Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Kula masa da maman saba?
Wayarsa ya d'auka yakira number munirat, bugu uku ta d'auka, tayi tunanin baizo qasar ba, saboda acan dinma da number sa yake kiranta, cikin 6acin rai yace "yau kinje kinga mama ne kinji ko tana buqatar wani abu?"

Munirat tafara kame kame, cikin borin kunya tace "yanzun Nan nake shirin zuwa ingano ta, Allah yasa de bacemaka tayi nayi mata laifi ba"


Baice mata komai ba kawai kashe wayar yayi, yadaga murya cikin fishi da 6acin rai ya kwalawa daya daga cikin masu aiki kira, jin muryar Mahmud Wakili yau da Kansa yana kiran me aiki yasa jikin masu aikin yakama karkarwa

Saboda ba kulasu yake ba,baya shiga shirginsu, idan yazo falon kowa nemansa kake karasa saide dagashi Sai mama, Amma yau gashi yana kira Kuma da alama akusa yake, ransa a6ace yake, cikin sassarfa wata yarinya ta qaraso, ya kalleta yace "jeki kiramin me kula da mama"(=F<
@&)

Cikin sauri ta juya zuwa Dakin Aisha.

Mama ta kalleshi tace "Aida karabu da'ita, yanzu kana 6ata mata rai zata dinga daure min fuska tana shamin qamshi, nagama lura haushi na takeji saboda Dan sabanin da muka samu rannan,nikuma hakan damuna yake narasa dalili"

'Yar aikin tana zuwa ta ganta cikin blanket, yaye bargon tayi,jikinta na karkarwa muryarta na rawa tace "Aisha kizo inji yalla6ai , yanason ganinki"

Aisha ko bude idonta batayi ba, saboda bayanta dayake mata mugun ciwo, ga ciwon qirji ko dogon numfashi takasa ja, ahankali ta bude Dan qaramin bakinta tace "banda lafiya..., kije kice masa banida lafiya bazan iya tashi ba"

Gaban yarinyar ne yafadi, yaushe zata Iya Kallan idon yalla6ai da Hajiya Mama tace musu Aisha tace bazata iya zuwa ba? To Amma ganin yanayin datake cikin yasa ta juya tafice daga d'akin cikin sanyin jiki, tana zuwa falon ta tsugunna qasa, kanta qasa tace "yalla6ai tana kwance, batada lafiya ne"

Cikin sauri mama tace "subhanallah.... Ashe shiyasa batazo ba"
Duk yanda mama takai da rashin kirki, tana tsoron jinya, bare Kuma Aisha datake bata kulawa yanda ya dace, ta juya ta kalli Shahaab tace"muje kadubamin ita Dan Allah, idan Kuma Asbiti zamuje saimu tafi yanzu"

Tsananin mamaki yakama Shahaab, Wai wacce irin yarinya mama tasamu haka? Yaga fuskar maman ta sauya alamun tausayawa, wacce yarinya ce me sa'ah haka?
Kallan me aikin yayi, har yanzu fuskarsa a daure take, yace"kije kice nace tazo"

Juyawa me aikin tayi cikin sauri Takoma Dakin Aisha, Badon ranta yasoba haka ta daure tatashi, Riga da siket ne ajikinta na atamfa,kayan sunyi mata daidai, hips dinta yayi dass acikin siket din, rigar yar qarama daidai da'ita,dan kwalin kayan yadan Zame alamun kawai dorashi tayi bai gama dauruwa ba, gashin kanta me santsi yafara futowa tagaban goshinta, futowa sukai zuwa falon, Bayan ciwon baya da qirji da takeji harda wata irin faduwar gaba da takeji tun safe.

Kanta yana qasa har suka qaraso kusa da mama, me aikin data kirata ta kalleshi tace "yalla6ai gata" sannan ta juya cikin sauri tabar falon

Hankalinsa yana kan wayarsa yana dannawa, Mama ta kalleta tace "sannu AISHA"

Jin sunan Aisha da'aka kira yasa yadago Kansa cikin sauri, Adede lokacin itama ta d'ago kanta ta kalleshi,(=F<
@&)

Idonsu ne yasarqe cikin na juna, cikin wata irin faduwar gaba Aisha ta bude bakinta, cikin zuciyarta tace "Shahaab...."
cikin sauri yatashi tsaye haryana wullar da wayar hannunsa.

