Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

naqi sanar da'ita"

Tace"meyasa to?"

Qasa yayi da muryarsa cikin sigar rad'a Yace"tonariga nasan size din abuna, tun lokacin Dana riqesu a hannuna naji yanayin girman su, kawai de banso a saka brezian ne, nafison ki zauna Ahaka, banason abinda zaimin shamaki dasu...."

Cikin sauri tace"dan Allah nide kayi shiru...."

Dariya yayi yace"nayi shiru, shikkenan? Ya shirye shiryen biki?"

Bakinta ta turo gaba tace"yanzu zan fara,inaso zamuyi Walima nida malaman makarantar Dana koyar,sannan zansa gobe ayi saukar alqur'ani, zan basu sadaka idan sun gama suyi mana addu'ah Allah yabamu Zaman lafiya Kuma yabani haihuwa Mai Albarka, yanzu zaka Bani kudin Walima, da kudin fita daga dandali, da kudin gyaran jiki, da kudin uwa da uba"

Jan zuciya yayi, yarasa Yaya akai yarinyar Nan Takeda Hankali da hangen nesa, ko kadan shi baiyi wannan tunanin ba na saukar alqur'ani, Amma gashi yarinyar yar cikinsa tana cewa za'a musu, wanne irin so take masa ne? Dame ya kamata yasaka mata? Cikin tsokana yace"hardasu kudin uwa da uba? To ai mama ce zata baki wannan Bani ba,itace uwar, Kuma itace uban, kudin gyaran jiki Kuma babu maganar sa, aure saura kwana uku wanne irin gyaran jiki? Ki zauna Ahaka yanda kike,karki gyara min komai ahakan kinfi kyau, Shima na fita daga dandali kiyafemin shi kawai"

Kamar zatayi kuka tace"tabdi, duk wadda zatai aure fa mijin ko abokan sa suna bayarwa, Kuma ni sai kace a a, to Yaya zanyi da mutanan da zasuzo walimar?"

Cikin sauri yace"yanzu de abun Bana zafi bane,zan turo miki number Ramadan ki kirashi shine Abokina zai baki duk wannan kudin, akwai number mama itama ki tambayeta na uwa da uba,nikuma zanbada kudin gyaran jikin, Dana saukar alqur'ani da za'ayi, Amma ai gyaran jikin na kwana uku ne, tunda bikin saura kwana uku, Dan haka kudin kwana uku zan turo"

Cikin sauri tace"ai baka bada kudin anko bama, harshi"

Yace"kuma de? Kinga kimin lissafin komai kawai kifadamin, wannan Garin naku bidi'ar tayi yawa maamah, fadamin nawane kudin gaba daya?"

Tace"kudin uwa da uba dubu biyu, na gyaran jiki dubu hamsin, na anko dubu ashirin,na fita daga dandali dubu biyar, na Walima Kuma duk yanda yasamu, abinda Allah yahore, nasauka Kuma zan basu dakaina"

Murmushi yayi,komai zatayi tsakaninta da Allah take fada, babu ruwanta da zuga kudi akan komai kasancewar tasan yana dashi, ya tabbatar inda watace kudin dazata yanka masa Sai yayi yawa sosai, amma ita gashi tana fadar komai yanda yake, abinda bata saniba shine ba kudi ba, inda Ana bada rai, dazai iya mallaka mata nasa, tariga tagama siyeshi da kyawawan halayenta, cikin tsokana yace"yanzu maamah duk wannan uban kudin nine zan bayar?gaskiya yayi yawa, Ina laifin ma gaba daya dubu hamsin atalauce? Albarka ake nema ai"

Cikin shagwa6a tace"Allah kowa fa Ana bashi,Kuma gyaran jiki bakai akeyiwa ba"

Murmushi yayi yace"nibance kimin gyaran jiki ba,yanda kike da kimfi kyau, kinsan yanda kikeda kyau kuwa?"

Cikin shagwa6a tace"nide gaskiya kabamu"

Yace"shikkenan, zan turo miki number Ramadan,kifada masa, zai Baku"

Cikin sauri tace"to,saida safe"

Yace"to kiss me..."

