Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

d'ago ta daka masa harara da fareren idonta tareda murguda masa d'an qaramin bakinta,yana ganin abinda tamasa yafaki idonsu Hajja ya motsa fatar bakinsa yasakar mata kiss ahankali,karaf akan idon Abba (>Ø-Ý=ØFÞ<Øûß
@&þ=ØHÞ)
Aisha kuwa tana ganin abinda yayi tayi sauri ta sunkuyar da idonta, Abba kuwa cikin sauri ya kawar da Idonsa yayi murmushi cikin ransa yace"dole yarinya tadinga bijiremin tadage lalle Sai Kai"
Ummah da mamaki yagama kamata ta kalli Shahaab tace"wanne irin abinci kake magana bawan Allah?"

Abba ya kalli Ummah da Hajja yace"wannan fa Mahmud Wakili ne, Wanda yaturo da Azumi akayi Rabon abinci agarin Nan?"

Hajja ta kalli mama tanuna Shahaab tace"wannan shine Mahmud dinki?"


Cikin sauri mama ta daga Kai tace"shine Aysha, shi kadai nahaifa, inde kinji Ana cewa Mahmud Wakili to Mahmud dinane, ashe de alqawarin mu nasaka sunaye ya tabbata, Rabon abinci Kuma babu Wanda yaturo, shida Kansa yazo, a lokacin nariga na fidda rai da ganin Aysha Sulaiman, sainayi masa magana akan yazo jihar Jigawa yagina gidan marayu, ko Allah zaisa watan watarana Yaya, kokuma jikokin Aysha zasu kasance a gidan, ta wannan hanyar ne zan iya taimakonta saboda bansan inda zan ganta ba, Nasaka anyi cigiyar duk a banza,Bayan yazo sunyi maganar aikin shida Gwamnatin Jihar, saiya raba kayan abinci, to kunji dalilin zuwansa Nan Garin, dama shine Wanda nake dashi Wanda zai tsayamin akan nemanki, toshi tunda yaji nace masa muddin naganki Sai na aura masa yarki, Tofa shikkenan yayi biris da maganar neman naki, saboda bayason nabashi wadda bayaso, yad'auki son duniya yad'ora wa matarsa, shi Dan boko, ba zaiyi wa matarsa kishiya ba, Amma dayake Allah yaso kamashi, saiya saka masa son Aisha, soyaiya ta kamashi dumu-dumu, Idonsa yarufe,ya manta da batun Qin qarin aure,Sai gashi da Kansa yazo min da maganar inzo in nema masa auren Aisha, inkikaga yanda yake son Aisha saikiyi mamaki, harfa company yabata, Alokacin da akayi kyautar na tambayi abokinsa wacece Aisha? Nasan tare suke qulla komai, Amma Shima saiya 6oyemin, akace mama ai jinake dake yake, waini za'a yiwa wayo, Amma da aka 6oyemin din Sai gashi de anzo wajena inzo neman aure, to Dama mun samu Sa6ani da takwarar tawa, sainace zanzo inbata haquri, ashe ni Allah ne yayi zan hadu dake...."

Tajuya ta kalli Shahaab tace"idan baka auri yar qawata ba ai gashinan zaka auri jikar qawata"

Cikin sauri Hajja tace"kamfani fa kikace Aysha?shiyasa da yarinyar Nan tadawo tazo da kudi ajakarta tace mana Wai me gidan ne yabata naji tsoro, saboda kar ace daga zuwa aiki yarinya ta qwacewa matar gida Miji, saide Kuma bakisan wani abu ba, ai ita takwarar Taki akwai Wanda takeso, tad'auki son duniya ta dorawa wannan jarababban yaro(=Ø3Þ)
Uban Nata har dukanta yayi akansa, saboda Dafarko akwai Wanda mukeso mubata inusa, yarinyar Nan tunda tahadu da wannan saurayi ta bijire tace lalle saishi, ita batason inusa, to yanzu ma idan muka bata Mahmud din naki muna Nan dake wannan Yaron zai dawo yaqara hure mata kunne, qarshe tazo tace bazata auri Mahmud dinba, Amma wata kusan ai tafi wata, shi wancen saurayin biro yabata shikkenan ta rikice akansa, Amma ga Wanda yabaka kyautar kamfani banda rashin Hankali me akai-akai wani biro? Aini idona idon Shahaab, hakuma ce zata rabani dashi, Kuma infada miki yaqi futowa fa? Shirme ne kawai irinna takwarar ki"

Cikin sauri Abba da yasan komai yayi qasa da Kansa, Aisha kuwa murmushi tayi Shikuwa Shahaab yana jin haka yayi qasa da Kansa, yaude yakawo Kansa wajan Hajja Sai ta Allah Kuma.

