Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

zuciya yasaki yace"kiyi hakuri, Dana dawo nagaji ne dayawa, saina kwanta bacci bansamu damar kiranki ba,kin haqura?"

Cikin shagwa6a tace"Uhm...
nide ban haqura ba"

Yanda tayi masa maganar cikin shagwa6a hakane yasa yaja fillo ya rungume a qirjinsa tareda Lumshe Idonsa, ahankali cikin lallashi yace"tome kike so?"

Cikin sauri tace"saika cemin kana sona sau Dari"

Murmushi yasaki yace"shikkenan?"

Tace"eh"

Babu musu yafara furta"i luv you, I luv you.....saida yafada sau d'ari cif, kamar yanda ta buqata, sannan yace"nagama"

Ajiyar zuciya tasaki Tace"ka fanshi kanka,to ya gajiya?"

Ahankali yace"Alhamdulillah, but nagaji sosai maaamah, please kizo"

Cikin sauri tace"ina?"

Yace"kizo yanzu....wajena....inason tausa"

Murmushi tayi tace"aiban iyaba"

Cikin sauri yace"aizan Koya miki, Amma nafison kimin iya cinyoyina"

Cikin sauri tarufe fuskarta taqi bashi amsa, yace"kinji? Zakimin?"

Cikin sauri tace"zan mintsineka idan kasake fadamin haka"

Murmushi yayi yace"wacce qasa kike so aje ahado miki kayan lefe?"

Sai taji tambayar tasa tazo mata a bazata, har yanzu idan yayi wani abun mamaki ne yake sake kamata, Amma idan ta tuna da Mahmud Wakili take tare, saita daina mamaki, ajiyar zuciya tayi tace"nanan qasar ma yayi"

Cikin sauri yace"no, kifadamin qasar dakikeso Sai ahado miki,kinga bamuda isasshen lokaci dayawa"

Ahankali tace"ni bansan na inane yake da kyau ba, nabaka za6i, kayimin duk abinda Allah yahore ma, Amma karka takura kanka, kayi abinda Allah yahore ma kawai"

Wani irin sonta yaji yasake shiga ransa, yar qarama da'ita Amma sai Hankali, cikin jin dadi yace"toshikkenan za'a kawo insha Allah,please kiss me Maaamah, Ina kewarki"

Tace"kaiii, tayaya to? Waima Ina matarka kakirani a'irin wannan lokacin?"

Yace"tana dakinta, nide kimin abuna"
Yaqare maganar cikin sigar shagwa6a.

Ahankali tace"to tayaya?"

Yace"Ahakan"

Ahankali ta juya ta kalli Hajja, taga bangon Dakin take kallo tana bacci, ajiyar zuciya tasake yi sannan ta Lumshe idonta tasakar masa kiss tacikin wayar

Lumshe Idonsa yayi, cikin sigar rad'a yace"please maaamah cigaba, karki dena kinji...."

Ahankali taci gaba da kissing din wayar akai-akai yana jinta, jiyake kamar shi takeyi wa,babu musu Shima yafara maida mata, lokaci daya taji yanayin ta yana neman sauya wa, cak ta tsaya ta daina abinda take yi, Idonsa a Lumshe yace"why?"

Cikin shagwa6a tace"ni
... Nifa...uhm ni wallahi..."

"wani iri kikeji?"

Ya katse mata maganar Tata ta hanyar jefa mata wannan tambayar, babu musu tace"um"

Murmushi yasaki yace"Nima haka nakeji, shiyasa na matsu naganki acikin gidana, matsayin matata, mekikeso nayi Miki a rayuwa Maaamah?"

Cikin rashin Sani tace"kamarya?"

Fillonsa yasake rungume wa yace"kome kike so kifadamin"

Cikin shagwa6a tace"ni kainakeso"

Cikin jin dadi yace"sai Kuma me?"

Cikin jin nauyi tace" Sai waya idan Allah ya hore "

Murmushi yasaki yace"waya kike so?"

Cikin sauri Tace"eh"

Yace"kibari idan muka tafi Dubai honeymoon saiki za6i wadda kike so"

Ahankali tace"to"

Yace"todan sake min kiss din sainayi bacci kinji?"