Mama ta kallashi da tsananin mamaki tace "MAHMUD lafiya?"

Jin sunan da mama takirashi dashi ne yasa gaban Aisha yayi wata irin Fad'uwa,cikin tsananin mamaki ta motsa dan qaramin bakinta cikin sigar rad'a tace "MAHMUD?"










narasa ta cewa yau... <<
@&=


Idan kinsan baki Sai Shahaab ba kika karanta, wallahi tallahi ban yafe miki ba, nabarki keda ubangijinki, warana zai mana sakayya



0164549488
Amina muhammad
GTbank

08033300034





Amnah
'<
ASH~HAB




Kasa Bawa mama amsa yayi, Sai kallon Aisha dayake Idonsa sun furfuto alamun rashin gaskiya, cikin ransa yafara karanta "innalillahi wa inna ilaihirraji'un...."

Jin bai bata amsa ba yasa tasake kallon sa tace "SHAHAAB mekake kallo ne?"

Ahankali Aisha ta sunkuyar da kanta, cikin ranta tasake maimaita sunan SHAHAAB, ta tabbata de shine Mahmud Wakili.

Kansa ya sunkuyar qasa, jiyake kamar qasa ta bude yashige Dan kunya, tun haduwar idonsu na farko ko kadan yakasa hada ido da Aisha, mama ta janyo Aisha kusa da'ita tace "Aisha meyake damunki? Menene yake miki ciwo?" ta qarasa maganar tana Kai hannunta wuyan Aishan ko zataji zazza6i, cikin sauri kuwa ta janye hannunta tace "Subhanallah, aikuwa jikin naki da zafi sosai, zazza6i ne yake damunki?"

Magana takeson yi Amma kuka ne yakeson qwace mata, wani irin qullutun abu takeji ya tsaya mata a maqoshi Shahaab ya cuceta....tana bude baki da nufin magana saita saki wani irin kuka harda shashsheka.

Lokaci daya mama tasake rikicewa, tace"irin wannan kukan Aisha kamar anyi miki mutuwa, kinga muje Asbiti kawai, yafi sauqi"

Cikin tsananin kuka tace"mama Gara kibarni inmutu"
Kansa yana qasa, Amma jin wannan furucin Nata yasa ya runtse Idonsa, yasan cewa Dashi take.

Mama tayi ajiyar zuciya sannan ta sassauta murya tace "fadamin meyake damunki?"
cikin kuka tace "bayana ne yake ciwo, da qirjina, Kuma wani irin abu nakeji aciki"

Mama tasaki salati kamar de yanda Hajja takeyi,ta qare da fadin"innalillahi... "

Tajuya ta kalli Shahaab da Kansa yake qasa har yanzu, saide idanunsa sunyi wani ja kamar me shirin kuka, tace" dubamin ita gani karfa aje ko cancer ce"

Jin sunan jinyar data fada yasa Aisha tasake sakin wani irin kuka, Shikuwa Shahaab Kansa aqasa ya Girgiza wa mama Kai, mama tace"tsoronta kake jine?"

Kafin yabata amsa ta janyo Aisha jikinta, tasaka hannu tayi qasa da zip din rigarta, sannan tayi qasa da rigar, Allah yaso tasaka vest,Amma babu brezia, lokaci daya baqar vest dinta tafuto fili, mama ta kalli Shahaab tace"duba kagani Shahaab"

Runtse Idonsa yayi,=mama taqi tadena Kiran sunansa, magana daya biyu saita kira sunansa, taqi tagane cewa yau bayason Kiran sunan Nan nasa.
Ahankali yadago Kansa ya kalli inda take, Idonsa ya sauka akan tsayaiyun qirjinta, tunda yake zuwa garinsu , kullum cikin hijab yake ganinta, baita6a ganin baiwar da Allah yayi mata ta qirjinta ba,kasa janye Idonsa yayi daga kallon su, jiyake kamar ya fusgota jikinsa kozaiji dadin lallashin ta