Mama tayi dariya ta kalli Hajja tace"to yanzu ai gashinan yafuto, Mahmud din nawa Aishine Shahaab din"

Cikin sauri Hajja ta zaro idonta(=Ø3Þ) tace"Shahaab?"

Cikin sauri yayi qasa da Kansa yafara Sosa qeyarsa, Ummah kuwa dariya ce ta kamata, Sai yanzu ne ta gane dalilin dayasa tun dazu yake sunkuyar dakai, ashe suruki ne dakansa.

Mama tayi dariya tace"to yanzu mun futo Aysha, Sai abamu auren Aisha"

Hajja tayi dariya tace"narasa ma mezance wallahi"
Tajuya ta d'akawa Aisha duka abaya har saida tad'an yi qara, sannan tace"dan gidanku kinaji inata zuba ko zunguri na bakyayi ba?"

Ummah tayi dariya tace"Hajja Ai zancen yaqare"

Mama ta kalli Shahaab da Kansa ke qasa tace"narasa gane wannan kunya daka aro ka yafa wa kanka Shahaab, agida fa sassafe kazo min falo ka zauna kanaso muyi muzo gidansu Aisha, yanzu Kuma gamu a gidan Amma kakasa kallon Aishan ma, to ai shikkenan ga abokinka Nan, saika bashi haquri ka nemi auren awajansa, yau aboki yazo wajan abokinsa neman auren yarsa"

Dariya sukai gaba dayansu, Abba yace"nikam babu komai wallahi, dama komai an ai katashi ne cikin rashin Sani, Amma komai ai yawuce, Allah ya nuna mana lokacin ya basu Zaman lafiya"

Ummah tace"Amin-Amin, aimune da godia Hajiya, Allah yasaka da alkhairi anata dawainiya damu, bagamu ba, baga yaran muba, Allah yasaka da alkhairi"

Mama tace"duk abinda Shahaab yamuku ai Kansa yayi wa, idan zai dauki duniya yabawa jinin Aysha Sulaiman, wallahi banida damuwa, yayiwa wasu ma bare Kuma Aysha? Aysha ai mahaifiyar sa ce, yanda nake da iko akansa itama haka take dashi"

Tajuya ta kalli Aisha tace"takwara ta matso kusa Dani mana,Allah sarki kullum saita dinga Cewa a kakarta ta daukeni, ganina take kamar Hajja kakarta, ashe kuwa yarinya da gaske take nidin kakarta ce"

Murmushi sukayi, Aisha ta taso ta zauna agefen mama kanta sunkuye aqasa, Hajja tace"Aisha kenan, sarkin tsiwa, waini Kam Aysha Mahmud dinki yaransa nawa yanzu? Ni nawa Mahmud din Aisha ce ta farko, saikuma jabir yana qasashen waje Mahmud dinki ya turashi karatu, sukenan su biyu"

Jikin mama ne yayi Sanyi, ahankali tace"wadannan jikokin naki su zan kalla Nima ince ga jikokina, saboda har yanzu Allah bai Bawa Shahaab haihuwa ba, shiyasa na damu akan yaqara aure, saboda likitoci sun tabbatar lafiyarsa kalau, shikuma yaqi yayi auren ko Allah zaisa Shima muga yayansa, to yanzu de Ina fatan idan akayi auren da Aishan, ko Allah zaisa ita tasamu cikin"

Hajja tace"ciki kuwa,insha Allah anayin auren zata samu,auren yanzu da anakai yarinya zakiga tasamu ciki kamar Dama abakin qofa tayi tuntu6e dashi?yo Allah natuba jikar qawata jummai fa watanta Tara cif-cif ta haihu, idan kikai lissafi zakiga inajin a ranar damuka Kai yarinyar a ranar tasamu ciki, shegiyar jaraba duk ta cika mazan, dama akan ga6a suke, shiyasa anakai musu yarinyar suke haike mata...."(=ØHÞ>Ø-Ý)

Ummah najin haka tatashi Dasauri tace"bari azuba muku ruwan alwala naji Ana Kiran sallar magrib"

Shahaab kuwa kunya ce ta kamashi cikin sauri yadan Sosa Kansa, Shima abban cikin kunya ya kalleshi yace"muje masallaci yalla6ai"

Aikuwa cikin sauri yatashi suka fice.