Ahankali tasakar masa kiss din, ya Lumshe Idonsa yace"nifa banji ba"

Sake yimasa wani tayi,nanma yace baiji ba, saida tayi masa sau uku, sannan sukai sallama, daga Nan tatafi gidansu Walida suka fara tsare tsaren yanda walimar tasu zata kasance.

Washe gari kuwa akayi saukar alqur'ani a gidan limamin Garin, tafadi buqatar Mahmud Nason haihuwa aka saka shi acikin addu'ah, saikuma addu'ar Zaman lafiya da kwanciyar Hankali Mai dorewa da akayi musu, Bayan angama suka nufi wajan Walima inda aka rabawa mutane snacks,kowacce take away ansaka Rabin kaza, da doughnut, meat fie, cake, saikuma lemo da ruwa, awajan walimar faty ta sameta, domin kuwa isowarsu kenan daga kano

RANA BATA QARYA

Tun safe aketa kafa rumfuna a filin ball din Garin,yayinda manyan motoci suke sake buda hanyoyi yanda motocin baqi masu zuwa Daurin aure, zasu Sakata su wala, Abba yashiga busy sosai, Sai siyan qwaryar nono yake Ana turasu gida, acan gidan Kuma Ummah da mutanan ta sunata Dama nonon tareda fura da kwakwa wadda suka gogata tun Daren jiya, amarya tana wajan kwalliya tareda qawarta Walida da Faty,gaba daya Garin cika yayi da baqi, daga kan Yan kasuwa, Yan siyasa, harma da ma'aikatansu na hukumar efcc.


Ana dab da daura aure motar daya Dauko shata tundaga dutse tafaso Kai cikin Garin, yasake girma, yazama saurayi, yayi wani irin fari kamar ba jabir din Ummah da Abba da Hajja ba, Kai tsaye yace wa direban taxi din suwuce wajan Daurin aure, suna zuwa kuwa yafuto yabashi kudinsa, ya rataya school bag dinsa Mai kyau a bayansa, Shima yafada cikin wata rumfa ya tsugunna kamar yanda mutanan cikin rumfar suke zaune, daga nesa yake hango Abba yaci babbar riga dinkin shadda fara qal, Sai Fara'ah yakeyi, Allah Allah yake adaura auren yasamu ya qarasa wajan mahaifinsa,ango kuwa baisamu damar ganinsa ba, rabonsa dashi tunda sukai waya yasanar dashi yaduba account dinsa yatura masa kudin jirgi ya shirya yazo bikin shima.

aikuwa ko minti ashirin jabir baiyi ba, aka daura auren Aisha Mahmud, da angonta Mahmud Wakili, akan sadaki naira dubu Dari biyu lakadan ba ajalan ba.



(to masu son shiga jirgi fa su shirya kar Hajja A'i tarufe qofa >Ø#Ý)


Littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda MAHALICCINKI, Saboda nide ban yafe miki ba.

300 ne kacal

0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034




Mrs Usman ce
'<Øûß

Page 19



'Daurin auren daya kawo surutu da kace-nace a tsakanin mutanan qauyen, dayawa daga cikin su Badon sunsan waye mijin ba, zasu iya cewa anriga ansaida Aisha ne.
Inusa dayake tsugunne agefe yayi saurin goge qwallar Idonsa, rayuwa kenan, yana son Aisha ashe ita ba matarsa bace, yariga yasan tayi masa Nisa, babu yanda zaiyi yanzu saide yayi mata fatan alkhairi.


Ango kuwa yana tareda manyan mutane Bayan Daurin aure anata gaggaisa wa,dayawa daga cikin mutanan suit ce ajikinsu hancinsu manne da takunkumi, Wanda hakan zai baka tabbacin cewa Yan hukumar efcc ne,kawai ruwan pictures ake ta d'auka tareda shi,yayi masifar kyau cikin shadda fara sol, iri daya data Abba, Ramadan dayake Fama da wasu mutanan shima farar shaddar yasaka Sai sukai kyau susu ukun kamar Dama can har Abban abokinsu ne.