Daqyar ya Girgiza Kansa yace "babu komai mama,basai na dubaba nasan ba cancer bane"

Mama tace "a a ta6a kaji de, kar naje yar mutane ta gamu da cuta awajena"

Har zuwa wannan lokacin Aisha taqi yarda tasake kallon sa, kwata-kwata jitayi batason ganinsa, ahankali tafara Girgiza wa mama Kai jin furucin datayi, cikin tausaya wa mama tace"bari Aisha,Mahmud likita ne,zai dubaki yanda yakamata, idan mukaje Asbiti ma kina fadar abinda yake damunki kamar yanda kika fadamin yanzu, to suma dole zasu duba, a Asbiti wajan doctor zan tura ki bansan mezai miki ba, Amma shi wannan agabana yake, Kuma akan idona zai dubaki, idan ba cancer bane shikkenan"

Tajuya ta kalleshi tace"dubata"

Ahankali yafara takowa kusa da'ita,wani irin baqin ciki taji yakamata, meyasa mama zata mata haka? Shikkenan daga cewa tanajin abu me zafi a qirjinta Sai ace yazo yaduba ta? To me zai duba? Bata gama tunanin taba taji yad'ora hannunsa akan vest dinta, runtse idonta tasake yi wasu hawaye masu zafi suna sake zubo mata, wani irin kuka tasaki lokacin dataji hannunsa akan boobs dinta.

Shi Kansa hannunsa rawa yake kamar yana ta6a wani abu me shocking, duk da tasaman vest yad'ora hannun nasa, hakan bai hanashi jin wani irin mugun dadi ba, wani irin abu yaji tundaga Kansa har zuwa tafin qafarsa, lokaci daya yanayin sa yafara sauya wa, baisan lokacin daya dora d'ayan hannunsa akan dayan Breast dinba, murzawa yake ahankali yana jin wani irin dadi na fitar Hankali.
Hawaye ne suke zuba daga idonta, gashi mama ta riqeta, tanaji tana Gani mutumin daya cuceta, ya yaudare ta, shine yake ta6a mata nono, idonta a rufe suke taqi yarda ta bude idonta bare ta kalleshi, tabbas tayi Dana sanin mu'amula da mutum mayaudari kamar sa.
Shahaab kuwa gaba daya ya manta mama tana wajan,dede nipples dinta yake murzawa ahankali,duk yanda zuciyar sa take hanashi kwata-kwata yakasa dainawa, jiyake kamar ya fuzgota jikinsa yad'ora bakinsa akansu(=F<
@&=3)

Adede wannan lokacin munirat ta riskesu, dama tazo duba mama ne saboda Kiran da Shahaab yayi mata awaya yana fada ko taje tagano mama yau?

Gabanta ne yayi wata irin faduwa ganin mama riqeda baquwarta, shikuma hannuwansa duka biyun suna kan qirjin yarinyar yana murzawa, idon yarinyar ta kalla taga idonta a rufe, Amma bata gama tantance wa dadi takeji yasa tarufe idon, kokuma kuka takeyi ba,lokaci d'aya taji ta tsani yarinyar, yanzu me mama take aikata wa haka?

Kuka ta Fashe dashi, sannan Tajuya tafice da gudu daga falon, mama tabita da kallo ta saki tsaki tace "kishin banza,kishin wofi,inda ace nabarshi yana zuwa asbitin saiki hanashi duba kowacce mace kenan, ni Dana badan iska bane"

Tajuya ta kalli Aisha cikin fada tace "kekuma koki tsaya ko cancer ta kama ki, Dana likita ne badan iska ba"

Tajuya ta kalli Shahaab Wanda kwata kwata baisan ma mama tana magana ba,cikin qaguwa da abinda yake tace "Wai baka gama bane?"(==H)