Mama tayi murmushi tace"kinga Kin kori yaran naki, gaba d'ayansu sun watse"

Hajja tace"Allah nake fada miki haka mazan suke, watama da za'a yi jinkiri adan daga Daurin auren to da a gidansu zai fara rage zafi, wannan fitina har Ina?"

Cikin sauri itama Aisha ta silale tayi dakin Hajja, tanajin mama ta cewa Hajja"aikuwa Shima dannaki Ina tunanin haka yake, Dan mahaifinsa ba sauqi, idan kikaga yanda yakebin takwarata da kallo Sai abun yabaki tsoro,shiyasa nake jin tsoro kar aure yazo abawa yarinya magunguna Tasha yazo yayi 6arna"

Hajja tace"to Aysha itada zataje gidan kishiya akaita haka babu Dan tsumi?, itama matar tasa ai kinsan kintsawa zata sake yi"

Mama tace"Eh da wannan Kuma,toki bata maganin Mai kyau da inganci, inkanada kyau saika qara da wanka, yanda yake rawar jiki akan takwarar Nan tawa Gara yajita da zaqinta"

Haushi ne yakama Aisha, wannan mutanen basuda damuwa wallahi, dama de halinsu ne yazo daya shiyasa abotar tasu ta Dore, Wai mutum ake cewa yayi zaqi saikace wani chocolate(=ØÞ)

Ruwan alwala da Ummah ta gabatar musu a buta, shine ya katse musu zancen nasu, Kuma ko ajikinsu Ummah tana jinsu suke wannan maganganun, Kuma ahakan ita surukar su ce(=ØÞ).

******

Su Abba suna fita kofar gida sukaga cincirindon mutane suntaru a kofar gidan, cikinsu harda Mai Gari, mamaki yakama Abba, kafin yayi magana maigari ya kalli Abba yace"mamuda yanzu Yara suke fada mana anga Mahmud Wakili agidanka, shine mukayi gayya mukazo mu shaida, saikuma muyi musa godia akan abun alkhairi daya aiko mana kwanaki"

Shahaab yana jin haka yayi murmushi yace"babu komai baba, Bana buqatar godiar ku, ai komai Dan Allah nayi, Allah yaqara hore mana domin mu samu qwarin gwiwar taimakon naqasa damu"

Gaba dayansu suka amsa da ''amin'', daga Nan Kuma suka babbashi hannu sukai musabaha suka wuce masallaci gaba dayansu.


Bayan su Hajja sun idar da sallah aka kawo wutar nefa, Dakin Hajja suka koma gaba d'ayansu har Ummah, Aisha ta zubowa mama abincin data gama dafawa me miyar kaji, ta zauna tafara bata abincin kamar de a Abuja, tanacin abincinta fanka tana fifitasu, Hajja ta kama ha6a tace"ikon Allah,kaga wani sabon Salo yanzu Aysha abincin ma abaki takwarar Taki take baki? Shiyasa fa idan Naga Aisha tana cin abinci nake tunawa dake, komai kina yinsa kamar yar sarki, Kuma Sai akayi dace kinyi kudi, mulki Kuma Sai Allah"

Murmushi mama tayi tace"ai Aysha, shiyasa kullum nake qara godewa Allah, Shahaab yana sona, yanamin biyaiya yanda bakya zato, shida Kansa yake nemomin Mai kula Dani, Kuma duk cikin Wanda yake kawo min nafijin dadin aikin Aisha fiye da kowa, saboda itace take min komai tsakani da Allah babu 6oye-6oye, tana kulawa Dani kamar Nina haife ta, cin abinci Kuma Aysha ai Yanzu na rage yanga, tunda Wakili yarasu na watsar da Gayu, yanzu Shahaab ne yake wannan cin abinci kamar bayaso, haka zai Sani agaba wataran lalle saina bashi abinci dakaina, nikuma ince Ina matarka, jeka ta baka"

