike da dauriyar da ba zaka ce wani abu na damun sa ba ya ɗago yace "You see them, irin su ne ke jawo mana masifu da bala'i, irin su basu cancanci zama sojoji ba, they don't only betrayed aikin su but their self and nation at large, irin wadannan ne za'a basu tsaron dukiya da rayukan mutane, we have plenty of them, i know plenty of them, and aduk sadda wani abu ya haɗa ni dasu i must make sure i expose them no matter what, bana haɗa inuwa ɗaya da munafukai musamman idan ta ’bangaren aiki na ne, those bandits know any of our plans shiyasa suke kashe mu so easily ba tare da sun sha wuya, but that is over from today insha Allah, we must put an end to all this zuwa gobe insha Allah, zamu canza spot ɗin zama yanzu, we should move to another place, muje mu gama duk wani shirye-shiryen mu a chan, and those villains we will deal with them later, come on everyone let's move" yana faɗin haka yayi gaba nan duk sauran suka miƙe sukaje suka fara shirin canza spot ɗin zama.
[9/23, 9:44 PM] My Love: ©️AmjadJiddher

💋BANI DA ZABI💋
( I have no choice)

As I said early duk yanda book dinan yazo maku ku karba,saboda na riga na tsara shi a haka.

Heart breaking episode 🥺💔

045...*







*2 WEEKS AFTER*







________Yau satin su Omar biyu kenan a cikin wannan jeji inda kullum abu ɗaya suke fama dashi shine yaƙi da ƴan ta'addan nan.



Sosai sukayi ƙoƙari wurin rage kaso 70 cikin wannan ƴan ta'addan, inda a yanzu shugaban ƴan ta'addan kawai suke hari, sai dai kama shi ba abu mai sauƙi bane shiyasa suke kama wasu daga cikin yaran nashi dan samun information dangane da inda yake ’boye.



Wani daga cikin yaran suka tsare a gaba suna tambayar sa inda shugaban su yake, sai dai taurin kai irin nasa koh kaɗan yaƙi bari ya faɗi gaskiya duk kuwa da azabar da ya sha.



Ganin bayida niyyar faɗin gaskiya ’bata musu lokaci kawai zaiyi ya sanƴa Omar cewa "Kill him."



Babu ’bata lokaci wani soja ya saita kansa tare da basa alburushi ɗaya take ya faɗi ya mace.



Wani daga cikin yaran aka sake ɗaukowa wanda duk suke zazzaune a tsare tare da tambayar sa inda ogan su yake.



Washe korayen haƙoran sa yayi cike da bushewar zuciya yace "Sai dai fah ku kashe ni nima amma alƙawari na ɗauka zan kare uban gida na da dukkanin rai na."



"Kill him" ya faɗa take sojan nan ya harbe kansa ya faɗi ya mutu.



Wani aka sake ɗaukowa aka zaunar dashi, saita bindigar sojan yayi a kansa tare da tambayar sa inda ogan su yake.



Sosai jikin sa ke rawa tsoro duk ta cika masa zuciya ga kuma ƴan uwan sa wadanda suka ƙi faɗan gaskiya aka kashe su.



"Talk" sojan ya daka masa tsawa.



Cike da kyarma yace "Zan... zan faɗa, amma dan Allah kada ku kashe ni inada iyalan da nake ɗaukar nauyin su a gida, i have a wife and a daughter idan kuka kashe ni zasu shiga wani hali" ya ƙarashe cikin kuka.



Kallon Omar da ya tsare fuska yana kallon mutumin sojan yayi, kauda kai Omar yayi yana gyara zaman shi tare da ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya.



Ganin haka ya sanƴa sojan nan sake saita masa bindigar da kyau yace "I won't kill you if you tell the truth."



Cike da tsoro ya fara bada bayanan inda ogan nasu yake inda wani soja kuma yake jotting duk abubuwan da ya faɗa cikin takarda har ya gama bada bayanan.



