Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

afalon saide Aisha ta jiyo sautin dariyar su, wani lokacin tayi musu vedio wataran Kuma ta dinga kallon su tanajin farinciki acikin ranta.


Har zuwa lokacin Hajja tana gidan,idan sungaji da Zaman gidan itada mama haka zasuyiwa Shahaab magana yasa a fitar dasu wani wajan Sudan Sha iska su dawo, ahankali ahankali rayuwa take tafiya har Daddy yafara rarrafe, tunda yafara rarrafe mama ta Dena ajiye wayarta aqasa, idan tea aka kawo musu saide su riqe a hannun su, baya ta6a zama shi kadai, idan kuwa aka jishi shiru babu 6arna to yasamu wani abun ne yana lalata shi, shine zakaji shi shiru, gaba daya falon mama yazama kamar falon renon Yara uku saboda yanda aka baje masa kayan wasa, haka zai zauna daga shi Sai pampers yana wasansa afalon, suma masu aikin gidan inde sunzo falo Tofa Sai sunyi masa wasa zasu wuce, ganinsu dayake yau da gobe yasa baya musu qiwa, saide in baiga wani yashigo falon ba, yanzu zai fara daga hannu yana kuka alamun yanaso a dauke shi.

Tunda Shahaab yatafi lagos Kwanansa biyu bai dawo ba, yau yana hanyar dawowa yakira Aisha yace tahada masa cake idan yazo zaici, gashi su mama basa Nan, Kuma tunda taji Yakirata yafada mata hakan tasan cewa to bayason na ma'aikatan gidan ne, ta kalli Daddy dayake wasa cikin motar wasan Yara, ta dauke shi ta goyashi suka shige kitchen tafara aikinta tana masa magana kamar wanda yake jinta, Shikuwa gwarancinsa yake ma yana saka hannunsa abaki, Bayan tagama hada komai tasaka butter da suger tana mixing tace"Daddy na d'an Albarka yau ai zaka barni in yiwa Abbanka cake ko?"

Tadauko qwai tafasa taci gaba da mixing, Hankalinta yayi kan abinda take batayi aune ba taga Daddy yaja fulawar data ajiye ya kwaro musu ita kansu, lokaci daya ta tsorata tasaki qara saboda zubar fulawar kawai taji, shikuma qaran data saki ne yasa ya tsorata yasaki kuka Kuma ya qanqame bowl din yaqi saki, baqin ciki yakama Aisha(=ØÞ).


Tunda yashigo kitchen din ya tsaya abakin qofar kitchen din yana kallonsu, sosai tayi masa kyau da goyon Daddy musanman da yaji tana masa magana kamar Dame Hankali take magana, ganin aikin da Daddy yayi mata yasa ya tuntsire da dariya yafara yimusu vedio, juyowa tayi ta kalleshi da fuskarta data cika da fulawa tafashe da Kuka, qaraso wa yayi kitchen din ya qwace bowl din hannun Daddy sannan ya kunce mata shi, kuka take sosai cikin kukan tace"kana ganin abinda yamin fa, ya 6are baki yanamin kuka kamar bashine yamin laifin ba"

Cikin jin dadi ya janyo ta jikinsa ya rungumesu gaba daya, sannan yafara kad'e mata fulawar yana lallashin ta, daqyar yasamu tayi shiru sannan yace"ai nine nace amin cake din, to abarshi tunda Daddy yahana"

Cikin shagwa6a ta kalleshi takai masa Dukan wasa a qirjinsa.


Da daddare suna zaune a part dinsu suna kallo, Sanye take cikin rigar bacci tana kallon film din da ake haskawa, agefe daya Kuma waya take da faty tana sanar da'ita ansaka ranar bikin ta, shikuma Shahaab yana zauna aqasan kafet yana aiki a computer, yayinda Daddy yake Gefe yana wasa, saida tagama wayar sannan ta kalli Shahaab tace"Uncle ansaka ranar bikin faty fa, nanda wata shida"

Hankalinsa yana kan aikin dayake yace"Allah yakaimu, Amma Ina tunanin zuwa lokacin Bama Nan ai, inaso muje umara gaba dayanmu, dasu Ummah dasu Hajja, daga Nan Kuma zamu je muga jabir"

Cikin farinciki tace"Uncle Saudia zamu tafi gaba dayanmu?"