Hajja tace"ai shikkenan,idan akai auren saita dora daga inda ta tsaya"

Saida sukai sallar ishsha'i sannan suka dawo gida, Abba ne yayi waya aka kawo wa securities lemuka da ruwa, sannan Shahaab yace suje hotel cikin dutse su kwana, zasuyi waya gobe, direban daya kawo su yabawa kudi masu yawa, daga Nan suka tafi gaba dayansu.

suna zuwa gida Kai tsaye d'akin Abba suka wuce, Abba yafuto yayiwa Ummah magana aka kaiwa Shahaab ruwan wanka, sannan yaje yayi masa magana, ankai ruwan wanka bandaki, shikuma yawuce Dakin Ummah, saida sukaji shigar sa bandakin sannan Abba yace"bari infita asiyo kayan shayi, idan yafuto saiki sa Aisha takai masa abinci, saiya kwanta acan, nikuma saina taho Nan mukwanta"

Ummah tace"to saika dawo, ataho mana da qwai da Dan dankalin turawa in za'a samu, Sai ahada ayi amfani dashi"

Amsa mata yayi, sannan yafuto daga d'akin, dakinsa yakoma ya futowa da Shahaab wata sabuwar jallabiya daya siyo ta tundaga Saudia a zuwansa Umarah, ya ajiye masa ita akan gadon, sannan ya ajiye masa turare da man shafawa, yafice daga gidan cikin sauri.

Yana futowa daga wanka Dama tunanin kayan sakawa yake, Sai yayi tozali da kayan akan gado, murmushi yayi, yarufe Dakin sannan yacire kayan jikinsa gaba daya, yasaka jallabiyar yafeshe jikinsa da turare,Sai a lokacin yasaki ajiyar zuciya yad'auki wayarsa yakira Ramadan yana bashi labarin komai.


Saida Ummah ta danja lokaci sosai Wanda Takeda tabbacin yagama shirya wa sannan ta zuba masa abincin da kanta, ta bude fridge din Hajja tad'auki kunun Aya masu sanya ta juye su a jug, tahada komai, tashiga Dakin Hajja, duk suna fira Aisha tana game a wayar Hajja, Ummah ta kalleta Tace"Qawar Hajja ga abinci Nan tashi kikai masa Dakin Abbanki"

Cikin nutsuwa tace"to Ummah"
tatashi tasaka hijab dinta, Tajuya zata fita.

Cikin sauri mama Tace"A a takwara, dawo ki fesa turare Sai kije, dama can danake barinki kina haduwa dashi babu shiri, bansan menene a tsakanin Kuba, yanzu Kam dole yaga canji ai"

Murmushi Ummah tayi,Cikin kunya Aisha ta fesa turaren sannan tafuto ta dauki abincin ta wuce Dakin Abba, saida tayi sallama kafin tashiga, waya yake Amma yana jin sallamar ta yakashe wayar yace"shigo mana"

Shiga Dakin tayi, ta'ajiye abincin aqasa, sannan tafara zuba masa, ko kadan taqi kallon sa, Shikuwa tun shigowar ta yakafeta da ido yana kallonta, saida tagama zubawa sannan
Ahankali tace masa"gashi"

Murmushi yayi babu musu ya kar6i abincin yafara ci, dadin abincin yasa yadan Lumshe Idonsa, sannan yabude ya kalleta yace"abincin yayi dadi "

Murmushi tayi batace komai ba, Shima bai sake magana ba, saida yagama cin abincin, yaci sosai kuwa, sannan ta tsiyaya masa kunun ayar adan qaramin cup tamiqa masa, hannu biyu yasa yakarbi cup din yahada da hannunta yariqe, sannan yakai bakinsa ya shanye,yaji kunun ayar akwai dadi, yasaki hannunta yace"qaromin"

Cikin sauri taqara masa, yasake hadawa da hannunta yashanye, sannan ya zare kofin da dayan hannunsa, hannunsa dayake riqe da'ita Kuma bai saketa, cikin sauri tafara kokarin qwace hannunta , shikuma yaqi sakinta saima gefen hijabinta daya riqe yana tsoron karta gudu, cikin faduwar gaba tace"dakin Abba nefa, kasakar min hannu karyazo, Allah idan yaganni duka zaimin"

Idonsa ya Lumshe sannan yabude, cikin sigar rad'a yace"bazai zoba fa, meyasa kike wahalar Dani?kika gudo gida bakya tsoron a sacemin ke a hanya ko?"