Ana Rabon Goro Abba yatashi yafuto yanufi gida wannan babbar riga Sai tashi sama take(=ØÞ)

Cikin sauri jabir ya bishi ya rungume shi tabaya, Abba yana juyowa yaga jabir, cikin tsananin murna yace"jabir?,Wai Kai dinne da gaske?"

Cikin murna yace"nine Abba, angon ne yace Nima in shirya inzo Daurin aure"

Abba ya Girgiza Kansa cikin farinciki yaruqoshi tareda fadin"ikon Allah, to muje, muqarasa cikin gidan"

Adede lokacin su Aisha suka dawo daga wajan kwalliya, anyi mata kwalliya daidai misali bamai yawa ba, tana Sanye cikin farin leshi Riga da zani, dinkin rigar anyi mata bubu,ta daura zanin akan rigar, da farin mayafi me girma, qafar ta taci wani takalmi me tsinin gaske, wuyan ta da hannayenta yasha Adon gold, Sai Jan lallen da aka mata da zanen fulawa na baqin lalle Wanda farar fatarta tasake haska lallen, sosai ta dauki hankalin mutane, jabir yana ganin ta yace"qawar Hajja amarya"

Tanajin muryarsa ta yaye mayafin kanta tatafi da sauri ta rungume shi, gaba daya mutanan wajan Sai dariya suke musu, Abba kuwa bai kulasu ba samari yake kira suka shiga cikin gidan suna futowa da furar da aka Dama wadda taji qanqara tayi Sanyi sosai, Kai tsaye wajan Daurin auren suke kaita, yayinda gidan Jummai Kuma aketa futowa da take aways na abinci Wanda Abba yasa aka kira masa masu girkin hotel's takanas tundaga dutse, sukazo tun asuba suka fara aikin girkin Yan Daurin aure, girki me dadi da tsafta Wanda kowa yaci saiya so yaqara.


Su Aisha suna shiga cikin gidan aka fara amarya, amarya, amarya Ansha kyau, kowa da irin abunda yake fada, mutane da Yara Yan unguwa Sai Binta suke duk inda tayi, yayinda jabir yayi wajan Ummah yashige jikinta, cikin farinciki tajashi sukayi wajan Hajja.

Anan tsakar gidansu aka fara yimata photuna da mutane, kowa soyake yayi photon da'ita, ita kuwa magana take Ina Hajja, Amma Hajja tana can Kai yadau zafi tana Fama da mutane, daqyar fatin kano taje ta janyota, itama leshi ne ajikin ta Wanda Hajiya Mama ta aiko matashi da wasu kayaiyakin Wanda zata saka ranar auren, photon aka fara yimusu itada Aisha, anyi musu yafi a dadi, mutane Sai jira suke Hajja tafita sunaso ayi musu da amaryar, Amma Hajja ta kame Sai style take sauya wa, ango ne yashigo tareda abokan su, Sai Alokacin Hajja tayi can tana musu sannu da zuwa, a tsatstsaye aka kawo musu fura basu Sha Bama, suka gaggaisa da iyayen dakuma sauran dangi, wanda basu ganshi ba suka ganshi, sannan Ramadan yajashi yahade su da Aisha ya kalli me daukar photo yace"yimusu da sauri kafin muwuce"

Shahaab de kunya ce ta kama shi ganin yanda dangin Aishan gaba daya hankalin su yadawo Kansa, shiyasa tunda yashigo bai yarda ya Kalle taba, Amma yanzu da Ramadan yahada su, sosai ya shagala akallonta, harma ya manta inda suke, ya manta da akwai mutane awajan, ya rungume ta tabaya, tundaga Nan masu waya suka fara sana'ah, hannunsa yad'ora akan hips dinta, sannan yazuba mata ido, aka fara daukar photon, Hajja ta Girgiza kanta, cikin qasa da murya tace"fitsararre Dama yasa ba, ni nayi mamakin wannan kunyar"(=ØÞ)

Yayi tunanin angama photon, yasaketa yayi hanyar fita, me camera yasake cewa a a ya dakata Sud'an sauya style tukunna, dole haka yadawo yariqe hannayenta aka sake yimusu, sannan cikin dabara ya mintsine ta ahannun suka fice shida Ramadan, da sauran mutanan dasuka shigo.