Wani irin kukan shagwa6a tasaka masa, Wanda ita kanta batasan ta'iya shi ba,Adede lokacin Ramadan yadawo Dakin, ganin hakan Shima yasa yayi murmushi cikin sauri yace"to shikkenan,naji... Na haqura,Kidena min kuka, mayi magana gobe,please kiyi addu'ah"

Ahankali tace"to"tareda Lumshe idonta, kiss yasakar mata ta cikin wayar me ratsa jiki, sannan yakashe wayar.

Ahankali ta ajiye wayar itama, tafara shafa addu'ah ajikinta, Hajja tasaki ajiyar zuciya tace"ummm qarshan duniya yazo, irin wannan sumba azahiri qiri-qiri munaji muna Gani fisabilillahi kamar ba 'ya'yan hausawa ba?mesunan qawa kina masa irin wannan shagwa6ar ba waya ba ko duniya kikace kinaso ai dole yabaki"(=ØFÞ<Øûß
@&þ=ØHÞ=Ø3Þ=Ø2Þ>Ø-Ý)

Lokaci daya Aisha ta runtse idonta,=ØÞ shikkenan Kuma Hajja taji komai(>Ø&Ý<Øûß
@&þ)








Please kuyi haquri da wannan ba yawa, mu hadu zuwa yammah insha Allah=ØOÞ


Shahaab littafin kudi ne, ki biya naira 300 kacal ki karanta halak dinki, muddin kika karanta baki biyaba wallahi tallahi nabarki da MAHALICCINKI ban yafeba=ØEÞ=ØÜ


0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034






Mrs Usman
'<Øûß





Page 40




"wannan d'a na Aysha da jaraba yake,yazo Nan yasaki agaba da naci ko Ina yabar matar tasa?"

Shiru Aisha tayi takasa bata amsa

Taci gaba da cewa "ai kina Jina Sarai,kishirya gobe dutse zamu tafi,akwai wajan wadda zan kaiki 'yar'uwar jummai ce, munyi waya tace nakai ki gobe, bansaniba inaga 'Dan gyare gyare zatasa a miki"

Sai a lokacin tace"Allah yakaimu"

Sannan ta ajiye wayar agefen fillo tashafa addu'ah tareda juyawa ta kwanta.

Saide baccin kwata kwata yaqi zuwa, tunanin sa ne yadawo mata Sabo fill,tanajin yanda yanayin ta yake sauya wa zuwa sha'awa, lokaci daya dukiyar fulaninta suka fara yimata qaiqayi, haka tayi haquri har batasan lokacin da bacci ya dauketa ba.


******

Shima a nasa 6angaren Lumshe Idonsa yayi, ya tabbatar cewa inda tana kusa dashi, babu abinda zai Hana ya kaiwa boobs dinta hannu, ya matsu sosai, halin da yake ciki yayi masa zafi dayawa, yadaiji lokacin da Ramadan ya dauro alwala yazo yacire kayan jikinsa ya kwanta, Amma shi Kansa baisan inda Hankalinsa yatafi ba, yana rungume da fillo kawai juya Kansa yake ahankali, Ramadan ya juya ya kalleshi duk da cikin duhu suke saida yaga halinda yake ciki, tausayi yabashi, yadaisan ba ciwon kan da yakeyi ne yasa shi haka ba, saboda ciwon Kai ba zaisa mutum ya rungume fillo haka cikin yanayi ba, ajiyar zuciya yasauke yace"kayi haquri mana, ai ankusa, Kuma....bata Nan, dasai kaje kaganta may be kasamu relief"

Ahankali yace"gara da batanan ai,Gara da Bana ganinta,because komai ma zai iya faruwa idan Ina ganinta"
Ramadan ya Girgiza Kansa yace"kuma da hakan ma,kadinga azumi kafin lokacin, zaka Dan samu sauqi ko Yaya ne"