Cikin shagwa6a tace"toba mamace ba"

Cikin wani irin yanayi na buqata yace"metayi?"

Saida ta turo bakinta gaba sannan tace"video fa ta nunamin, Wai nice dakai"

Hannunsa dake riqeda ita yasa ya shafa dogon hancinta, cikin sauri ta Lumshe idonta, yayi kasa da bakinsa yad'ora lips dinsa daidai kunnanta yace"kinga videon?"

Cikin sauri ta daga masa Kai alamun tagani, murmushi yayi yace"saiki shirya, dannima saikinmin irinsa"

Wata irin kunya ce ta kamata, cikin sauri tarufe idonta da hannunta,yanayinsa yaji yana sauya wa, cikin rad'a yasake ce mata"me kika Sakamin acikin kunun Aya?"

Cikin sauri ta Girgiza kanta, yadage mata girarsa guda yace"really? To meyasa nake jina wani irin?"

Kallan sa tayi tace"menene wani iri?"

Yace"bakisan wani iri ba?"

Cikin rashin Sani tace"ni bansani ba"

Murmushi yayi yace"to infada miki yanda yake?"

Cikin sauri Tace"A a "

cikin yanayin rad'a yace mata "why?"

Kanta ta Girgiza masa tace"dakin Abba nefa, tsoro nakeji, Nika denamin wannan maganar cikin rad'a, wani iri nakeji "

Dariya ce ta kamashi, babu musu yasake ta sannan yace"yanzu kinsan wani iri kenan ko?Maaama na lura bakya tausayi na,kinfi tausayin mama akaina,shiyasa kika zama tauraruwa awajanta,dakika taho haka ta dinga tambayata naduba Naga inda kike? Ajima tasake cewa anga Aishan kuwa?saida nakawo ta har gida, sannan nasamawa kaina , da zuciyata lafiya, Amma Kuma gashi ke Sai wahalar mata Dani kike...."







Yaya labarin Anty munirat ne? >ØÝ


Mutara zuwa anjima =ØOÞ


Idan kika karanta baki biyaba nabarki keda mahaliccinki, littafin kudi ne, 300 ne kacal, ki biya ki karanta karki karanta haqqin wani

0164549488
Amina muhammad
GTbank



Number
08033300034









Amnah El Yaqoub
'




BASAJA TAKU NA UKU


"momy wallahi bazan iyaba,nariga nagama yanke hukunci akan zamana dashi, bazan ta6a bude idona a gidannan Inga Mahmud yana tareda wata matar Bayan niba, mahaifiyar sa itace matsala ta, Kuma yanzu nagama da wannan matsalar, saikuma yarinyar, agabana fa yarinyar tazo gidannan Amma saboda qiyaiyar da mahaifiyar sa take nunamin harta cusa masa ra'ayin yarinyar, wallahi anayin kuskuren daura musu aure wallahi saide yayi biyu babu.... Babu nidin, babu itan..."
taqarasa maganar cikin matsanancin kuka.

Saida tayi kukan ta sosai, sannan momynta tasaki ajiyar zuciya tace"mekike shirin aikata wa munirat?,kifadamin menene shirin ki nagaba? Ni tunda kika fadamin maganar abunda nakawo raina shine kawai muje wajan malamai ayi roqon Allah akan Allah ya watsa lamarin, ya fitar masa da yarinyar daga Kansa, a cireta acikin zuciyar sa, Amma ita mahaifiyar sa menene Nata aciki? Shifa shine me auren, duk tsiya shine yakai mata maganar zaiyi auren harta samu take fada miki magana akan haka, Amma yanzu de fadamin shirin ki nagaba, idan naji yayi daidai da nawa shikkenan"

Cikin kuka tace"momy kamar ni? Ai abun kunya ne ace mijina zai qara aure, momy kishiya fa zaimin, qawayena dariya zasumin suce Dama Bana kula dashi yanda ya kamata,momy dame na ragi Mahmud? Kullum cikin gyara nake, ita mahaifiyar tasa ai itace take kitsa masa komai, idan tace yau ya auri mata uku, to adaran zai aura saboda yana jin maganar ta"

Cikin sauri momy ta katseta tace"yanzu mekika yanke akan hakan?"