Sauran mutane Yan Daurin aure sukai ta masa Allah yasanya alkhairi yayinda wayarsa datake cikin aljihunsa alert yake ta shigowa na mutane daban daban babu qaqqautawa, banda masu turo masa message na Allah ya sanya Alkhairi

Saida yagama da jama'arsa, sannan sukayi shirin tafiya, inda yayi magana da Abba agefe, sannan yashige mota suka dauki hanya, daga Nan sauran mutane Yan Daurin aure kowa yafara tafiya, Sai mutanan Garin kawai.

(nabarki da Allah inde kika krnta baki biyaba)

******

Mutanene a zazzaune acikin Babban falon Hajiya Mama, duk Wanda ka kalla kasan gogaggun masu kudi ne sukazo, kowa takama kujera ta hakimce daga masu danna waya Sai masu fira, Sai masu daukar pictures a falon, Sai yanmata masu Hawa tiktok Ana vedio, yayinda ma'aikatan gidan suke kawowa kowa abinci Wanda yaji nama da ganyaiyaki, yanda ciki da wajan gidan yatara Jama'ah hakanne zaisa kasan cewa Ana gagarumin biki a gidan.

Hajiya zaliha dake Gefe a zaune itada mama wadda take Sanye da leshi irinna Hajja sak, tace"gaskiya Hajiya Aisha tsarin gidan naki yasake kyau, sainaga baki ta6a gyaran gida yayi kyau sosai kamar wannan lokacin ba,ansake fenti ansake komai duk acikin wannan qanqanin lokacin"

Mama tayi ajiyar zuciya tace"duk aikin Dan gidanki ne, shifa tunda wannan aure yazo, yakasa zaune yakasa tsaye,ko zumudin Dayayi a aurensa na farko,bakai wannan ba,abun har mamaki da tsoro yake bani"

Hajiya zaliha tayi murmushi tace"nikam Hajiya Aisha, gulma ajali inba'ayi ba amutu, tun tafiyar mu Dubai hado lefen Nan nakeso na tambayeki meyasa yasaki munirat ne?karfa mutane su zagemu ace Dan zai qara aure ne"

Mama tasaki ajiyar zuciya tace"Hajiya Zaliha munirat rabuwa da'ita ai shine yafi, idan bai rabu da'ita Bama to muddin yakawo wannan amaryar cikin gidannan to tashin Hankali za'a yi, bazasu zauna lafiya ba, sofa tayi ta kasheni"

Hajiya zaliha ta zaro idonta waje(=Ø3Þ) sannan tace"kisa?"

Mama tace"kisa fa, shine da yaji tana wayar tana fadawa masu zuwa su kashenin yanda zasu shigo har dakina, saiya saketa, bnda sata datake qunduma masa a wannan Zaman nasu, infada miki, Nan sukazo itada uwarta suka gama borin kunyar su, daga qarshe da sukaga babu Riba suka qarewa Mahmud Gorin haihuwa suka tashi suka tafi"

Hajiya Zaliha tasaki ajiyar zuciya tace"tabdi, lalle munirat anyi butulu, menene Shahaab baiyi mata ba? Kullum suna yawo qasa qasa saikace tsuntsaye, banji dadi ba wallahi, Amma dakika min maganar Gorin haihuwa, saiki tunamin da wani magani da aka kawowa wata yarinya saqo ta hannu na, shekararta Tara babu haihuwa,Amma tana shan wannan magani, wallahi saiga ciki, sauran sa yana Nan agidana, idan ankawo amaryar,zanzo har gida inbata Tasha,in Allah ya yarda Shima zai haihu, haihuwa lokaci ce ai"

Mama tace"to Allah yasa adace Hajiya zaliha"


Haka suka dinga firarsu Sai yamma masu kidan qwarya suka zo, mama ta sauya Kaya suka fita compound aka sake shagalin biki anan, Sai wajan magrib masu kidan suka tashi, daga Nan Kuma Yan yinin biki kowa yayi haramar tafiya, Hajiya zaliha ta dinga bin kowa tana fada masa akwai dinner da za'ayi Bayan ankawo amarya.