Cikin sauri yadaga masa Kai batare da yace komai ba, daqyar bacci yayi nasarar dauke shi.
Asubar fari yatashi yashige wanka kasancewar yayi mafarkin ta tana masa tausa,Sanadin haka yaji shi jalaf... Dole saida yayi wanka sannan yatada kabbarar sallah, saida ya idar yafara lazimi sannan yaji za'a shiga sallar asuba, Ramadan ya tasa, Shima ya'iyo alwala sannan suka wuce masallaci, basu dawo gida ba saida gari yayi haske, suna zuwa Ramadan yahada masa tea Mai kauri yasha tareda magungunan sa, sannan suka kwanta, sosai Shahaab yayi bacci yanda ya kamata kasancewar bai samu yayi baccin ba da daddare, Sai wajan Sha daya da kwata na safe yatashi, Alokacin har Ramadan yayi wanka ya shirya yana kwance yana kallo, Shima tashi yayi yashige toilet yayi wanka, sannan yafuto ya shirya, sosai yaji shi garau kamar bashine jiya baida lafiya ba, ko kadan bayajin ciwon komai yanzu, Kai tsaye part din mama suka wuce, tana zaune afalo tana ganinsu tatashi tanufeshi, hannayenta ta miqa ta riqe fuskarsa tana fadin"yaya jikin Naka?tun dazu nake zuwa Naga Kuna bacci Baku tashi ba"

Murmushi yayi yariqe hannayenta data kama fuskarsa dashi yace"naji sauqi mama, Ramadan yabani magani Nasha, banajin ciwon komai yanzu"

Cikin jin dadi tace"Alhamdulillah"

Tajuya ta kalli Ramadan dayake kallon su yana murmushi, har yanzu yarasa gane waye yafi son wani acikinsu?
Mama Tace"Ramadan muje kuci abinci"

Bayanta sukabi, Kai tsaye suka wuce dinning, saida suka gama cin abinci suka danyi firar duniya, sannan Ramadan yawuce gida, Shikuwa Shahaab Kansa yad'ora kan cinyar mama, duk masu aikin dasuke zuwa wajan ta idan suka ganshi mamaki suke, Babban mutum kamar shi Amma har gobe kamar yaro yake awajan mahaifiyarsa, ganin masu yimata sallamar ba qarewa zasuyi ba yasa yatashi yashige dakinta yaci gaba da kallon acan.


(banyafewa Wanda ya karanta batareda ya biyaba)


******

Tafe suke da Hajja hannun Aisha d'aukeda kayanta, duk inda suka wuce Sai an gaishe da Hajja, tagaban shagon inusa suka wuce yataso da sauri suka gaisa da Hajja, Sai kallon Aisha yake qasa-qasa, yaso ace ita kadai ce dasun 'Dan zanta, suna wucewa Hajja tace "mesunan qawa mubi titi kawai,zaifi sauri"

Aisha tace"haba Hajja, aqasa ma Ana miki irin wannan gaisuwar idan muka hau titi Kuma ai sai ta Allah"

Hajja tace"ai nafiso inganni atitin Ana Hajja A'i, Ina d'aga hannu Inacewa na'am"

Dariya Aisha tayi tace"Saikace wata 'yar siyasa?wallahi bazamubi titi ba"

Haka suka dinga tafiya ta lungu da saqo har suka qarasa inda zasuhau mota, basu dade da zuwaba suka samu mota suka wuce dutse, Bayan sunje gidan sun huta Hajja tayi haramar dawowa gida, inda taqara yiwa Aisha fada akan magungunan ta na Sanyi ta dinga Sha kullum kartayi wasa dashi, matar mesuna Anty Mariya itace taraka Hajja, sannan tadawo gidan, sosai takejan Aisha da zance harta saki jikinta suke dan firarsu, washe gari tafara yimata gyaran jiki safe da Kuma yammah.

******

Yau Kam da shirin office yatashi, har mamaki yabawa mama yanda yake kokarin kula da aikinsa, inda wanine wannan rashin lafiyar tasa saiya dauka mata hutu awajan aiki, ko abinci baici ba saboda azumi daya dauka,yana kokarin shiga mota aka fara ruwan sama kamar da bakin kwarya, haka yashige suka wuce saide babu damar gudu, awajan aikin ma sunyi mamakin ganinsa duba da yanda Ramadan yake fada musu cewa bayajin dadi kwana biyu, sosai yayi aiki ranar,su kansu ma'aikatan sunsan Mahmud Wakili yadawo aiki, saboda yanda yasa aka riqe mutane basu tafi gida akan lokaci ba, Amma duk da hakan sun riga shi tafiya gida, shi bai tashi ba Sai yamma lis, koda wasa baiyi gigin Kiran Aisha ba, yasan cewa yana jin muryarta zai shagala ya manta da komai, Kuma ga azumi dayake, shiyasa ya tsaya tsayin daka wajan ganin yayi aikin yanda ya kamata, hakan ne yasa Hankalinsa yakoma kan aikin, Bayan yadawo gida wanka kawai yayi, ya shirya cikin qananun Kaya, wandon Jeans dakuma qaramar Riga wadda tayi masa mutuqar kyau,lokaci daya ya rikide yakoma tamkar saurayi Dan shekara talatin da uku, yasa hannu yad'auki system dinsa yayi wajan mama,zama tayi akusa dashi ta ajiye masa takardun companyn daya Bawa Aisha tace"Shahaab kayan Nan sunyi Maka kyau sosai kodan basaka qananun kayan kakeba?kullum daga suit Sai suit, manyan kayan ma basakasu kake ba"