Cikin 6acin rai tace"zaki Gani momy" daga Nan takashe wayarta.

Zagaya Dakin taci gaba dayi, idonta yayi jajir saboda kuka da 6acin rai, ahankali tasake Kai hannu ta share Hawayen daya sake zubo mata, tunda taga har dare yayi basu dawo ba, hakan yana nufin acan zasu kwana kenan, bata kirashi ba, haka Shima bai nemeta ba, abunda yaqara qona mata rai kenan, yanzu haka yana can tareda wannan yarinyar me cusa kan masifa, kokuma yanzu ma yana can tana bashi abinda tafara bashi anan hartaja Hankalinsa akanta.

To ni made bansaniba munirat, bari muje mugani idan hakane ko bashin ake=ØÞ=ØHÞ<ØÃß<Øûß
@&þ


(littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda ALLAH)


******


Harararsa tayi,cikin qasa qasa da murya tace"ni ban wahalar dakai ba"

Cikin sauri yace"gashinan kuwa,Bayan abunda nakoya miki ma yau ko tayani bakiyi ba,Amma last time saboda mugunta haka kike ta tsotsar bakina, ko tausayamin bakiyi ba,bakiyi tunanin zan iya fita daga dakinki nahadu dawani afalo yaga yanayi na, yayi tunanin wani abu a tsakanin muba"

Cikin sauri ta kalleshi tace"bakaine Kamin ba"

Cikin sauri Shima yace"yawwa to tunda hakane meyasa ni yau din bazakimin ba?"

Kafin tabashi amsa, suka jiyo muryar mama akusa da qofar Dakin tace"Aisha taso mutafi zamu rufe qofa, lokacin bacci yayi"=ØÞ=Ø3Þ

Cikin sauri ta matsa daga kusa dashi tareda zare hannunta daga cikin nashi hannun, Shima murmushi yayi ya shafa sumar Kansa, yasan mama saboda shi takeso Aisha tatafi, kafin tafuto daga d'akin suka jiyo muryar Hajja tana cewa mama"harsun gama zancen ne? Dakin rabu dasu tunda yau din basu samu waje sun zanta ba"

Cikin sauri mama Tace"A a,bakisan Shahaab bane, saurin bacci gareshi, yanzu haka idan agida ne datuni yayi bacci"=ØJÞ

Tasake daga murya tace"Aisha!"

Cikin sauri Aisha dasukai shiru sunajin surutun mama da Hajja tatashi tsaye zata fice, ahankali Shima yamiqe tsaye yabiyo bayanta, zata bude labulan Dakin kenan yayi saurin fuzgota tafada jikinsa, wata irin wawuyar runguma yayi mata tareda d'ora Kansa akan kafadar ta, kamar jaririn da uwarsa ta dade bata bashi nono ba, haka yake sakin ajiyar zuciya, yanda yake jin tudun dukiyar fulaninta akan qirjinsa, hakan ne yasa yasake matseta sosai ajikinsa yanda zaifi jin abun sosai a qirjinsa, shiru tayi ko kadan batayi gigin hanashi ba, Idonsa a Lumshe, yad'ora bakinsa akan kunanta,cikin rad'a yace"ina sonki,kici gaba da sonah please"

Daga masa Kai tayi alamun to, saide itama kanta tarasa meyasa taqi raba jikinta da nashi,yanda tayi luf akan faffadan qirjinsa jitayi kamar su dauwama Ahaka, Adede lokacin Kuma Hajja tace"kode basa cikin Dakin ne? Naji shiru...."(=ØÞ)

Sai Alokacin taraba jikinta da nashi, tafice ahankali,mama tana ganin futowar ta tasaki ajiyar zuciya, tasan halin danta, akan idonta ma Yaya aka kare da wannan shegen kallon nasa dayake yiwa yarinyar, har Mahmud din za'a cewa a barshi da Aisha su zanta?>ØÝ
Kuma acikin daki su biyu?>ØÝ

Hannun Aishan takama suka wuce Dakin Hajja,yanda taji qamshin turaren yarinyar ya sauya akan Wanda tafita dashi, shine ya tabbatar mata da cewa Mahmud ba ido yazuba mata ba, Amma taji dadi tunda taga Hajja bata fahimci komai ba, Gara ayi magana guda daya gobe Dasafe, abawa Mahmud yarinyar Nan tun kafin azo ayi abun kunya.