Su Shahaab kuwa basu dawo gidaba Sai dare,baima nemi mama ba, kwanciya yayi cikeda gajiya batareda 6ata lokaci ba bacci yayi awon gaba dashi.


******

Kwana biyu Bayan biki, su Hajja sukai shirin tafiya Abuja Bayan sun gama sallamar kowa, fridge dinta tabawa jummai shi, anyi Rabon robobi da dubulan da alkaki na biki, Abba Kam har kuka saida yayi lokacin dayake sallama da mutanan Arziqi Wanda akai Zaman mutunci dasu, gaba dayansu mutum goma ne masu tafiyar, Ummah, Abba, Hajja, Aisha, jabir, jummai, Walida, fati, da mutum daya dangin baban Abba, da mutum daya dangin Ummah, shatar mota suka dauka aka kaisu kano, saboda tacan zasu tashi,Aisha tana Sanye cikin material fuskarta tayi kyau sosai duk da ba kwalliya tayi ba, Amma kana ganin ta kaga amarya, karfe goma shadaya jirginsu yatashi, Sai shabiyu dawani abu suka gama komai Bayan saukarsu, motoci guda biyu sukazo suka dauke su Sai gidan Hajiya Mama.

Aisha dayake tasan gidan tad'an zauna agarin nadan lokaci, batayi wani Kalle Kalle ba, Amma Hajja Kam hanci ta bude da ido tana kallo, Sai surutu suke itada jummai, gashi sun riqe Aisha sun sata atsakiya su Ala dole awajansu amarya zata zauna.

Suna zuwa gida Hajja taga ruwan sojoji

Ta kalli jummai tace"jummai irin wannan sojojin Ina mutum zai iya watayawa yanda yakeso, kinga Dadin qauye fa kenan"

Jummai tace"um ai Hajja A'i wannan dinma wata sabuwar duniyar ce, kiduba kiga gida fa kamar baza'a mutu ba"

Aisha de tana jinsu kanta yana lullu6e cikin mayafi, driver yana tsayawa Hajja takamo hannunta tace"futo da qafar Dama, ki karanta addu'oi aranki harmu shiga"

Haka akayi kuwa, hannunta cikin na Hajja suka qarasa falon bakinta d'aukeda addu'ah, suna zuwa Hajiya Mama tareda Hajiya zaliha suka tashi suka tar6esu cikin farinciki, zama sukai a falon nanfa fira ta 6arke yayinda baqi suka zama Yan kallo Sai kallon aljannar duniyar gidan suke, Hajja ta kalli Mama tace"Aysha Yakubu Wai Dama anan kike rayuwa?"

Mama tayi murmushi Tace"Anan nake, kema yanzu ai kinzo kenan"

Hajja tayi ajiyar zuciya tace"to irin wannan gida inji de bakya mantawa da sallah ko?"(>Ø#Ý)

Dariya tabawa mutanan falon gaba dayansu, Hajiya zaliha tamiqe taja hannun Aisha Suka wuce Dakin mama, suna zuwa Aisha tasake gaishe ta, cikin jin dadi tace"ke bude idonki Kisha iska, wadancen tsofaffin babu me cewa bude mayafinki ta firarsu suke"

Cikin murmushi tacire mayafin Nata, Hajiya zaliha tace"masha Allah" ganin yanda amaryar tasu Takeda kyau kamar ita tayi kanta.