Murmushi yayi baice mata komai ba, itama tasan ba lalle ne Dama ya tanka ba, danhaka tace"ga wannan takardun, ka ajiye mata awajanka, idan tazo saika bata"

Hankalinsa yana kan computer yayi murmushi yace"to mama"

Tace"bakaci abinci bafa, gashi ankusa Kiran sallar magrib, kaje office kawuni kana aiki, yanzu kadawo gida maimakon kahuta Kuma ka dora dawani aikin"

Tsayawa yayi da abinda yake yace"azumi nake yi,saide ahadamin tea idan nadawo daga masallaci Kuma zanci farfesun kaza medan yaji"

Cikin sauri tace"to" sannan ta wuce kitchen, Dakanta tahado masa tea din, sannan tasa me aiki tayi masa farfesun kaza, a gabansa ta ajiye masa tea din Sai turiri yake, saida ya jira aka kira sallah sannan yasha tea din, yawuce masallaci, baidawo ba saida yayi sallar ishsha'i, mama ce Dakanta tafara bashi farfesun, ta kalli yanda yake neman cinyewa, cikin jin dadi tace"kaida bakason yaji meyasa yau kakeci?"

Yace"mama banajin testing abakina, shiyasa"

Tace"may be saboda rashin lafiyar kane,wacce qasa zamu tafi ne nida Hajiya Zaliha, saboda hado kayan lefen takwara?"

Kafadunsa yadaga yace"duk inda ya muku mama, na tambayeta tace na Nan qasar takeso"

Mama Tace"A a, bazai iyuba, saide asiyo komai acan abunda babu Kuma Sai Asiya anan din"

Yace"toshikkenan Allah yakaiku lafiya"

Kafin tayi magana momy tayi sallama cikin falon itada munirat, lokaci daya Shahaab yature hannun mama datake bashi farfesu, fuskarsa ta sauya,yanda kasan bai ta6a yin dariya ba haka yakoma, yad'ora kafa daya Kan daya, yad'auki computer sa yaci gaba da aikin dayake, ganinta ne yasa gaba daya yaji komai yafita daga ransa

Mama ta Kalle su Bayan sun qaraso tace"sannunku da zuwa"

Momy tace"yauwa Hajiya Aisha, Ina wuninmu?"

Cikin sakin fuska mama tace"lafiya kalau Alhamdulillahi" ta kalli munirat da kanta ke qasa tace"munirat?"

Cikin sauri tace"ina wuni mama"

Mama tace"lafiya kalau munirat, Kuma yanzu munirat dankun samu Sa6ani keda mutumin naki saiki tafi gida maimakon kizo ki sanar Dani?"

Munirat ta daga Kai ta kalli Shahaab, taga Hankalinsa yana kan computer ko kallon inda suke baiyi ba,Sai taga yaqara yin wani kyau yakoma kamar bashi ba, yanda ya daure fuska kad'ai yasa taji wani irin kwarjinin sa yashige ta, cikin sauri tayi qasa da kanta