Tasowa Omar yayi ya amshi takardar tare da karance dukkanin bayanan, damƙe takardar yayi a hannun sa tare da juyawa ya fice, ba tare da wani damuwa ba wannan sojan ya saita kan wannan mutumin ya harbe shi har zuwa lahira, haka ma sauran da suka rage a tsare.



Omar studying ɗin location ɗin yake, tabbas ba ƙaramin tazara bane tsakanin su da inda mugun yake, ba kuma ƙaramin wuri mai hatsari bane inda yake ɗin, but koh da kuwa zasu rasa ransu ne sunyi alƙawarin kawo ƙarshen duk wani azzalumi muddin al'umma zata zauna cikin ƙoshin lafiya.



Sake ɗaura ɗamarar wata sabuwar tafiyar sukayi suka kama hanƴar zuwa neman wannan shugaban ƴan ta'addan nan.



Sunyi tafiyar kwanaki kusan biyar kafin su iso jejin da yake, wani irin deadly jeji ne dake tsakanin ƙasar Iraq da Iran, duhun jejin kaɗai ya isa ya firgitar da ruhin ɗan Adam, ga kuma wani irin uban tekun da ya zaga jejin baki ɗaya ya sanƴa shi tsakiya.



Yaɗa zango sukayi dan hutawa, tare da shirin cikin tsakar dare zasu yiwa wannan ƴan ta'addah dirar mikiya.



Omar kasa bacci yayi cikin wannan daren, tunanin yadda rayuwar sa ta kasance kawai yake, bai ta'ba tunanin zai iya kaiwa warhaka a raye ba bayan doguwar gwagwarmayar da suka sha a baya, da tunanin yadda zasu kawo ƙarshen wannan ɗan ta'addan fal cikin zuciyar sa har dare ya ratsa sosai, lokacin har wasu daga cikin sojojin sun farka daga ƴar guntuwar baccin da sukayi sun fara shirye-shiryen attacking.



Omar da idanun sa sukayi kamar na wani mai shaye-shaye tsabar rashin bacci miƙewa yayi ya hau zaga jejin yana duba wasu abubuwa.



Bai dawo ba har sai da yaran suka gama shiri, kasancewar shi kaɗai ne yanzu jagoran su ɗayan Captain ɗin bai taho ba sakamakon mummunar raunin da akayi masa.



"All done sir" wani soja ya faɗa.



Kai Omar ya jinjina yace "Let's move."



Tafiya suka kama kowanne cikin shirin attacking, ta wata tsohuwar gada da kiris ya rage ta rabe biyu ta tarwatse tsabar tsufar ta suka bi izuwa cikin ainihin dajin.



Sunyi tafiya mai nisan gaske

Cike da takatsantsan irin na aikin su suka ƙaraso inda wannan mutumin yake, wani tsohon gini mai girman gaske ne ɗaya tal a jejin, inda yaran sa ke kai komo kowanne da bindiga a hannun sa.



Hannu Omar yayi wa mabiyan nasa suka samu suka la'be jikin bishiyu.



Saita abin maganar dake kunnen sa yayi yace "We won't attack now, seems like suna cikin shiri koh da yaushe, i will distract their attention after that then you take over."



"Yes Sire" suka faɗa kasancewar suna jin abinda yake faɗa ta abin dake kunnen su.



Sosai Omar ke ƙarewa wurin kallo, inda ya hango empty spot ɗin da babu kowa a ta wurin.



Lalla’bawa yayi cike da kwarewar aikin sa ya isa ga wannan wurin, hango wasu na zuwa ya sanƴa shi saurin la'bewa yana rataye bindigar sa a kafaɗa tare da zaro wuƙa a ƙasar rigar sa.



Isowar su keda wuya yaci musu ta gaba baiyi wata-wata ba ya lumawa ɗaya wuƙar nan a gefen wuya, kafin ɗayan yayi wani kwakkwaran yunƙuri tuni ya haɗo kansa da gini yana yanke masa wuya da wuƙar.





Lalla’bawa ya cigaba dayi yana kutsa kai cikin gidan, silently yake kashe su ɗaya bayan ɗaya wurin amfani da hannun sa ya murɗe musu wuya kokuma da wuƙar sa.