Waya Hajiya zaliha tayi, Mai gyaran Kai tazo har gida, Kai tsaye d'akin mama tashigo suka wuce toilet itada Aisha,kanta dayasha wanki aka sake warware wa, aka wanke shi, sannan tabarta a toilet din, Hajiya zaliha takai mata ruwan dafaffan lalle Wanda yaji humra yar ubansu, tace ta daure kanta sannan tayi wanka dashi, wankan tashiga tana tunani a ranta wanne irin so mutanan Nan sukewa Shahaab ne? Kowa kokari yake yaga yayi mata abu duk de Dan saboda shi, tana gama wankan tafuto, matar tasake gyara mata kanta, tashafa mata mayuka masu qamshi, sannan tayi musu sallama tatafi, wata hadaddiyar shadda dataji aiki tabata tace"saka wannan kayan, Bari inje kitchen in dawo"

Aisha tace"to nagode"

Ta kar6i kayan tafara kokarin sakawa, yayinda Hajiya zaliha ta wuce kitchen tahado mata fruit Wanda ta hadashi da maganin mata, sannan ta fasa mata madara peak ta ruwa aciki, takawo mata tace Tashanye shi tas, cikin ladabi ta karba tafara Sha, dadin dataji ne yasa ta shanye shi duka, Nan da Nan ta nemi yunwar da takeji tarasa, Hajiya zaliha tace"toki kwanta kihuta, anjima za'a tafi dinner, idan me kwalliya tazo saiki shirya ku fara"


Tace"toshikkenan Anty Nagode"

Cikin jin dadi Hajiya zaliha tafice tareda rufo mata Dakin, tana zuwa falon taga Shahaab a tsugunne yana gaida mutanan jigawa, shadda ce ajikinsa milk colour, wadda taqara qawata kyakykyawan zatinsa, Bayan sungama gaisawa da baqin yadan daga Kai yana Kalle Kalle ko zaisa Aisha Amma shiru ne babu bayani, Kuma babu Wanda yace masa tana daki yashiga,Mama kuwa da tasan ma'anar Kallen Kallen dayake saitace"ka manta wani abu ne?"

Cikin sauri ya Girgiza Kansa yace"a a mama"

Sannan ya kalli agogon hannunsa yace"bari inje"

Cikin sauri yatashi yafice daga falon,jabir yayi sauri yabi bayansa.

Hajja tayi murmushi Dan itama ta gane wayake nema.

Bakinta cikeda naman kaza Wanda aka kawo musu hade da lemuka da abinci, tace"Aysha, takwararki fa yake nema"

Abba da Ummah sukai murmushi, yayinda Walida da faty suka hada ido suma suke qus-qus daga Gefe,sauran baqin maza da'akazo dasu kuwa daya daga cikin su ya ajiye lemon dayake Sha yace"to Hajiya Atura masa ita mana"
Mama kuwa saita basar dasu ta hanyar fada musu cewa"tana daki na, shirya wa take, inajin bata gama bane"

Nan da Nan kuwa taga sun yarda da maganar Tata, tasan halin danta Sarai, yanda yarinya Tasha gyara idonta idon Shahaab tsaf zai iyayin abun kunya ga surukai Baja-Baja agida, Gara tayi zamanta adaki idan ankai masa ita saiya ganta(=ØÞ).

Firarsu sukaci gaba dayi anan Hajja take tambayar Ina surukarta matar Shahaab, Nan take mama tafara Basu labarin mutuwar auren Shahaab da munirat, sosai labarin yadakesu kasancewar sude a qauye abune me girma kaji zancen kisan Kai.


Aisha kuwa tana ganin fitar Hajiya zaliha tatashi ta kunna kallo, Nan Hankalinta yayi kan kallon tun tana fahimta har bacci yafara fizgarta daga qarshe ta gyara kwanciyar ta tafara bacci, bata tashi ba Sai wajan karfe biyu da kwata, cikin sauri tayi sallah, tana zaune tana azkar Walida da faty suka shigo suka kawo mata abinci, tana faracin abincin suka fara bata labarin zuwan Shahaab,Sai dariya suke, faty tace"ni wallahi tausayi ma yabani, yad'an kakkalli mutanan falon yaga bata Nan Kuma abun tausayi mama tana cewa wayake nema saiya ce babu komai, inda nice ai saide suga nagudu wajan mijina"

Walida tace"to Rasa kunya, shi din cemiki akai ya haqura ne? Rabu da abinda kake so kinji, yanzu haka muna fita zai lalla6o wajan matarsa"