Yace"insha Allah"

Cikin jin dadi taje ta rungume shi tasakar masa kiss tace"wayyo Allah, Amma naji dadi uncle, mungode Allah yasaka da alkhairi yaqara budi"

Cak ya dauketa yadorata akan cinyarsa yace"Amin, idan kinyi waya da qawar ki ta jigawa kifada mata Faisal yamin magana yanaso inje gidansu in nema masa aurenta"

Fari tayi da idonta tace"wai Walida?"

Kansa yadaga mata yana sake gyara mata gashin kanta, cikin jin dadi tace"zan fada mata, Bari inkirata ma yanzu"

Tafadi haka tana qoqarin tashi daga kan cinyarsa, cikin sauri ya riqeta yace"Haba madam"

Murmushi tasaki kafin tayi magana yafara waigawa falon yace"ina Yaron Nan yake ne?"

Tashi tayi daga cinyarsa tace"inaga wasa yake"

Shima tashi yayi yana nemansa, acan suka hangoshi yana rarrafe yana bin ball dinsa yanaso ya dauko ta, cikin sauri Shahaab yadauko shi suka dawo kan kujera suka zauna ya kalli Aisha yace"yazaki barshi yana rarrafe a tile maamah?"

Tace"to Uncle akan cinyata zaiyi?na'isa in Hana Daddy rarrafe?tayaya ma zan San yatafi?"

Goge wa Yaron qafa yakeyi, sannan yadora mata shi akan cinyarta yace"ki kula dashi karki sake barinsa yana rarrafe a tile please,Bari in Dauko takardu adaki"

Aisha ta Girgiza kanta, Shima Daddy qoqarin zamewa yake zai sauka, babu musu kuwa ta sauke shi, wajan kallo yanufa ya zubawa TV ido yana kallo, itama Hankalinta yana kan kallon saijin ihun kukan Yaron tayi, cikin sauri ta nufeshi, Shahaab ma da yaji kukan yayi yawa cikin sauri yafuto daga d'akin hannunsa d'aukeda takardu yanufeta sannan ya karbi Daddy yace"me aka masa yake wannan uban kukan?"

Cikin damuwa tace"ni wallahi ban lura ba, Sai kukan sa naji, speaker yaja tafado masa ahannunsa shine yake wannan kukan"

Cikin sauri yaduba hannun yaga har yatsun sun danyi ja kasancewar sa fari, iska yadan hura masa a hannun sannan ya kalleta yace"maamah, kifadamin tsakaninki da Allah Anya ba cizon yaron Nan kikai ba?"(>ØÝ=ØÞ)

Cikin sauri ta d'ago ta Kalle shi tace"nashiga uku Uncle??"

Cikin damuwa shima yace"maamah idan cizon nasa kikai ma Yaya zanyi dake?"yana fadar haka yajuya da Yaron suka shige daki, ita Kam murmushi ma tayi tabi bayansu Dakin, gaba dayansu su biyun suka hadu suka lallashi Yaron har bacci ya dauke shi sannan ne Kuma suka shirya=ØÞ

Rayuwa tana juyawa Izuwa yini, yini yana juyawa Izuwa kwana, kwana yakoma sati, sati yakoma wata har Daddy Yacika wata goma, Adede lokacin Kuma suka shirya gaba dayansu suka tafi Umara, Mama,Hajja,Ummah,Abba, Shahaab, Aisha, dakuma Daddy, satin su biyu a Saudia, Adede lokacin Kuma akai bikin faty,Walida Kuma ansaka rana wata uku masu zuwa itada Faisal Yaron Hajiya zaliha,kana ganinsu kasan family ne daya amsa sunan sa Family Kuma suke cikin kwanciyar Hankali da walwala, daga Saudia Australia suka wuce wajan Jabir, yayi murna sosai da ganinsu ya girma yasake zama saurayi, yana ganin Daddy ya dauke shi bacci ne kawai yake raba shi da Yaron, satinsu biyu a qasar, suka dawo Nigeria.