Cikin sauri yadan kalleta sannan cikin shaqaqqiyar murya yace "Ina dubawa ne...."(=F<
@&)

Ahankali yasake kama breast din Gaba dayansa, Saida yasake murzasu sosai, sannan ya janye hannunsa Badon yaso ba, ya kalli mama, cikin wani irin yanayi na kasala da sha'awa yace "ba cancer bane mama, ciwon Bayan ma nafi tunanin mp ne ya janyo haka,zanyi magana akawo mata magunguna"
Yana fadar haka yayi sauri yafice daga falon cikin tashin hankali, yana cikin yanayi, gashi mama tasake sashi yafada cikin yanayin da yafi nada.

Kai tsaye d'akin sa yawuce bai nufi inda munirat take ba, yana shiga ya kulle Dakin tare zubar da duk kayan dayake gaban mirror, shi shi kadai yake watsi da kayan Dakin su fillo da bedsheet din Dakin babu abinda baiyi wurgi dashi ba, cikin tashin hankali ya zauna akan gado tare hargitsa sumar Kansa, cikin wata irin murya kamar zai Fashe da Kuka yace "innalillahi wa inna ilaihirraji'un.... Ya Allah, komai yazo qarshe, na tabbatar tadena yarda Dani...."

Wayarsa yadauka yakira Ramadan, bugu daya ya amsa, cikin rawar murya yace "Ramadan komai ya lalace, yau maaama nagani acikin gidana Ramadan"

Daga can 6angaren Ramadan yace "innalillahi... Garin Yaya? Metazo yi Abuja Kuma?"

Bai iya Bawa Ramadan amsa ba Sai wani abu da yaji me dumi yana sakko wa akan kumatunsa, hannunsa yakai ya goge Hawayen, sannan yace "yarinya tana ganin girmana, kunsa nayi mata qarya, yanzu nasan bazata sake yarda Dani ba, kunyar kallon idonta nake Ramadan, saida nace zan fada mata gaskiya, banga amfanin 6oye mata gaskiya ba, kasani nayi mata qarya"

Cikin kwantar da Hankali Ramadan yace"amma aika gane tana sonka da gaskiya ko?"

Haushi ne yasa Shahaab yakashe wayarsa, kwanciya yayi akan gadon tareda dora hannunsa akan mararsa, wannan masifa Dame tayi kama?(>)


(idan kinsan baki biyaba kika karanta Allah ya'isa nah, Kuma bazan taba yafe miki ba, tun Bana Allah ya'isa kunsa nafara, duk wadda ta takaranta inde bata biyaba wallahi itada MAHALICCINTA)


******


Har dare, Aisha tana kuka, idonta yayi jajir saboda kukan da Tasha, abincin da aka kawo mata da magungunan ko Sha batayi ba, daqyar ta lalla6a tayi sallah sannan ta rafka uban tagumi hannu biyu, hawaye ne yasake zubo mata lokacin data tuna da Hajja, inda tare Takeda Hajja ko hannunta bazata Bari ata6a mata ba, gashinan yakama Sai murza mata qirji yake gaba daya Sai ciwo suke mata, hartana cewa danta ba dan iska bane Inba Dan iska bane shida akace yata6a yaji menene aciki, to menene zaisa yakai hannunsa kan nipples dinta?.