Aisha tace"kude wallahi kuncika sa ido, a falon ma Kuna zaune gulma kuke? Ninasan Bani yake nemaba, idan nemana yake bazai 6oyewa mama ba, fada mata zaiyi"

Faty tace"wallahi ke yake nema, abinda mutane yagani a falon gamu Nan reras shiyasa yafita da sauri? Bafa waya kuke ba, rabonki dashi tun ranar Daurin aurenku, Shima Ina ganin ku ba magana kukai ba, Shima narasa dalilin sa naqin siya miki waya"

Walida tace"tunda kikaga haka may be bayason tayi waya da maza ne, kin Kuma San waya da daukan Hankali, tana haduwa da wani saurayin yanzu zaija hankalin ta kamar yanda Shima ya janyewa inusa hankalin ta"(=ØÞ)

Dariya sukayi, Aisha tace"wallahi Bahaka bane, zai siyamin, yace Sai lokacin da muka tafi honeymoon Dubai, dakaina ma yace zan za6i wadda tamin"

Walida da faty suka hada baki sukace"wowww!"

Sannan faty tace"kinsan Allah?, kima shirya,yanda mutumin Nan yakashe kudi wajan aurenki, to ajikinki zai fanshe, nasan jikinki saiya fada miki, tas saiya huce gajiyarsa infada miki, barema yanzu babu matarsa, aikuma Saita Allah"

Cikin mamaki ta kalli faty fuskarta d'aukeda tsananin mamaki tace"kamarya babu matarsa?"

Nan take suka fada mata labarin da mama ta basu akan rabuwa auren nasu, jikinta ne yayi Sanyi sosai, tausayin sa ya kamata, Kuma koda wasa bai ta6a fada mata cewa yasaki munirat ba, itade tunda take dashi bata ta6ajin ya kushe matarsa a gabanta ba, ko maganar ta ma ba yayi, yana kokarin ganin ya mantar da'ita cewa yanada aure, Kuma hakan shine daidai, shine tabbacin mutum yasan darajar matarsa saboda bai 6atata awajan yarinyar dayake nema ba, ajiyar zuciya tayi tace"Allah yarufa asiri,idan akwai alkhairi a zamansu tare Allah yadawo da'ita dakinta, idan Kuma babu Allah yasa tabarmin abuna nikadai"

Dariya suka saka gaba dayansu,haka sukaci gaba da firarsu suna kallo kad'an kad'an, har Mai kwalliya tazo, anan tace subasu waje zata yiwa amarya kwalliya,idan angama Nata Sai ayi wa qawaye dasu mama, haka suka futo daga d'akin tareda rufo musu qofar.

Hajiya zaliha ce tadawo Dakin ta kawowa Aisha kayan sakawa, wani material ne Mai kyau dinkin doguwar Riga, taimaka mata tayi tasaka kayan, dinkin kuwa yayi Mata d'as ajikinta, sannan tafuto daga d'akin, suka fara kwalliyar, andauki lokaci sosai Ana wannan kwalliya, sannan akayi mata dauri Mai kyau, dogon gashin kanta akayi mata wani irin style dashi.

Ba'a gamawa mutane kwalliya da dawuri ba kasancewar a nutse takeyin komai,aikuwa tuni motocin dazasu kaisu wajan dinner sunzo, mama da Hajja kuwa basu tafi ba saida Shahaab yazo mama takama hannun Aisha tasaka ta acikin motar dazasu tafi, sannan itama driver yadaukesu itada Hajja, su kansu ma'aikatan gidan sunsan Ana biki a gidan domin kuwa mama saida tabawa kowa pass din shiga.