Momy kuwa baqin ciki ne ya kamata, banda munirat tana son Yaron Nan babu abinda zaisa tazo gidannan, idan dukiyar ce ai sun samu abinda suka samu a qarqashin sa, yanzu saboda Allah a matsayin ta na mahaifiyar munirat yadaga Kai ya kalleta ma ya gagara, bare tayi tunanin samun gaisuwa,ajiyar zuciya tayi tace"Hajiya Aisha ayi hakuri Dan Allah,kinsan halin 'Dan yau, ka haife shi baka haifi halinsa ba,ni nafi tunanin anshiga tsakanin Mahmoud da munirat ne, banda haka yanda yarannan suke son junansu yaushe har Mahmud zai iya sakin munirat,tunda yafara neman aure de kema kinsan iyayen yarinyar bazasu zauna ba, dole zasu shiga su fita domin araba Mahmud da matarsa,abinda yaji tana waya akai Kuma asalin abun ma badake take ba, da wata mata take,tana so tad'auki nauyin wani film na ita matar, saboda haka ga yarinya Nan nadawo da'ita, yayi hakuri ya maida ta dakinta tunda akwai sauran igiya guda daya"

Mama ta kalli momy tace"Wato Hajiya zan'iya daukar komai akan baqar magana Amma banda cin zarafin qawata, wannan yarinyar da Shahaab yake nema jikar qawata ce danayi shekara da shekaru Ina nemanta, kinga kuwa ni nake da alaqa da Aisha,nasan halin qawata, batasan ma akwai malaman tsubbu a duniya ba bare taje tasa araba Mahmud da munirat, koba wannan Bama bai kamata kice Wai anshiga anfita tsakanin sa da munirat ba,wannan kamar daukan haqqi ne tunda ba Gani kikai da idonki ba"

Munirat ta kalli mama cikin sauri, dama Aisha jikar qawar mama ce? Qawarta datake 6ata ran Shahaab saboda ita,? qawarta datake sa ta ajiye soyaiyar datakeyi wa Shahaab tayi masa cin mutunci saboda yaqi Nemo mata ita? Inhakane Kam dole ran mama ya6aci, tunda akan wannan qawar Tata harta iya 6ata ran danta na cikinta, to kuwa babu ran Wanda bazata 6ataba, cikin 6acin rai momy tace"to Hajiya Aisha menene laifi danna fadi haka?ranar wanka ba'a 6oyon cibi, yakamata ki fadi abinda yake ranki Kai tsaye, Nima na fadi nawa inyaso asan inda za'a Nemo maslaha, Munirat fa ta fadamin komai, tacemin tun farko kece kika daure masa gindi yanemi yarinyar,ni Ina ganin dama can kin Riga kinsan jikar qawar kice, shiyasa qarfi da yaji saida kikasan yanda kikai kika cusa masa ra'ayin yarinyar, Kuma wannan de ba soyaiya yake mata ba, sha'awar ta yake, banda haka Yaya za'ayi ace daga ta6a nonon yarinya shikkenan saiya dage saiya aure ta,? soyaiya guda daya ce, Kuma ita Mahmud yakewa munirat sannan...."

Bata qarasa maganar datake ba Shahaab yayi jifa da computer sa dake kan cinyarsa, cikin 6acin rai ya kalli momy sannan yafara kokarin tashi tsaye, cikin sauri mama tasa hannu ta riqe shi, tajashi yakoma kan kujera ya zauna, munirat kuwa hawaye tafara ganin yanda momynta ta lalata komai, cikin sauri itama ta riqe hannun momynta.

Cikin 6acin rai momy ta kalli Shahaab dayake huci tace"fitsararre dukana zakayi ne?idan ma bazaka maida ta dakinta bane menene abun tasowa haka kamar hayaqi zaka iyo kanmu? sanin kanka ne munirat haqurin zama take dakai, meza'ai da namiji juya, marar haihuwa?a wannan lokacin shekara biyar tayi yawa zaku rabu saboda rashin haihuwar ka, Amma haka ta zauna dakai shekara da shekaru duk da tasan baka haihuwa, Amma ita kowa yasan gadon haihuwa tayi,ai rufa Maka asiri take, kaje ka auri yarinyar kagani idan zata Iya zama dakai Ahaka baka haihuwa"

Hannunsa ya dunqule waje guda,yarasa meyasa mama ta riqe shi, yaso ta rabu dashi da tuni labari yasha bam-bam,wayar sa yadauka yayi danne-danne sannan yayi jifa da wayar.
mama ta runtse idonta cikeda dacin zuciya sannan ta kalli momy tace"kingama?"