Bayan sati daya Aisha da Shahaab suna zaune afalon su suna kallon Ball, gaba daya hankalin sa yana kan ball din da'ake bugawa, Aisha ma daba sanin Yan ball tayi ba tazuba ido tana Kallonsu har aka gama wasan, taga an nuno wani matashin saurayi da yaro ahannunsa dagashi har Yaron Sanye suke cikin kayan ball Sai mutane yakewa sign a takardar dasuke bashi, sosai yake Fara'ah dimples dinsa Sai lotsawa suke, Yaron hannunsa yadaga masa yana gudu da Yaron sosai alamun ball din dasuka buga tamasa dadi, Shahaab yayi murmushi yace"wannan Yaron bayaji"

Aisha ta juya ta kalleshi tace"musulmi ne?"

Murmushi yayi tace"sosai kuwa,d'an asalin Niger ne,Amma a Nigeria suke, family dinsa da kowa da kowa da matarsa duk suna kano,sunansa BIG BROTHER, but wasu suna kiransa BABBAN YAYA,ya'iya ball sosai"

Aisha tayi ajiyar zuciya tace"um, ku kuka San Yan Ball Uncle"
Juyawar dazatai taga Daddy yabude fos dinta yafuto da kudin ciki Yan Dari biyar biyar da dubu dubu gaba daya ya yaiyaga su, cikin 6acin rai ta daki Yaron tace"Daddy kudi kake yagawa haka?"

Cikin sauri Shahaab ya kalleta, Jiyayi kamar shi ta daka,lokaci daya yafara huci yana Kai zuciyar sa nesa, jiyake kamar ya Fashe, daqyar ya'iya controlling kansa yace"maamah duka? Yanzu Harkin fara Dukan yaron Nan agabana maamah?"

Cikin 6acin rai ta kalleshi tace"Uncle kudi fa yake yagawa, idan Bana dukansa bazai ta6a gane yayi laifi ko baiyi ba"

Yace"to kudi Kuma saiki masa irin wannan Dukan? Ina laifin ma kisamu tsinken tsintsiyar laushi? Kidena masa irin wannan Dukan kinji nafada miki, idan kika sake Kuma zakiga abinda zai biyo baya"

Haushi yakama Aisha,baqin ciki ne yasa batasan lokacin data sake kaiwa Yaron duka ba, Shahaab yana ganin haka yatashi tsaye, tana ganin yatashi tsaye takwasa a guje tayi dakinta, tana kokarin rufewa yayi nasarar shiga Dakin, akan gado suka zube, yajata jikinsa ya matse ta, dariya tafara tana kokarin qwatar kanta, tasan zata Iya shan wahala awajansa, inde akan Daddy ne, shiyasa tun kafin yayi mata wani abu takai hannunta tata6o masa inda tasan cewa dole yayi saranda, Shima anasa 6angaren hannunsa bibbiyu yad'ora akan nashanunta yana murza mata nipples d'in da qarfi, cikin muryarsa Mai cikeda buqata yace"meyasa bakya jine maaa-mahhhh"

Yafadi sunan Nata a rarrabe, cikin kissa tafara zuba masa kukan shagwa6a, hakan ne yasake tunzurashi yaci gaba da aikata mata saqo, cikin tsananin azaba taji cikinta yayi wata irin murdawa, Nan da Nan tasaki kukan na gaske, cikin kuka tace"Uncle cikina, zan mutu Uncle"

Idonsa a Lumshe suke, Amma yanda yaji tayi masa magana cikin serious, yasa yabude Idonsa yakai Kallonsa gareta, ganin halin datake ciki yasa cikin tashin hankali ya dauketa, yadawo falo yad'auki Daddy suka futo, Adede lokacin mama da Hajja suna compound din gidan suna zancen su, ganin yanda ya Dauko Aisha a hannu yasa suka iyo wajan sa cikin damuwa, mama tace"muje Asbiti kawai, ciwon ciki abun tsoro ne"

Cikin sauri yace"ku zauna mama, Bari muje nakaita"

Hajja Tace"A a, Zaman me zamuyi? Muje kawai"

Babu musu suka dunguma zuwa Asbiti gaba dayansu, suna zuwa likita tabata taimakon gaggawa aka daura mata ruwa tareda allurai, Sai Alokacin tasamu bacci, gaba dayansu sunyi shiru suna mamakin wannan ciwon ciki na Aisha, cikin ikon Allah tafarka cikin qanqanin lokaci, Adede lokacin Kuma Likitan tadawo fuskarta d'aukeda murmushi ta kalli Shahaab tace"yalla6ai Yaron baba fa bayason guje-guje da tsalle-tsalle, congratulation madam tana d'aukeda juna biyu"

Cikin sauri Aisha ta tatashi zaune, Shahaab kuwa wani irin farinciki ne ya kamashi yace"Dr da gaske?"