Wani ya hango shi kaɗai yana ta patrol take ya taka cikin sanɗa, ya isa gareshi, ɗan bubbuga kafaɗar sa Omar yayi, yana juyowa ya gwara masa kansa tare da murɗe masa wuya take ya mace, jan gawar sa Omar yayi zuwa wani lungu ya cire kayan jikin ɗan ta'addan zuwa jikin sa, tare da rufe fuskar sa kamar yadda sukeyi ba zaka ta'ba zaton ba shi bane ba.



Bindigar sa ya ɗauka ya fito ya hau kutsa kai cikin gidan, saita abin kunnen sa yayi yace "Ku fara aikin ku."



Bai wuci da ƴan seconds ba ya fara jiyo harbe-harbe, kan kace miye kuma suma ƴan ta'addan sun san da zuwan sojojin.



Duk fara fitowa sukayi suna ratsa Omar da yayi basaja cikin su ba tare da sun gane cewar ba ɗan uwan su bane ba.



Da haka Omar ya isa ga Main inda ogan nasu yake, dai-dai lokacin da ya fito kenan shima da bindiga a hannun sa, karo sukaci da Omar, take ya waigo cike da hargowa cikin muryar larabci yake cewa "Bakada hankali ne, mai kakeyi anan ƴan uwan ka na chan suna faɗa, so kake ka mutu."



Kallon sa Omar keyi tabbas shine wannan ɗan ta'addan nan da akayi shekaru da shekaru ana neman sa, kallon fuskar sa dake ɗauke da ido ɗaya Omar keyi yana dunƙule hannayen sa cike da wani irin ’bacin rai zuciyar sa na wani irin tafarfasa.



"Move" ya daka masa tsawa, Omar ganin kada plan ɗinsa yayi faliling ya sanƴa shi saurin wucewa yayi gaba.



Omar gani yayi yabi wani lungu maimakon yayi hanƴar da kowa ke bi, ba tare da ’bata lokaci ba yayi reverse ya dawo tare da fara bin sa a baya cikin sanɗa da alama dai so yake ya tsere.



Binsa Omar yayi har izuwa wani wuri, Inda ƙofa ce ta baya kuma wurin ba'a jiyo hayaniyar harbi sosai, da alama dai ta nan yakeson tserewa.



Buɗe ƙofar yayi ya fita cikin gudu yana waige-waige, take Omar yayi saurin mara masa baya, idanun sa ne suka sauƙa kan Omar dake biyo sa.



Dakatawa yayi yana kallon Omar yace "Bakada hankali ne, zaka dinga biyo ni, na biya ka ne dan ka dinga tsaron lafiya ta, koh so kake ka mutu yanzun nan."



Omar tsaye yayi yana kallon sa kafin kuma a hankali ya kai hannu ya yaye rufar da yayi wa fuskar sa.



Kallon Omar yake kafin kuma ya ƙece da dariya cike da mugunta, sai da yayi mai isar sa yace "Kana tunanin zaka iya ganin baya na ne, ba'a halicci wanda zai ga bayan Aliey ba, baku isa ku dakatar dani daga abinda nayi niyya ba, kunyi kaɗan koh sojojin wannan ƙasar sun kasa bale kai ƙaramin ƙwaron da aka ɗauko daga wata ƙasa chan" ya ƙarashe cikin hura hanci yana buga ƙirjin sa.



"Maybe you should say that in your next life" cewar Omar tare da ajiye bindigar hannun sa yana tunkaro shi.



Da gudu shima mutumin yazo take faɗa da ƙaurace tsakanin su.



Omar baiyi mamakin ƙarfi irin na mutumin ba koh kaɗan, haka suka cigaba da faɗar kowa na gwadawa ɗan uwan sa ƙarfin sa, sosai suka yiwa juna jina-jina.



Zaro wuƙa mutumin yayi a ƙasar wandon sa tare da saita gefen cikin Omar da ya kawo masa blow yana luma masa wuƙar.