Hawaye ne suka sake zubo mata, dole zata tafi gida, bazai iyu ta zauna Ana ta6a mata nono ba, gashinan yayi mata da zafi Sai ciwo suke mata, idan taci gaba da zama a gidan tsaf wataran zata masa abinda bai Ta6a zato ba, dama can bada gaskiya yake mu'amulantar taba, hauka da shirme yasa takasa gane cewa me Shahaab zaiyi da yar qauye kamar ta?
Dama yaudara ce takawo shi, tunda dayazo ma 6oye mata koshi waye yayi, hatta garinsu ce mata yayi shidan maiduguri ne, yace bashida aure ashe yana mata, haka Kuma yaqi yarda yahadu da mahaifinta koda yaushe saide Yakirata mota koda wasa bai ta6a cewa yanaso yaga Abban taba Sai lokacin dayazo yace mata zaiyi tafiya, Shima Dan yasha bakinta ne shiyasa ya shirya mata wannan yaudarar,kaiii yaudarar tayi yawa, tasa hannu ta share Hawayen idonta, Sai yanzu ne takejin haushin kanta, taji ta tsani kanta sakamakon tunawa datayi har bijrewa iyayenta tayi, saboda shi, daga qarshe ga abunda yafaru, dama ance duk Wanda baiji maganar iyayensa ba,to yana tareda matsala, tun kafin taci gaba da ganin wannan matsalar Gara Takoma gida ta roqi iyayenta gafara sannan Kuma tashawo kan inusa, tana zaune tana tunani har qarfe shadaya da rabi na dare yayi batare data Sani ba

Shabiyu daidai yafuto daga d'akin sa, tun Bayan barinsa part din mama daya shiga daki baisake futowa ba Sai yanzu, Kai tsaye d'akin munirat yawuce, tana kwance akan gadonta, ta dora hannunta daya akan goshinta Wanda yake mata barazanar rabewa biyu, idonnan ya kumbura suntum saboda kuka, tanajin shigowar sa Amma tayi masa mursisi ta nuna kamar batason yashigo dakinba, zama yayi akan gadon tareda janyo ta jikinsa, ahankali yabude bakinsa yace "munirat...."

Cikin sauri ta qwace jikinta tareda matsawa can Gefe,
Bai saurare taba yajata jikinsa ya rungume ta, kuka tasaki Mai cin rai, baice mata komai ba Sai bayanta daya Dan bubbuga alamun tayi shiru, daga Nan yajata suka kwanta, tun yana jin kukan ta har yaji tayi shiru jikinta yasaki alamun tayi bacci.

Har qarfe daya saura Idonsa biyu bai runtsa ba, Ada idan yadawo daga tafiya qarfe goma yayi yawa ya kwanta, Amma yau shine har daya saura Idonsa ko alamun bacci babu, inda Dane yadade bai kasance da matarsa ba to kwana biyu ne zuwa uku, idan tashiga hannunsa kuwa saita koka, Amma yanzu shine yayi tafiyar wata daya da 'Yan kwanaki Amma ko kadan baiji yana sha'awar munirat ba, tunanin sa gaba daya yana wajan Aisha,ya dade rabonsa da matarsa, yadawo daga doguwar tafiya Kuma mama ta tarbeshi da wadannan abubuwan na Aisha masu wuyar mantawa.

Ya tabbatar da cewa bazata taba saurarensa ba koda yaje inda take yanzu, Amma Kuma tayaya zai tunkareta yabata haquri agaban mutane da rana? Idan mama ta ganshi ta'ina zai fara yimata bayani? Ahankali yazame munirat daga jikinsa, batareda tunanin komai ba yafice daga d'akin, Kai tsaye yanufi part din mama.

Yana zuwa yaga part din shiru alamun duk sunyi bacci, saida yasake kallon ko'ina ya tabbatar babu wani mahaluqi dayake falon sannan yawuce Dakin da yaga Aisha tafuto daga ciki dazu, kama handle din Dakin yayi yatura, yashiga cikin Dakin sannan ya maida Dakin yarufe, baiyi mamakin ganin ta a zaune akan sallaya ba, kanta yana cikin cinyoyinta, qamshin turaren dataji ne yasa taqi d'ago kanta bare ta kalli inda yake.

Jin gina yayi da jikin qofar Dakin yazuba mata ido yana kallon ta, gabansa faduwa yake yarasa ta'ina zai fara yimata magana? Ahankali yasaki ajiyar zuciya sannan ya qaraso wajan ta ya tsugunna gab da'ita har tanajin yanda hannunsa yake gogar Nata, cikin muryar rad'a yace "ki... kki... kiyi hakuri"

Tana jinsa, Amma taqi d'ago kanta ta kalleshi, wani irin haushin sa takeji, ko menene yakawo shi dakinta cikin dare? Wata zuciyar tace da'ita abinda bai gamaba yazo ya qarasa, wani irin tsaki tasaki cikin ranta, tasake cusa kanta cikin cinyoyinta, ganin hakan datayi yasa yasan cewa ba bacci take ba, ajiyar zuciya yasauke yasake cewa"nasan cewa nime laifi ne awajanki, banyi komai ba saida dalili Maaamah, Dan girman Allah kiyi hakuri ki yafemin..."