Cikin farinciki tace"sosai yalla6ai"


Hajja da mama ma cikin farinciki suka daga hannu suna yiwa Allah godia, bata dauki tsawon lokaci ba suka sallamesu suka dawo gida, suna zuwa gida ta wuce part dinsu, acan dinma dakinta ta wuce ta zauna abakin gado tafashe dawani irin kuka, tunda suka taho a hanya ya lura kawai sune suke budurinsu, Aisha bata cewa komai, kwata kwata ya lura batayi farinciki da samun cikin ba, lokaci daya jikinsa yayi Sanyi, shiyasa yanayin parking da yaga tafita daga motar yasan cewa akwai damuwa, su mama kuwa basu lura da sauyin yanayin taba, suma part dinsu suka wuce, ahankali ya kalli part dinsu yasaki ajiyar zuciya sannan yabi Bayan Aisha.


Yana shiga kuwa, yaga bata falon, Kai tsaye dakinta yawuce, tun kafin yashiga Dakin ya tsinka yi muryar ta tana kuka, jikinsa ne yayi Sanyi kalau, yaja ya tsaya abakin kofar d'akin tareda harde hannunsa a qirjinsa yana kallonta, Sarai taji shigowar sa, Amma bata daga Kai ta kalleshi ba, asalima kukan ta taci gaba dayi, ajiyar zuciya yasauke yatako yaqaraso cikin Dakin ya zauna akusa da'ita yace"maamah"

Tayi shiru bata amsa masaba, Kallan ta yayi yace"atunani na zakiyi murna ne da kyautar da Allah yayi mana maamah, bansaniba ko kin daina sonane shiyasa bakya son ki hada jini dani"

Cikin kuka ta daga kanta tace"Daddy fa ko yayeshi banyi ba....kuma yanzu harna sake yin wani cikin"

Idonsa ya Lumshe sannan yabude, yace" bazanga laifin ki ba idan kinyi watsi da kyautar da Allah yayi miki, saboda Sai wannan shekarar ne Zaki cika shekara goma Sha Tara, Amma ni shekaru na arba'in dawani abu, banda Ina cikin jin dadi dakuma yanayin jikina ke kanki kinsan cewa niba qaramin mutum bane maamah,kiduba kigani fa Sai yanzu ne nafara haihuwa, kafin ace yarana sun girma sun fara taimaka min nariga na tsufa, shekara ta goma Sha da aure ban haihu ba Sai yanzu ne Allah ya dubeni yabani Daddy, Kuma yanzu saboda butulci irin nawa Sai inqi wata kyautar Dayayi min?maamah ko Daddy bekai wata goma ba kika samu ciki zanyi murna da hakan,Amma idan zubarwa kike so kiyi Nima saina miki allurar, idan hakan zaisa kiyi farinciki, saide Kuma agaba idan Allah yahanamu haihuwar har abada, karkiyi kuka Dani, kiyi kuka da kanki"

Hawayen idonta tashare tace"ni bazan zubar da ciki naba,Nasha wahala a haihuwar Daddy, Kuma ko shekara biyu beyi ba, gashi yanzu wata wahalar zan sake fuskanta"

Janyota yayi jikinsa ya rungumeta sosai sannan yace"maamah haihuwa ta Allah ce,insha Allah, Allah zai saukeki lafiya, kiyi hakuri Dan girman Allah kidinga haifamin Yara wallahi inaso koda Yan biyu Zaki dinga haifamin"

Cikin shagwa6a tace"Kuma ma idan na daki Daddy saika dinga min fada, ban Isa inyi masa wani abun ba saika dinga yin abu kamar zaka rufeni da duka, to ahakan ne zakace indinga haihuwa"

Murmushi yasaki ganin ta sakko yanzu Kuma mita takeyi, cikin nutsuwa yace"inde akan Daddy ne na daina, wallahi na daina ki masa komai ma inde tarbiya Zaki bashi,Shima Wanda Zaki Haifa din nabaki Dama kihadasu kimusu tarbiya yanda ya kamata, shikkenan abinda kike so?"