Munirat ta Fashe da Kuka tace"momy kin 6atamin komai, inason Mahmud momy Amma kinzo kin rusamin farinciki na,mama Dan Allah kiyi hakuri sharrin shaidan ne, Dan Allah mama ki hanashi auren Aisha, wallahi nayi alqawarin zan gyara komai, zanyi masa duk abinda yakeso, Amma Dan Allah mama karki barshi ya auri Aisha, wallahi banason ganin da Aisha, saboda Ina ganin tane a matsayin wadda tashigo cikin rayuwar mu tayi mana katangar qarfe nida Mahmud"

Mama ta Girgiza kanta ta kalli momy tace"idan kun gama zaku iya tafiya,Mahmud de d'anane, to bazai maida munirat ba tunda babu dole, Kuma kusa aranku INSHA ALLAHU Sai kunga 'ya'yan Mahmud da idanunku"

Kafin momy tasake magana sojoji guda biyu suka shigo bisa umarni Mahmud, kallansu momy sukai daya daga cikin su Yace"Hajiya please go out"

Cikin sauri momy ta Kalle su, sannan ta kalli Mahmud, Shikuwa Mahmud baice komai ba, dayan sojan yakai hannu yana kokarin ta6a momy yana fadin "idan bazaku fitaba zamu iya fita daku"

Cikin sauri munirat tafice tana share hawaye, momy ma tabi bayanta tana d'ura ashar.

Saida yaga fitarsu sannan yahade hannayensa waje daya, yad'ora goshinsa akan hannun nasa daya hade, mama tasaki ajiyar zuciya ta kalleshi tace"wannan dalilin ne yasa naso tun farko ka qara aure matarka ta haihu akan idon munirat Sai tasan cewa lafiyarka kalau itace juya, to soyaiya ta rufe Maka ido kakasa gane Ina na dosa, banda rashin mutunci kije ki fadawa mahaifiyar ki qarya da gaskiya sannan kizo Nan kinamin kuka inyi haquri?, inda ace Aisha ta bayyana da wuri wallahi da ko zaka mutu ita zaka fara aura,nasan cewa nida Aysha mun wuce qawaye saide yan'uwa, danhaka koda jikar ta tayi Maka Gorin haihuwa kanta tayiwa tunda kun Riga kun zama daya"

Jin yayi shiru ne yasa takai hannu tata6ashi, yana d'ago Kansa taga hawaye yana zuba A'idonsa,(=ØFÞ<Øûß
@&þ)
cikin sauri tace"subhanallah...."

Sannan tamatsa kusa dashi tajashi jikinta tana bubbuga bayansa alamar lallashi, Sai Alokacin yasaki wani irin kuka mecin rai, sosai yake kuka harda shashsheka,cikin sigar lallashi mama tace"menene abun kukan Kuma?"

Cikin kuka yace"mama da gaske ni juya ne Bana haihuwa ko?da gaske itama Aisha zata gujeni saboda rashin haihuwa ta?zatace narabu da'ita ko mama?" ya qarasa maganar cikin hawaye

Cikin sauri tajashi jikinta ta rungume shi sosai, saboda gaba daya ya karya mata zuciya, batasan lokacin dataji qwalla tacika mata idonta ba, cikin sauri tasa hannu ta goge, sannan cikin lallashi tace"mahmuuuud" taja sunan nasa, sannan taci gaba da cewa "waye yace Maka baka haihuwa?ni lafiyar Dana kalau,kana haihuwa, idan ka auri Aisha zata Haifa Maka Yara dozin-dozin,insha Allah kunayin aure Aisha zatasamu ciki, shiyasa nake baka maganin Sanyi ai, akwai sanyin dayake Hana mutum haihuwa, idan ma kanada shi maganin zai taimaka Maka wajan warkewa Sai kaga andace,kayi hakuri kadena kuka kaji?"
Tafadi hakan cikin lallashi

Cikin sauri ya Girgiza mata Kai sannan yazare jikinsa daga Nata yace"to mama kibani maganin zansha ,jiya ma baki Bani ba"

Murmushi tayi tatashi tad'auke masa computer tarufe ta, sannan ta wuce kitchen tafara hada masa maganin tana dariya, yau Gori yasa Shahaab dakansa yana neman magani, Amma ranar data bashi har wani yamutsa fuska yake shi ala dole bayason shan maganin, abinda bata saniba shine wannan maganin na qarfin maza data bashi shine yasa yake yatsina fuska, saboda shi yasan cewa yanzu hakama da qarfin sa=ØJÞ=ØHÞ
asalima tun munirat tana d'akin ta idan yayi kwana biyu zuwa uku bai nemeta ba Tofa suna haduwa babu sauqi, akan irin haka har taimakon Dr. yanema, to Amma Kuma ita mama bata Sani ba, gashi Sai sake d'ura masa maganin take, tana sake tunzurashi(=ØHÞ)