Wani irin kuka me sauti tasaki, batace masa komai ba Sai hannu data daga masa. (=ؐ)

Kallanta yayi, babu musu ya jijjiga Kansa tareda miqewa yafice daga d'akin, dama yasan cewa bazata saurare shi ba, haka yakoma part dinsa jikinsa a sanyaye, kan gadon yakoma ya kwanta, munirat tanajin kwanciyar sa tace "daga Ina kake? Ko yanzun ma wajan ta kakoma zaka sake taba mata nonon?"

Runtse idon sa yayi, ahankali yace "me kike nufi Danine munirat? Kina nufin zan iya neman mata awaje?"

Cikin fishi tace "idan ba neman matan kafara ba, kwanan ka nawa rabona dakai?Dakazo ka nemi wani abu awajena ne? An tura Maka tsayaiyan nono kana ta6awa yaushe zaka nemi nawa?kun cuceni wallahi, Kuma dole kasa yarinya qarama tadena ganina da qima da mutunci"

Murmushi yasaki kamar wanda baya cikin damuwa, ahankali ya fusgota jikinsa tareda tura hannunsa cikin yaluluwar rigar baccinta, yayiwa breast dinta wani irin kamu, sannan yafara kissing dinta.

Sosai yayi Nisa wajan nuna mata yanda yayi kewar ta, soyake ya mantar da'ita abunda tagani dazu, saide shi Kansa kawai yanayin Hakanne Amma kokadan bayajin sha'awar, saboda tashin hankalin dayake ciki,daga Nata bangaren itama Qin bashi hadin Kai tayi, Dan dole yarabu da'ita tareda juya mata baya yayi kwanciyar rub da ciki, itama kwanciyar ta ta gyara tarabu dashi, saide ko minti goma batayi ba taji Hankalinta yaqi kwanciya, yariga yata6o mata inda yake mata qaiqayi, ahankali ta juya ta rungume shi tabaya, yanajinta yarabu da'ita, sake Matsowa jikinsa tayi tana goga masa qirjinta a bayansa, saide hakan datake masa ma ba komai tatuna masa ba Sai Wanda yata6a dazu, ahankali yasaka hannunsa ya janye ta daga jikinsa, sannan yaja fillo ya rungume a qirjinsa.

Mamaki ne yakamata, yau itace take neman Mahmud Amma yana janye ta da hannunsa? Babu yanda ta'ita duk yanda take jin sha'awar sa haka ta qyaleshi.

Washe gari da safe tsaf ya shirya cikin suit dinsa, baisaka jacket dinba Sai zuba uban qamshi yake,soyake yafita domin shirye shiryen sabon company dazai bude, Wanda yayi alqawari zai Bawa matar datake da muhimmanci awajansa wato munirat ,tun qarfe takwas na safe suke masa waya, already har sun gama tsara komai, kawai jiransa ake yazo yasaka ranar daza'a bude companyn, baisan daliliba, haka kawai yake jin wani irin farinciki acikin ransa, Kuma yasan cewa hakan baya Rasa nasaba da kasancewar Aisha acikin gidansa,yarasa menene yakawo ta gidan a matsayin maiyiwa mama hidima, tayaya tazo? Dole itace zata bashi labari Kuma tana fishi, inda Dane ba lalle ya tsaya yin break fast ba saboda jiransa da ake, Amma yau Kam dole zai tsaya yaci abinci kodan yaganta ma.