Dan qaramin bakinta ta turo gaba cikin shagwa6ar de tasake cewa" Kuma kullum kullum kadinga yin abu daya ba shiyasa ma nasamu cikin da wuri ba"

Murmushi yasaki yace"maamah rigima...,maamah yin wannan abun ko rashin yinsa bashine yake kawo ciki ba,zan'iya yi sau daya ma kiga kin samu cikin"

Yasake sassauta muryarsa cikin rad'a yace"ni yanzu ma dazaki Bani Dakin min hajji da umara"

Cikin sauri takai masa Dukan wasa akan faffadan qirjinsa, cikin jin dadi yace"kinji maamah? Kinga Daddy yana wajan su Mama, kawai ma daga yau mu bar musu shi mukuma saimu raini cikin mu,Kuma yanzu ma nasan bazai dawo ba, kafin yadawo kinga saimu kwantar da qura"

Murmushi tayi tana masa wata irin harara Mai kalar Kallan soyaiya, Shima wani irin shu'umin kallo yake jifanta dashi batareda yace komai ba, kawai dai cikin dabara yatura hannunsa cikin rigarta yakamo nashanunta yafara aika musu da kyakykyawan saqo, dadin dataji ne yasa tabashi hadin Kai, lokaci daya suka haukace, ta manta da batun ciki tabaje yana abinda yaso da'ita,irin dadin dayaji tayi lokacin data samu cikin Daddy yanzun ma shi yaji, ita kanta dadi taji sosai taji kamar zata suma,lokaci daya tafara sakar masa kukan dad'i, hakan ne yasa Shima ya haukace mata yafara wani irin sambatu kwata kwata baisan inda kansa yakeba, dagashi har ita sun manta basu rufe qofar Dakin ba, hakanne yabawa mama damar jiyo wani irin ihu da nishi tundaga falo kasancewar Daddy yana kuka ta taho domin ta kawo musu shi, tun kafin ta qaraso tsakiyar falon ta juya cikin sauri tana jiyo yanda Shahaab yake wani irin kuka kamar bashi ba, kamar 6arauniya haka taja Kofar falon ta rufe musu kamar tana tsoron zasuji shigowar ta, saida tafuto daga part din sannan tasaki ajiyar zuciya ta kalli Daddy dayake hannunta tace"megida,in zakayi shiru tun wuri to kayi shiru,iyayenka sunyi Nisa ba zasuji kiraba"(=ØJÞ=ØHÞ)




SHAHAAB littafin kudi ne, 300 ne kacal idan kika karanta baki biyaba nabarki da MAHALICCINKI


0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number
08033300034









Amnah El Yaqoub
'<Øûß


ASH-HAB



page 26





Basu sararawa junansu ba saida suka dauki tsawon lokaci Mai yawa, Bayan komai yagama kammala babu Wanda yanemi Daddy acikinsu, wanka sukayi, Shahaab ya maida ta jikinsa yana sake nuna mata yanda yaji dadin baiyanar cikinta, dakuma alqawura iri iri akan yanda zai dinga basu kulawa daga ita har yaran dazata dinga Haifa masa.

A 6angaren mama, itama bata sake nemansu ba, taga alama sabon amarci sukeji, saide a 6angaren daya tanajin kunyar kanta idan ta tuna da abunda kunnuwanta suka jiye Nata dazun.


BAYAN SHEKARA DAYA

Sosai yayi masifar kyau cikin manyan Kaya fari tas, babbar rigar ta kar6i jikinsa, Yayinda fatar jikinsa take wani irin sheqi alamun jin dadi atare dashi, turare ya fesa yasake gyara Zaman hular Kansa.