Suna zuwa daki Aisha tahaye gadon Hajja ta kwanta tareda Lumshe idonta, sukan sabuwar hira suka dasa, yanayin yanda ya rungume tane yafado mata Arai,tasake tuna yanda ya furta mata cewa yana sonta ,wani irin yanayi take jinta aciki, cikin zuciyar ta tace"nima Ina sonka..."

Tun tana tunanin sa, har batasan bacci ya dauketa ba, Sai cikin dare ta farka taji su mama sunata zance itada Hajja, mamaki ya kamata, lalle an dade ba'a hadu ba, ita Kam juyi tasake yi taci gaba da baccinta.


A 6angaren Shahaab kuwa daqyar yasamu ya runtsa, Sai juyi yake yana murqususu shi kadai, yadade rabonsa da mace, yana fuskantar matsala ta kowacce jijiya ta jikinsa, yasan duk lokacin daya kama munirat a hannu, bazai mata da sauqi ba, saboda an dade ba'a hadu ba.(=ØHÞ)
Haka ya daure, yaci gaba da yakice tunanin Aishan daga ransa, Bai yarda tunanin Nata yajanyo masa wanka ba, saboda agidan surukai da kunya katashi da asuba aji kana wanka.=ØÞ


Su mama kuwa saida sukai sallar asuba sannan suka kwanta, Alokacin Kuma Aisha bata koma bacci ba, azkar takeyi har gari yayi haske,kowa yana bacci duk basu tashi ba,tafuto tad'auki tsintsinya tafara share gidan, yana jin qaran shara yafarka, wayarsa yaduba yaga bakwai da rabi na safe, tunda suka dawo daga masallaci da asuba shida Abba ya kwanta Sai bacci yasake daukansa saboda gajiya, wayar ya ajiye yatashi yayi miqa tareda salati, sannan ahankali yazo bakin kofar Dakin ya tsaya, yadan daga labulen kadan yaga waye yake shara, karyaje yafuto Kuma yaga Ummah.

Ahankali yadan leqa,saiya ga Aisha ce, ajiyar zuciya yasauke yanda ta sunkuya tana sharar hakanne yabashi damar hango tsayaiyun boobs dinta, wani irin abu yaji ya tsirga masa tundaga Kansa har qafafunsa,ya hadiye wani irin yawu,lokaci daya yanayin sa yafara sauya wa, hannunsa yatura cikin aljihun jallabiyar jikinsa, Gara sutafi daga gidannan, inba hakaba idan sukace zasu sake wasu kwanakin to yanada tabbacin wataran bazai iya Hana hannunsa ta6a wadannan abubuwan ba.(=Ø2Þ=ØHÞ )

Domin yaci gaba da kallon su sosai, saiya daga labulen yafuto ya tsaya abakin kofar Dakin, yaharde hannunsa a qirjinsa yana kallon ta, yadade a tsaye yana kallon ta, sannan yayi gyaran murya, cikin sauri ta d'ago kanta ta kalleshi, hannunsa yatura cikin aljihun jallabiyar jikinsa sannan yatako ahankali zuwa kusa da'ita yace"ina kwana?"

Kanta ta sunkuyar qasa,Babban mutum kamar wannan shine yake gaishe ta, Sai taji kunya ta kamata tace"lafiya kalau, dafatan kana lafiya"

Yace"um Gani nan de"

Kallan sa tayi da sauri, kafin tayi magana ya matso kusa da'ita, dan kwalin kanta ya janye qasa, lokaci daya dogon gashinta yafuto fili, cikin sauri tajujjuya ta kalli dakunan gidan, kar wani yafuto ya gansu, tana juyawa tana Kallan dakinsu Ummah hakanne yasa ta turo masa qeyarta, cikin sauri yasaka hannu yacire ribbon din kanta, dogon gashinta yabazu akan fuskarta, kallon sa tayi da sauri, kafin tayi magana yace"kinfi kyau ahaka"