Omar ji yayi numfashin sa ta ɗauke na wasu ƴan seconds lokacin da zafin wuƙar ta ziyarci duk ilahirin jikin sa, sosai jikin sa ya ɗau wani irin kyarma fuskar sa da ilahirin jikin sa duk sukayi wani irin jaa, zubewa yayi kan guiwowin sa idanun sa na ganin dishi-dishi, dariya mutumin ya fashe dashi cike da mugunta yana buga ƙirjin sa tare da hargowa kamar wani kura.



Ƙarasowa yayi yana zaga Omar ɗin yana wani irin hure-hure cike da alfahari da kanshi, riƙo kwalar rigar Omar ɗin da jikin sa ya gama sakewa yayi ya fara jansa a ƙasa har izuwa bakin gada inda ruwa ke gudana da ƙarfin gaske.



Komawa yayi ya ɗauko bindigar da Omar ya ajiye, da kyar Omar ya iya miƙewa kan guiwowin sa yana kallon mutumin da idanun sa dake gane masa dishi-dishi.



Dawowa mutumin yayi yace "Captain Omar, what a pity, the whole Captain Omar da ake ji dashi da kwazon sa a wurin aiki ne a haka, wa yace maka ana shiga gonan Aliey a fita da rai, lallai kayi matuƙar kuskuren fara hakan, yanzu kaga abinda ka jawowa kanka kana zaune ƙalau abin ka, ya kake tunanin zaka iya fita da ranka a wannan wurin yanzu, mutuwa zakayi dan kuwa babu mai fita da rai a duk lokacin da ya shigo fada ta."



Lumshe idanu Omar yayi, jikin sa na daɗa yin rauni, ƴar ƙaramar camera mutumin ya ciro daga aljihun sa, yace "Bara na kwashe ka video na nunawa duniya da dangin ka suga iriyar halakar da ɗansu kuma jarumin soja ya jefa kanshi, na tabbata zasu so sanin yadda jarumin ɗan su ya mutu koh ba haka ba?" ya faɗa cikin ƙecewa da dariya.



Kallon camera ɗin Omar da idanun sa ke rufuwa yana buɗe su da dukkanin ƙarfin sa yake, dan kuwa yayi alƙawarin ganin bayan Aliey kafin Allah ya ɗau ransa.



Hannu na rawa Omar ya kai hannu ƙasar wandon sa ba tare da sanin Aliey dake ta video yana surutai cike da shaƙiyan ci ba.



Sake maido camera ɗin yayi kan Omar bayan ya gama kwasar kansa kafin ya cigaba da faɗin "Na tabbata yanzu duniya baki ɗaya suna ganin wannan live video ɗin, sauran kuma na nuna musu yadda mutuwar ka zata kasance jarumi."



Da kyar Omar ya iya tattaro jarumtar sa ya miƙe tsaye kan ƙafafun sa yana tangarɗa, dariya Aliey ya fashe dashi yana kallon Omar ɗin.



Dafa kafaɗun sa Omar yayi kansa a ƙasa, Aliey ganin kamar babu abinda zai iya yi ne ya sanƴa bai ture shi ba dan a tunanin sa lokaci kaɗan ya rage masa ya mutu.



Omar lamo yayi kamar ba zai ɗago ba, damƙe allurar dake hannun sa yayi cikin abinda kuma bai wuci kiftawar idanu ba ya ɗago tare da da’ba wa Aliey wannan allurar a gefen wuya.



Wani irin ƙara ya saki cike da azaba yana jefar da camera ɗin, ɗagowa yayi tare da cire allurar daga wuyar sa, yunƙurawa yayi zai tashi yaji wuyar ta wani riƙe masa, kallon Omar yayi, nan Omar ya saki murmushi yace "I promise to put an end to you kafin na mutu, don't worry a hankali alluran zai bi duk jikin ka ya kashe duk wasu cells na jikin ka, wanda hakan zaiyi ajalin ka cikin minti ɗaya."