Cikin jin dadi tayi ajiyar zuciya Bayan tagama qarewa mijin Nata kallo, a koda yaushe Gani take kamar tafi sauran mata sa'ah kasancewar ta tare dashi, tanajin alfahri wani lokacin saboda tunawa datake itadin matar MAHMUD WAKILI ce, cikin shekara d'ayan Nan tasake murmurewa jikinta ya murje, bata hada qiba sosai ba, Amma kokadan babu alamun Rama atare da'ita, leshi ne ajikinta dinkin doguwar Riga, batayi wani Daurin dankwali Mai wahala ba, Sai sarqar gold da zoben gold dasuke hannayenta, cikin yanayin roqon alfarma tace"Uncle Dan Allah, tunda ankusa fara bada admission Nima Atemaka min mana, in danyi karatun Nan"

Cikin sauri ya kalleta, yayanta biyu, idan tafara karatu babu Wanda zaice tanada aure, yanzu nema girma da Dan Hankali suke sake shigar ta, yanda yakejinta a ransa baya tunanin zai iya barinta ta dinga cudanya tsakanin ta da wasu mazan, kafin yabata amsa Yaron dake kwance akan gadon yafara kuka, cikin sauri yasaka hannu ya tattare babbar rigar jikinsa, sannan yad'auki Yaron yana jijjiga shi, yasaka masa fida a bakinsa yana cewa"sorry sojana, kaida baka kuka, waya tabaka kake kuka? Ko saboda kaji mummynka zata gudu makaranta tabarmu ne, uhm?"

Aisha tana jinsa tayi murmushi tace"Uncle zaka barni?"

Cikin daure fuska ya kalleta yace"meyasa bazaki daina min wannan maganar bane?"

Cikin nutsuwa tace"Uncle ilmi shine jigon rayuwa,kasancewa ta atare dakai inajina kamar ban Rasa komai ba, banida damuwar komai, Ina rayuwa ta yanda nakeso, Amma Kuma ta wani 6angaren nasan narasa wani abu guda daya shine ilmi, kabarni inyi karatu Nima ko kadan ne, Kaga FEENAH saida tayi masters dinta sannan ta auri AHMAD Bayan gwagwar mayar dayasha yana nemanta(DANA SANI).

haka AMAL itama mijinta KARAM,shine yakaita har qasar waje domin ta qaro ilmi kasancewar sa Babban mutum Kuma Dan siyasa yasan cewa dole matarsa zatayi mu'amula da kowanne irin mutane,(BURINAH)

IMAN bata auri ALIYU ba, saida ta kammala degree dinta na farko, sannan ta aure shi Kuma suka zauna lafiya (WAZAN ZABA?)

sannan duk wahalar rayuwa da HANIFA Tasha, Bayan tayi aure HANIF shida Kansa ya maida ta makaranta(SHALELAN BABA) duk saboda suyi yaqi da jahilci.

Haka BABY tana cikin karatun sauyin qaddara tasa ta auri MK, Shima daga baya saida ta qarasa karatun ta(NI DAKE)

sannan duk girma irinna Familyn mazawaje,kaga yayansu mata basa dogon karatu, Amma NIHLA qaddara tasa saida tayi degree dinta a Abuja, sannan ta Auri ABBA, (DANGI 'DAYA)


Haka ASIM, shida Kansa yake koyawa INSAAF, karatu, Kuma shine ya zabi abinda yakeso tayi(INSAAF)

WAHEEDA Bayan Aurenta da NAUFAL tayi karatun ta a qasar waje (BABBAN YAYA).

Meyasa nibazaka barni ba Uncle?"

Ajiyar zuciya yasauke yace"saboda nabarki kiyi karatu duk kika min irin wannan dogon misalin?, to saiki qara da cewa MAHMUD WAKILI, EFCC CHIRMAN, shine kawai baibar matarsa AISHA MAHMUD, tayi karatu ba"

Yana fadin haka yafice daga d'akin hannunsa d'aukeda junior,Mai sunan kakan Aisha wato mijin Hajja, Ismail,suna kiransa da junior.

Qafafunta tafara bubbugawa aqasa cikin shagwa6a, sannan tasa hannu ta dauki wayarta da handbag dinta, tabiyo bayansa, basu zame ko'inaba Sai part din mama.


Suna zuwa sukaga mama da Hajja suma sungama shirya wa, Kai tsaye wajan su yanufa ya ajiye musu Yaron, sannan yawuce zaici abinci, itama bayansa tabi, suka fara cin abincin.