Maganin takawo masa na sanyin,babu musu yadauka ya shanye, cup din ta dauke sannan takai kitchen Sai gata ta dawo da tsumi, shima bashi tayi, saida yayi kamar zaiyi kuka sannan ya Kar6a Badon yaso ba, yashanye, mamaki yakama mama, hakan yana nufin maganin tsumin datake bashi shine bayaso, to meyasa bayaso? Wata zuciyar tace Gara de yasha koma lafiyarsa kalau, yanzu yanzu aka gama yimusu Gorin haihuwa, Gara ta tsumashi dakyau yanda zai dinga aiki babu kama hannun yaro, duk da tasan cewa yawan yin wannan abun bashine yake kawo cikin ba.


(banyafewa wadda ta karanta min littafi na free ba)


******


Da daddare yana kwance a falon dake part dinsa, kallo yake yana Dan daddana waya, yayinda yad'auki fillon kujera yad'ora akan cikin sa, kiran wayar Hajja yayi,Bayan sun gaisa yace"maamah bata kusane?"

Hajja tace"Aisha nasani ba maa-mah ba, shegen iyayi da kwainane ku ala dole Yan zamani bazaku kira sunayen ku ba,ina uwar taka? Bata wayar zanyi magana da'ita"(=ØÞ)

Kwanciyar sa ya gyara yace"kikira layinta mana, ni banida Kati bazaku cinye min sauran na cikin ba,magana nakeson yi da maamah"

Hajja tace"to Bari kaji inzaka ce Aisha ma kafada,bata Nan tatafi dutse, bansan Kuma ranar da zata dawo ba,inta dawo ma bazan bata wayar ba saboda damuna kuke Kuna hanani bacci"

Cikin sauri yace"tatafi dutse?Kuma kika Barta tatafi bata kirani ta tambayeni ba?"

Cikin sauri itama tace"andaura auren ne?Shahaab kafita daga idona in rufe, inbansa andaga auren Nan ba kace niba Hajja A'i bace"

Cikin sauri yace"shikkenan, ni Allah yabaki haquri saida safe"

Cikin sauri yakashe wayar, yasan Sarai zata Iya aikata wa, Gara yakashe wayar yabarta da hatsaniyar ta.

Haka kawai yaji ransa ya6aci, mezatai a dutse? Yanzu haka tana can kowa yana kallon ta, haka yadinga tsaki shi kadai kallonma kashe wa yayi, yasake Kiran waya yayi oder kayan furnitures komai da komai Wanda za'a zubawa Aisha, harda na part din mama gaba daya, dakuma nasa Dakin, sannan yatashi yaje ya kwanta.

(littafin kudi ne, ban yafeba idan kika karanta shi free)
******

Cikin kwanakin da basu wuce ashirin ba,Idan Kaga Aisha dole kasake kallon ta,Tasha gyaran jiki yanda ya kamata, magungunan mata kuwa Anty Mariya ce take hada mata su masu kyau tana bata ciki harda na qarin breast, Nan da Nan kuwa suka sake cika suka tsaya qyam, tayi haske tayi kyau sosai, kamar ba'itaba, gyara kawai ake mata saikuma nau'in girke girke datake sake Koya mata, tsawon wannan lokacin bata kira Shahaab ba, Shima daya gaji da tambayar Hajja yanda za'ayi ya sameta yaga de batada niyar hadashi da'ita, saiya denakira, yau kwana biyu kenan da kawo lefenta akwatunan ta goma Sha biyu, yanaso yakira yaji ko kayan sunyi mata kyau Amma Kuma babu yanda za'ayi ya sameta awaya, tareda Anty Mariya suka taho gida, Alokacin biki yarage saura kwana uku, Ummanta Sai kallon ta take tana ganin yanda taqara yin kyau sosai,dogon gashin Nan Nata yasha gyara Sai qyalli yake, Hajja kuwa kasa rufe baki tayi Sai Fara'ah take,tana qara yiwa Anty Mariya godia, daga Nan Hajja tajata suka shige daki zata nuna mata kayan lefe, itama Aishan Dakin Ummanta tatafi Dan tabar Hajja da Anty Mariya Sud'an gaggaisa, batayi tunanin har ankawo lefen ba, Ummah tabiyo ta daki tace"kin kira Mahmud kuwa tunda kika tafi?"