Idonta ta furfuto dashi waje, tsoro takeji kar wani yafuto ya gansu Ahaka, cikin takunsa me aji yaqaraso wajan ta, yad'ora hannunsa akanta, yafara wasa da gashin kamar zaiyi mata kalba dashi, cikin jin dadi yace"kawo tsintsiyar na tayaki sharar...."jin takun mutum ne yasa ya tsaya cak!
Shibe cigaba da wasa da gashin ba, shibe saki gashin ba, gyaran murya Abba yayi, cikin sauri suka juya, wata irin kunya ta kama Aisha, Shahaab kuwa cikin sauri yasaki gashin Nata tareda komawa Gefe yana Dan shafa sumar Kansa, Amma ko kadan yaqi kallon Idon Abba, Dan kwalinta ta maida kanta ta tsugunna Tace"Abba Ina kwana"

Ataqaice yace"lafiya"

Cikin sauri tashige daki, Shikuwa Shahaab Kansa yana qasa,yace"barka da futowa"

Abba yayi murmushi, a ransa yana mamakin yanda Shahaab baya iya 6oye soyaiyar dayake wa Aisha, yanzu inda tabashi tsintsinyar sharar zaiyi kenan?>ØÝ
Kansa ya Girgiza tareda bashi hannu yace"yalla6ai ya gajiya?"

Shahaab bai bashi hannun ba, ganin yanda yake jin kunya yasa abban yakama hannunsa sukayi hanyar waje, yana fada masa akwai yan'uwan mahaifinsa, yakamata suje su gaisa dasu.

Aisha kuwa saida taji fitarsu sannan tafuto tana qarasa sharar, hararar inda suka tsaya itada Shahaab tayi, cikin ranta tace"bashida kunya, gashinan yaja Abba yaganmu"

Saida tagama sharar, sannan taje ta tambayi Ummah abinda za'a dora, Sai umman tafuto suka fara harhada abun Karin kummallon tare,har zuwa lokacin Hajja da mama,Sunata bacci, basu tashi ba.

Sai wajan karfe goma su mama suka tashi, basu zauna Zaman cin abinci ba Sai wajan shadaya na safe, Alokacin harsu Abba sun dawo shida Shahaab, yakaishi yaga dangi, yaga iyayensa, sun kuma yi maganar neman auren Aisha da Shahaab yakeyi, anan suka tabbatar masa zasuzo har gida Sai ayi maganar agaban Hajja, Bayan sun dawo gida wanka yayi, ya maida kayansa na jiya, Amma baisaka babbar rigar ba, ta cikin kawai yabari Sai hularsa daya dora, Sai hakan yaqara yimasa kyau yakoma tamkar saurayi, anan tsakar gida sukaci abinci shida Abba, Aisha tana cikin daki bata futo wajan su ba, Shahaab Kansa na qasa yana danna wayarsa,Mama ta kalli Hajja tace"to Aysha ai sai kuyi shiri mutafi ko?"

Cikin sauri Hajja tace"ina zamuje?"

Mama tace"Abuja mana, kina tunanin zan Barku kuci gaba da rayuwa anan ne?"

Hajja Tace"A a, banfada miki ba, dade Ina cewa duk lokacin Dana ganki to wajanki zan koma kodan in rabu da jarabar mesunanki ,Amma Kuma yanzu tunda akwai alaqa, akwai dalili, bazan biki ba, zan jinkirta idan aka daura auren takwarar ki, sainabi Yan kaiwa amarya mutaho tare, kude turo motoci masu yawa, Dan inada jama'ah, kinga jummai ma nasan itama zatayi gayya,tunda ta dalilin ta ne har Allah ya hadani dake koba haka ba"(=ØÞ)

Mama tayi dariya tace"to uwar gayya,har yanzu de kina Nan da jama'arki kamar baya,to aini banice meturo muku motoci ba, kin ganshi Nan, kifada masa"

Hajja ta juya ta kalli Shahaab tace"Kai Shahaabu, kanajina
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On SHAHAAB
avatar
fateema

7 months ago

Reply

Allah yakara basira

avatar
taskar

7 months ago

Reply

Replying to fateema

Ameen

avatar
ummu-swabir

2 months ago

Reply

Thanks

Please Login or Register in order to submit comment