Daddy yana ganin junior yataho da gudu yadawo wajan Yaron yayi masa kiss a kumatunsa, Hajja ta kama baki ta kalli Mama tace"ikon Allah,wacce irin al'adace wannan? Kode awajan iyayen nasa yake Gani?"

Mama ma da mamaki ya kamata tace"oho musu, jarabar uban kadai ma ai zatasa wataran yayiwa uwar agaban Yaron, anan zai Gani"

Ta kalli Daddy tace"Daddy na karfa ka cijeshi"

Juyowa yayi ya kalli Mama yace"Mama Baby ne?"

Tace"eh"

Yasake cewa"mama Baby ne?"

Tace"eh Baby ne"

Dariya yasaki yace"Baby nane"

Mama tace"nikwa nasan Babynka ne, tunda uwarku daya ubanku daya"

Hajja tayi dariya jin hirar mama da Daddy, tad'auki wayarta takira jummai, Bayan sun gaisa tace"to jummai gamunan zuwa, yanzu zamu dauko hanya kiyi mana kunun Aya Mai dadi de"

Daga d'ayan bangaren jummai tace"to Hajja A'i, Allah yakawo ku lafiya"

Hajja tace"Amin"sannnan tafara shirin kashe wayar, cikin sauri jummai tace"nikam Hajja A'i gulma ajali inba'ayi ba amutu, tun rannan kike cemin zakuzo nace ganin gida zaku zo ne kokuma wani abunne yataso?"

Hajja tace"kai jummai da gulma kike, to zamu zo taro ne, mijin Mai sunan qawa zai bude gidan marayun daya gina"

Cikin sauri jummai tace"oho, to, tona gane yanzu, to saikun zo, Bari naturo a siyomin kwatar aya, Sai ayi muku"

Hajja ta kashe wayar, Adede lokacin su Aisha suka gama cin abincin, suna zuwa Aisha ta dauki Junior, suka futo gaba dayansu, motoci biyu suka yi, suka wuce Airport,acan suka hadu dasu Abba da Ummah, basu dade da zuwaba, jirginsu yatashi.


Bayan sun sauka agarin ko zama basu yi ba, jummai tataho gidan, daga Nan manyan gari suma suka shishshiga mota sukai ayari gaba dayansu, suka wuce wajan taron, waje Yacika maqil da mutane, Gwamnatin Jihar ta basu hadin Kai yanda ya kamata, har akai taron bude gidan marayun lafiya, aka gama lafiya, su Aisha Kam gida suka iyo, Amma mazan duk suna can,kasancewar baqin da suka zazzo basu gama tafiya ba.


Acikin gidansu Aisha Bayan kowa yayi wanka gaba dayansu bajewa sukai a Babban falon Hajja wadda aka qawata shi da kayan more rayuwa, yaji kujeru kamar ba'a cikin Garin CHAMO, gidan yake ba.

Jummai ce tayi sallama takawo musu kunun ayar da Hajja tace ayi musu, mama Tasha Dan kadan ta ajiye, Aisha kuwa waya ce a hannunta tana turawa Shahaab saqo,Yayinda junior yake bacci akan kujera, Daddy kuwa daga shi Sai Dan qaramin wandon Yara tareda singlet yana wasa da ball a Dan qaramin tsakar gidan nasu, Hajja tad'auki kunun ayar Tasha, cikin sauri ta ajiye ta kalli jummai tace"jummai wannan aiba kunun Aya bane, kwata kwata babu gardin ayar abaki, wannan ai ruwan daurayar nawa kunun ayar ne, ni Dama tunda naji kince Zaki siyo kwatar Aya nasan cewa Sai ahankali"

Jummai ta gyara zamanta sannan tacire mayafin kanta tace"ke kwantar da Hankalinki, na yanzun ne nake zunduma masa ruwa, Aida Ina murna kin Bani firji na kama kunun Aya inayi ka'in da na'in, Ina farinciki zan samu kudi, to wallahi inayi jikokina suke shanye wa, baifi in samu ribar nera talatin ba, itama talatin din inbawa Dan talla ita, nikam Aina Dena yima"

Daddy yabugo ball tafado d'akin, yace"goooo, Hajja bugo"

Hajja tace"inani Ina ball Daddy?"