Cikin sauri tace"Ummah bamuyi waya ba, itace ta hanani kiransa tace nabari yafara haduwa Dani tukunna zaifi doki na"

Murmushi Ummah tayi tace"ai komai yazo qarshe, kikira shi idan kin huta, Dan kullum saiya kira wayar Hajja Ina jinsu suna fada"

Murmushi tayi tace"to Ummah"

Wani magani ta Dauko tabata tace"kitashi kije bayangida kiyi tsugunno da wannan, kibari yashiga jikinki sosai"

Tace"to Ummah"

Sai dare tashiga Dakin Hajja anan taci Karo da akwatuna, saitayi turus ta tsaya daga bakin kofar, Hajja ta kalleta tace"kayan lefen ki ne,shekaran jiya aka kawo su"

Shigowa tayi ta zauna batare data budeba tace"sunyi kyau sosai"

Hajja tafara budesu tace" keda baki dubaba? Bari ki gansu, harda sarqar gold aciki kusan Kala uku, saina dauke miki su na 6oye saboda Yan kallon Kaya kar a dauke a nemeta arasa, Dan kullum Sai mutane sunzo ganin Kaya, Amma ni me sunan qawa banga rigar nono ko daya acikin kayan naki ba"(=ØHÞ)

Bakinta tata6e tace"shikkenan kawai,inajin anmanta, Hajja kibani waya nakirashi,"

Hajja tace"um kirashi Kam, yanda yake bugomin safe, rana, dare, Gara ki kirashi Nima nahuta" ta qarasa maganar tana bata wayar, sannan tafice tabar mata d'akin

Yana ganin Kiran yayi rejecting, yakira, tana dauka da yaji muryarta ce yasaki wata irin ajiyar zuciya a6oye,cikin nutsuwa tace"ina wuni"

"lafiya" yabata amsa a taqaice, tanajin haka tasan cewa fishi yake, murmushi tayi tace"fishi?"

"uhm" shine kawai abinda yace
Kwanciya tayi a gadon tazare wayar daga kunnan ta, ta dora bakinta akai tasakar masa kiss guda uku, Sannan ta maida wayar kan kunnan tace"Daya agoshi, daya akumatu, daya akan lips dinka"

Murmushi yasaki yace"keko....,kinma raina min Hankali, ni zakiyi wa wayo? Kikama hanya kitafi wani gari, keda kike da hidima a gabanki, me zakije kiyi awani gari har kusan sati uku? Kuma koki kirani, inma mutuwa zanyi inmutu ke babu ruwanki"

Cikin sauri Tace"A a, bazaka mutu ba,insha Allah kana Nan araye tare Dani, saina Haifa Maka 'yanbiyu ka gansu kayi rayuwa tare dasu"

Wannan kalmar ta haihuwa daga fada masa, itace tasa yamanta da laifin data masa, yasaki ransa, cikin sauri yace"da gaske Zaki haifamin Yara maamah?"

Fari tayi da idonta tace"insha Allah"

Ajiyar zuciya yasauke yace"ina sonki sosai, kinga kayan naki komai yayi?"

Tace"nagani sunyi kyau sosai, kayi kokari, Allah yaqara budi, Allah yasa gaba kafi haka, sunyi kyau, Kuma sun birgeni, Amma Wanda yasiyo kayan yafimin kyau fiyeda kayan...."

Cikin jin dadi yace"da gaske?"

Tayi qasa da murya tace"sosai"

Murmushi yayi yace"zakiga babu bra aciki, saida mama ta tambayeni menene size dinki nace bakya gida, Bama waya, idan kinzo Garin Sai muje ki siyo Wanda tamiki, nikuma nafada mata haka ne kawai danta rabu Dani,da niyya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On SHAHAAB
avatar
fateema

7 months ago

Reply

Allah yakara basira

avatar
taskar

7 months ago

Reply

Replying to fateema

Ameen

avatar
ummu-swabir

2 months ago

Reply

Thanks

Please Login or Register in order to submit comment