Munirat tana wanka danhaka yafice shi kadai, Kai tsaye part din maman yanufa, yana zuwa kuwa yaga ma'aikatan sun gama shirya komai akan dinning, mama tana zaune, yayinda Aisha take tsaye tana qoqarin hada mata tea, yau taji jikin Nata dadan qarfi, babu zazza6in ya sauka tun Bayan datasha magani cikin dare, wani irin dadi yaji, cikin takunsa me aji ya qarasa dinning din tareda sallama, mama ta kalleshi tace "nayi tunanin zaka huta ne bazaka fita ba?"

Saida yadan kalli Aisha yaga tahade girar sama data qasa, yasaki murmushi sannan yace "akwai mutanan dasuke jirana ne dangane da bude wannan sabon companyn, shiyasa zan fita, Amma bazan dade ba zan dawo"

Kafin mama tabashi amsa, qasa-qasa Aisha tace "Ina kwana"

Murmushi yasaki, yasan cewa Dan kada mama taji taqi gaida shi ne, shiyasa tayi masa wannan gaisuwar, Amma Badon hakaba Shima yasan bazai samu gaisuwa agareta ba

Maimakon ya amsa Sai yayi shiru tareda zuba mata ido yana Binta da wani irin mayen kallo,har zuwa wannan lokacin bai zauna ba, yanda Aisha take a tsaye tana qoqarin hada tea din, haka shima yakama daya daga cikin kujerar dinning din yariqe, wani irin nishadi yake ji a ransa harma ya manta cewa mama tana wajan.

Mama ta d'ago zata masa magana taji Aisha ta gaishe shi Amma yaqi amsawa saita kamashi yana kallon ta, cikin mamaki tace "menene kake kallon ta,kokuma yanda kake tuhumar 6arayin Gwamnati itama tuhumar ta kake?,to wannan de Batada abun dazaka tuhumeta akansa"

Murmushi yasaki, dimples dinsa suka futo, yaja kujerar yana qoqarin zama, Hips dinta ya kalla yanda suka sake bajewa fiyeda ranar daya fara ganin ta, ya tuna tsayaiyun breast dinta yanda yake matsa su cikin nishadi kamar karya daina, cikin qasa-qasa da murya yace "tana dashi mana"

Mama tace "au tanada abun tuhumar kace?"

Cikin sauri Aisha tabar wajan, domin kuwa Dama mama tace inde danta yana waje toka Barta tagana da danta,qasa-qasa yabi bayanta da kallo, cikin zuciyar sa yace "wannan ai itace yakamata a tuhumeta, tunda harta mallaki wad'annan abubuwan Kuma ta sace Min zuciya ai dole na tuhumeta, kamata yayi ma nasaka ta adaki na kulle kofar nafara tuhumar ta tayaya akai ta mallaki wannan kayan alatun?(=
)

Mama dataji yayi shiru itama saita share shi tafara cin abincinta, sun kusa gamawa kenan sannan munirat tafuto itama taja kujera ta zauna tafara cin abinci Bayan ta gaida mama.

******

Da yamma Bayan yadawo yana zaune a part dinsa yanashan Lemo, ya kalli munirat yayi mata magana, ciki ciki ta amsa masa, ahankali yasake ce mata "ki shirya jibi zamuyi taron bude sabon company, kece nafara fadawa, idan da wadanda Zaki gayyata saiki sanar dasu"

Wani irin farinciki ne yakama munirat, batasan lokacin data rungume Shiba, nuna masa tayi batasan cewa ita zai mallaka wa kamfanin ba, cikin kissa tace "Congratulation my Dear, Ina tayaka murnar bude sabon company, Allah yasa mu mora"

Mamaki ya kamashi,tabbas yasan yamata laifi saboda abinda tagani jiya yana yiwa Aisha, Amma Kuma yanda tad'auki zafi da fishi akan hakan kawai lokaci daya yanzu daga jin maganar company harta manta abinda yafaru? Cikin mamakin sauyinta na lokaci daya yace "Amin ya Allah"

Tashi yayi yatafi wajan mama domin itama ya sanar da'ita, yana fita munirat tad'auki wayarta tafara Kiran Yan gidansu tana sanar dasu jibi akwai taro, Shahaab zai mallaka mata sabon company, Bayan takira yan'uwanta, saita koma kan qawayenta, babu Wanda bata kiraba, acikin danginta ma wanda ta dade bata kirashi ba yau ta kirashi, saboda tana so ta kankarowa kanta daraja a'idon duniya.