Tunda tashiga motar kanta yake qasa takasa kallon sa, batasan meyasa ba, haka kawai ta tsinci kanta da kunyar sa, wani irin kwarjini yayi mata badan kadan ba, tun shigowar ta yake waya bai daina ba har saida tafiya tayi nisa,hukumar suce tad'auki nauyin yin dinner, shi Kansa direban daya dauki amarya da ango Shima daga hukumar aka turo shi, yanaso yajata jikinsa Amma Kuma yana son jan girman sa saboda wannan ma'aikacin nasu dayake driving, ahankali yamatsa kusa da'ita tareda Dan daga net din data yafa akanta, yana kallon fuskarta yafara tasbihi ga Allah, tabbas yasan tayi kyau sosai ranar Daurin aurensu, Amma Kuma daya ganta yau, saiya ga ranar Daurin auren ba komai tayi ba, Dan qaramin bakinta ya kalla yaji kamar yahade bakinsu, shiyasa yaji taqaicin rashin Ramadan akusa, yaso ace shine yake driving, da saide yarufe Idonsa, Amma babu abinda zai hanashi hade bakinsa da Nata, idonta dayake Lumshe ya kalla, gashin idonta ya kwanta yayi luf...,ahankali yad'ora lips dinsa akan kumatunta yasakar mata kiss, cikin rad'a yace"kinyi kyau"
Sannan yasaki net din, yajuya yana kallon titi kamar bashine yayi abinda ya aikata yanzu ba, azahiri kallon titi yake, kasancewar shine yake zaune agefen Dama ita Kuma tana hagu, hakan ne yasa yazura hannun sa na hagu ta bayanta, yayinda hannunsa na Dama yake danna waye, shi Kansa baisan meyake danna waba (=Ø2Þ)

Hips dinta yariqe da hannun daya zura ta bayanta, ahankali tad'an motsa alamun bata so,cikin nutsuwa yayi sama da hannunsa ya dorashi akan dukiyar fulaninta guda d'aya yayi masa wata irin matsa, lokaci daya Aisha taqame a zaune, gabanta ne yafadi, cikin sauri ta juya ta kalleshi, Amma sai taga Hankalinsa yana kan waya, ganin ta firgita dayawa tana nema ta tona masa asiri yasa yasake ta, Adede lokacin Kuma suka qaraso wajan, kasancewar lokaci yaja yasa suna zuwa yakama hannunta suka shige ciki, ta ko'ina girma ake bashi, waje ya tsaru iya tsaruwa, duk Wanda ka kalla saide kaga yatsuke cikin suit,ango da amarya dakuma mutanan gida sune kawai basu saka suit ba, Amma jabir ma tasa suit din yasaka.

Suna qarasa wa ciki kawai haske kake Gani na camera tako Ina yana tashi, an gudanar da taro lafiya,anyi Rabon kayaiyaki yanda ya kamata, amarya da ango sunsha pictures da video, lamarin dayasa kafafen sada zumunta suke ta surutu akan bikin, yanda masoyan sa suke posting din vedion bikin ne yasa munirat tagani, Wanda taji kamar tahadiyi zuciya ta mutu, yayinda qawayenta dasuke gefenta suna mata dannar qirji suke sake zigata, dayawa daga cikin su tunzurata suke har hakan yasa tayi wani quduri marar kyau acikin zuciyarta.


Sai qarfe goma na dare, suka nufi gida,hannun Aisha yana cikin na mama har suka qaraso gida, anan part din mama gaba dayansu baqin suka kwana, kowa yariga yagaji, Kuma babu Wanda yake tareda yunwa kasancewar anci Ansha awajan dinner, shiyasa suna dawowa kowa ya kwanta, su faty ne basuyi bacci da wuri ba itada Walida sunata aikin danna waya suna posting pictures din amarya da ango.

Sai shadaya da wani abu Shahaab yadawo gida, yariga yasan cewa Aisha tana tare da iyayenta, shiyasa yayi tunanin tafiya part dinsa Shima,saide duk yanda yaso yayi bacci bai samu ya runtsa ba Sai gab da asuba, hakan ne yasa ya makara a sallar asuba.


Bayan yadawo daga masallaci kuwa kwanciya yasake yi yana ramakon bacci, Sai wajan azahar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On SHAHAAB
avatar
fateema

7 months ago

Reply

Allah yakara basira

avatar
taskar

7 months ago

Reply

Replying to fateema

Ameen

avatar
ummu-swabir

2 months ago

Reply

Thanks

Please Login or Register in order to submit comment