Jummai ta kalli daddy, sannan tajuya ta kalli Hajja tace" Hajja A'i gulma ajali....."

Kafin ta qarasa mama tayi dariya tace" fadi maganar da kike so kawai jummai"

Jummai tasake kallon Daddy, sannan ta kalli Hajja tace"shi wannan Yaron Jikan ki, zance ne kokuma Dan ki, bashine Yaron da Aisha ta Haifa ba?"

Mama tayi murmushi tace" shine mana, Daddy ne"

Jummai ta Jinjina Kai sannan ta kalli Daddy tace"kai yaka zonan"

Babu musu Daddy yazo wajan ta, ta kalleshi tace"yaya sunanka?"

Kai tsaye yace" Daddy"

Tasake cewa "shekarar ka nawa?"

Yace"hudu, biyar, shida"

Jummai tajuya ta kalli su mama tace"kaiiii, wannan Yaron bashine Aisha ta Haifa ba, yaro shekara biyu yake wannan surutun mu idan anan ne ai Musanta shekarun nasa zamuyi, ai wannan saide muce yabawa shekara biyar baya"

Adede lokacin Shahaab da Abba suka shigo,Shahaab yana jin abinda jummai tace yayi murmushi sannan ya tsugunna yana gaishe ta, cikin mutunta wa ta amsa tana sake tayaashi muryar bude gidan marayun da akai, cikin nutsuwa yatashi yawuce Dakin dasuka sauka, Shima Abba dakinsa yawuce Dama agajiye yake.


Aisha tana ganin shigar sa daki ta wuce kitchen tadauko masa awarar qwai, da damammiyar fura ta wuce Dakin, tana zuwa kuwa ta ganshi a kwance alamun hutawa yake, zama tayi akusa dashi tace"Uncle tashi Kaci awara da fura"

Babu musu yatashi, tafara bashi awarar abaki, yanaci yana hadawa da fura Mai Sanyi, saida ta tabbatar ya qoshi, sannan ta maida kayan kitchen tadawo Dakin Daddy yana biye abayanta

Shahaab ya kalli Yaron yace"Daddy zonan"

Yana zuwa yaja shi jikinsa cikin wayo yace"kanason sweet"

Daddy yace"Eh inaso"

Cikin sauri Shahaab yace"yawwa, to kaje Abba yabaka, yanacan da sweet dayawa awajansa, idan kagama Sha ka tsaya acan katayashi wasa, tun dazu yake nemanka"=ØJÞ=Ø2Þ

Cikin gudu daddy yafice daga d'akin, Aisha ta kalleshi, kafin tayi magana ya fuzgota jikinsa, hararar wasa tayi masa tafara nuna masa falo da hannunta, cikin tsananin buqata yace"to menene?"

Tace" Uncle, kaji tsoron Allah kaji tsoron mutum ukun Nan, Hajja, mama, dakuma iya Jummai"(=ØÞ>Ø#Ý)

Idonsa a Lumshe, cikeda jaraba yace"idan bamuyi Bama bazasu daina mana surutu ba, kawai Gara muyi abunmu, munci abinci munsha ruwa, ba aikin komai zamuyi ba to menene yarage?"

Ya qarasa maganar yana yi mata wani irin kallo Mai kashe jiki, kanta ta Girgiza tafara kokarin raba jikinta da nashi, sake rungume ta yayi cikin shagwa6a yace"nide kibani Abuna, ya kamata anemawa junior qanwa, dama kina cewa kinason Baby girl, toba saimu samo masa Baby girl yar jigawa ba?"

Cikin shagwa6a tace" Uncle kaima fa kasan cewa bazaka iya control din kanka kayi shiru ba, sannan..... "

Cikin sauri ya katse ta yace" tayaya zan'iya control din kaina a wannan yanayin? But tunda
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On SHAHAAB
avatar
fateema

7 months ago

Reply

Allah yakara basira

avatar
taskar

7 months ago

Reply

Replying to fateema

Ameen

avatar
ummu-swabir

2 months ago

Reply

Thanks

Please Login or Register in order to submit comment