Waro idanu Aliey da koh ina na jikin sa ya saki baya iya ta'buka komai yayi, rarrafawa Omar yayi tare da ɗaukar camera ɗin yana kallo.



Murmushi yayi yace "A'eesha, please forgive me, i can't make it to be with you again, am sorry, am sorry Mom, am sorry Dad, please forgive me..." maganar tasa ce ta ƙaƙare sakamakon aman jinin da ya fara, yarda camera ɗin yayi yana cigaba da tari da aman jini "I Love You A'eesha" ya furta da tun ƙarfin sa take kuma ya faɗi anan wurin warwas babu alamun rai.



Dai-dai lokacin Helecopter ɗin sojoji ya iso wannan wurin ya sauƙo, ɗaukar Omar sukayi dama kuma gawan Aliey suka bar wurin.





********************





_______Aisha tun bayan faruwar wulaƙancin da ta yiwa Omar take kaffa-kaffa da ƴan gidan nasu, musamman ma Hajiya Kaka da Mama, su kuwa koh kici kanki basu sake ce mata ba.



Sosai ta takuru dan kuwa gani take kamar fushi koh haushin ta sukeji, nan kuwa duk tunanin ta ne ke bata hakan dan ita kanta tasan abinda tayi bata kyauta ba har ma takejin haushin kanta na aikata hakan.



Ita kaɗai ke zama a ɗaki tayi ta tunanin da batasan ranar yankewar sa ba, tunda Musty ya kawo mata saƙon da Omar ya faɗa masa a waya jikin ta ya sake yin sanƴi take kuma nadamar abinda ta aikata masa.



Dukda yau sati biyu da faruwar hakan kwata-kwata ta daina samun kyakkyawar sukuni, kullum tunanin ta bai wuci halin da yake ciki ba dukda kuwa tana matuƙar ƙoƙarin ganin ta yakice tunanin nasa daga ranta amma duk a banza.



Zaune take tsakiyar bed ta haɗa kai da guiwa, tunanin rashin ganin al'adar ta na wannan watan da batayi ba take, ɗagowa tayi ta duba wayar ta tare da sake duba date taga har 18 alhalin kuma a 15 yakamata taga period ɗinta, tunani tayi koh maybe canjin yanayi ne shiyasa lokacin zuwan nashi ya canza.



Tana nan zaune abin duniya duk ya ishe ta ga kuma faɗuwar gaba da takeji tun wayewar garin yau, haka nan ta yini babu wani kwakkwaran kwazo tattare da ita.



Da dare kuwa lokacin kowa na falo yana kallo sai dai babu Aisha da yanzu ɗaki ya zame mata wurin zama.



Shigowa Haiydar yayi falon fuskar nan tasa ɗauke da alamun tashin hankali, kallon ƴan falon yayi tare da duba abinda suke kallo tashar Zee World ne suna kallon shirin *This Is Fate* wanda ake nunawa ƙarfe tara zuwa goman dare.



"Lafiya ka shigowa mutane babu sallama, gidan kafirai kazo koh miye" cewar Hajiya Kaka cikin aika masa da harara.



Samun wuri yayi ya zauna, kallon Nusy yayi yace "Ke canza tashar nan zuwa Aljazeera.



Turo baki Nusy tayi dan kuwa koh kaɗan batason kallon shirin ya bar ta,



"A wane dalilin zata canza muna cikin kallon mu?" cewar Hajiya Kaka.



"Ina Aisha?."



Ta’be baki Hajiya Kaka tayi tace "Kai nan har tambaya kake inda take, tana chan ɗaki mana tunda ta zama matar kulle bata fitowa cikin mutane."



"Canza tashar nan zuwa Aljazeera nace" ya sake faɗa yana kallon Nusy.



Turo baki tayi tana ƙunƙunai ta tashi tare da ɗaukar remote ɗin ta canza tashar tare da juyawa cike da haushi zata koma ɗaki, abinda kunnuwan ta suka jiyo mata ne ya sanƴa ta dakatawa tana dawowa ta zauna.