Murmushi take ta saki ita kadai tana lissafa irin mutanan dazata dauka aiki a qarqashin companynta.

Tun daga ranar dasuka hadu a dinning bai sake ganin Aisha ba, yasan kuma Sarai fishi take dashi, shi Kansa idan ya tuna da yawan qaryaiyakin Dayayi mata saiya ji tabbas duk hukuncin data masa din hakan yayi, koda yazo wajan mama baya ganin ta, gaba daya a kwana dayan dabai ganta ba, duk Sai Idonsa suka fada.
anar bude company Shahaab tun sassafe yafita, Aisha kuwa tana d'akin mama, yau tasaki ranta ganin yanda maman take janta ajiki, itace ta fesa mata turare sannan ta kalleta tace "mama kinyi kyau sosai, nasan idan kikaje wajan Nan Sai kowa yace mama nah tafi ta kowa kyau"

Murmushi tayi tace "ki shirya muje"

Cikin sauri tace"a a mama, zan zauna agida inyi miki girki me dadi kafin ki dawo"
Bakomai ne yasa tafadi hakan ba Sai Shahaab da batason Gani, sosai ranta yabaci saboda abunda yamata, Sanadin sa tafara ja'inja da mahaifinta, duk yanda take da kunya saboda Shahaab tafuto fili ta fadawa Abban ta cewa itade Shahaab take so.


Cikin farinciki mama tace "to shikkenan"

Hannunta Aisha ta kama suma futo har compound din gidan, driver yad'auki mama, sannan ita Kuma tajuyo cikin gida.

Wajan taro yayi tsari da kyau yanda yakamata, manyan mutane Yan kasuwa da sauran abokan huldarsa sun halarci taron, Bayan anbude taro da addu'ah anyi Yan jawabai, daya daga cikin masu ruwa da tsaki akan aikin companyn yatashi yafara bayanin yanda sukayi aikin companyn cikeda inganci dakuma ingantattun kayan aiki daga qasar waje.


Munirat tana hakimce agefe guda ita da bataliyar mutanan ta, taci Gayu harta gaji, ta matsu a kirata a matsayin mamallakiyar company, momynta Sai zungurinta take alamun itama ta matsu Akira munirat din.

Ramadan yana kusa da mama, acan Gefe Kuma Shahaab ne yayi masifar kyau cikin manyan Kaya, Ramadan yasake kallon girman wannan company Amma cikin ransa yana mamakin irin son da Shahaab yakewa munirat, tun ranar dayace zai mallakawa wani mutum Mai mutuqar muhimmanci yasan cewa ba kowa zai Bawa ba face munirat.

Bayan gama bayanin company da abundaya qunsa aka Bawa Shahaab damar magana domin nunawa mutanan dasuka halarci taron jin dadinsa dakuma godia agaresu.

Tashi yayi cikin nutsuwa yafara da gaida mutanan wajan sannan yad'ora da cewa "a rayuwa inajin dadin yanda mamana take Bani kulawa, da yanda ta tsaya tsayin daka wajan ganin ta inganta min rayuwa ta, banida abinda zance da mama face godia, sune jin dadina itada matata munirat"

Munirat tayi wani fari da idonta tana sake hura hanci,wajan yayi tsit kowa yana jin yanda Mahmud din yake magana kamar bayaso, saida yasake kallon kowa sannan yaci gaba da cewa "saide wannan company, ban ginashi da sunana ba, tun farko akwai wadda nayi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On SHAHAAB
avatar
fateema

7 months ago

Reply

Allah yakara basira

avatar
taskar

7 months ago

Reply

Replying to fateema

Ameen

avatar
ummu-swabir

2 months ago

Reply

Thanks

Please Login or Register in order to submit comment