Labarai ake nunawa kan faɗan dake wakana tsakanin sojojin Iraq da fitaccen ɗan Ta'addan nan Aliey wanda ya addabe su tsawon shekaru inda yau gashi Allah yayi ƙarshen sa yazo.



Karanta headline ɗin labarin tayi, take ta kwala wani irin ihu tare da furta "Inalillahi wa inna ilaihi raji'un" tana miƙewa tsaye tare da dafa ƙirji.



Haka ma falon ya ƙacame da kalmar "Inalillahi wa inna ilaihi raji'un."



Nusy kuwa tuni hawaye suka jiƙe mata fuska sharƙaf ganin an sanƴa hoton Omar an rubuta _Tragedy as Nigerian Army, Captain Omar Abubakar Sadik confirmed dead over Iraq crisis_ sai kuma Live video ɗin da Aliey ya kwasa ya biyo baya.



Babu abinda kakeji a falon sai kukan Nusy da Zahra sai kuma shessheƙar Hajiya Kaka.



Haiydar da idanun sa sukayi ja shiru yayi jikin sa yayi wani irin bala'in sanƴi sakamakon yadda mutuwar tayi mugun ratsa shi.



Aisha tunda ta jiyo salatin Nusy da ihun ta ta fito daga ɗakin hankali tashe zuciyar ta kamar zata faso ƙirji ta fito tsabar gudu.



Jaa tayi ta tsaya idanun ta akan TV ɗin, kasa ƙifta idanun ta da ta fara gani dishi-dishi tayi, ga kuma wasu irin hawaye da suka cika mata idanun taf, zuciyar ta na wani irin gudun kamar zai faso ƙirjin ta, jikin ta ne ya kama wani irin rawa haka ma bakin ta, wani irin razanannenn ƙara Aisha ta saki dai-dai lokacin da taga ya faɗi tare da furta cewar yana sonta, a matuƙar tsorace suka juyo suna kallon ta kan suyi wani yunƙurin kuwa tuni ta faɗi sume.
[9/23, 9:44 PM] My Love: ©️AmjadJiddher

💋BANI D ZABI💋
(I have no choice).

Ur comment make Am feel I no get problems 🔥😹❤️

AKACE SUTURA ITACE MUTUM!
Tabbas Wannan batun hHaka yake .
‘Yar uwa Ina kike sayan laces ? Na tabbata duk inda kike saya Bekai namu quality da kyau ba .
INA MATA MAABOTA KWALLIYA ?
INA MATA MASU JII DA KANSU TA FANNIN SUTURA ? GA DAMA TA SAME KU
NAZO MAKU DA SHAHARARRIYA KUMA FITTACIYA DA TA TSAYA TSAYIN DAKA DAN GANIN TA FITAR DA MATA YAN UWANTA KUNYA MUSANMAN MATA ‘YAN KWALISA WAYANDA BSAJIN KYASHIN FITAR DA KUDI KO NAWANE WAJEN GANIN SUN FITA KUNYA ,ZAKU SAMU DUK WANI NAU’IN LACES MASU MATUKAR KYAU DA QUALITY BASE NA ZUZUTA MAKU BA AMMAN TABBAS KUNSAN YANDA LAGOS LACES SUKE DA MATUKAR KYAU KO BAKI SANI BA NASAN ZAKIJI LABARI AWANI WURIN .YAR UWA KI FITAR DA KUDI KI FITA KUNYA LACE DIN DA ZAKI SAKA KIYI SHEKARU DASHI BATARE DA KIN SAKE GANIN IRINSHI AJIKIN WATA BA MAZA KU HANZARTA ZUWA WAJEN OUM ASHRAF DOMIN KU FITAR DA KANKU KUNYA KU TUNTUBETA A NUMBER WAYAR TA KAMAR HAKA 07086226402. DOMIN SAMUN NAKU A FARASHI ME MATUKAR SAUKI ,KAR KU JIRA ABAKU LABARI KAYANTA TESTED AND TRUSTED NE ,AKWAI DIFFERENT DESIGN HATTA PACKAGE NA ANKO

Please Login or Register in order to submit comment